Mijin Novel

Dai dai lokacin qarfe biyu saura na rana ne,tana zaune cikin madaidaicin falon nata wanda ya wadatu da tsafta,gefe guda kayan yaranta ne data debosu daga kan igiya bayan sun bushe tana ninkesu daya bayan daya tana tarawa a gefanta,gefe daya na zuciyarta cunkushe suke da tunani kala daban daban da taketa qoqarin kauda su.
Idanunta tadaga sanda taji an yaye labulen,maman ummi ce ke shigowa hannunta dauke da qaramar yarinyarta da take goyo,idanu mmn amir(mamallakiyar dakin) tabita dasu tana karantarta,lokaci guda duka ta zabge ta rame tayi firgai firgai,haka taci gaba da kallonta harta samu kan daya daga cikin kujerun tazauna sannan ta aje ummi,wadda tana ajeta ta rarrafa tayi wajen mmn amir,yarinyar na qarasowa ta dauketa tana juyata gami dayi mata wasa yarinyar tasoma dariya
“Yanzu maman amir kina ganin zamanmu a haka yayi dai dai kenan?,munaji muna gani haka baban amir zai sake kawo mana wata cikinmu?,muna zamanmu muda yaranmu cikin kwanciyar hankali zai debo mana matsala?” Ta qarashe maganar wanda kana jin sautin muryarta kasan cewa ba qaramin tashin hankalo bane cikin zuciyarta,daga kai mmn amir tayi daga wasan da takewa ummi ta dubi mmn ummin,ba shakka kishi abune mai ciwo dacin zukata,kuma ita kanta zuciyarta kullu yaumin ba cikin dadi take ba duk da cewa ba wannan ne farau a kanta ba,amma ita kishiya kullum sabuwace a wajen mutum,saidai wannan ba komai bane idan aka kwatanta da sanda xa’a auro mata mmn ummin,banda Allah yasanya ta hadu da iyaye nagari,takuma yi yaqi da zuciyarta da wataqila yanzun hakan ba wannan zancan ake ba,cikin kwantar da murya tace
“To yazamuyi mmn ummi?,baban amir dai bamu muka haifeshi ba bare muce zamu hanashi abinda yayi niyya” kai take kadawa da sauri
“Zamu iya hanashi mmn amir indai zamu hada kai mu duka biyun muyi masa bore kamar yadda nakeyi yanzun,yanxunma abinda yasa haqata ta kasa cimma gaci saboda ni kadai naketa qoqarina kinqi kisa min hannu” qaramin murmushi ya subuce daga fuskar mmn amir tana duban mmn ummin,ta tuna wasu shekaru baya da suka shude,lallai wanzami baison jarfa
“Mmn ummi,abinda nakeso ki gane shine,dukkanmu qarqashin bbn amir muke nida ke gaba daya,duk wani abu da zamuyi don mu tashi hankali komu hanashi aure bamu da riba don Allah ne ya halasta masa,bugu da qari da haka nayi a baya da wala’alla nima bana bigiren da nake kai a yanzu,abinda dai na gayamikin shi zanci gaba da gaya miki,kiyita haquri ki kauda kai,komai yayi farko yana da qarshe,kuma babu wani abu dawwamamme sai ikon Allah,watarana sai labari,hakanan me haquri shike da riba” miqewa mmn ummi tayi cikin fushi da rashin gamsuwa,baki tadan tabe
“Munaji muna gani mmn amir wlh zamu zama ‘yan kallo idan bamuyi da gaske ba,ke kuwa kinsan yadda yarinyarnan ta mallake baban amir?,hala bai taba waya da ita a gabanki bane saini daya raina?” Murmushi ta sake saki
“Ba rainakin da yayi,face ke da kokaqi tsayawa ki fahinci komai⦔
“Mmn amir” mmn ummi tayi saurin dakatar da ita
“Wallahi wallahi yarinyar ban labarinta kaf yazomin kunnena,duk cika da batsewar unguwarsu babu tantiriyar yarinya mara kunya irinta,inata boye miki ina miki hannunka mai sanda amma na fuskanci baki gane ba,yana daya daga cikin abinda yasa hankalina yasake tashi kenan,bin malamai take kamar tashin hankali,ki fuskanta mmn amir muyiwa kanmu gata tun batazo ta fiddamu daga cikin yaranmu ba” tsai tayi tana duban yadda mmn ummi ta sake firgicewa,sai data gama sannan tace
“Zauna don Allah mmn ummi muyi magana ta qarshe dake” kaman bazata zauna ba,amma dole tazauna din don neman hadin kai da mafita take,sai data tattara dukka hankalinta akanta sannan tace
“Kin yarda da Allah mmn ummi?” Kaita gyada tana dubanta