Hausa Novels

Khaleesah 1

Khaleesah
1;

Related Articles


Gudu take tana waige waige kmr xata tashi sama da ganinta kasan tana cikin tashin hankali, daga ita sae riga da skirt ko dankwali bbu kanta bare takalmi, kuka kawae take tana kiran Allah a

xuciyarta, da ta juya kuma sae taga suna biye da ita suma kmr xa su tashi sama, don ma ta iya gudun da tuni sun kamata, ganin hanyar da take kai hanyace mai tsayin gske yasa ta sha wani corner da ta ga, tana shan kwanar kuwa taga wasu mutane su kusan biyar duk suna sanye da suit kusa da wani kantamemen gate suna magana, ta karasa gun su ta xube gabansu tana mayar da

numfashi da kyar a tsorace ta fara magana “don Allah don Annabi ku taimake ni kashe ni xa su yi wllhh,” gaba daya suka tsaya kallonta da mamaki, ta fashe da matsanancin kuka ganin sun yi shiru cikin tashin hankali tace “don Allah fa nace maku,” kurar da suka hango da kuma takun mutane yasa wani daga cikinsu ya fixgota ya jefar bayan flowers din dake shuke a inda suke, har

mutanen suka sha kwana suka karaso inda suke a guje kmr xasu tashi sama, wani kato daga cikinsu mai murya kmr ta trumpet yana xaro ido yace “kun ga wata yarinya ta bi ta nn,” gaba dayansu suka tsaya kmr wasu sha sha shai aka rasa mae ce ma gardawan komai, cikin tsawa daya daga cikinsu yace “ba magana ake maku ba kun tsaya kmr wasu Zombies,” wanda ya jefata cikin flower ne ya juya ya bi can kasan layi da kallo alamar can tayi, katon yace “can ta bi,” ya gyada masa kai suka kwasa a guje gaba dayansu suna tada kura da manyan booths din dake kafafunsu, gaba daya abokan suka sauke ajiyar xuciya, ya karasa kusa da flowern da sauri yana lekata ya nuna mata gate yace “tashi ki shiga gate din can,” da

sauri ta tashi ta shiga gate din da ya nuna mata, daya daga cikinsu yace “look guyz mu bar nn, its nt safe in here,” kan su kai ga basa amsa wasu daga cikin gardawan mutanen suka dawo a fusace suka yo kansu kuma, cikin tsawa wani guntun cikinsu yace “kun tabbata can yarinyar nn ta bi,” wnn karan ma wanda ya jefata cikin flower ne ya basu amsa yace “eh can ta bi baku ganta bane?” wani ya galla masa mugun harara a fusace yace “kai kadae ne mai magana a nn? Su sauran kurame ne” da sauri gaba dayansu kmr sun hada baki

suka ce “can ta bi yallabae” hkn yasa suka juya suka sake bin inda aka nuna masu, lkci daya suka sake sauke ajiyar xuciya daya daga cikinsu yace “kun ga tafiyata, ba dani xa ayi wnn ba,” yana fadin hka yyi hanyar motarsa ya shige yyi gaba. Wanda ya nuna mata gate ya shiga cikin gate din sauran ukun na biye da shi a baya suka kullo gate din, tana durkushe karkashin wata bishiya ta hade kanta da

gwiwa tana kuka a hankali, ya karaso inda take ya tsaya dan nesa da ita yace “xuwa anjima sae ki samu ki fita……

” ta mike tsaye da sauri tana girgixa masa kai a rude tana hawaye tace “don Allah don annabi ku taimaka min kar ku bar ni a nn wllh kashe ni xasuyi,” ya yo waje da ido yana kallonta yace “me xa muyi maki kuma?” daya daga abokansa yace “kai dalla ka taho mu bar nn uban me kuma xa muyi mata da ya wuce wnn,” xae yi magana wani daga cikinsu yyi masa alamar ya xo da hannu, ya karasa gun abokan nasa gaba daya suka hadu waje

daya, bayan kmr minti biyar ya dawo inda take yana kallonta ya ciro bundle din kudi ya mika mata yace “ki je duk inda xa ki da baxa a kashe ki ba,” ta girgixa kai tana kuka ssae tace “to ni ban san inda xa ni ba ku taimakeni don Allah,” ya daka mata tsawa yace “wani taimakon kuma xamu yi maki da ya

wuce wnn kina da hankali kuwa,” kan tace komai ya ajiye mata kudin gefenta yace “xan ma mai gadi magana xae jira har ki fita kafin ya rufe gate, Allah ya tsare,” yana kai wa nn ya juya da sauri yyi gun abokansa suka karasa gun mai gadi suka masa magana snn suka fice daga gate din. By #Mrs Haiydar.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button