Hausa Novels

Kawar yata ce hausa novel

 *KAWAR* *'YATA* *CE* 

®�
GASKIYA WRITERS ASSOCIATION�
{ Gaskiya É—aya ce daga Æ™inta sai É“ata, burinmu mu faÉ—akar da al’umma domin ribantar duniya da kuma lahira. }

Related Articles
     🎐 ```G•W•A```🎐

GASKIYA DOKIN ƘARFE•🏇🏼

Story & written
By
Sumayya A Shehu

            Page 1 

Kwance take saman wani makekin gado mai Kyau tana rerah kuka mai ban tausayi kamar ranta zai fita…

Takun da taji ne kamar za’a shigo wajan ta yasa ta k’ara karfin kukan da takeyi a hankali ya bud’e kofan ya shigo…

Ya kifeta da ido yana kallon ta a zuciyar shi na zafi saboda kuksn nata Jin shi yake kamar ana soka mai mashi a zuciya…

A hankali ya tako zuwa gare ta Yana hawa kan gadon, ta zabura ta mike kamar wata zararriya…

Sai kuma ta kuma fashewa da kuka ta dur kusa gaban sa ta hade hannayen ta waje daya tana cewa….

“Daddy dan Allah ka kyale Ni nayi rayuwata pls”

Tana fadin “Daddy Ni fa ‘yar kace kada kayi min haka” Daddy ta fashe da kuka mai ban tausayi shikon…

Yana kallon ta tana kuka ji yake kamar ransa zai fita don duk duniya baya son jin kukan mace…

Balle ma na masoyiyar shi Koda ma abinda yake ma gudu kuma dai Babu yadda zaiyi da hukuncin ubangiji….

Yana cikin tinanin yaji Abu ya fadi daf, da sauri yaza bura yaga ko miye Ashe ita ce ta fadi sumammiya…

Hankalin shi ya tashi sosai da sauri ya k’arasu wajan ta Yana girgiza ta Amma yaji ko motsi Bata yi…

Jikin shi na karkarwa ya dauko ruwa ya shafa Mata Nan take tayi ajiyar zuciya shi kuma Yana ta fadin….

“Alhmdllh” tana dawo wa haiyacin ta ta zabura daga jikin shi a hankali ya fara magana yadda zata jishi…

“Fateema kiyi hakuri Wallahi bayin Kai na bane Allah ya riga ya rubuta sai na aure ki”

Ai kowa bai garasa ba ta kuma fashewa da kuka yana Bata hakuri Amma kamar ma Bata San da mutum a wajan ba….

Muje zuwa

Comment
and
share
1/23/20, 11:43 AM – +234 706 211 8047: 💦💦💦💦💦💦
💦💦💦💦
💦💦

KAWAR ‘YATA CE

®�
GASKIYA WRITERS ASSOCIATION�
{ Gaskiya É—aya ce daga Æ™inta sai É“ata, burinmu mu faÉ—akar da al’umma domin ribantar duniya da kuma lahira. }

     🎐 ```G•W•A```🎐

GASKIYA DOKIN ƘARFE•🏇🏼

Story & written
By
Sumayya A shehu

    Page 2

Duk abinda yace har ya gama Bata dashi komai ba kuka take har bacci yayi awun gaba da ita….

Kwanci yar ta ya gyarama yaja mata bargo yara gemata haskin wuta ya ficewar shi…

Yana komawa kai tsaye part d’inshi ya wuce toilet yaje yayi alwalla ya shinfid’a sallaya yafara gabatar da sallah nafila yana kai ma Allah kukan shi…..

Yana haka har bacci yayi awun gaba dashi a saman sallaya…..

Kiran sallah farin ne yata dasu dashi har ita dan bawanda yayi bacci mai dad’i…..

Tana tashi da addu’a a bakin ta toilet taje ta d’auro alwalla ta fara gabatar da raka’atanil fajar kafin atada sallah …..

Tana kan sallaya daddy yashigo ya tasheta yagan ta har tatashi bai ce da ita komai ba ya fice….

Dan ko kadan bata d’ago takalle shi ba tana kan sallaya akatada sallah tashi tayi tayi sallah bayan takammala tafara azkar har gari yafara haske …

Alamun za’a shigo wa d’akin taji dan haka da sauri tatashi ta kulle d’akin Alk’ur’ani tadauku tafara Karantawa ko zataji sauk’in abinda takeji …

Koda ya k’arasa yaga takulle dakin sai yayi murmushi ya koma part dinsa yana shiga ya kwanta yana aikin tunani, dadai yaga tunanin ba mai k’arewa bane tashi yayi yaje part din Hjy Hadiza uwar gidanshi …..,

Da sallama yashiga falon Amma bata nan yak’arasa bedroom d’inta…,

Koda ya k’arasa tsaye yayi yana kallonta tashirya tayi kyau sosai idan kaganta ba zaka ce tana da shekara sama da arba’in ba, turare ta d’auka ta feshe jikin ta dashi tana kammalawa ta taku har gabansa da takun ta mai jan hankalin shi sai kace babu abunda kedamun ta…. ,

Tana karasu wa da murmushi tafara gaidashi cikin kisa da iya duniyan ce,

Shi Kuma yana amswa yana tambayar ta yasuka tashi ita da yaranshi ,

tace “duk Lafiya k’alau suka tashi “,
tak’ara da cewa ….

“Ya amaryar mu ?” yace “Lafiya k’alau take “, sai tace ‘ muje Berakfast dan nasan yunwa kakeji ka kira amarya kafin nakira su zainab”, yace “tom….”

Tana fita yabita da kallo yana murmushi shima part d’insa ya koma yayi wanka yashirya yafito …

Ba laifi koshi yayi k’yau yafi to cikin wata shadda Ash could tunda yafito Hjy ke sakar masa murmushi koda yak’arasu su Zainab da Ummi da Khulsum sunk’arasu suna fad’i, “daddy ina kwana ….”

Cikin fara’a sa yake amsawa da lafiya k’alau ya tambaye su yasuka tashi suma suka ce Lafiya k’alau Momy tajama sa kujerar dinning yazauna suma suka zauna…..,

Yace “ina Nabila take?”, sai Mummy tace ” k’ila bata tashiba”, sai yace “Khulsum jekikira Antyn ki”, tace tom….

Tashi tayi tatafi Mumy har tafara had’a ma Daddy tea ta kalleshi da kulawa tace “ina ‘yata koma nace k’anwata tana fad’a”, tana murmushi , yace “oh Allah nasha’afa …..”,

Sai mummy tace “tun yanzu zaka fara barmin ita da yunwa koh…”

yace “A’a tuba nike, ayiman afuwa “, yana had’e hannayensa waje d’aya , Zainab ya kalla yace ” taki ki kira ta “, tace ” toh Daddy “,

Muje zuwa

Commet
Nd
Shaya
1/23/20, 11:48 AM – +234 706 211 8047: 💦💦💦💦💦💦💦
💦💦💦💦
💦💦

 *KAWAR* *'YATA* *CE* 

®�
GASKIYA WRITERS ASSOCIATION�
{ Gaskiya É—aya ce daga Æ™inta sai É“ata, burinmu mu faÉ—akar da al’umma domin ribantar duniya da kuma lahira. }

     🎐 ```G•W•A```🎐

GASKIYA DOKIN ƘARFE•🏇🏼

Story & written
By
Sumayya A shehu

     Page 3

Tashi tayi tatafi a hankali tafara hawa step step d’in, kuda ta kawo bakin k’ofar knocking tafara, jin ba’ayi magana ba yasa ta tura k’ofar falon da sallama ba kowa a falon yasa ta wuce bedroom.

Saman gadu tasameta kwance, ta k’arasa ta zauna bakin gadon tad’au lokaci kafin ,tace mata “kitasu muyi Berakfast ke kad’ay mukeji ra Daddy yace na kiraki,”

Hankali tafara bud’a idon ta wa inda suka kunbure saboda kuka, arazane zainab ta kalle ta Amma tadake tace “kuka Kika kwana kinayi kenan ?” ta tsare ta da ido fuskara ta had’e ba alamun wasa a tari da ita,

Hankali ta sake je fumata wata tambayar “Daddy ne baki so shiya sa kika kwana kina kuka “.?

Da sauri tafara gargiza mata Kai Tana kuma sanya wani kuka tana cewa “wallahi kunyar ku nakeji .zeey kuyi hak’uri wallahi ba lafina bane please”

Tana had’e hannayinta sai datayi kuka sosai kafin tayi shuru.

A hankali zainab take magana “tace kada kisama ranki damuwa dok abunda Allah ya k’addara mutum yayi to sai yayi ko yana so ko baya so ,Dan haka kitashi muje muyi breakfast in har bakisun muyi fad’a”. Fateema tace ” naji bari nashirya”,

Toilet tashiga tayi wanka ta fito bata tsaya wata kwalliya ba.tasan ya material mai k’yau duk da batayi kwalliya ba tayi kyau , mayafi ta d’auku ta sanya ta taku wajan Zainab tace “muje “.

Kallon ta tayi har tasu tayi mgn Kuma tafasa tace muje,

Suka fara tafiya har zasu fita Zainab tace “dan Allah kisake jikinki kada Daddy ya d’auka dukanki akayi “, tana murmushi tana kallon ta,

Bata ce komai ba suka fara tafiya cikin natsuwa har suka sakko,

Tunda suka fara sakkowa hankali Daddy yakoma kansu har suka k’ars so, Zainab tajema ta kujera tazauna kafin itama ta zauna,

Tunda tazauna Daddy yakafeta da ido yanaji kamar ana k’ara mishi sonta a zuciyarshi,

Duk abunda yake Mummy na kallonshi Amma tayi kamar bata gasniba sai dai ita kad’ay tasan mitake ayyanawa a zuciyarta,

Tana Zama ahakali tafara gaida Mummy cikin natsuwa Mummy ta amsa da fara’a a fuskarta sannan tace “Daddy ina kwana”, kanta na k’asa tana wasa da stones din mayafinta….

Ya amsa yana murmushi, akafara breakfast bakajin mutsin komai sai na cokali har sun kusa kammalawa Nabila ta k’araso tana ta yatsine fuska,

Ta gaida Mummy Daddy tazauna tana had’a tea ahankali Fateema ta d’ago kanta tace “Anty Nabila inkwana “,

Sai tayi kamar bataji ba kallon da Daddy kemata yasa mummy tace “Nabila baki gaida Antyn ku Fateema ba”, sai da suka had’a ido da Mummy sannan tace ” ina kwana”

Ta amsa tana murmushi

Tunda ta zauna bata ci komai ba, spoon d’in hannuta take ta juyawa da taga bazata iya ciba sai tashi tayi tana Kiran Alhmdllh , Mummy tace “badai harkin tashiba “, tace “Allah mummy na k’oshi”, mummy tace “mekika ci ?”, tace ” naci Mumy “, tace “yayi zamu hudu anjima , “

Part d’inta takoma Daddy yana kallonsu baice komiba dan yasan baci zatayi ba shiyasa ma yace Zainab takira ta ,

Dan shi Koda yaje ba bazata zoba ..

Ahankali take tafiya har ta k’araso falon ta tazauna bisa kujerar falon d’akin tabi da kallo tana fad’in “gaskiya ankashe naira a wurinnan Kuma tasan bakowa yayi wannan aikin ba sai Daddy, dan tasan iyayinta bawani karfine dasu ba dazau yima ta haka ba,

Ita har mamakin daddy takeyi da ya rufe ido sai da ya aureta

Tunda tatafi Daddy yaji baza iya cin komai ,ba ,

To fah🤔

Muje zuwa

Commet
Nd
Share
1/23/20, 11:48 AM – +234 706 211 8047: 💦💦💦💦💦💦💦
💦💦💦💦
💦💦

 *K'AWAR* *'YA TA* *CE*

®�
GASKIYA WRITERS ASSOCIATION�
{ Gaskiya É—aya ce daga Æ™inta sai É“ata, burinmu mu faÉ—akar da al’umma domin ribantar duniya da kuma lahira. }

     🎐 ```G•W•A```🎐

GASKIYA DOKIN ƘARFE•🏇🏼

Story & written
By
Sumayya A shehu

       *Page 4*

Amma bai nunana ba sai da akaiyi seconds sannna yatashi.

” yace Hajiya ni zan fita dan akwai wasu mutane dake jirana.

“tace to Alhaji Allah ya kiyaye hanya. “Yace ameen”.har yakai bakin k’ofa zai fi ya sake wata maganar.

” Nayi man tuwa fah d’akin Fateema”.

Hajiya tace tau sai da ya wuce tabishi da wani kallo.

Dan tasan ba abinda yaman ta yana dai sunne ya ganta .

Ta koma ta zauna inda yaranta ke zaune

Tana cikin tunani aka turo k’ofa da ido ya kafeta yana kallonta a hakali ya k’arasa cikin fallon yazo ya zauna kujerar dake facing d’inta ya zauna.

Yana kallonta kanta na k’asa sun d’auki lokaci a haka sai cen yace. “Kin tashi lafiya?”.

kamar za tayi kuka, tace “Eh” jikinta na karkarwa.

Daya lura da hakan ya tashi zai fice har yakai bakin kofa yace. “Akwai kayan abinci a sashinki ki duba duk abinda babu idan nadawo ki gayamin”.

Bai tsaya yaji mizatace ba yafice warsa.

Yana fita ta kifa kanta ta fara kuka, mai ban tausai sai da ta gaji dan kanta tayi shuru.

Alamun za’a shigo sashinta yasa tayi sauri ta shiga toilet wanke fuskar ta tayi sannan tad’auki k’aramin towel ta goge fuskar ta dashi sannan ta fito.

Kwance, ta sameta saman kujere kallo d’aya Zainab tayi mata ta maida hankalinta da wayar data keyi ..

Sai data kammala tace. “Kina can kina kuka ko?”.

Hmmm miki ka maida ni hali batari da ta kalleta ba.

tace sarki kuka filon dake kusa da ita ta jefa mata. “5ace nice sarki kuka?”. “Tace eh d’in”.

Tace zaki gane suna cikin firar, sai ga Khulsum ta zo da gudunta ta fad’a jikin Fateema tana cewa. “Anty shine zaki tafi bandani”. Ta fad’a kamar zatayi kuka.

Magana tayi mata tace.

” Lokacin dana tafi kina school shiyasa banje dake ba”.

tace “To in zaki tafiya zaki je dani?”.

Tace.

“Sosai ma”.

Tace “Anty yau me zaki girka muna mai dadi?”.

Tambayarta tayi da cewa. “Mekike son ci ? Autar Mummy”.

Da murnushi a fuskarta tace yauwa .”Anty shiyasa nake k’ara sonki”.

Fateema tayi mumushi tace. “Tuwun shinkafa miyar ganye”. Fateema tace “Yanzo ko zamu shiga kitchen nida Zee.

Tace. “Yauwa Antyn”. tace Anty harda kunun Aya kinji Antyna, irin na ranar nan tace naji zanyi miki har zata yi magana zainab ta daka mata tsawar da tasa kata yin shuru bata shirya ba.

Tace.”Kuma baza a yiba”. Aikuwa Khulsum ta fara canja fuska zatayi kuka Fatima tace. “Kada kiyi kuka, yanzu zan miki zo nan”.

Tace. “To Auntyna nagode”. tashi tayi ta fita tana murna.

Tana fita Fateema tace ma Zainab “Ki tashi mu shiga kitchen”.tace “Wani kitchen Kuma?”. tace “Dan Allah ki bari a kwana biyu kafin ki fara shiga kitchen nasan akwai gajiya a tare dake.

“A’a kitashi mutafi kinji kada Mummy tazo taga ba ayi komai ba.

Tace “A’a nasan zatasa ayi”. Ta ce nida tasu muje tace tau naji Zainab ta kuma cewa kinsan yau friends d’in mu zasu zo koh.

Tace “Da gaskey?”.tace da gaskey nake tace to tasu mu je dan nasan d’azu Aysha sunzo ba aikin daza muyi kinsani koh tace to muje.

Mummy ko tunda Daddy ya fita tako ma falonta tana ta zagayin d’aki.

Can ta jawu waya da ke gabanta tad’an na wata number ringi da ba wuce biyu ba aka d’auka tace.

“Hajiya yaushe ne zaku zo?”.Banjj mi akace ba a d’ayan b’an garin.

Naji tace banga wata alamaba atari da ita wada zata nuna haka tace sai dai kun shigo …….

Suna shiga kitchen takunnan gas sannan ta d’ora ruwan tuwun.shinkafa bayan ta kammala.

Sannan ta gyara kayammiya miya tayi blending sannan ta d’aura miya.

2 dai_dai suka kammala sannan suka jera saman dinning suka wace domin gabatar da sallah.

Part d’inta ta Kuma toilet taje tayi wanka kana tad’aura alwalla.

Koda tafito wardrobe tab’ud’e ta d’auko hijab da abin sallah tafara ga batar da nafila kana tayi sallah azzahar

Bayan takammala azkar, sannan taje gaban mirrow tashafe jikin ta da mayuka maso kamshi.

Bata tsaya wata k’walliya ba dan yanzo bata gaban ta riga da sikt tasanya na ataffa duk da batayi kwalliya ba bai laifi tayi kyau,

Muje zuwa

Commet
Nd
Share
1/23/20, 11:48 AM – +234 706 211 8047: 💦💦💦💦💦💦💦
💦💦💦💦
💦💦

 *K'AWAR* *'YATA* *CE* 

®�
GASKIYA WRITERS ASSOCIATION�
{ Gaskiya É—aya ce daga Æ™inta sai É“ata, burinmu mu faÉ—akar da al’umma domin ribantar duniya da kuma lahira. }

     🎐 ```G•W•A```🎐

GASKIYA DOKIN ƘARFE•🏇🏼

Story & written
By

   *Sumy*�



            *Page 5*

Parlour ta zauna tana tunani, cikin haka taji kamar hayani na tashi Kuma kamar part d’intane za’a shigo .

Da sauri tayi bedroom d’inta ta tad’auku mayafi tafito tana fitowa suna shigowa.

Tun Basu shigo parlour ba suke kirin amarya Daddy mu kina inane .

Tana jinsu tayi kamar bata jiba zuciyarta na kuna

Sai zeey “tace musu Dan Allah kudaina dan yanzo tana iyayimuna kuka.

” Ta kuma cewa dan Allah kada kuje kuyi tada mun ta da surutu .

Aysha “tace sai munyi d’in ko zaki hanamu ne ?

Batace dasu kumi ba suka k’araso parlour.

Saman kujera suka ganta tayi tagumi da alamu kuka ta keyi

Da sallama suka k’arasu parlour Basu damu darashi amsawar da batayiba haka sukakarasu wajanta.

Maryam da sauri taje wurin da take zaune taja jikin ta kamar jira take ta k’ara fashewa da wani sabon kuka, mai ban tausai.

Cikinsu Babu Wanda ya hanata duk jikin su yayi sanyi sai can Maryam tayi k’arfin halin magana ta fara lallashinta itama tana kuka da k’yar tayi shuru tana Bata magana tana cewa.

“Duk abuinda ya samu bawa rubutacene dan haka kiyi hak’uri kuka, bashine mafita ba”.

Dan haka duk abunda kikeji ke ajeshi Ki rike mijinki ki dauka aljanna Kika zo nema bawani abuba dan haka kinatsu ki rik’i mijin ki inhar kinason kwanciyar hankalinki da na iyayinki please”

Dan Allah Teema kizamu mai biyayya ga mijinki da dangin sa kizauna da kowa lafiya Kuma kicigaba da mutun tasu dan Allah.

Ahakali tafara dagu kanta tana cewa insha Allahu zanyi kada kisamu damu haka suka cigaba da firarsu har suka samu tasaki jikin ta suna cikin fira Ummi tazo.

“Tace anty Zainab

Mummy naki ranki.

“Tace Tau kije zanzo “tace to sai Fateema” tace Ummi ba ko gaisuwa “tace ai na gaisheki tana yatsani fuska.

Fateema tayi mumushi Zainab har zata kaima Ummi duka ta gudu.

“Tana cewa sai nagayama mumy

Zainab tace Zaki gani bayan ummi tafita Zainab “tace Dan Allah kiyi hakuri abuda ummi tayi.

Bata Kai da K’ara sawa ba tace haba miye haka zeey? kedai tashi kije kiran da Mummy kemiki.

” Tace naji tashi tayi tanacewa subari tazo.

” Suka ce to tana fita Aysha tada wo kusa da Fateema “tace ke ki bude kunniki wallahi kada ki soma kice Zaki walakanta Daddy gabansu wllh duk son da zeey kemiki saikun samu matsala.

Dan haka Kiki yaye kinji ko kuma kici gaba da ba Mummy girmanta haka Suma ‘yauwansu Fateema ‘tace kada kusamu damu insha Allah zan ki yayi.

Sai can Aysha “ta ce to tashi ki daukumuna kazar amarci tana Fada tana kallon.
Fateema tana dariya

Fateema tacanja fuska alamun zatayi kuka maryam takaima Aysha duk tana cewa teemana k’yaleta kinji “tace to my sweet.

maryam nasan ke kaday kikadamu Dani.

Zainab tun kafin takarasu dakin Mummy tagane cewa Mummy tayi baki Kuma tasan baza su wuce su mama shafa ba.

tana shigowa da sallam suka amsamata .

“Sukace kinacan wajan kanwa uwarki koh.

Zainab taba ta fuska batace dasu kumaiba Mummy “tace bazaki gaidasu bane ‘tace inayininku Hajiya Hafsa “tace bamasu kibari sai kanwar ubanki tabaki dama ehe .

“Yakara da “cewa Kuma kije kikiramana ita in zata zo sai Hajiya kubura _tace karma tazo wallahi inci ubanta a gidannan sai Mummy “tace bakiji anma magana ba kin zobu ma mutane ido batace kumaiba tafito tana kuka,

saida tagama kuka,nta tana mai tausayin Fateema dan tasan kowaye su. sannan ta tafi takirata.

Koda tashiga tasamisu suna fira Aysha natayima fateema tsiya.

ahankali takarasu sai da ta zauna sannan “tace Teema Mummy nakiranki “tace to tana mikewa “tace my sweet maryam kubari nazo.

“Tace to ta gyara mayafinta sannan tafice tana fita.

Zainab tabi bayanta atari suka k’arasa part din mumy a parlour ta same su

Da sallam tak’arasa suna ganninta gaba dayan su suka zubamata ido suna kallon ta.

Saboda kallon da sukemata duk ta tsagu

ahankali suka karasu wajansu suka samu wuje suka zauna Hajiya Binta “taca ma zainab kitashi kibamu waje kinzo kijimi zamuce ko.

Girgizamata Kai tafarayi.

Tadaga mata tsawa da gudu Zainab tabar parlour tana kuka,

Fitarta keda wuya Hajiya shafa tace amarya Alhaji baki laifi gabadayan su suka kwashe d dariya harda tafi suna nuninta hawaya suka rika bulbula akumatunta batace dasu kumaiba har suka ga ma yima tsiya sukace tatashi tabasu wuri .

Har zata mik’e Hajiya Luba “tace ke kunyi ganganci keda iyayinki kishi da group7

Har zata sake magana tafasa tana mai nunama Fateema k’ofa

da kir ta iya tashi har zatafi ta Hajiya binta “tace saura idan yadawo ki gayamai ehe.

Bata ce komi ba haka take tafiya har takai part dinta inda ta barsu nan tasa mesu jikin ta asanyaye ta zauna.

Maryam “tace sweet teema lafiya dai koh.

“Tace lafiya k’alau tana murmushin karfin hali Amma Zainab bata yaddaba tadai k’yaleta batace kumiba.

Haka sukayi tafirarsu har magarib sukayi sallah sannan sukayimusu sallam to fah na Fateema tafar rikice musu da k’ir tabarsu suka tafi tafiyar suke da wuya ta fara San arta sai da tayi mai isarta sannan tayi shuru .

Toilet taje ta sakar ma kanta ruwa sannan ta É—oro Alwala tayi sallah sannan tafara aikin ta na tunani .

Daddy tunda yafita aiki ya hanashi fitowa Yana tason ya dawo Amma Babu hali shi ai bai samu kan saba sai dab da magarib .

Ya fito koda yafito anata kiraye-kirayen sallah masallaci ya wuce bayan ya angama magarib bai fito ba sai da akayi sallahe Isha’i.

Sannan yayo gida Yana shigowa part ÆŠinsa ya wuce bayan yayi wanka yana fitowa rik’e da towel yana gogar jikinsa Mummy ta shigo taci kwalliya tayi kyau sosai tak’arasa tana “cewa Alhaji kadawo “yace kinganni sai yanzu. “ta ce Allah tun dazu mu ke ta ji ran dawowar ka.

Tana karb’e towel d’in dake hannusa tana Ƙarasa goge masa jikin sa.

cike da duniyan ci bayan ta kammala ta shafe shi da mayuka masu Ƙamshi ta Ɗauko mishi kaya marasa nauyi .

bayan ya kammala sanya kayan parolurn yaje yazauna ta kawo mi shi abinci ya d’an ci ba sosai ba “yace ya Ƙoshi.

Dan shi ba abincin ke gaban shi ba .

Burinshi yaje ya ganta ko zai samu natsuwa.

Nan Mummy tayi tajansa da fira Amma duk abunda take zuciyar shi naga haskin idaniyarshi .

tana tayi masa fira wata yana fahinta wata ko sai yace eh.

Haka har su ka kai goman dare ba tare da ya samu yagan taba.

Daya ga abun ba mai Ƙarewa bane “yace wai ina yaran nan?”.

“Tace tunda akayi sallah suka shege ÆŠaku nan su ban kuma Jin motsin suba”.

yace “Ok”.

“Yace bari na tashi naje naga Ƙanwarki”.

Yana faÉ—in haka sai da gabanta yafad’i amma tada ke tayi mumushi tace “to muje na raka”.

Yace “kidai haÉ—a min ruwan lipton kafin nafito”

Tace “to dan ba haka ta soba”.
tace “zan haÉ—a”

yace “ok” yafice ..

Tunda ta kammala sallah take kan sallaya tayi kuka, tayi tunani har bacci ya É—auketa a haka.

Daddy ya same ta ya ƙaraso wajan ta a hankali yakai hannun shi yana shafar fuskar ta.

Ji tayi kamar wani abu na shafar fuskar ta da sauri ta buÉ—e ido .

Suka had’a ido da sauri ta miÆ™e zaune jikin ta sai rawa yake “tace Daddy ina wuni sai da ya lumshe ido yace “kina lafiya”.

tace “lafiya k’alau”

kanta na Ƙasa tashi yayi yazo dab da ita ya zauna yana “cewa “mi kika ci yau?”.

yana kallon ta ba tace komai ba tashi yayi yaje wurin Mummy yasa ta haÉ—a mishi tea ya kawo ma.

ya kawo mata mik’a mata kofin yayi ta karb’a.

Ahakali ta ke sha har ta sha sosai.

Sannan ya zuba mata abinci yace “kici” tace “Daddy na Ƙoshi”

Yace “kici ko kad’an pls” saboda kunyar sa da ta keji a hankali ta soma ci taci ba sosai ba tace “ta Ƙoshi” ruwa ya kawo mata tasha yace ko ke fa.

sunda É—e bai tashi ba ita ma bata ce komai ba a haka har bacci ya É—auke ta.

Ya maida ta saman gado ya gyarama ta Kwanciya ya rage mata hasken wuta yajawo mata Ƙofa ya fitowar sa.

Yakoma part ÆŠinsa Koda yakoma Mummy tana nan tana jiransa tace “ka dawo?” yace

“eh”

Lafiya take ko yace “eh” Dan Shima bacci yakeji ko lipton bai tsaya shaba ya kwanta bai jima da kwanciya ba bacci ya É—auke shi……

Muje zuwa

Commet
Nd
Share
1/23/20, 11:48 AM – +234 706 211 8047: 💦💦💦💦💦💦💦
💦💦💦💦
💦

 *K'AWAR* *'YATA* *CE* 

®�
GASKIYA WRITERS ASSOCIATION�
{ Gaskiya É—aya ce daga Æ™inta sai É“ata, burinmu mu faÉ—akar da al’umma domin ribantar duniya da kuma lahira. }

     🎐 ```G•W•A```🎐

GASKIYA DOKIN ƘARFE•🏇🏼

Story & written
By
Sumy

BISMILLAHI RAHAMANIR RAHIM

*page 6*

Kiran sallar farin Daddy yafarka da addu’a a bakinsa.

Tashi yayi ya shiga toilet ya watsa ruwa ya d’uru alwala yafi to

sai da yayi na fila yakai kukan shi wajan ubangiji bayan ya kammala ya tashi Mummy.

Cikin magagin bacci tace “natashi”

Fita yayi yayi part d’inta Koda yaje akan sallaya yagan ta karasowa yayi yace “Ashe kin tashi?”

Tace “eh”

Daddy wucewa yayi masallaci bayan ankamala sallah bai shigo gidaba sai da gari yayi haske .

Yadda yabar Mummy haka yasameta.

Da sauri yak’arasa wajan ta.

Yana cewa” Hajiya baki tashiba? kitashi gari har yayi haske”

Ahankali take b’ud’e idonta ta sauka kan gado part dinta takoma sai da tayi abunda takeyi sannan tayi sallah .

Koda Fateema takamala sallah tayi azkar ta gyara komai na part d’inta tayi wanka tashirya bai laifi tayi kyau kwance take saman kujera tana Tunani umman ta.

Da Baban ta da k’anneta kewar su ,dok, ta addabe ta.

Kuma gashi yanzun ko waya bata da ita bale taji ‘yan gidan su.

Jitayi yau tana sun jin muryar Ummn ta taji bazata iya hakura ba tashi tayi waje zata je dakin Zainab.

Steps day ta taka suka hada ido Daddy shima yazo wajanta .

Da sauri ta kuma ta zauna bisa kujerar falon hankali yataku zuwa gareta.

da sauri ta ce Daddy ,”in kwana?” kallon ta yayi yace “lafiya k’alau sannan yakara da cewa “ina zakije kamar ba zatayi magana ba tace “wurin Zainab”

“Yin me i Yana kafeta da ido .

Tace “wayar ta zan karb’o nak’ira Umman ta tana fad’i kamar wadda akayima tilas.

Fita yayi bajima da fitaba yadawo riki da kwalin waya a hannunsa mika mata wayar yayi ta karb’a

Yace akwai slm aciki yakuma yace “Dan Allah Fateema kiyi hakuri kinji wllahi sonki ne ya rufemin ido bana ganin kumai sai ke.

” Dan Allah inason kiba ni had’in Kai muyi Zama na amana wllahi Fateema ba dan naci zarafinki ba na aureki.

” Nasan ni ma laifine gareki Amma “Dan Allah ki yafemin .

Kamar wani karami yaro Daddy dok ya rakicema ta.

Ita abun nashi yanzo har tsoro yake ba tace “Daddy dan Allah kaje kada Mummy tashigo please”

Kamar tayi kuka yace “ko tashigo mizatayi ?

ta “a’a Daddy wllahi kunyar ta nakeji tana mafashewa d kuka,

Yace “naji daina kuka yanzo zan tafi Amma kishirya a kowani lokaci zakimin rakiya bai jira mizatace ba yafice

Da kallo tabishi tana koma Mai Mai tawa rakiya Kuma tanasheri hawaye wai yau daddy ne a ma tsayin mijin ta .

Wayar tadauka ta kunna ta taga akwai slm tunani tayi akwai kude a wayar kowa.

Number daya ce kuma tasan ta Daddy ce.

Ganin tayi k’ila ba kud’i a ciki Kuma gashi tanasu jin Ummanta .

Tashi tayi taje wajan zainab takar b’o wayar dan wannan ba Kati aciki .

Sauka tayi taje dakin Zainab koda tasau ka taga falon dok ayamutse tayi mamaki Amma ita dai yau Ummanta takesun ji shiyasa bata bi takan sa ba.

Ta wuce d’ikin Zainab knocking tayi taji ba’a yi magana ba takoma wani knocking da yake d’a kin su d’aya da anty Nabila.

Afusace tafito tabud’e k’ofa a tunanin ta Zainab ce tana b’ud’ewa zatashi ga da sauri ta tunku d’e ta ba wani shiri tajita k’asa daf .

Da sauri Zainab dake toilet tafito ganin Nabila bakin k’ofa yasa ta k’arasuwa da sauri.

Fateema tagani tana k’ukarin tashi Amma tagaza da hanzar tayo wajan ta tana mik’ar da ita.

Tana cewa “baki ji ciyoba ko? ta ce”eh”

Nabila ta karasu wajan su tana huci da yatsa take nuninta tana cewa “kada ki kuskura ki Kuma d’auku kazamar k’afarki ta ma cuta ki zo dak’in nan .

Wllahi kika K’ara sai kinyi dana sanin.

muna fukar banza muna fukar yaufi.

Mai fuskar muna fakai Ida aka ganta kamar ta Allah.

Kamar haya niya Mummy taji dasauri tafi to tana kallon su bakin k’ofa Amma kumai batace ba.

Asalima dadi taji abin da Nabila ta yi ma Fateema Zainab data ga cin mutuncin bama k’arewa ba ne.

Ta ce “haba anty Nabila Dan Allah kibari kin tureta yanzo da ta jiciyo fa? mizaki ce ?

Nabila tace “Oh har yanzo kinan Baki rabu da itaba Kena Koh?

“Amma anyi asararriya awajin nan dok abunda tamiki bazaki bartaba kenan?”kin fison ta d uwari ki.?

Tana mai janyo Zainab tana Sanya ta ad’aki .

Taci “ke kuma kafin na k’irga uku kin bar wurn nan tana kuka kasa kasa zuciyarta na Kuna tafa ra takawa sannu sannu.

Har zata far hawa steps din farin Mummy tayi sauri tace “amarya mu Fateema yau ya akayi akabar falon kaca kaca haka.

Tsayi tayi bata ce kumai ba Mummy tace “fateema kobakijiba ne.

Dan Mummy nuna tayi kamar bata San miya faro ba .

A hankali tace “yanzo nakesun nayi Mummy” .

Tace to “a yi sauri pls” dan yau muna da baki ta ce “to Mummy.

A haka tafara gyaran gida tanayi ta goge kwalla har ta gyara falon tsaf.

ta San ya turarin hayaki masu kamshi gaske bajimawa gida yadau kamshi .

tana kammalwa kitchen ta wuce ta hada break fast ta jera a dinning sannan ta wuce part dinta .

shigar ta keda wuya tafashi da kuka tana mai tausayi kanta tajima a haka daga baya tashi tayi tayi wanka takwan ta

Wayar da Daddy yakawo ma take ta juyawa tana tunani yazatayi tanasun jin iyayin ta wani hali suke ciki Amma bata samuba tana haka har bacci ya dauke ta.

Daddy baima San wanasn da ake tuyawaba Dan Yana ko mawa part dinshi anty shi tayimishi Kiran gaugawa shiya sa ko breakfast ba tsaya yi ba yafita

Ita ce bata farka ba sai sha biyu saura cikinta yafa suwa alamun yauwa takeji Dan rabunta d abinci tun darin da Daddy ya tsareta sai taci.

da sauri tayi kitchen d’inta ta had’a tea tasha sannan taji dama koshi da k’ir ta iya Sha .

Tana zaune saman kujerar falon kulsum tazo da gudunta tana cewa “anty Fateema dake zaune tace “na am” kulsum .

Ta fada jikin ta tace “anty mummy nakiranki gabanta sai da yafadi acikin ran ta tana ta fadin Allah kasa lafiya.

Tashi tayi suka sauku ita d kulsum tun kafin takarasu suka fara antayama ta hararar datasa hanjin cikin juyawa.

Na take jikin ta yadau rawa haka takarasu wajan su su uku ne zaune cikin shiga ta alfarma kuwace naji d nira da gayo kallo daya zaka musu kaga suna kama da Mummy.

Koba a fad’a ba dagani family d’in Mummy ne.

Hajiya Asma’ u data daka mata tsawa bata san lokaci da kuka Mai k’arfi y kub’ucema taba .

Dan ita gaba d’aya tsoron su takeji

jikin ta na karkarwa ta k’arasu gabansu

Dan gaba d’ayan su ba alamun Wasa atari dasu kafin takai wajan su ta dur kusa tafara kuka,

Hajiya karima tace “baki mayi kuka ba wllahi sai nan gaba.

Mutukar kikace Zaki ciga ba da Zama gidannan wllahi ko kukan jini sai kinyi.

Bata ce musu komiba kuka take mai ban tausai sai dayar tace “ina mai baki sha wara tun ba aje ku anaba kibar gidan.

Wllahi ku kiyi Dana sanin zuwaki duniya.

Suna gama fadar haka Nabila tace “kuma kije ki duramuna abinci rana kuma idan kin gama kije d’akina ki gyaramin.

Kuma kije ki gyaramin Wanda anty Mimi zata zauna dan nasan kowa ni lokaci zata zo.

kuma wllahi dok bakiyi min dai dai ba jikin ki zai gayamiki jikin ta nakar karw tatashi ta tafi kitchen tana kuka.

Zainab ko dok tanajinsu Amma Mummy ta hana tace kumai .

Sai dai tashige d’aki tayi ta kuka tana mai tausayi teemar ta .

Haka tawuni aiki ita abba ta samu kanta ba sai daf da magarib Dan Koda tagama aikin d akasata Mummy tace ta “dura na dare .

Daddy kiran Mummy yayi yace mata tafiya takamashi tayi mashi addu ‘a tace adawo lfy .

Tana kwance wayar da Daddy yakawo mata ta fara rura tayi mamakin mai kiranta Amma dan tasan bawan da yasan ta da wannan slm .

dauka tayi taga mekiran ta har wayar ta tsinke aka Kuma Kira .

Haka tad’a ka takara a kunninta batayi magana sai da yayi a jiyar zuciya sallama yayi mata sai yanzo tage ne. kowaye .

kenan daddy ne kamar bazata ammasa ba amma ta “amsa yace “kin wuni “lafiya

tace “lafiy kalau

Yaci “kin ga ban dawo ba ko tafiya takamin yanzo Amma kiyi hakuri kwana hudu ne zanyi insha Allah.

Zan dawo aiyi min addu a.

Kamar bazatayi magana ba tace “Allah yaka lafiya yamai daku lafiya.

Wani dadine yaziyarci zuciyarshi Yana Kiran “amen ameen.

yace “kuma dok abuda kikesu kimin magana kuma anty sa’ a zatazo kowane lokaci zaki iya ganin ta.

Kinji kiyi hakuri idan nadawo har wajan su Umma zankai ki kinji ko.

Tace “to yace “mikika ci ta ce “abinci yace “nasan bakici komiba.

” Amma Dan Allah ki tausayamin kici ko zan samu sukuni.

Gajiya da wayar tayi tace “to yanzo bari naje na ce.

Yace
” yauwa Bata bari ya koma magana ba ta yanke wayar .

Tunda Daddy yatafi kullum ciki aika ce ai kace take Zainab tayi kuka har tagaji watarana takan fake idon su Mummy taje ta tayata.

Haka taka shanan wuyar aiki har lokacin dawowar Daddy.

Ranar da Daddy zaidawo tun wuri Mummy ta aika a kirata .

Muje zuwa

Commet
Nd
Share
1/23/20, 11:48 AM – +234 706 211 8047: 💦💦💦💦💦💦💦
💦💦💦💦
💦💦

 *K'AWAR* *'YATA* *CE* 

®�
GASKIYA WRITERS ASSOCIATION�
{ Gaskiya É—aya ce daga Æ™inta sai É“ata, burinmu mu faÉ—akar da al’umma domin ribantar duniya da kuma lahira. }

     🎐 ```G•W•A```🎐

GASKIYA DOKIN ƘARFE•🏇🏼

Story & written
By
Sumy

BISMILLAHI RAHAMANIR RAHIM

         *Page7*

Tashi tayi dan ta fara aiki tana sau kowa Mmmy itama ta fito.

Gaida Mummy tayi tamsa tana cewa “kinsa yau Alhaji zai dawo dan haka ayi sauri a gyara gida Sannan ashiga kitchen basai nafad’i miki kalar abinci da yake soba kin sani ko?”

Bata ce komai ba sai da Mummy tak’ara cewa “kinyi shuru kamar badake nakiba?”

Tace “eh” nasani”

Mummy wuce war ta tayi batari da tace komai ba.

Tana ganin Mummy ta wuce ta fara tsaf tace gida har zata fara morping taji ana sallama.

Amsawa taiyi tana mai juyuwa dan taga wake sallama.

Marmushi tayi tana mai k’arasuwa gare ta tana cewa

“gwaggo “in kwana?

Bata karb’amata ba tambaya ta jefu mata.

“Waya saki aiki da sassafin nan?”

“Ko masu aiki basa nan”

“Ina mutanin gidan suke?”

,Dok, a jere taje famata su kuma ba wanda ta k’arb’a .

Shuru tayi bata ce komai ba dan bata san mizata ce ba dan tasan halin yayar Daddy akwai iya fitina.

Tana cikin tunani taji tace “Fateema dake na ke fah?”

D’ago kanta tayi a kasa tace “Mummy na d’aki”.

Batama bari tak’arasa fad’a ba ta wuce part din Mommy.

Knocking tayi mata Mommy tace “waye?

“Hajiya sa’a ce kisameni falon.

Batsaya jin miza tace ba ta wuce warta.

Inda tabar ta anan tasame ta kallon ta tayi da kulawa tace “kije kishirya fita zamu yanzo .

Tace “to kamar mai koyun tafiya haka takeyin tafiya har taka part dinta.

Hajiya sa’a zaune tayi saman kujera ta d’ura k’afa d’aya kan d’aya tana karka d’awa.

Haka Mummy ta same ta ta k’arasu ta zauna tana mai cewa “Hajiya kece da safen nan?”

Sai data yima ta kallon sama da kasa ta “eh nice”

Tace “wayasa Fateema aiki da safen nan?

“Shin ma ina masu aiki ne? Ko “Ina yaranki?

“Ko kin dauka aiki yakawo ta “eh”

Tace a’a “Hajiya ban sanya ta ba ita ce dai tasanya kanta”

Tace “naji ,dok, da haka akiyaye gaba,

Suna cikin hakaFateema ta k’arasu gabansu

Hajiya sa’a taci “kin fito tace “eh nafi to”,

Hajiya sa’a tace ma Mummy “wai Ina yaran nan suke?

Mummy tace “suna d’aki”

Hajiya sa’a tace” kice suna can suna hutu ga baiwa ankawomuku mai yimuku aiki ko?”

Tace” a’a Hajiya

Tace to bari kiji daga yau wallahi kada akasake sata akin in dai ba dan ra’ayi kan ta tayi ba.”

Indai ba haka ba ni da kaina zan dau mataki tana mai mikewa tsaye tace “Fateema muje,”

Da ido mummy tabisu zuciyar ta na kuna tana cewa “wannan matar tanasu tazame mata matsala,

Suna fita cikin wata mota suka shiga direban yatada mota suka bar gida.

Inda zai kaisu Hajiya sa’a ta fad’imishi bai zame dasu ko inaba sai wata unguwa gaban wani ma dai_dai cin gida suka tsaya .

Bala laifi shima gidan yana da kyau dan shima ginin zamanine.

Fitowa sukayi cikin mota suka K’ara sa cikin gida da sallamar su .

Suna shiga wasu yan mata su gaishe su kai tsaye Hajiya sa’a falon gidan suka wuce suka zaina,

Wayar ta ta d’auku takira wata number bajima sai ga wata mata tafi to .

Zata Kai sa’a r Hajiya sa’a da fara’ar ta ta k’arasu suka gaisa da Hajiya sa’a .

Nima na gaisheta ta amsa tana fara’a bayan an gama gasawa .

Hajiya sa’a ta gyara Zama tace “inason agyaramin gatan tanuna Fateema ayimata ,dok, abunda akema amare ,

“Sannan inason akoya mata abubu gyaran jikin da yadda akeyin su ke duk abunda kikasan mace zata nema wajan gyaran jikin a koyama shi.”

Tace Hajiya kada kidamu idan wannan ne kamar angama kud’i mausu yawa Hajiya sa’a ta bata tace gasu afara dasu.

Har tamik’e tace “Hajiya a kula sosai dan cikin manyan mata za’a kaita dan haka abata huru mai kyau.”

Tace “Fateema ni zan wuce i dan inkwana biyu zan dawo kinji kuma ,dok Abu da akace kiyi kiyi kinji kiyi hakura please”

Har zata wuce Fateema tace “Hajiya ta juyu tace ‘Fateema ko kinasu wani abu ne?”

Kanta tad’aga mata
Tace “to miye?”

Tace “inasun nayi waya da Umma ta
tace “badamuwa yanzo zan ba direba ya kawo miki tace to.”

Tace “Hajiya Ummu zan wuce Amma zan ba direba yakawo mata sakon ta tace to “Hajiya sai kinji mu tace tom nagude sai anjima”,

Tana fita mota ta shiga direba yamai data gidan ta taba shi wata leda tace yakoma yakai ma Hajiya Ummu a ba Fateema,

Tunda suka fita Mummy take tunanin akan Hajiya sa’a dake sun kawoma cikas dan haka dole taje suzauna da group7
dan bazata zuba ma Hajiya sa’a ido ba

Tashi tayi taje d’akin su Zainab dan sutashi ak’arasa aiki kafin Daddy ya dawo .

Muje zuwa

Commet
Nd
Share
1/23/20, 11:48 AM – +234 706 211 8047: 💦💦💦💦💦💦💦
💦💦💦💦
💦💦

 *KAWAR* *'YATA* *CE* 

®�
GASKIYA WRITERS ASSOCIATION�
{ Gaskiya É—aya ce daga Æ™inta sai É“ata, burinmu mu faÉ—akar da al’umma domin ribantar duniya da kuma lahira. }

     🎐 ```G•W•A```🎐

GASKIYA DOKIN ƘARFE•🏇🏼

Story & written
By
Sumy

            *Page 8*

Kai tsaye d’akin su tawuce Koda taje kowace su kwance ta tasame ta Nabila tana rik’e da waya ita kuma Zainab na karatun wani novel,

Mummy magana tayi musu Sannan masuka san ta shigo d’akin,

Tace “kutashi kuje ak’arasa aiki kunsan yau ne Daddy ku zaidawo ko.?”

Zainab tace “da gaskey Mummy?”

Mummy tace “zan miki karya ne?”

Tace “a’ah”.

Tace to “kutashi kuyi sauri “

Nabila tace “Mummy Ina ita waccan Fateema komu zamuyi mata aiki ne?”

Mummy tace “hmmm kedai bari yanzo akanta Hajiya sa’a ba abunda bata cemin ba yanzo mahaka ta jeta sunfi ta.”

Nabila tace “mekika ce Mummy.”

Tace “abunda kunneki yajimiki” .

Nabila tace “Mummy yanzo Ina suka je?”

Tace “nima bansani ba.”

Kowanin su kallon Mummy yakeyi ba wanda ya koma cewa komai,

Nabil tace”wai yaushe Hajiyar Mufida tazo Gidan nan”

Mummy tace “da safen nan tazo.”

Mummy tace “kutashi lokaci natafiya ba ayi komai ba.”

“Suka ce to”

Tashi sukayi ita dai Zainab tunda Mummy ta ke magana bata ce komai ba asalima ita tausayama Fateema takeyi,

Nabila tace “mubari tadawo wallahi ,Dok, bata fad’amuna ida suka jeba sai tayi kuka a gidan nan.”

Zainab ita dai fita tayi tafara aiki ita Kuma Nabila sai da tagama cin fitinar ta San nan tafi to ,

Tace wai “yaushe Hafsatu mai aiki zata dawo?”

Mummy “tace satin nan idan suka gama biki zata dawo.”

Dan ita Nabila ba gwanar aiki ce ba shiyasa komai bata iyaba Zainab ce keyi ko girki ita ce Amma Nabila shara da wanke_wanke kad’ai takeyi Amma koshi ba koda yaushe ba,

Haka saka cigaba da aiki Mummy ko takoma d’aki tana tunanin mafita,

Sai da Hajiya sa’a ta tafi Hajiya Ummu takai Fateema wani d’aki tace “gashi nan ki zauna kafin mugama aikin.”

Tace “to”

Bayan tafita Fateema tabi d’akin da kallo karamin d’akin ne mai had’i da toilet d’auke yake da gado da k’ara mar wardrobe d’akin yayi mata kyau sosai tana cikin haka Hajiya Ummu tazo takawao mata sakon da Hajiya sa’a tabama direba yakawo,

Karb’a tayi sai da tabari Hajiya Ummu ta fice Sannan ta bud’a tana b’ud’ewa waya tagani mai kyau kunnawa tayi ta duba ta ga akwai slm Kuma aikwai kud’i aciki cahji tasanya dan ba cahji aciki sai takira Umma ta,

Tashi tayi tashi ga toilet tayi wanka tana fitowa gyara jikin ta tayi ta kwanta ba ita tashiba sai da akayi sallah azahar tashi tayi tayo alwalla tayi sallah bayan ta kammala ta d’auku wayar ta kunna tasa number Umma ta takira,

Sai da takusa tsinkewa aka d’aka ajiyar zuciya tasaki mai k’arfi shuru tayi batayi magana ba sai data ji ana sallama

Muryar kanen ta taji yana sallam da sauri tace “Nasir Ina Umma?”

Yace “Anty kece ?”

Tace “eh nice”

Yace “ga Umma”

Ta ce “to”

Umma yamik’ama sallama tayi tanajin muryar Umma ta fashe da kuka,

Acan b’agarin Umma shuru tayi sai can tayi k’arafin halin cewa “tunda kuka zakiyi to sai anjima” ai da sauri tace “Dan Allah Umma kada ki tsinke kitsaya tana share hawayin ta.

Umma tace “waye cemiki kuka, na magani da ace kuka na magani kin san da ba ayi auren nan ba, dan haka kisama zuciyar ki salama shawara daya zan baki kiyi hakuri ki dauka wan’nan tana daga cikin jarabawarki dan haka ki tsa ya ki canye ta kuma kibi mijin ki sau da k’afa kada ki d’auka wani abu kika zonema agida a’a kid’auka aljanarki kikazo nema.”

Haka Umma tayi tayi mata nasiha har taji sanyi a zuciyar ta ,

Tace Umma” insha Allah zan yi”

tace “to Allah yayi miki albarka”

tace “Ameen”

Sunjima” suna fira sai can taci “Umma yaushe su anty Fauziya zasu zo”.

Tace “bansani ba sai munyi waya zan tambaye ta”.

Tace “to Umma”

Umma tace “kashe wayar zuwa anjima dan gabaki nan nayi tace “to Umma ki gaishe da babana dan banida number kowa tace “to zasuji”

Wani dad’i taji dataji muryar Umma ta,

Tana cikin haka wata yarinya ta tashigo da sallama takawa mata abinci tace “gashi tace” to nagode” tace “Kuma tace in “kingama kizo a fara aiki “tace to ganinan zowa “.

Bayan ta kammala ta tafi suka fara aiki Hajiya Ummu ta fara nuna mata wasu abubuwa,

2 dai_dai suka kammala Sannan kuwa yakama gabansa ,

Mummy koda ta koma da’kin tayi wanka tashirya tayi kyau tana jiran dawowar Daddy har yamma tayi bai k’irata ba sai can wayar ta tafa rura da sauri ta d’auku wayar ta tana karawa a kunne ta,

Tace “ka k’arasu ne?”

Yace “a’a Hajiya kuyi hakuri dan bazan samu dawowa ba wallahi har yanzo bamu gama aiki ba k’ila ma sai nan da sati uku ku biyu”.

Bata bari ya k’arasaba ta yanke wayar ….

Muje zuwa

Commet
Nd
Share
1/23/20, 11:48 AM – +234 706 211 8047: 💦💦💦💦💦💦💦
💦💦💦💦
💦💦

 *K'AWAR* *'YATA* *CE* 

®�
GASKIYA WRITERS ASSOCIATION�
{ Gaskiya É—aya ce daga Æ™inta sai É“ata, burinmu mu faÉ—akar da al’umma domin ribantar duniya da kuma lahira. }

     🎐 ```G•W•A```🎐

GASKIYA DOKIN ƘARFE•🏇🏼

Story & written
By
Sumy

Godiya mai tarin yawa ga sister me Gwaza da aunty baby Allah yabar zumci mai d’urewa

BISMILLAHI RAHAMANIR RAHIM

            *Page 9*

Mummy wani bakin ciki ne yaru feta batasan lokacin da takai zaune ba,

Shiko Daddy daya ga takashe wayar yace “bari yabar zuwa anjima dan yasan yanzu tayi fushi koya Kuma kira ba d’auka zatayi ba.”

Kuma yakira wayar Fateema ita kashe ma nata yake, amma bari yabari ko zuwa anjima,

Mummy tace “shikenan yanzun Alhaji ya ruguzama ta abunda tashirya”.

Waya ta d’auka takira Hajiya Shafa tana gayama ta abunda Daddy yace ,

Hajiya Shafa tace “koda ma Ina sun nakiraki nagaya miki gobe zamuyi meeting saboda ko yanzo abunda yafaru dake shine yakesun faruwa da daya daga cikinmu”.

Mummy tace “cikin mu kuma?”

Hajiya Shafa tace “sai dai mun had’u”

Mummy tace ina
za’a yi meeting d’in?

Hajiya Shafa tace
“Gidan Hajiya Binta”.

Tace “to yayi sai mun had’u”

Suna gama waya Mummy tafara kai komu acikin da’ki,

Tace “nasan ba Aikin kowa bane sai na Hajiya sa’a kuma dole zamu taka mata birki “

Gaba d’ayan su bawanda yayi baccin kirki dan kowa buri shi safeya ta waye su had’u meeting ko za’a samu mafita,

Musamman wadda abun yasha fa yanzo,

Tunda gari ya waye kowanin su burinshi yayi sauri yaje suji matakin daza su d’auka dan baza su zubama wan nan lamarin ido ba,

Ko breakfast d’in kirki Mummy bata tsaya yiba tafi to,

Kai tsaye d’akin su Nabila tashiga taga basa ciki falo ta wuce acan tasame su suna breakfast k’arasu wa tayi wurin su da sauri Kulsum tace “Mummy fita zakiyi?

Mummy tace “eh” fita zanyi “

Tace “Mummy zan biki”

Tace “a’a kibari in Auntyn ki zasu fita suje dake”.

Tace “to Mummy zasuje dani ko?”

Mummy tace “eh”

Mummy ta kalle su Nabila tace “ni zanfi ta”.

Adawo lafiya suka kayi mata ,

Direba Mummy takira tafad’a mishi idan zaika ta,

Yace “to Hajiya”

Suna kawowa mai gadi na bud’ema wata mota shima direba Mummy yakutsa hancin motar sa yashiga yanayin yana packing Mummy ta fito ,

Mummy tace “Hajiya Luba kice tare munka k’arasu” sunama juna murmushi tace “kedai bari Hajiya Hadiza na k’agara safiya tayi dan naga abunda baka dauka komai ba shiya kesun baka matsala”.

Suna masu karasawa cikin parlour d’in daza’a meeting ,

Da sallama suka shiga Hajiya Shafa suka amsamu su, k’arasu wa sukayi suna cewa Har kun iso Hajiya Luba tace “nace ma nice zan fara zuwa Ashe ku rigani”

Hajiya Shafa tace “badole muzu da wuri ba naga wanki hula nasun yakai mu dare”.

Hajiya Binta batace komai ba dan ita tata ta isheta ,

Suna haka su Hajiya Suwaiba ita da Hajiya Sha’awa da Hajiya Jamila suka K’ara su,

Basu jima da K’ara su waba aka fara meeting Hajiya Shafa tace “nasan wasu daga cikinmu basu san danmi aka kira meeting d’in gau gawa ba,

To bakomai bane sai abuda yafaru sati biyu da nawace shike sun kuma faruwa yanzo,

Dan haka kusani idan
mukayi sake kojibi shi zai K’ara faruwa dan haka bazamu zubama masu so ganin bayammu ido ba.”

Kowanin su shuru yayi bai ce komai ba ,
Sai can Mummy tace “wai wace acikin mu?”

Hajiya Shafa tace “buku gane abunda nake nufiba ne naji kowa yayi shuru ?”

Sai hajiya Luba tace “munso a ganar damu”

Hajiya Shafa tace “to kunsan Alhaji Mansur zai K’ara aure?”

Dakarfi suka ce “mikika ce?”

Tace “abunda kukaji”

Takara da cewa “tun kafin Hajiya Binta ta sani, nasani, “

Dan bayan Alhaji ya dawo jiyi bai jima da shigowaba Hajiya sa’a tazo bayan mun gaisa tacemin ina yake nace yana d’akisa”

wucewa tayi tasameshi sai dana bari tajima dashiga natashi domin nashiga ina kawowa k’ufar naji tace “yanzo bazasu barshi sati biyu ba”

Yace “Hajiya munyi munyi sun k’in yarda dan haka mukace to Allah yakaimu ai da sati biyu da wata d’aya duk dayane inda rai da lafiya tace “to shikenan Allah yakaimu lokaci”

yace “ameen”

Tace mishi “ni zan wuce yace “to Hajiya takara dace wa “kaima inajiran taka”, banji abunda yace mata ba dan takamu haryar fita nikam nakuma wurin danake zaune,

Dan haka dole ne muta kama Hajiya sa’a birki dan wallahi wannan karun bazamu zuba mata ido ba”.

Sai can ta koma cewa “Amma kubani nan da kwana biyu komai nayanke zan nemeku “.

Hajiya Binta tace to “dan wallahi nikam bazan iya zama da kishiya ba.”

Haka kowa yayi tafad’in abunda zaiyi,

Ahaka taru ya watse sai nan da kwana biyu,..

Wacece Hajiya sa’a ?”,

Muje zuwa

Commet
Nd
Share
1/23/20, 11:48 AM – +234 706 211 8047: 💦💦💦💦💦💦💦
💦💦💦💦
💦💦

 *KAWAR* *'YATA* *CE* 

®�
GASKIYA WRITERS ASSOCIATION�
{ Gaskiya É—aya ce daga Æ™inta sai É“ata, burinmu mu faÉ—akar da al’umma domin ribantar duniya da kuma lahira. }

     🎐 ```G•W•A```🎐

GASKIYA DOKIN ƘARFE•🏇🏼

Story & written
By
Sumy

BISMILLAHI RAHAMANIR RAHIM

Page1�0�

Hajiya Sa’a ta kasan ce yaya ce ga maza jin su Mummy ,Su takwas iyayin su suka haifa kuma ita kad’aya ce mace kuma ita ce babbarsu

Alhaji Muhammad shine mahaifinsu yana da rufin asiri dai dai gwargwado dan akwaishi da wadatar zuci shiyasa mutane da dama sukemishi kallon mai kud’i.

Matan shi biyu da Halima da maryam

Yaransu takwas Halima ita ce uwargida san nan Maryam ita ce amarya.

Mama Halima itake da yara shidda sa’adatu da Aliyu da Nura da Abdullahi da Ahamad da Mansur.

Ita koh Gwaggo Maryam tana da yara biyu da Sulaiman da Abbas.

Suna kiranta gwaggo saboda ita da Alhaji Muhammad auren zumunci ne sukayi dan d’iyar k’anin Baban shi ce.

Mama Halima da gwaggo maraya suna zaman lafiya sosai dan idan kagansu bazakace kiyoshi ba ne dan suna zaman mutunci kowacin su nada hakuri da kawai ci dan shi baza ka iya babbace yaran su ba.

Kuma Alhaji Muhammad baya nuna ma kowacin su babbanci haka ma yaran shi yana kulada su dai dai gwargwado kuma kowanin su yasan
yashi makarantar addini da ta zamani haka suka ciga da rawuwar su babu fada babu zagi.

Lokacin da Sa’adatu takammala secondary School,

Tasu ta cigaba da karatunta dan har baban a bukiyar ta Amina yasamu musu admission d’in usuman dan Fodiyo unversity Amma baban ta yace a’a”.

Sai intayi aure mijin ta yabar ta amma shikam bazai barta ta tacigaba ba.

Tayi kuka har ta gaji dan haka dole ta tsayda wanda zata aura
cikin samarin ta,

Wanda ta tsayad dayake shima dan boko ne kuma yace zai bar ta taci gaba da karatunta.

Ba ad’au lokaci ba akayi auren Sa’adatu da Umar inda suke cikin kwanciya hankali da k’aunar juna.

Kuma bata jima ba ta fara karatunta a Usuman dan Fodiyo .

Sukuma kannen ta maza suna Karatu Kuma suna zuwa kasuwa wanji mahaifinsu Nura da Sulaiman da Abdullahi suke zowa kasuwa.

Ahamad da Mansur da Aliyu suke gyaran mota .

Kuma da lokacin karatu islamiya yayi komai suke yi zasu barshi suje.

Haka mana boko kowane su ya nada tashi basara Dai dai gwargwado ,

Aliyu da Abdullahi da Sulaiman tari suka kammala secondary School,

Kuma cikin sa’a suka samu admission,

Haka karatunsu yaciga da tafiya har suka kammala digree d’in su nafarin cikin ikon Allah suna gamawa mijin yayar su Sa’adatu ya samar musu Aiki ,

Ita Kuma a lokacin Sa’adatu har ta kammala karatun ta tafara Aiki dan tana kammalawa mijin ta yanemu mata Aikin asbiti.

Alokacin tana da yara uku Mufida Khdija da Ammar.

Haka rayuwa taci gaba data fiya alokacin ne kuma Baban su yace Aliyu da Sulaiman da Abdullahi su fitar da matar aure dan yace bazasu joining masters ba sai saunyi aure,

Koda ma Aliyu yana da wadda yake so dan tunda yaje service wata makarkata secondary yahad’u Shafa’atu tun lokacin suka fara soyayya,

Shima Sulaiman yakawo tashi Fateema amma anfi kiran ta da Binta daya ke unguwar su daya malam Usuman shine mahaifinta matan shi biyu yana da kirki sosai kuma ko d’iyan shi ba laifi sunada tarbiya,

Shima Abdullahi yakawo tashi Lubabatu d’iya ce ga Alhaji ma’azu yana dakirki sosai harkar kasu wanci tahad’a su inda wani lokaci Alhaji ma’azu yakan aiki Abdullahi gidan sa acan ne ya had’u da Lubabatu.

Ba’a d’au lokace ba aka aikama iyayin yaran kuma kowanen su yayi na’am dajin d’an Alhaji Muhammad kesun ‘yar shi,

Bawani lokace aka d’auka ba akayi bikin su,

Inda kowane su yatare a sabon gidan da yagina ma kansa,

Idan alokacin Ahamad da Nura da Mansur suka samu admission,

Bajimawa suma suka fara karatu ,

Suma basujima da aureba suka joining masters dinsu

Haka rayuwa taci gaba datafiya Kuma arzikin su na k’ara yawa .

Inda alokacin sun kammala masters d’insu sukuma su Nura da Ahamad da Mansur sun kammala digree su .

Kuma alokacin har sun kawo matan da zasu aura.

Idan Nura yakawo kanwar abukin shi Suwaiba wadda suka dai dai ta da ita .

Shima Ahamad yakawo tashi Sha’awa tana da kiri dan ranr yaje wani shago dake kusa da unguwar su bayan ya saye abunda zai saya yabi ya yafito Ashe wajan bayan kud’i wayar shi ta fad’i bai sani ba,

Ita Kuma bayan ta gama sayayyar da zatayi fitowa dazata yi taga waya yashe ak’asa tasa hannu ta d’aka tace kowaye ai zay Kira ,

Sai da yakoma gida yaga ba waya kira yayi tad’auka tayi mishi kwatancin gidansu yazo yakar ba.

Tunda ga lokaci suka fara soyayya

Shiko mansur wani Alhaji Abubakar dan siyasane sosai gyara mota ya had’a shi da Mansur yana son Mansur har yaka sance wani Abu idan zaiyi sai shawar ce Mansur yasan ya Mansur jikin shi yad’auke shi kamar d’a.

Dan haka gidan Alhaji Abubakar yakoma kamar gidansu Mansur.

Alhaji Abubakar matar shi d’aya sunan ta Hajiya Asuma’u yana da yara biyar macci hud’u namiji d’aya.

Hadiza da Rukayya da Shamsiya da Hauwa wadda akifi sani da jidda sai autan su Marwan.

Tunda Hadiza taga Mansur tafara shige ma sa shikoma baya su yayi ta kauce mata yana daure mata Amma taki dainawa har yagaji yafara sake mata .

Shikoma Alhaji Abubakar yad’auka soyayya suke yaji dad’i sosai dan haka yasame mahaifin Mansur yasheda mishi yaba Mansur d’iyar shi Hadiza koma nan badaji mawaba za’a yi biki Baban su Mansur yayi mishi godiya sosai.

Bayan Alhaji Abubakar ya wuce Alhaji Muhammad yashiga gidansa yana fad’ama matan sa Suma sunyi murna sosai .

Shikuma Munsur koda yaji hankalinshi inyayi dubu yatashi….

Yace shi fah ba sonta yakeyiba yana dai kulata ne saboda Baban ta,

Mahaifinsu yace ko baya son ta sai aure ta tunda mahaifinta yabashi ita.

Hakan akayi aure ba dan rashi yasu ba.

Akowa Hadiza tana ganin Mansur da gaske ba son ta yake ba hankalin ta yatashi har tagaya mamar ta mamar ta ce takwantar da hakalinta tace mama dan baki yadda yakemin ba.

Mama tace naji dok zai daina anjima zan Aiko Rukayya takawo miki wani abu kuma duk yadda akace kiyi kiyi inhar kina son yadai na yin abunda yakemiki.

Tace tau mama zanyi inajiran ta sai tazo tace “to yayi .

Aikowa tunda ga wan’nan lokaci Mansur yakauda zancin wani rashin so,

Dan yariga yafad’a hannu su Hajiya Asuma’u .

Haka rayuwa takasan ce musu kowanin nakula da iyalinshi kuma da iyayinsu dan yanzo har Aikin Haji sunkai iyayin su suma sunje har matan sun je .

Inda a lokacin kowanin su nada yara Abdullahi .yaran shi biyar
Aysha Saudat Nasir Safuwan da Alamin.

Inda Sulaiman ma haka Halima suna cemata (Mimi) saboda sunan mahaifiyar su sai Walid sai Usuman sai Mubarak sai Yusuf .

Sai Aliyu yana da yara uku Jawad da Muhammad amma suna kirinshi (baffa) saboda sunan mahaifinsu ne dashi sai Hafsa.

Muje zuwa

Commet
Nd
Share
1/23/20, 11:48 AM – +234 706 211 8047: 💦💦💦💦💦💦💦
💦💦💦💦
💦💦

 *KAWAR* *'YATA* *CE* 

®�
GASKIYA WRITERS ASSOCIATION�
{ Gaskiya É—aya ce daga Æ™inta sai É“ata, burinmu mu faÉ—akar da al’umma domin ribantar duniya da kuma lahira. }

     🎐 ```G•W•A```🎐

GASKIYA DOKIN ƘARFE•🏇🏼

Story & written
By
Sumy�

BISMILLAHI RAHAMANIR RAHIM

     *Page11* 1�1�

Haka rayuwa taci gaba da tafiya da dad’i ba dad’i.

Su Nura nada yara d’aya, Allah yayima Alhaji Muhammad rasuwa mutuwar da ta girgiza family dinshi, dan ankwanta dashi ba’a tashi dashi ba.

Allah yak’ar b’e abun sa, sunyi kuka har sungaji.

Itama Mama Halima wata biyu da rasuwar Alhaji itama tabashi tace ga garinku.

Sosai suka shiga tashin hankali dan cikin su bama iya lallashi dan uwansa haka suka kasance babu mai iya wani abun kirki.

Musamman dasu kaga ga gwaggo Maryam har gadon asibiti ta kwanta, hakalinsu yatashi sosai ,wasu sunyi kuka, wasu ko sunyi na zuci haka rayuwa ta cigaba da tafiya .

Inda yanzo kulawarsu gabaki daya, suka tattara ta ga gwaggo Maryam dok abunda take su sunayi mata shi sosai kuma dok abunda tace musu sunayi mata biyya,haka suka cigaba da tafiyar da rayuwar su.

Lokaci yatafi abubuwa sun sauya inda a lokacin iyalin su sun k’ara yawu .

Dan a lokacin Mansur da Hadiza nada yara biyar , Maryam wadda taci sunan gwaggo Maryam Amma suna kiran ta (Maram),sai Nabila sai Zainab sai Asma’u wadda taci sunan Mamar Mummy Hajiya Asuma’u amma suna kiran ta da(Ummi) sai Ummu kulsum wadda suke kira kulsum .

Kuma daga nan haihu tayi tsayin ta da farko Alhaji Mansur yadauka Hajiya Hadiza wani abu tayi ,amma daga baya yaga itama tadamu da d’au kewar haihuwar dan gaskaya tana son ta haifi namiji kuba komai ai ita ce da komai .

Tunda yaga ta birkici ido rufe haihu take neman tayi hardai ma yanzo taga komai nashigo masa takowace hanya dan haka bazata yadda wata tazo ta haifi d’a namiji ba,? tace “bazan ma biri tashigo bale ko macci ta haifa.

Dan yanzo kowanin su ya gina wani fantamemen gida Kuma har sun sa lakaci da zasu tare.

Aikowa matan najin a sanya lokaci da zasu tare suka shirya meeting domin sanya sabowar d’amara dan su atunaninsu majan su aure zasu k’ara.

Dan alokacin shama Abbas za’ayi aurinsa da wata yarinya jamila.

Ai babban tashin hakali garesu duk bafi neman matar da Alhaji Mansur da Aliyu Da Sulaiman sukayiba .

Aikowa kar kasu kaga yadda su Mama Safa Da Mummy Hadiza Da Binta suka d’au hauka saka d’ura saman kansu .

Aikowa babu shiri suka je wurin malamman su
sai da suka tabbatar musu in aurine baza’ashi ba sannan hankalin su yad’a kwanta, dan sun san malamman su namusu aiki mai kyau.

Bayan sundawo gida sai suke nunama mazan su a komai lokaci ne dashi Kuma ai zasu zauna lafiya da su amaren.

Aikowa mazan su sukaji dad’i dan haka komai zasuyi sai sun gayamusu dan ko lefe su suka ba kud’i suka had’u abunda sukesu .

Hidama fa takan kama idan yayari su Sa’adatu ta koma besy dan har hutu tadauka wajan aikin ta tada wu gida ita da yaran ta dan tagaji da yawon da takeyi.

Biki yaraye saura kwana uku ida su Hajiya Safa suka koma komawa wajan malamman su suka koma sheida musu tabbas baza’ayi aurin ba su sa ido suyi kallo.

Aikowa ansanya amare lalle duk abunda akeyi na alada angabatar .

Ranar jumu’a da safe su Alhaji Mansur suka kawo ma gwaggo Maryam da yayar su da k’annen mahaifinsu goro a rabama muta ne.

Haka kuwanin su yarabama mutanin unguwarsu goro.

Abu kamar had’in baki bayan sallah jumu’a sai gasu sunzo gidan malam Usuman k’anin mahaifinsu , bayan su gaisa yace musu lafiya sukace magana zasuyi dashi yace to suwuci falon haka suka wuce .

Bayan sun zauna Alhaji Aliyu yace dama abunda keta fi damu akan maganar aurin nanne yace “to ina ji ” yace dama wata tafiyace takama mu kuma za’a d’au lokaci bamu dawo ba shine muka yanke shawara kawai mufasa aurin dan haka afad’ama iyayinsu suyi hakuri munfasa kuma duk abunda muka basu mun bar musu har lefe har sadaki”.

Malam Usuman yace ai “wannan maganr banza ce dan zaku tafiya zai sa afasa aure?

Tashi sukayi Sana mai cemasa “yayi hakuri Kuma yaba iyayin yaran hakuri dan yanzo saura minti biyar jirgin su ya d’aga”.

Malam usuman yace “ni zaku mada karamin mutu?.”

Hakuri sukayi tabashi sukace kuma “bazasu samu zuwa wajan gwaggo ba yagayama ta. “

Basu tsaya Jin mezaiciba suka bari gidan da sauri .

Aikowa malam Usuman kai kawo yafari yi a falon yarasa ma mizaiyi .

Dayaga zaman da yake bashine mafitaba dole yatashi yaje gidan abukin sa malam Garba yafad’a masa abunda akeciki.

Malam Garba hukuri yayi taba malam Usuman yana kwantara masa da hankali yace kuma haka Allah yak’addara koda ma can ba matan su ne ba, dan haka tun lokaci bai jemana ba muje mugayama iyayin yaran.

Da k’ar malam Usuman yayadda zaije .

Malam Usuman yace to mufar wajan ita mahaifiyar su dan ko ita bata san mi ake ciki ba.

Yace “to muje.”

Koda sukaje gidan ana ta aiki ‘yan uwa na kusa dana nesa ma duk sunzo.

Kai tsaye d’akin gwaggo Maryam sukaje suka sameta ita da jikukin ta su Mufida, gaida Malam Usuman da Malam Garba sukayi sannan su Mufida suka fita daga d’akin.

Sai da Malam Usuman ya gyara zama yafad’i mata duk abunda ke faruwa.

Tace wallahi Malam Usuman basu isa su samuyi kunyaba nan take tad’au zafi tafara fad’a kun San mai hukuri bai iya fad’a ba sai da ta tsaya , san malam Garba da malam Usuman suka fara kwantara mata da hankali suna bata baki tayi hakuri kada suyi jayayya da ikon Allah .

Ko ita dak’ar suka shawu kanta Amma badan ta hakuraba ita bak’in cikin ta ma wadda Mansur zai aura d’iya k’anwar mamar su Halima ce wato margayiya.

Suna cikin tattaunawa yayar su Sa’adatu ta shigo d’akin ganin su Malam Usuman da Malam Garba yasa tasu ta koma amma sai gwaggo Halima tace “kidawo kiji abunda k’annen ki suka samu.”

Dawo wa tayi tace “gwaggo misuka yi hala?.

Nan malam Garba yafad’a mata abunda kefaruwa .

Aikowa irin yadda tanuna tama fisu shiga tashin hankali tace wallahi baba basu isaba, su cimana mutun ce sujewo mana abin abad’a ba .

Nan malam Usuman da Malam Garba sukayi tabata hakuri tace Baba kasan wadda Mansur zai aura d’iyar mama Safeya ce k’anwar mamar mu Kuma wada Aliyu zai aura d’iyar muk’uciya taci , nan tasan yamusu wana kuka maiban tausai ,sun wahala kafin tasauko.

Haka sukayi tabata hakuri har tace musu ta hakura.

Nan suka tafi gidan iyayin yaran suka fad’a musu dayake duk kan su dattawa ne suka ce Allah ne bai rubutu matan su ba ne .

Haka sukadawo suka fad’a ma gwaggo Maryam tace “to Allah kasa haka shine alhairi”.

Haka akayi bikin Abbas jikin su duk asanyaye dan su Mansur da Aliyu ko wayar su ba’asamu .

Tunda ga wan’na lokaci sukashiga sawar boye da ita ita bata nemesu ba suma basu nemeta .

Sukuma su Hajiya Safa ba k’aramin dad’i sukajiba, dan haka suka koma wurin malamman su suka yimusu godiya sanan kuma suka ce sun aiyimusu aikin wannda indai mace ce bazasu iya d’aga ido sukalleta ba koda a ce jinin su ce.

Haka aka tabbatar musu da Aki ayi angama.

Tundaga lokaci su Hajiya Safa suka mallake mazajin su sai yadda suka ce haka zasuyi ko suna su ko basasu.

Ko wuri gwaggo Maryam ma sun dai na zuwa iyakara su da ita suyi mata aike .

Abun nabasu mamaki har yadawo Basu tsoro ita da yayar su Sa’adatu .

Dan watarana tanajin ancewa ga Sulaman can d’an ta yazo gidan su matar shi Banta Amma ita rabun data ganshi har ta manta.

Dan shi Hajiya Sa’a tasauku daga fushin datakeyi dasu.

Suka tashi neman taimako makarkata islmiya haka ma ta zauri sadaka suka sanyi ai musu safkar k’ur ‘ani, haka suka dage wajan neman taimako ita da gwaggo Maryam.

Muje zuwa

Commet
Nd
Shere
1/23/20, 11:48 AM – +234 706 211 8047: 💦💦💦💦💦💦💦
💦💦💦💦
💦💦

 *KAWAR* *'YATA* *CE* 

®�
GASKIYA WRITERS ASSOCIATION�
{ Gaskiya É—aya ce daga Æ™inta sai É“ata, burinmu mu faÉ—akar da al’umma domin ribantar duniya da kuma lahira. }

     🎐 ```G•W•A```🎐

GASKIYA DOKIN ƘARFE•🏇🏼

Story & written
By
Sumy

BISMILLAHI RAMANIR RAHIM

     Page1�2�

Haka, suka cigaba da neman tema ku, ita da gwaggo Maryam, har Malam Usuman yasa hannu dan yace”, wannan abu baza’a k’yaleba a zoba musu ido ba sai yadda sukayi”.

Gwaggo Maryam abu duk yadame ta, ta rame har ciyo sai da takwan ta dan ma Hajiya Sa’a koda yaushe tana leko ta, ita da yaran ta.

Dan ita gwaggo Maryam gani take ace yara bakwai duk, ba mai leko ta, data tunu haka sai ciyon ta yatashi, Hajiya “,sa’a tayi tayi mata magana ta tarage sa tuneni arain ta amma taki.

Tace “,Sa’adatu bazan iyaba ina dai rukon Allah sauki, kiduba kiga fah jiya zanje barka Ina fita nakawo gidan su Binta naga Sulaman yakawo yaranshi gidan kuma yagan ni amma sai yayi kamar bai sanni ba, tana mai fashewa da kuka.

Itama Sa’adatu abun yab’ata mata rai Amma tadake tana bata hakuri tace komai lokacene da shi tayi taba ta hakuri har ta d’an sauka.

Kiran Baban su Mufida tayi “,taneman ya bar Mufida da Khadija suzo wanjan gwaggo, dan kar abar ta bakowa kuma taga kamar ciyonta,, nasu tashi”.

Yace ,”bakumai yace “,takirasu tagaya musu dan baya gida , yakar dacewa , Allah ya bata lafiya sai nazo anjima”. Tace “,to”

Bayan su Mufida sunzo shima Baban su yazo tabishi suka koma gida.

Shigar su keda wuya tafad’a jikin shi tana kuka, mai cinrai.

Bai hanata ba sai datayi mai isar ta sannan yafara lallashin ta yanuna mata tace ,”gaba da hukuri komai mai wucewa ne, da k’ar yasamu tayi shuru, nan take itama zazzab’i yarufe ta, sai da tasha magani takwan ta, ya gyara Mata kwanciya sannan shima ya kwanta.

Haka, rayuwa taci gaba da tafiya.

Haka skacigaba daneman tai mako basusa gajiya ba.

Suma su Hajiya Safa ,”haka suka cigaba da kaima malamman su kud’i aiyi musu aiki lokaci lokaci.

Ance dai komai da lokacin shi duk abunda kasa Allah gaba zaka dace komai tsawun lokaci, mai hakuri natari da riba.

Komai kakeyi, arayuwa kasa naci da hakuri, dan shi _ko malamin arbiya yace “, duk , wanda yanacema bukun kufa wata rana za’a b’ud’e masa, koda kara tune kanace natabbatar, koda _k’wak’walwa_ka, bata d’auka wata rana zata d’auka, dan haka ko rok’un Allah ne ,kana ce kada kasa gajiya .

Aikowa ranar gwaggo Maryam tana zaune ita da Mufida suna fira, sallama taji anayi ,sun d’auka ma Ammar ne, gwaggo Maryam tace ,”bazaka shigo ba?”.

Wanda taga yashigo yasata mikewa tsaye bata kara Ida mikewaba biyu suka, yashigo

Kallon, kallon, suka farayi tsakanin su, kowanisu yara sa bak’in magana, hamdale tafariyi ma Allah da kirari ,kana tayi k’arfan halin tace wa “,miya kawo ku gidana ?”.

Bawanda yasamu bak’in magana, tsawa ,tadaka musu,tace” ,Meya kawoku gida na?” kufitar min daga gida, ku akwai wanda yaginamin shi, acikin ko?”.

Konan bawanda yayi magana, gwaiwowi su ,”saka fara kaiwa kasa suna neman gafarar ta, da yafiyar ta”.

Amma tayi kamar bata tab’a sanan inda suka fitoba .

Tace ,”kubarmin gidana inba haka ba zan fad’i mumunar kalma akan ku, abunda ban tab’ayi akanku ba to yanzo, zanyi “.

Bashiri suka tashi suna masu fitar da hawaye, dan su basu tab’a gani tayi fushe ba, balema irin haka.

Jikin su a sanyaye haka suka fito a gidan, asuron gida suka tsaya, suka yanke shawara suje gidan Malam Usuman.

Aliyu yayi k’arfin halin, cewa “mukira sauran sai muje tare kumai nene ayi agabansu.

Haka kowa, sukayi sukara su, bajimawa suma suka k’arasu.

Bayan sun k’arasu, suka wuce gidan Malam Usuman.

Fitarasu keda wuya ciyon gwaggoj, Maryam yatashi, aikowa tarin da Mufida tajine ,da sauri tak’arasu wajan ta.

Waya, tad’au ka ,takira Mamar ta, tagayama ta, abunda kefaruwa, aibata k’arasa ba Hajiya Sa’a taci gatan zuwa.

Koda Hajiya Sa’a ta karasu, gwaggo Maryam tayi nisa kamar ma bazatayi rai ba, yadda Hajiya Sa’a ,taga gwaggo Maryam batasan lokacin da kuka yakufuce mata ba.

Jinta na karkarwa takira mijin ta, tashe damasa abunda kefaruwa,

Yace ,”gashinan zuwa” bai tsaya jin mizata ceba yayanke wayar.

Da sauri yafigo muta yazo, baicemusu komai ba yad’auku ta yakai mota suma suka bi yonshi yasa ta mota bai tsaya da ita ko inaba sai wata babbar hospital dake kusa da unguwar su.

Dauri nurses suka zo da gadun da ak d’ura Mara lafiya aka d’ura ta suka wuce emergency da ita aka fara bata taimako cikin ikon Allah numfashin ta yadawo dai dai.

Hajiya Sa’a in ba ,”anbatun Allah ba ,ba abunda takeyi har sada taga Doctor yafito da sauri takarasu wajan Doctor dayake yasan ta yace ,”Doctor kwantar da hankalinki komai yadawo dai dai yanzo tasamu bacci fatarmu Allah yakiyaye gaba .

Da ,”Ameen ta amsa tanamai ajiyar zuciya ita da mijin ta Alhaji Umar.

Sai da yaga komai ya lafa yace ,”musu shi zaije yadawo, godiya tamishi kana ya wuce.

Suna kawowa k’ufar gidan Malam Usuman Kai tsaye suka wuce, da sallama suka k’arasa ciki falon sa,suka sameshi yana kallon labaru da sauri yamai da hankalinsa inda ake sallam.

Da kallo yabisu har suka Ida shigawa, bai cemusu komaiba.

Gasheshi ,”suka fara yi, bai cemusu komaiba.

Sai can,”yace yanzo damikoka zo?”.

“,Hak’uri suka fara bashi akan abunda sukayi mishi “.

Yace ,”nibakuyimin komai ba, wad’anda kukawa, su zakuba hakuri bani ba.

Amma ,”wallah ni kumban mamaki, wai da hankalin ku, da llimiku, aci kunzab’e matan ku, sama da iyayinku, Kuna sun ku gama da duniyan lafiya kowa,?”.

Fad’a da nasiha yayi musu sosai, kana yad’ura, dacewa ,kukara rik’i ibadar ku sakaci da ibada nasa shed’annu suyi galaba da mutum”.

Hanyoyi yayi tad’urasu akai, kana yace ,” yanzo kutashi kuje kuneme gafar mahaiyar ku”.

Suka ce “,daga cin muka fito wallahi ko saurarin muma taki”.

Yace “,nasan za’ayi haka ,wallahi tayi kukan, dare, tayi narana, har tausai takebani, shiyasa bako da yaushe nake zuwa ba.

Sa’adatu ce ke zuwa kuwani lokaci saboda yanzo bawata cikarkar lafiya ne da ita ba”.

Amma “,yanzo kutashi muje can wajanta”.

Suka ce “,to”.

Tashi sukayi suka shaga mota, har Malam Usuman, Basu tsaya ko inaba sai k’ufar gidan.

Malam Usuman yafara shiga da sallamar sa sannan Suma suka bibayanshi.

Mufida ta ,amsa musu, dan lokacin tadawo dan daukar musu, abunda zasu affani.

Gaida Malam Usuman tayi, yakarba, “yace Ina Maryam take?”.

Tace “,batada lafiya yanzo, haka muna asbiti ankwantashe ta”.
Yace
“,Yaushe abun yasame ta?”.

“,Tace yanzo”.

Aliyu “,yace bayan fitar mu?”.

Ta”,eh”.

Nan take hankalinsu ya Ida tashi, a tare suka tambayar ta ,”wace hospital?”.

Fad’i musu tayi suka ce “tatasu sutafi”.

Dasauri tahad’a kayan ta tabisu suka tafi.

Koda su k’arasa cikin d’akin, gwaggo Maryam bacci takeyi, ita ko Hajiya Sa’a tana sallah.

Wuri suka Samu suka zauna suna masu nadama da bikin cikin abunda sukayi.

Hajiya Sa’a tana gama sallah Malam Usuman yace ,”Ashe ciyon Maryam tashi yayi?”.

Tace “,eh” Baba amma yanzo, da sauk”.

Yace “,Allah Kara sauki”

Take “, ameen”.

Sarai tagan su amma tayi kamar bata gansu ba.

Da day daya, suka fara gasheta ,amsamu su tayi kamar, bawani abunda ke faruwa.

Aliyu Yace “,yaya dan Allah kigafarce mu wallahi sharin shiad’a ne da sun zucya” .

Batace musu komai ba har suka gama abunda suke fad’a.

Gwaggo Maryam ita abbata farka ba sai daf da magarib lokacin Hajiya Sa’a tana sallah .

Ahankali, take bud’e ido, har Saida tagama bud’e idonta , abunda yafaru ta tunu tace,” tasan mafarkin da tasabayine basuna suka zogare taba.” tana Mai zubar da hawaye.

Bayan takammala sallah, alamun farkawar ta taji, dasauri ta k’arasu, tana ,”cewa gwaggo kin farka?”.

Hawayin dataga na zuba aidon ta yasata cewa “,gwaggo ko akwai wurin da ke miki ciyo?”.

Batayi magana ba, ita ko Hajiya Sa’a har zataje takira doctor sai taji anrik’e hannu.
Tace “,a’a Sa’adatu ba ,abunda kemin ciyo, nadai yi mafarkin da na saba”.

Tace “a’a gwaggo yanzo ba mafarkin bane basujima da bari wajan nanba Kuma nasan yanzo zasuzo”.

Tace “,to Allah kasa”.
Tace “,Ameen”

Bajimawa ko, sai gasu sun zo ,zaune suka sameta rik’e da kufi ahannuta tanashan tea.

D’ay, bayan d’aya, suka fara shugowa har suka shigo gaba d’aya, da ido take kallon su .

Gaisheta suka farayi Amma ba ,Wanda ttakarbma ma

Haka suka rinka jinyar ta kullum suna can Amma bawanda ta tab’a yima magana.

Kwananta uku akasela meta, dan taji sauki sosai, haka suka dawo gida kullum suna saman hanyar gidan, kuma har yanzo, inba sallama ba ba abunda ke, had’asu.

Sunyi Bata hakur har sugaji amma ko kallo basu samuba da ita har yayar su.

Dan haka suka yanke shawara suje sugayama Malam Usuman.

Bayan “,sungaya masa yace suje gashinan zowa”.

Sai da yabiya gidan Malam Garba yafad’a masa abunda kefaruwa Malam Garba yace “,to muje”.

Haka suka Isa gidan bayan sunyi sallam, tabasu izinin shiga, suka shigo, bayan sungama yima ta yajiki, suka d’aura da cewa ,”kuma gami da yaran nan ne, dan Allah kiyi hakuri, sunyi kuskure kuma sungane kuskurinsu, duk, da munsan bayin kansu bane da haka dan Allah kiyi hakuri.

Dak’ir sukasamu tayi hakuri Amma kushi da sharad’i Malam Garba yace “,to akirasu”.

Bayan ankirasu Malam Usuman yace “, munajinki”.

Gwaggo Maryam tace “,na d’aya shine suje suneme yafiyar yayar su Sa’adatu.”

Tace “,na biyu kowanen su Ina sun yasake aure ma’ana inasun sukara mata”.

Tace “,kuma babu dole “.

Da ,”sauri suka cemata sun amince”.

Nan su Malam Usuman “,suka fara fad’i Alhmdllh”.

Nan Malam Garba yayi musu nasiha mai ratsa jiki, yasa musu albarka, yace ,”sutashi suje gidan yayar su”.

Suka ce “,to”.

Haka suka tashi sukaje gidan inbanda ma mijinta sanannena agari da baza su gane gidan ba.

Suna kowowa mufida da Ammar zasu fita, da sauri takara suwajan su.

Gashesu tafara yi kana tayi musu iso zuwa falon bak’i.

Sai da takawo musu abunsha sannan taje, tafadama Momy su.

Koda Hajiya Sa’a ta k’arasa falon, tsaye tayi nabin su da kallo suma haka.

Suleman yace ,”Yaya dan Allah, ki karasu kizauna please”.

Ahankali tataku har takawo tazauna saman kujera.

Sun d’au lokacin bawanda ya iya cewa komai.

Sai can Munsur yayi k’arfin halin, fara magan,

Yace ,”dan Allah kiyi hakuri munsan muyi ba dai dai ba duk ni nasan bayin kammu neba, wallahi yaya kaba d’aya mantawa muka yi damuna da wasu ‘yan uwa dan Allah yaya kugafar cemu”.

Nan suma suka fara bata hakuri.

Tace bakumai,” Allah yaya femuna”.

Nan sukacigaba da fira har suke gayamata abunda gwaggo Maryam tace musu.

Tace “,amma gwaggo tayimin dai dai, saura kuma naji shuru”.

Suka ce ,”a’a wallahi zamu samu matan nan bada jimawa ba”.

Sai Alhaji mansu yayi gyaran muraya yace ni gaskiya Ina da wadda nake so duk da nikaina inaganin abun ba maiyuwa ba ne dan nayi taciri abun araina amma kamar lokacin nakesa shi ,bansa yadda zamisilta muku yadda nakeson yarinya ba “.

Yakuma cewa “,kunsa kuwace ce?”.

“Suka ce a’a”.

Sai da ya d’au lokaci, yana mai duk’ar da kanshi a kasa, saboda abun yayi mishi nauyi fad’a a aharshe.

Yace ,” Fateem K’awar ‘yata Zainab”.

Nura da Abbas tari suka had’a baki wajan kiran “,mika ce?”.

Yace ,”abunda kukaji nafad’a”.

Hajiya Sa’a dataga zasu kawo mata wata hujjar da bata yadda da ita ba, tace ,”kuda kata”.

Gabadaya, sukayi shuru, tace ,”Mansur kana son ta ko?”.

Yace “Inson ta Hajiya”.

Tace ,”ita yarinya nason ka?”
Yace ,”ita yarinya batama san Inson taba”.

Tace “to kaje kasameta kagaya mata, nikuma daganan na d’ura inda katsaye”.

Yace ,”Hajiya ta ina zan fara?”.

Tace “,kota ina za kafara kafini sani, kuma kwana biyu na baka kazo kagayamin mi ake ciki”.

Ta “,kuma cewa kuma akowani lokaci anajiran tako”.

Suka “ce insha Allah.”

Sai da suka ci hararsu ,sannan, sukayi mata sallam suka tafi.

Muje zuwa

Commet
Nd
Share
1/23/20, 11:48 AM – +234 706 211 8047: 💦💦💦💦💦💦💦
💦💦💦💦
💦💦

KAWAR’YATA CE

®�
GASKIYA WRITERS ASSOCIATION�
{ Gaskiya d’aya ce daga k’inta Sai b’ata, burinmu mu fad’akar da al’umma domin ribantar duniya da lahira.}

    🎐G. W. A🎐

GASKIYA DOKIN K’ARFE🏇

Story & writing
By
Sumy

Dedicated to my innaro🥰

BISMILLAHI RAHAMANIR RAHIM

Page 1�3�

Bayan kwana biyu sai alhaji mansur yaje ya gayama hajiya sa’a, “Yace ya fad’a mata Amma Dana fad’amata sai Naga duk ta rikice, sai hajiya sa’a tace “Badai ka fad’amata ba”? Yace “eh hajiya na fad’amata”.

Tace “To kaban address din gidan su” yabata address d’in gidan su, tace “Kataya mu da addu’a Allah yasa a dace. “Yace ai hajiya addu’a kullum cikin yinta muke, Dan haka Ni zan wuce duk abinda ake ciki muyi waya,”Tace to Allah ya kiyaye Amma kowane lokaci zan iya shigowa gidan naku “, yace “To hajiya yaya” ya mata sallama yatafi.

Bayan hajiya sa’a taje gidan su fatima dak’yar suka amince da maganar bayan fafatawar da akayi dasu.

A b’angaren su Hajiya Shafa suna ik’irarin cewa ba macen da ita Isa ta shigo gidan su Bale har tayi kishi dasu.

Cikin ikon Allah aka d’aura auren Alhaji mansur da Fatima aikuwa jikin su Hajiya Shafa yayi sanyi, Amma duk da haka basu yarda makaman ya’kin suba.

Cigaban labari

Tunda Daddy yayi tafiya bai sake Kiran mommy ba, har Saida yayi kwana biyu saboda ayyuka dasuka rik’esa bai samu kiranta ba lokacin daya kirata bai mayi tunanin zata d’auka ba, can sai ta d’auka “Yace fushi akeyi ne Dani”? Tace “Ni bana fushi dakai yace “Allah yasa, dafatar Kuna lafiya”? Tace “Lafiya k’alau muke” yace “Ina Yara da k’anwar ki na Kira wayar ta a kashe”?

Tace “Ai kafini sanin inda take” “Yace dana San inda take ai bazan tambaye ki ba” tace “ka tambayi yayar ka” yace “Hajiya sa’a”? Tace “eh ita” “Yace ki gaidaman da Yara na” Tace “zasu ji” sukayi sallama ya kashe waya.

Ya Kira Hajiya sa’a bayan sungama gaisawa yace “Fatima na wurin ki?”, Tace “eh tana wurina ko da wani abun ne?” Yace “A’ah dama Kira nayi naji ko tana lafiya”, Tace lafiyar ta k’alau” har zata katse wayar yayi sauri yace “Yaya!” “Tace Koda wani abun ne?” yace “eh, Bata kusa ne a Bata wayar?” Tace “wace?” Yace “Fatima” Tace “Bata kusa” har zata sake katse wayar yace “Yaya Dan Allah idan nayi wani laifi ne a yafemani ayi hak’uri” Tace “inaga kamanta gwagwar mayar da muka shiga kafin iyayen ta subamu auren ta” yace “wllahi A’a Yaya ban Manta ba” Tace A’a kamanta Mana, Dan inda baka Manta ba da bazaka barta a matsayin ‘yar aiki ba, to wallahi bari kaji bazan d’auka ba idan har ‘yar aiki ce bakuda ka nemota, Kuma kajawa matar ka kunne itada yaranta ba ‘yar aiki bace aka kawo masu “.

Yace “Wallahi Yaya banma San da cewa ana sata aiki ba, Amma kiyi hak’uri” ta k’ara d’aukar zafi tace “Inako zaka sani tunda baka kula da ita, Tace Kuma idan Kai baka d’au mataki ba wallahi nida kaina zan d’auka” tayi tamasa fad’a, shidai hak’uri kawai yake Bata daga k’arshe dai tace ta hak’ura ya bari ta turomasa number Fatima.

Bayan sungama waya takira Hajiya Ummu Tace “Ga mijin Fatima Nan zai Kira ta nuna mata yadda zatayi wayar dashi, danso nake tun a waya tarikitar dashi ya kasa hak’ura har sai ya kirani yace a mayar Masa da matar sa”.

Hajiya Ummu Tace “Baki da matsala indai wannan ne” ta mata sallama, sannan ta tashi taje d’akin da Fatima take shigarta keda wuya wayar Fatima tafara ruri, ta tsaya a bakin k’ofa tana kallon Fatima Tace mata ” Ba wayar ki bace take ringing?” Fatima Tace “eh itace” Hajiya Ummu Tace “kid’au ka Mana koba mijinki bane yake Kira?” Tace “eh shine” Tace “ki d’auka Mana Kuma kisan yadda Zaki magana dashi ba kamar yadda zakiyi da sauran mutane ba, ki lank’wasa muryar ki ki karai rayata” koda Hajiya Ummu takai k’arshen maganar ta har Kiran ya katse wani ya saki shigowa.

Fatima ta d’auka tace “Assalamu Alaikum” tana Mai jin kunyar hajiya Ummu, ajiyar zuciya yafara yi Mai k’arfi kamin ya amsa sallamar da “Wa’alaikumus Salam” Tace “Daddy Ina wuni?” Yace “Lafiya k’alau kwana biyu nabar jinki nayi missing d’inki sosai, Baki ko nema na” Tace “Hmmmm Daddy ya aiki?” Yace aiki Alhamdullillah Yaya ta d’auke Mani ke ko? Amma idan nadawo Zaki koma ko?” Tace “umm” hajiya Ummu ta Harare ta ta mata alama da ba haka zata ce ba Tace “eh zan dawo” yace “yauwa” haka yayi tajan ta da fira tana nok’ewa duk da hajiya Ummu na hararar ta, Amma ta kasa sakin jiki dashi sosai.

Yace “Fatima Baki ma kewata ba ko?” Tace “A’a Daddy nayi kewar ka” yace “Hmmm kozaki zo kitayani aiki idan nagama muzo tare?” Dayake wayar a handsfree take sai Hajiya Ummu ta harereta, Tace “duk yadda kace Daddy” yace ohk “inaso kizo idan na kammala aikin da nake sai mu dawo tare” tace “to Daddy” daganan sukayi sallama da ita.

Bayan sun kammala wayar hajiya Ummu Tace “yanzu Fatima haka zakije kina wannan kunyar, koma miye gara ki ajeshi tun anan tunda Allah ya Riga da ya k’addara mijinki ne ba yadda zakiyi, Kuma aljannar kice Zaki nema idan kin tsaya Dan kanki idan ma Baki nema ba Dan kanki kowa tashi tafishe shi, Dan ko mamar ki aljannar ta take nema.

Dan Haka kema ki tsaya kinemi taki, Tace “insha Allah zan kiyaye nagode” Tace “Allah yasa danma Kar watarana naje gidan ki Naga sab’anin abunda nakoya maki Allah zamu sab’a dake” Tace insha Allah hajiya bazamu sab’a ba”.

A b’angaren Alhaji kuwa bayn sun gama waya da Fatima ya Kira Hajiya sa’a, yace “Yaya dama k’anwar ki nakeso ki aramani tazo ta tayani aiki kamin na kammala saimu dawo tare” Tace “bazan bayar ba salon kamayar da ita ‘yar aiki” yace “haba Yaya Wallahi bazan mayar da ita ‘yar aiki ba, karmuyi haka dake pls” Tace “bafa zan bayar ba Dan haka sai anjima” tafad’i haka tana Mai niyyar katse kiran.

“Yace Dan girman Allah Yaya kada ki kashe ki bani ita sati biyu kacal ne zamuyi kamin na k’arasa mu dawo” Tace “Sai nayi shawara, idan nyi shawara zan Kira ka” ta datse kiran.

Bayn sun gama waya da daddy hajiya sa’a ta Kira hajiya Ummu tafad’a mata yadda sukayi da daddy, Tace tanason a k’ara shirya Fatima saboda tasan ko gobe Tace ma Daddy ta yarda biza kawai zaisa a mata ta biyoshi.

Kuma Bata shirya bashi ita ba yanzu sai komai ya kammala, Tace “kinsan cikin manya matane zata kishi banaso a samu matsala ko kad’an” Hajiya Ummu Tace” Baki da matsala indai akan wannan ne, Sukayi sallama.

Bayan kwana biyu daddy ya shama hajiya sa’a Kai Dan Allah ta yarda ta turomasa Fatima dak’yar ta yarda, murna a wurin sa ba’a cewa komai Yana ta murnar Fatima zataje wurin sa.

Bata yarda zata bashi itaba Saida ta gindaya Mai sharad’i “idn har suka dawo bataga Fatima ta canza ba shida ita har abada,” “yace ya yarda bama za’a samu matsala ba” Tace “zuwa ranar Friday za’a mata biza” yace “Allah ya kaimu” Tace “Ameen” sukayi sallama.

Tundaga lokacin Nan kullum sai ya Kira Fatima, mafi akasarin wayar su a gaban hajiya Ummu takeyi tana koya mata yadda zata Masa magana aikuwa ya k’ara rud’ewa yaga duk Jumu’a ta dad’e Bata zoba.

Burinshi kawai Jumu’a tazo ranar da zaiga Fatima shi ko zai samu natsuwa, haka akayi ta shirya Fatima kamin ranar Friday Koda ranar Friday tayi idan kaga fatima bazaka gane taba saboda yadda Tasha gyara.

Fatan ta sai walkiya takeyi tayi sulb’i ga wani fresh din datayi ga wani sihirtaccen kamshi da takeyi…………

Muje zuwa

Comment
And
Share
1/23/20, 11:48 AM – +234 706 211 8047: 💦💦💦💦💦💦💦
💦💦💦💦
💦💦

     *KAWAR 'YATA CE*

®�
GASKIYA WRITERS ASSOCIATION�
{ Gaskiya d’aya ce daga k’inta sai b’ata burinmu mu fad’akar da al’umma domin ribantar duniya da lahira.}

  🎐G. W. A🎐

GASKIYA DOKIN K’ARFE.🏇

Story & writing
By
Sumy

BISMILLAHI RAHAMANIR RAHIM

Page1�4�

A b’angaren su Hajiya Shafa sun sake shirya meeting d’in, kamar yada suka Saba had’uwa su bakwai yau ma sun Had’u, bayan gabatar da gaishe -gaishe tsakanin su mommy Tace.”A gaskiya naga abun nan yak’ici yak’i cinyewa, kuma gashi Hajiya Sa’a ta d’auke yarinyar nan bansan a inda takai taba nayi bincike iya bincike bangane inda takai taba, kuma an tabbatar man da fatima Bata gidan, Hajiya Sa’a dan Haka nake so aman bincike akan ina ne Hajiya Sa’a ta kai Fatima”.

Hajiya Shafa tace “yaushe tazo ta d’auke ta?”. Mommy Tace “wllhy bayan tafiyar Alhaji tazo ta d’auke ta”. suka ce “ai baki gayamana ba tun lokacin da sai mu San abunyi”. Tace “ai nazo nafad’a sai naji ance auren Alhaji sulaiman za’ayi shiyasa hankali na ya d’auku ban fad’aba”.

Nan suka ce “bari harda shi zamu sa a bincika a inda yarinyar take”.

Tace hakan ma yayi dan dai ni gaskiya banaso yarinyar ta zauna a gidan, kwata- kwata bana so ace wannan yarinyar itace kishiya ta koda ta zauna a gidan nafiso ta zauna a matsayin’yar aiki na, amma ba’a matsayin kishiya ba ko bai sake ta ba sunji sungani zata iya zama to a maisar Mani ita a matsayin ‘yar aiki gidana dan banaso ace kishiyata ce.

Hajiya binta Tace “Nima dai gaskiya a san abinyi dan bama son ace tashigo gidan”.

suka ce dukkan mu yakama ta mu d’au mataki dan tunda biyu suka fara, suma sauran a can sukayi.

Hajiya Shafa tace “hakan ma suke nufi dan da Hajiya Sa’a baza ta cema Alhaji Aliyu ba saura shi ina tunanin gaba d’aya take son su kara, kuma wallahi Bata isa ba Dan bazamu k’yaleta ta ba Muna kallon ta, Dole mu d’au mataki akanta”.

Haka dai suka k’arasa meeting d’in su, sun yanke shawarar sake ziyarar malaman su kafin jibi Dan ita Hajiya Hadiza gaba d’aya ta rud’e tafiso a mayar da yarinyar gidan ta ta cigaba da mata bauta, Dan bataso yarinyar ta zauna a gidan Hajiya Sa’a a haka dai suka watse daga gidan.

Mommy na komawa gida ta iske su Zainab a falo suka mata sannu da zuwa, ta amsa sannan ta d’aura dacewa.

“Angama aikin gida Hala?”.

Suka ce eh Khalsum tace “Mommy Wai yaushe Daddy zai dawo ne?”.

Tace “sai Nan da sati biyu yace zai dawo”.Tace “Allah Mommy nidai ki kaini wurin daddy” Tace “naji zan kaiki” Tace “to nidai Mommy ki Kira Mani shi pls”.
Tayi maganar kamar wanda take shirin yi kuka.

Tace “bazan kiraba ki bari idan ya kira zan Baki”.

Da k’yar’ir tasamu Khulsum ta k’yaleta dan a gajiye take, burinta kawai tashiga d’akin ta kwanta.

Har zata shiga bedroom d’inta tace “Zainab kimana girki ko kad’an ne”.

Zainab ce ta bata amsa da cewa,”Toh Mummy”.

Mumy Kallonta ta maida ga Nabila dake kwance tace “Ke meza kiyi?”.

D’agowa tayi ta kalleta sannan tace. Hmmmmmm Mummy kinsan yau a gajiye na dawo daga school, bazan iyayin komai ba”.

Mummy tace “ke daman Nabila ba aiki kike soba”.

Tana gama fad’in haka ta wucewarta d’aki.

Zainab ce ta tashi ta shiga kitchen ,inda ita kuma Nabila takoma d’ikin su ta kwanta.

Bayan ta kammala aikin ta tayi wanka ta gabatar da sallah,tunanin Fateema tashiga yi kwana biyu bata jita ba, tunda Mummy Mufida tazo suka tafi tare bata saki jin taba.

Tashi tayi taje d’akin Mumy bayan tayi mata knocking ta bata damar ta shigo bayan tashigo tace. “Mummy wai ina Fateema, har yanzu tana gidan Mummy Mufida?”.

Mummy ce ta bata amsar da cewa. “Ban saniba ai ina kula dake kwana biyu duk kinbi kin shiga tunanin k’anwar ubaki batan ko?”.

Tace ” a’a Mummy naga har yanzo basu dawo ba shine na tambaya ko lafiya?”.

Kina iya kiran Daddy ki tambayeshi. A nan tsaye Mummy ta fita ta barta.

D’ak’in su ta koma wayar ta d’auka takira Daddy, bayan sun gama gaisawa, take ce masa.

“Daddy kwana biyu Banga Anty Fatima ba, kuka san wurin da take?”.

Yace “eh tana can gidan Hajiya Sa’a”.

Daga d’ayan b’angaran aka bata amsar.

tace “to” har zai katse wayar, tace Daddy ko kanada number ta?”.

Yace “eh bari na turumiki”.

Tace “tau Daddy nagode”.

Bayan ya turomata number Kiran Fateema tayi ringing wayar ta fara yi bai wuce uku ba ta d’auka, ta kara a kunnen ta, azoton ta ma t d’auka Daddy ne.

Sallamr dataji ne yasa ta gane mai maganar tace. “My sweet heart kece?”.

Tace. Ba wani my sweet heart, yanzo Teema har Zaki iya kwana biyu ba tare da kinji niba hmm yanzo nasan kin daina sona”.

Fateema tace” a’a wallahi kimin uzuri yanzo abubuwa sumin yawa kuma ke kanki kinsani”.

Zainab tace bawani,yanzu ina kike ko kina gidan Hajiyar Mufida?”.

Tace “a’a bana can”.

Tace “to kina Ina ne?” Tace wallahi bansan sunan unguwarba, dan bantaba zuwan taba.
Zainab “tace yanzo baki gidan Hajiya kenan?”.

Tace “eh” ba can na koma wani gida ne takawoni”.

Tace “wani gidan kenan?”.

Tace. ” Kedai bari Zainab,ganinna banajin dad’i zaman gidan”.

tace “to niki gayamin gidan mana”.

Tace “ni bansan yadda zance miki ba”.

Tace “tau na gode sai Kiyi ta b’oyewa wataran ai zan sani”.

Nan suga cigaba da hira daga baya Zainab tama sallama “.

Da yamma duk suna falo zaune suna fira gaba d’ayansu, sai Zainab tace “Mummy muyi waya Daddy harma yabani number Fateema,tace kunyi waya da ita ne?”.

tace “eh Mummy munyi”.

Mummy tace ta gayamiki inda take?.

A’a kawai dai tacemin tana gidan wata mata acan Hajiyar Mufida takai ta”.

Mummy tace “wace matar kenan?”.

tace bansaniba dan nima nace ta gayamin amma bata gayamin ba

Mummy tace d’auku wayar ki ki k’ara tambayar ta wace matar ?”.

Waya ta d’auku ta kira Fatima tace “my sweet heart ya dai?”Zainab tace kinga nasake kiranki ko” Fateema tace “eh” sai Zainab tace wai bazaki gayamin gidan da kikeba, gashi inso nakawo miki ziyara”.

Fateema tace “wallahi bansan ba amma bari na tambaya Hajiyar naji”.
tace to”.

Tashi tayi taje d’akin Hajiya Ummu ta tambayeta, sai Hajiya Ummu tace wa
zaki ba address tace Zainab, dayake Hajiya Ummu tasani kuma gamida su, sai tace kibari zan tambaya Hajiya Sa’a duku yadda tace zan gayamiki” , tace “tom ,amma yanzo zaki kirata dan kar takuma kira bansan mi zance mataba kuma inajin kunyar ta”.

Tace to “bari nakirata”.

Mummy nagani Zainab taka tse wayar tace taga miki ne ?” ,Tace a’a Mummy ta katse wayar” Mummy tace, “saki kira in bazata gaya mikiba to bani wayar” Zainab sake kiran Fateema tayi ita koma Fateema tana ganin kira ya sake shigowa tarasa yadda zatayi tad’auka, da bara tafad’ama ta sai tad’au wayar Zainab tace, baki sunne na kawomiki ziyara ne?” Tace, a’a zeey Hajiya sallah take Amma idan ta gama ku message zan turamiki tari da address d’in gidan”.

Tace “to yayi inajira dan idan kinturu da safe zaki ganni”.

Tace yayi agaida su Mummy da Aunty Nabila da Khulsum” ,tace duk zasuji kilama har Khulsum nazo miki da ita tace, dana jidad’i sosai dan nayi missing d’in ta”.

Fateema tace yasu Aysha kuna waya dasu”Zainab tace, eh” muna waya”.

Fateema tace” turumin number su Zainab tace, naki sai akin turumin nima zan turumiki” tace, yayi “.

Bayan sun kammala waya Mummy takale Zainab tace nasan bazata gayamiki Ida aka kaita ba”.

Mummy waya tad’aka takira Hajiya Shafa taga yamata abun da ake ciki Hajiya Shafa tace, ma Mummy tasa Zainab ta rink’a kiran ta har sai tasamu muna gidan da take, dan kinga idan akasamu muna wurin datake sai musan abunyi”.

Mummy tace, “shikenan yanzo nan zan sata gaba sata k’ara kiranta”.

Bayan sun kammala waya Mummy tafito falo tace Zainab Bata turuminki message din ba?”.

Tace Mummy bata turuba amma idan taturu zan gayamiki”.

Tace, “gaskiya kam idan taturu kigayamin nima inasun naje dan bamusan halin da take ciki ba, kuma koba kamai yakama ta Muje musan ida take”.

tace nima shiyasa nakesun taturumin dan nakai mata ziyara”.

A b’angarin Hajiya Ummu Hajiya Sa’a takira taga yamata ta abinda ake ciki Hajiya Sa’a tace a’a kada kuskura agayamata na gayamiki gada a fad’amusu kibarsu dan yanzu bakisan dami zasu zoba, tace wayar ma ta Fateema kab’eta ki kasheta, zan ba mijinta number ki yarink’a kira dataki antaga ki k’arb’a” tace, to Hajiya”.

A can b’angaran Mummy kuwa ajima kad’an tace, “Zainab taturu miki message?” Ta a’a bata taturuba” gaba tasata tace tak’ara kiranta taji, k’iran Fateema tayi taji wayar akashe.

Tace “Mmmy wayar akashe take”.

Mumy tace a kashe, hannun ta na karkarwa tace, baniwaya nak’ira “.

Waya Zainab tamik’a mata kira tayi akacemata akashe take.

Hankalin Mummy inyayi dubu yatashi tace, “tasan wannan ba akin kowa bane bace na Hajiya Sa’a”.

Waya tad’au ka takira Hajiya Shafa taga yamata ta abinda ake ciki, Hajiya Shafa tace k’yalesu ai gobe ku Ina take zamu sani dan zamu fad’i ma malam abinda akeci dan Wallahi inta ci riba wancan karan wannan karen bazata ciba da ita har shi kanshi Alhajin”.

A can b’agarin Daddy duk, yak’agara jumu’a tayi ta zo kodan ya koma gida. .

Suma su Mummy sun k’agara Safeya tayi suje wurin malamin su.

Ita Hajiya Sa’a ta k’agara Safiya tayi taje ta ja musu kunne, kada a kuskura agaya musu inda Fateema take….

Muje zuwa

Comment
Nd
Share
1/23/20, 11:48 AM – +234 706 211 8047: 💦💦💦💦💦💦💦
💦💦💦💦
💦💦

 *KAWAR* *'YATA* *CE* 

®�
GASKIYA WRITERS ASSOCIATION�
{ Gaskiya É—aya ce daga Æ™inta sai É“ata, burinmu mu faÉ—akar da al’umma domin ribantar duniya da kuma lahira. }

     🎐 ```G•W•A```🎐

GASKIYA DOKIN ƘARFE•🏇🏼

Story & written
By
Sumy�

BISMILLAH RAHAMAR RaHIM

   *Page* 1�5�

Tunda safe Hajiya Sa’a ta shirya taje gidan Hajiya Ummu, koda taje a d’akin da Fateema take acan tasamu Hajiya Ummu, tana k’ara gyaran ta.

Bayan sun gama gaisawa sai Hajiya Sa’a “tace Fateema ke kika ba Zainab number ki?”.

Fateema “tace a’a Hajiya bani nabata ba”.

Tace “to sai in shi Mansur d’in yabata?”

Fateema tace, “wallahi bansani ba”.

Sai Hajiya Sa’a tace ma Hajiya Ummu, “kinsan gobe ne zasu wuce.”

Hajiya ummu tace, “ina sane shiyasa nak’ara k’ok’artawa kafin gobe mukammala komai”.

Sai Hajiya Sa’a tace,” yauwa.”sannan ta mayar da kallon ta ga Fateema taci gaba da cewa,” kina bukatar wani Abu? dan kila har gidan ku zanje.”

Fateema tace,” a’a Hajiya, ki dai ce ina gashesu.

Hajiya sa’a tace,” insha Allah zangaya musu”.

Hajiya Sa’a da fitar ta,bata tsaya ko inaba ba sai gidansu Fateema.

Da fara’a Ummu Fateema ta tarb’e ta.

Bayan sun gama gaisawa, Hajiya Sa’a tafad’ama ta tafiyar Fateema gobe.

Mahaifiyar Fatima tayi murmushi, sannan tayi musu fatan alhairi.

Mik’e wa tayi ta d’auko wasu Kaya aleda ta mik’awa Hajiya sa’a tace,”ga sak’o ki Kai wa fatima.

Hajiya sa’a ta amshi kayan, sannan sukayi bankwana ta tashi ta tafi.

Ab’angaren su Mummy tunda safe taje gidan Hajiya Safa,basu b’ata lokaci ba suka kama hanya sukaje wurin malamin su.

Koda sukaje mutane sunyi yawa, sai da suka bari mutane sun rage sannan suka shiga.

Bayan sun kai gaisuwa gareshi sannan suka k’ara kora musu bayani, Hajiya Safa tace, “Malam gamida maganar da kasani ce har yanzu abu yak’i k’arewa.

Malam Yayi murmushi irin na mayaudaran malamai yace,”ku tsaya na duba maku na gani.”

Wani babban faranti yajawo wanda aka zuba yashi aciki.

yatsun hannun sa d’aya, yasa yafara layi _layi, jin kad’an kana yad’ago ya kallesu yace,” gaskiya gamida ita Fateema, akwai wani b’oyayyen wani abu, wanda nakasa ganin miye shi, amma kubari nan da kwana biyu kuda wo, amma gami da wannan auren da kuke tsammani, to baza’ayi shi ba, amma kusa ido kuyi kallo”.

Sukace,” to Malam, dan Allah ak’ara dubamana, dan Yanzu ma haka sun d’auke ta daga gida, kuma Malam, dan Allah ina son acire son da ‘yata Zainab kema Fateema, saboda abun nadamu na.

Malam yace,”bakida matsala.

Wani d’aurin magani yabata, yace kizoba mata ga abinci ko lemu tasha ki tabbatar da tasha shi.

Ta mik’a Hannu ta amshi maganin tace,”to Malam na good.”

Malam Yayi dariya yace,”aiku na waje na ne, kuje kawai zakiga abunda zai faruwa,

Haka suka dawo gida, da dad’i ba dad’i,.

Mummy kai tsaye d’akin su Zainab tace wuce.

Kwance ta same ta Mummy tace,” Zainab yau mi kika girka mana?”.

Zainab tace”, Mummy kindawo?”.

Mummy tace,”Yanzu nadawo, kin gama abinci?”

Zainab tace,”nakusa kammalawa.

Mummy tace,”to bari nak’arasa, dan nasan ke kad’ai ce kikayi aiki banda Nabila”.

Zainab tace,”a’a Mummy,kibari nakusa k’arasawa. kedama kika dawo Yanzu.”

Mummy tace,”ko yanzun nadawo, nagaya miki ni zan k’arasa girkin.dan haka banasun gardama.”

Zainab tace,”to Mummy gani nayi kamar kingaji, amma kiyi hak’uri”.

D’akinta ta tafi ta rage kayan jikin ta tasa marasa nauyi, tafito kai tsaye ta nufi kitchen, ta cikaba da aikin.

kununun aya tahad’a tasanya kayan gyaran shi yayi dad’i sosai, d’akin ta ta koma tad’auko kullin maganin da akabata, tadawo kitchen,kofi tad’auko tazuba kunun ayar sannan tazuba maganin a ciki ta d’an jujjuya Shi sannan ta b’oye sauran da sauri.

Dakin Zainab din ta nufa tace,”Zainab taso kiji.”Zainab Tace,”to mummy.

Tana fad’a Mata ta juya ta koma kitchen d’in.

A kitchen tasame ta tace,” Mummy gani.”

Mummyn ta juyo ta kalleta tana murmushi tace,” Dama kunun Aya ne na had’a naji kamar baiyi dad’i ba,amma kisha kiji dan kinsan ni bancika gane dad’in abunba”.

Mik’o mata kofin tayi tace,”ki sha kiji”.

Karb’a tayi tana maikaiwa abakin ta.

Gabaki d’aya, tashanye Shi, saboda tana tsananin sonshi sosai.

Kofin tamik’a wa Mummy tana cewa,” Mummy k’aramun yayi dad’i sosai”.

Mummy tayi wata irin dariya ta Jin dad’in samun nasara tace,”sarkin kwad’ayin kunun Aya,to bazan k’araba.”

Zainab ta marairaice tace,” Mummy dan Allah ki karaman ko kad’an ne”.

Mummy “tace kije zuwa anjima idan yayi sanyi sai kisha”.

Zainab cikin murnarta to,”to mummy.”

Dak’in su takoma, tunda takama hanyar d’akin su sai ta dunga Jin kamar juwa nad’aukar ta.

Da k’yar takai d’akin su,tana zuwa saman gadon ta ta kwanta,bata jima da kwanciya ba wani bacci mara dad’i yad’auke ta.

Aikuwa Mummy tunda taga Zainab tasha kunun Aya take cikin Jin dad’i dan har Hajiya Safa saida takira tagayama ta, aiko sunji dad’i sosai sukace yanzu sai mujira abunda zai biyo baya.

Zainab tunda ta kwanta ba ita tafarka ba sai yamma,afigice ta mike saboda wani mugun mafarkin da tayi,gaban ta yadinga dukan uku_ uku.

Nabila dake zaune gefen gadon takalle ta tace,” lafiyar ki kuwa?”.

Zainab tace,” lafiya k’alau, mikika gani?”.

Nabila tace,”nagakin wani tashi a har gitse?”.

Zainab ta share zufar data feso Mata tace,”ba komai.”

Tashi tayi tashiga toilet ta watsama jikin ta ruwa tayi alwalla dan tarama sallah la’asar.

Har dare haka takejin jikin ta kamar ba dad’i.

Koda Mummy ta tambaye ta sai tace,” ba komai mummy.”

Mummy bata k’ara cewa komai ba, saboda tasan kafin jikin ta ya warware sai zuwa gobe.

Daddy tun cikin dare yakira Hajiya Sa’a.

ita har tsoro taji data ji kira dai_dai wan’nan lokacin.

Bata ma tsaya duba waya kirata ba, d’auka tayi takara akunnen ta.

Muryarsa da taji ne yasa tace,”Shan wai kaine, lafiya kuwa ka kirani cikin daren nan?”.

Yace Kiyi hak’uri Hajiya,kinsan lokaci ba d’aya ba ne, nace bari nak’ara tuna miki,kinsan karfe tare ne zasu tashi.

“Hajiya Sa’a tace,” ina sane ban man taba, kuma bari kaji idan kadame ni ba inda zataje”Hak’uri yabata yayi mata sallama.

Har zata koma bacci taga hud’u saura dan haka tashi tayi ta d’auro alwalla tafara gabatar da nafiloli har akayi kiran sallah.

Hajiya Ummu da gama sallah asuba taje d’akin Fateema, koda taje saman sallaya tasame ta, tace,”Fateema kitaso muk’arasa kafin Hajiya Sa’a takaraso”.

Fatima tace, “to” tana mai tashi daga saman sallaya.

Hakata cigaba da gyaran ta har Hajiya Sa’a tak’araso, koda tazo har Fateema tayi wanka tayi breakfast tashirya.

Bayan sun gaisa Hajiya Sa’a tace,” tashirya ko, dan saura minti talatin su tashi”.

Hajiya Ummu tace, “komai angama, ke kad’ai muke jira”.

Godiyya Hajiya Sa’a tayi mata, tad’auko kud’i masu yawa taba Hajiya Ummu.

Hajiya ummu ta fara zuba godiya, sannan tayi masu fatan alhairi.

Kiran Fateema tayi, bayan tak’ara fad’a mata wasu abubuwan,sai ta rakasu har wajan motar su, saida taga sun d’aga sannan ta koma cikin gida cike da murnar kyautar da Hajiya Sa’a tayi mata.

Koda suka k’arasa filin jirgi, saura miti biyar jirgin yatashi.

Don mutane har sun farashiga, aikuwa ana kawowa gare ta, gabaki daya jikin ta yafara karkarwa.

Aikuwa sai tafashe da kuka, tana cewa dan Allah ku maida ni wurin Umma na.

Hakuri Hajiya tayi taba ta har suka samu ta shiga jirgin.

Hajiya Sa’a sai da taga tashinsu sannan takira Daddy ta fad’a mashi sun taso.

Muje zuwa

Comment
Nd
Share
1/23/20, 11:48 AM – +234 706 211 8047: 💦💦💦💦💦💦
💦💦💦💦
💦💦

KAWAR ‘YATA CE

®�
GASKIYA WRITERS ASSOCIATION�
{ Gaskiya É—aya ce daga Æ™inta sai É“ata, burinmu mu faÉ—akar da al’umma domin ribantar duniya da kuma lahira. }

     🎐 ```G•W•A```🎐

GASKIYA DOKIN ƘARFE•🏇🏼

Story & written
By
Sumy✍�

BISMILLAHI RAHAMANIR RAHIM

   *Page* 1�6�

Kai tsaye Hajiya Sa’a bata tsaye ko ina ba sai gidan Gwaggo Maryam koda taje a falo tasame ta tana kallon labarun hausa, da sallam tashiga falo.

Amsawa Gwaggo Maryam tayi dauke da murmushi a fuskar ta, tace,” Sa’adatu ce?”

Tace, “Gwaggo nice, daga filin jirgi nake kinsan yau amaryar Munsur zata je wajansa”Gwaggo Maryam tace to yanzo sun tashi ne?”.

“Hajiya Sa’a “tace eh yanzo suka tashi”fatar alhairi Gwaggo Maryam tayi musu, taÆ™ara da cewa, ” Sa’adatu nace wai yabatun amaryar Sulaiman bansa kijin me akeciba”.

Hajiya Sa’a “tace Gwaggo kinsa yanzo komai munkammala, gamida auren nashi lokacin da sukace kawai mukejira” sai Gwaggo Maryam tace” yanzo saura kwana nawa?” Hajiya Sa’a tace sati biyu yarage yanzo har É—aurin aure” gwaggo Maryam tace to itama yarinyar kina kulata kamar yadda kikema Fatima ko?”.

“Hajiya Sa’a tace, gwaggo ai wannan basai na tsaye gyaran taba dan kinga ba kamar Fatima ce ba”.

Gwaggo Maryam tace “kin tabbata ko?”.

Bayan sunyi firar dasukeyi Hajiya Sa’a sallam tayima Gwaggo ta koma gidan ta.

Tunda tashiga jirgi takife kai da gwaiwar ta, take ta kuka, har sauka bata saniba, sai da akafara fita wani saurayi dake kusa da ita yaga alamun batasan sun sauka ba dan haka ya É—an buga seat É—in da take zaune, kana taÉ—ago kanta wanda yake mata masifar ciyo, idonta sunyi jawur kamar garwashi, yace subuhanallah, yace wai dan Allah mike damunki? ” tunda kikashigo cin jirgin nan kike kuka har yanzo”.

Batace dashi komai ba dan ita batamasan miyake cewa ba saboda ko gane batayi sosai saboda kanta dakemata matsanan cin ciyo.

Dayaga alumun bazatayi magana ba jikarta yaÉ—aukar mata “yace muje ko”.

Kamar wata sauna haka tabi bayanshi har suka sauka.

Daddy ko tunda yaga jirginnsu yakusa sauka yakarasu airfort ya zauna yake ta jiran jirgin su yasauka yakusa minti talatin kafin jirgin yasauka, tunda mutane suka fara saukuwa yake ta zuba ido amma bagan taba.

Sai can yagan ta har tasauko sun jera ita da wannan saurayin, dasauri Daddy yatashi yaÆ™arasu wajan dasuke, Daddy kiran sunanta yayi da karfi, yace “Fatima”.

Cak tatsaya ita batayi gababa ita hatayi baya ba, saboda tagene shi, da sauri Daddy yakarasu kabanta yace Fatima baki ji ina kiranki ba? “.

Batace dashi komai ba sai wannan saurayi dasuke tare ne yayimasa magana bayan ya gaisheshi, yace inganin kamar bata da lafiya dan tun ajirgi take kuka”.

Ajiyar zuciya Daddy yasauke kana “yace masa nagode”yace bakomai jikarta yamiÆ™a ma Daddy yayi musu sallama ya wuce warsa.

Hannuta Daddy yaje yace Fatima muje gida kisha magani sai ki kwanta”binshi tayi batari datace masa kalaba har suka kawo wurin da motar shi take, budemata gidan gaba yayi kana shima yazo yashiga suka wuce gidan dayake zaune aciki.

Sai da yayi picking sannan yafito yazo yaɓuɗe mata ta fito, tana fitowa jiri yaɗibeta sauraka kaɗan tafaɗi dasauri ya tare ta tafaɗo jikin sa ita batama saniba saboda kanta dake mata matsanan cin ciyo.

jikinta yaji yayi zafi sosai “yace fatima dama baki da lafiya ne?”.

Bata ce masa koma ba dayaga alamun ba magana zatayiba, yarufe mota suka fara tafiya alamu yaga bazata iya tafiyar ba dan hak cak yaÉ—auketa kamar wata Æ´ar tsana bai tsaye da ita ko ina ba sai bedroom É—inshi kwan tarda ita yayi yafara koÆ™arin rage mata kayan jikin ta alamun taji kamar zaicira mata hijab, bashiri tasanya masa kuka tana cewa “Daddy dan Allah ka kyaleni banda lafiya” tana mai sanya mishi kuka.

“Yaci to naji” wayarsa yaÉ—auka yakira doctor.

Aikowa tanajin yakira doctor taÆ™ara sautin kukan datakeyi tana cewa, “nibanason doctor yazo” lallashin ta yafarayi yana bata hakuri yana cewa “ba allura zamikiba dubaki kwai zaiyi yabaki magani”.

Suna cikin hakan yaji kamar anayi masa knocking yace “mata ina zowa” tashi yayi yaje, kodayaje yaÉ“eÉ—e kofa doctor yagani, bayan sun gaisa yayima doctor iso har wurin datake kwance.

Akowa tana ganin yashigo da doctor takara Æ™arfin kukan datakeyi tana cewa Daddy na warke, kace yatafi yarsa pls”.

Da Æ™ir ya lallasheta ta tsaye doctor yadubata magani yarubuta mata sanan yace ma Daddy adaina sata cikin damu yanzo haka damuwa tayimata yawa”.

Daddy “yace, insha Allah” sallama doctor yayima Daddy kana yawucewar sa.

Daƙir Daddy yasamu taci wani abu tasha magani, batajima dashin maganiba bacci yayi awon gaba da ita saboda acikin magani da yarubuta har dana bacci akwai.

Daddy yanaganin tayi bacci ajeyar zuciya yasauke kana yatashi yashiga tolit ya watsa ruwa yafito bayan yatsane jikinsa daga ruwa bayan ya kammala abun da zaiyi godon datake kwance yaje yahau yace shama bari yaÉ—an kanwata kafin tafarka danshima a gajiye yake bayan ya kwanta jikin sa ya jewota yayimu rufa da bargo baijima da kwanciyaba bacci yayi awun gaba dashi.

Zainba koda tafarkar taji jikinta yasake bakamar jiyaba dan haka tana gama sallah tashi tayi taje kitchen ta haÉ—amusu brekafast bayan ta kammala abunda zatayi taje tayi wanka tashirya tafito falo kuda tafito har su Momy da Nabila da Kulsun da Ummi sun fito ita kaÉ—ai sukejira afara brekafast, tana karasuwa ta gaida momy da Nabila suma su Kulsum suka gaisheta, zamatayi suka fara berakfast.

Bayan sun kammal Zainba da Ummi suka dauke kayan da suka ɓata suka maisuwa kitchen, bayan sundawo suka zauna sukafara fira yaushe Daddy zaidawo.

Suna cikin firar sai Momy tace, “Zainba nace wai Fatima har yanzo bata turumikiba? “.

Zainba tace, “Momy kyaleta ni yanzo ko magar ta banaso saboda abunda tayimin jiya ya É“atamin rai, amma nasan ko inatake zatadawo kuma wallah sai tagane kurinta”.

Sai Momy tace, “nasan kodama bazata gayamikiba” Zainab tace” Momy kobata gayamin ba ai zata tabbata agidan Hajiyar su Mufida ba”.

Nabila tace kubarta ai nasan kafin Daddy yadawo zata dawo hmmm zata ci ubanta aigadannan”.

Zainba tashi tayi tace ni wallahi ko zancinta banasun anayimin dan sai naji zuciya ta na kuna”.

Momy murmushi cin nasara tayi kana itama tatashi ta koma part dinta….

Muje zuwa

Commet
Nd
Shere
1/23/20, 11:48 AM – +234 706 211 8047: 💦💦💦💦💦💦💦
💦💦💦💦
💦💦

 *KAWAR* *'YATA* *CE* 

®�
GASKIYA WRITERS ASSOCIATION�
{ Gaskiya É—aya ce daga Æ™inta sai É“ata, burinmu mu faÉ—akar da al’umma domin ribantar duniya da kuma lahira. }

     🎐 ```G•W•A```🎐

GASKIYA DOKIN ƘARFE•🏇🏼

Story & written
By
Sumy

BISMILLAHI RAHAMANR RAHIM

.

   Page1�7�

Tana shiga wayar ta taÉ—auko ta kira k’anwar mahaifiyar ta Hajiya Shafa, tagayamata abinda ke faruwa.

DaÉ—i taji tace saura yanzu auren Alhaji sulaiman muji mizai wakana.

Momy tace,”ai wannan auren baza’ayishi ba, Amma kisa ido kiyi kallo”.

Haka sukasha firarsu daga baya sukayi sallama.

Kamar amafarki yaji wayar sa sai ruri take, tashi yayi daniyar yakashe wayar.

Sunan da yagani ya bayyanane yasa shi yin picking batare da yashiyar ba.

Sallama yayi mata, bayan ta amsa masa Hajiya Sa’a tace, “Fatima tasauka?”

Alhaji yace, “Hajiya dan Allah kiyi hukuri bankiraki nagaya miki ba,”

Cikin b’acin rai tace,”ni ban tambayeka dogon turanci ba, tasauka ko bata sauka ba?”

Alhaji cikin rashin Jin dad’in abinda Yayi mata yace, “tasauka Hajiya.”

Bata bari taji mi zai ida cewaba ta yanke kiran.

Wayar yabi da kallo ya d’an yi murmushi yace, “Yaya hukuma, Allah ya huci zuciyar ki,ajiye wayar Yayi ya koma barcin sa.

Wani mafarki ne tayi mai ban tsoro za dan haka afigice tafarka da addu’ a abakinta, gabanta nata dukan uku uku.

Tashin datayi afirgice yasa Daddy yafarka, yana cemata, miya faru lafiya?” batayi masa magana ba tunanin mafarkin datayi takeyi.

Wani katon maciji ne yake bin ta, duk in da tayi sai yabita, dataga haka gudu tafarayi dan neman wurin b’oyo.

Aikuwa shi d’inma saurin ya k’ara yi yana biye da ita har takawo bakin Ƙofar É—akin su Zainab.

knocking tafara yi musu iya k’arfin ta.

Tana cikin knocking d’in Zainabu tafito da sauri taÉ“uÉ—e mata Æ™ofar.

Aikuwa tana ganin Fatima ce ta haÉ—e fuska tace, “lafiya kikemana knocking yanzon nan?”.

Fatima cikin saurin magana tace, “Zainba maciji ne yabiyoni, har takai Æ™afa É—aya É—akin da sunan tashiga, Zainba tasa dukkan k’arfinta ta turo Fatima waje, tamai do Æ™ofar tarufe, kuma dai dai lokacin da macijin nan ke kawowa.

Har yatada kai alamun zaiyi sara, itakuma Fatima tafarka.

Daddy yana mai cewa, “Fatima bakiji ne ina maki magana kinyi shuru yana kai hannunshi jikin ta.

Afirgice tadawo duniyar tunani da tashiga, aikowa suna haÉ—a ido da Daddy tafashe da kuka, tana mai faÉ—awa jikinsa, tana cewa, Daddy dan Allah kamai dani gida wurin Ummah na.dan ina ji ajikina kamar wani abu zai sameni pls”.

Ta k’ara fashewa da sabon kuka.

Sai datayi mai isarta sannan tayi shuru, Daddy yafara cewa, “Fatima dan kinyi mafarkin wani abu shikenan zaki ce wani abu zai sameki? kenan kin san gaibu?”

Da sauri taÉ—ago kanta takalleshi tanamai girgiza masa kai alamar a’a,.

Numfasawa Yayi yace,”to in har bakisan gaibu ba, kidaina cewa haka kinji”

Fatima tace, “to Daddy”

Daddy yace, “kuma kitashi kiyi addu’a kikoma bacci,da ikon Allah bazakiyi kowane mafarkiba.”

Fatima a tsorace tace, “Daddy bazan iya bacci ba.”

Kama hannunta Yayi ya mik’ar da ita Yana cewa, “to tashi ki je kiyi alwalla kiyi sallah.”

Ba musu ta tashi ta bishi har toilet ya rakata tayi alwalla.

Sallaya ta shimfid’a ta kabbara sallah,
shima Daddy alwallar yayo ya rab’a kusa da ita ya fara sallar, suna masu kai kukansu ga mahalicinsu.

Sai da sukayi sallah asubah saku tashi, ita tafara tashi taje takwan ta Daddy sai da yaga bacci yaÉ—auke ta sannan shima yaje ya kwanta.

Daddy yafara farkawa tashin sa ba jimawa itama tafarka, dasauri tatashi cikin jin kunya tayi toilet.

saida tayi wanka, tafito, inda tabarshi annan tasameshi.

Har zata wuce, kuma ta tsaya nesa dashi, ta na mai duƙawa tace, Daddy ina kwana.

Ido yazuba mata yana mai kallon ta kamar bazai karÉ“a ba, yace, “kintashi lafiya?” tace, “lafiya Æ™alau”.

Bata sake magana ba shima haka, shiri takeson tayi amma takasa, saboda kallon ta da yakeyi, daya fahimce haka tashi yayi yakoma parlour.

DaÉ—i taji dan haka taji daÉ—an shirya wa cikin tsanaki.

Bayan ta kammala shirin ta ta zauna tayi tagumi tana tunanin ‘yan gidan su.

shi kuma Daddy ganin lokaci yaja, dan haka tashi yayi yaje yakirata domin suyi breakfast dan yanasun yafita, dan haka kai tsaye yashiga d’akin a haka Daddy yashigo yasame ta.

Bata masan ya shigo ba sai da taji yace,”fatima lafiyarki Æ™alau kuwa?” tace, ” ba komai Daddy” yace, “yaza kice bakomai, kuma gashi na sameki kina tunani.”

Fatima tace ina son ne nayi waya da gidanmu ne,.”tana magana da kanta k’asa.

Daddy yace,”to naji zan baki waya, amma sai nadawo dan fita zanyi jirana akeyi, dan haka kizo muyi brekafast kinji”.

bamusu ta tashi tabi bayan shi sukaje sukayi breakfast.

Bayan sun kammala agorgoje yaje yashirya ya fito inda yabar ta anan yasame ta yace, “my teema ni zan wuce kiyi hukuri zan barki ke kaÉ—ai.”

Fatima tace, “ba komai Daddy Allah ya kiyaye hanya”.

Wani farin cikine ya ziyarce shi,bai san lokacin da yace,”my teema na nagode kwarai.”

Har yakai Æ™ofa zai fice,juyuwa yayi yace kishirya idan nadawo za mu zagaya gari”.

Ahankali tace, to” bai jime tace ba dan haka yace, “Fatima kobazaki jebane?”

Tace, “Daddy zanje saika dawo koh.” yace, “eh”

Kana yaficewar sa.

Muje zuwa

Comment
Nd
Shere
1/23/20, 11:48 AM – +234 706 211 8047: 💦💦💦💦💦💦💦
💦💦💦💦
💦💦

 *KAWAR* *'YATA* *CE* 

®�
GASKIYA WRITERS ASSOCIATION�
{ Gaskiya É—aya ce daga Æ™inta sai É“ata, burinmu mu faÉ—akar da al’umma domin ribantar duniya da kuma lahira. }

     🎐 ```G•W•A```🎐

GASKIYA DOKIN ƘARFE•🏇🏼

Story & written
By
Sumy

BISMILLAHI RAHAMANIR RAHIM

       *Page* 1�8�

Da kallo tabishi har yafita, hawaye suka fara zuba a idon ta, ahankali tafurta cewa, “nikuma haka tawa k’addara take,baban Æ™awa ta shine mijina.

Tana tunanin tana kuka Mai ban tausayi.

Sai datayi mai isarta sannan tayi shuru.

Tunani haÉ—uwar ta da Zainab tafarayi.

A watara akashirya debate a makarantarsu government school, ta Æ´an mata da private school, ta Æ´an mata.

Debate d’in daya É—au hankalin mutane da dama musamman malaman su.

Haka akaci gaba da fafatawa a wajan debate d’in, cikin ikon Allah makaran tar gwamnati ta canye, aikowa murna wajan malaman su ba’acewa komai.

Bayan an gama abunda za’ayi an raba kyautunkan da za’a raba, mutane suka fara watsewa, bayan mutane sun watse, akabar malamai da É—aliban dasukayi debate domin suyi metting, babban malamin su ya tashi yayi musu nasiha, yaÆ™ara da cewa,”kada kusama ranku komai, saboda bakuyi nasara ba, a’a kuma kunyi Æ™oÆ™ari sosai, kuma kada kuji haushin su kuÉ—auka haka shine mafi alhairi dan haka kada kusama ranku komai.”

Nunfasawa Yayi Sannan yaci gaba da cewa,” kuma kada kuÉ—auka dan kunfisu Æ™okarine, a’a kuÉ—auka Allah ne yabaku nasara.”

Haka yayi tayi musu nasiha har kowanensu sukaji zukatan su sunyi sanyi.

Bayan yagama bayani kowaninsu ya kama gabansa.

Bayan sun fito daga hall d’in dasukayi debate d’in. tana tsaye tana jiran abokan tafiyar ta, sai ji tayi anayi mata sallama, “Assalamu alaikum ya Fatima.”

Sallamar dataji anmata yasa ta kalli wajan da akemata sallamar.

Amsawa tayi tana mai kallon ta, sai tace mata,”da fatan kin gane ni.”

Fatima tayi murmushi tace, “sosai naganeki ba sunan ki Zainab ba? Ko bakece mukayi debate tare ba?”

Zainab tace, “eh nice,Amma Ina fatan zamu zama Æ™awayen juna.”

Fatima tayi murmushi tace,” miza hana, Allah dai kasama Æ™awancen albarka”.

Zainab tace, “ameen”sai Zainab tasake cewa, ko zan samu number ki?” Sai Fatima tace, “banida waye sai dai nabaki ta Ummatah”.

Sai Zainab tace “zaki iya bani inba damuwa”

Fatima tace, “badamuwa”

Bata number tayi itama Zainab ta rubutama ta tata sukayi sallama suka wuce akan sai sunyi waya.

Tunda ga wannan lokacin zumunci yaÉ—uru tsakaninsu, har suna kawoma junansu ziyara.

Har Zainab tasanya Baban ta ya maida Fatima makaran tarsu.don haka suka Zama makarantarsu d’aya.

Tunda ga wannan lokacin duk, abunda Daddy Zainab zaiyima ta sai yawa Fatima dan yanzu wata kulawa yake ba su yanaji dasu sosai.

Momy har mamakin Daddy takeyi, taga gabaki É—aya, ya É—auki kulawa yaba Zainab da Fatima ba kamar da ba.

Dan Daddy har wajan baban Fatima yaje yace masa,” “yana son yabashi Fatima takoma gidan sa da zama.sannan yak’ara dacewa amma inba damuwa.”

Baban Fatima sai da yayi ajiyar zuciya kana yace, “banki takaba,amma nasan ko ta koma wajan ka dazama to lalle yayana sai yadawo da ita, amma kayi hakuri zan shawarce shi, duk yadda muka yanke zan neme ka”.

Daddy yace, bakomai Baban Fatima.

Sannan ya mik’e tsaye Yana Mai cewa,” ni yanzu zan wuce, sai najika kenan.”

KuÉ—i masu yawa Daddy ya ajema Baban Fatima , yana cewa,” gasu aba yara.”

Baban Fatima yace, “haba Alhaji harda wata É—awainiya”

Daddy yayi murmushi yace, “a’a ko d’aya.”

Godiya Baban su Fatima yayimasa, yana mai rakashi har bakin motarsa kana ya shiga yawuce.shikuma Baban Fatima ya koma cikin gida.

Koda Baban Fatima yafaÉ—ama yayan sa, cewa yayi sam bazai yarda ba.

Dan haka,faÉ—ama Daddy duk yadda sukayi da yayanshi Yayi, sannan yahaÉ—a masa da ban hakuri.

Daddy yace, “bakomai tunda tana zuwa,watarana ma har kwana tanayi,ai ba komai”.

Tundaga wannan lokacin Fatima ita bata koma ba amma kamar ta koma dan idan kaganta agida bazakace ba Momy ta haifeta ba, duk, da ma Momy bason zaman nata takeyiba, dan bada son ranta take zama agidan ba.

Sai dan sanin halin Daddy datayi a yanzun.

Haka rayuwa taci gaba da tafiya har su Fatima suka kusa kammala makarantar su.

dan yanzu gaÉ—aya zaman ta yadawo gidan.

Duk da itama badan son ranta take zama gidan ba, sai dan Zainab da Daddy, domin kota koma gidansu, Daddy sai yaje shida Zainab sun É—aukota dan idan batanan ko abincin gidan Daddy baya ci.

Abun na d’aure ma Momy kai dan har saida takai da yimasa magana.

Yace, “mata kawai yanajin su ajikine saboda yaga suna ba karatunsu muhin manci shiyasa yake kara kulawa dasu”.

Momy tace, “to kadai rage, tunda ba su kad’ai ne ba, kuma fah, kada kamanta Zainab ce kaÉ—ai É—iyarka, bada Fatima ba.”

sai Daddy yace, “ni duk, É—aya na É—aukesu”

Momy bata sake magana ba tafita daga É—akinsa zuciyar ta na k’una.

Sai da tafice Daddy yace, nasan kishine bakomai ba inama acekin san me zuciyata ke ciki gami da ita Fatimar, da bansan mizaki kasance ba.

Babban tashin ahankalin Daddy duk bai wuce, ganin Fatima dawani saurayi suna zan ceba, aikuwa Daddy yashiga tashin hankali sosai, dan har sai da yakwanta,ciyo kwana biyu

Bayan yasamu sauk’i yakirata.

Bayan tazo ta gaida shi ya amsa. sai Daddy yace, “Fatima”.

É—ago kanta tayi ta Æ™alleshi,yace, “shekaran jiya, waye yazo wajanki kuna zance dashi?”.

Kasa tayi da kanta, batace komai ba, Daddy yace, “wai ba magana nake maki ba ne?”

konan batace komaiba, Daddy yace, “imma saurayinki ne to ki ajeshi waje daya, dan karatu nakeson kuyi ba soyayyaba, dan haka duk na sake ganinki dawani saurayi sai ranki ya É“aci, dan haka kitashi kitafi kuma ki gayama, Æ´ar uwarki sakona”.

Tashi tayi bata tsaya ko ina ba sai É—akin su.

Acan tasamu Zainab kwance, sannu sannu take tafiya kamar mai koyon tafiya, har ta kawo bakin gado ta zauna.

Zainab tad’ago kai ta kalleta tace, “my sweet sister, lafiya naganki haka, ko ankoma fad’a da hayat ne?”ahankali Fatima tace, “ko d’aya, takara da cewa, Daddy ne yaganmu shikaranjiya yazo fira, shine yanzu yakirani yamin kashedi akan karnasake kulashi, nan dai tagayama Zainab abunda Daddy yace.

Zainba tace, nikam gaskya nayi nisa wajan son Kabir , sai dai nace Allah ya tabbatarmuna da alhairi” dan dawanda keson Zainab da mai son Fatima abukaine dan lokacin da suka zo zance wajan Zainabu a lokacin Hayatudeen yaga Fatima, aikowa shikenan ya likemata saida yaga yasamu shiga a wajan ta.

Dan da farko tak’i saboda ita aganinta basudace ba badan komai ba sai dan shi iyayen sa masu haline ita saÉ“anin haka dan ita mahaifinta sai ya fitane suke samun abin kaiwa baki,

Zainab takara dacewa wai ma zaki tsaya jiran hayat d’inki har yadawo daga wajan karatu, koma naga kamar gidanku bazasu bari kicigaba da karatu ba har dai yadda nake ganin yanayin yayan babanku”.

Fatima tace, “nima haka nake gani,da wuya su barni” sai Zainab tace, “aikuwa da bansan yazamu kasan ceba, dan yanzu naga alamun, kina mutuwar sonshi”.

Sai Fatima tace, “yana iya tunda nayi ta kaucemasa amma yaki barina gashi yanzo abunda nakema godu yafaro dan nama dauka danace masa ba niba Æ´ar gidannan bace yara budani, amma a lokacin ma ya nuna yafisona, gashi yanzo yaddana kejinsa idan narashi bansan yazanyi ba”.

Tausayin ta yakama Zainab sosai dan tasan yadda takeson Hayatudeen dinnan koma koshi yana mutuwar sonta da har gidasu sunsan yana son Fatima dan ko Mamarshi naso Fatima sosai, danshi ma Fatima tak’ara yadda son gasky Hayatudeen kemata.

Kallon Zainab tayi dataga tayi shuru, tace, “my Zeey gobe zanje gida dan Ummah tace, nazo”sai Zainab tace, “to Allah yakaimu sai muje m muyi kwana biyu ko?” Fatima tace eh”.

Aranar haka ta wuni bawani kuzari ajikin tah..

Muje zuwa

Commet
Nd
Shere
1/23/20, 11:48 AM – +234 706 211 8047: 💦💦💦💦💦💦💦
💦💦💦💦
💦💦

 *KAWAR* *'YATA* *CE* 

®�
GASKIYA WRITERS ASSOCIATION�
{ Gaskiya É—aya ce daga Æ™inta sai É“ata, burinmu mu faÉ—akar da al’umma domin ribantar duniya da kuma lahira. }

     🎐 ```G•W•A```🎐

GASKIYA DOKIN ƘARFE•🏇🏼

Story & written
By
Sumy✍�

BISMILLAHI RAHAMANIR RAHIM

Congrtulations my baby intayaki murnar kammala `novel``` *`d'inkiBABUSHI* A ZUCIYATA Allah yabaki ladar faÉ—a karwar dakikayi .

Page19*

Da sassafe suka shirya bayan sunyi breakfast, d’akin momy sukaje sukayi mata sallama, kana suka wuce part d’in Daddy domin shi ma suyi masa sallama.

Da sallama suka shiga, bayan ya amsa musu suka gaishe shi, sannan suka fad’amasa inda zasuje,dak’ar yabar su,kuma kwana d’aya yabasu.

Aikowa sunje gidan kwanan su biyu basu dawo ba Daddy da yamma yaje dumin ya É—auko su.

Koda yaje gidan su Fatima ya aika akirasu amma akacemasa basunan suna gidan yayan Baban su Fatima.

Aikawa ya kuma yi yace, “yana so akira mashi su.”

sai kanwar Fatima mai suna Salma tafito, bayan ta gaisheshi tace, mishi,” Ummah tace, na faÉ—a maka, ko dama can Baba babba shine ya aika akirata, dan haka yanzu tana can gidan sa”.

Sai Daddy yace, “kinsan gidan ne?” tace, “eh nasani”.

Sai yace, “zo muje ki kaini gidan.”

Salma tace, “to bari nagayama ummah”.

Daddy yace, “to jeki”.

Batajima dashiga gidanba, ta fito, tace, muje Daddy hanya tamiƙe zatayi tafiya.

Sai yace, “Salma zo kishiga mota muje ko”.

Tace, “Daddy ba nisa nan ne bayan gidan.”

Daddy yace, “duk, da haka kizo muje dan ni daga can nake son na wuce”.

Tace, “to” tana mai dawowa tashiga tana shiga ya tada mota suka tafi tana mai nuna masa hanyar gidan, bakin Æ™ofar gidan yayi parking.

Sunayi parking Salma tace, “ashe Baba babba ma yana gida.”

kallon ta yayi yace, “ina yake ne?”.

Tace, “gashi can bisa tabarma zaune.”

Daddy yace, “to bari naje mu gaisa.”

Salma tace, “to tana mai fitowa acikin motar.

Koda takawo wurin Baba babba, gaisheshi tayi ya amsa.

kallon ta yayi yace, “waye yakawoki a Mota?”.

Salma tace, “Daddy su Aunty Zainab ne yace nakawoshi gidannan”.

Har yaso yasake yin magana yafasa, saboda Daddy daya tunkaro wajan dayake zaune.sai yace mata,”kina iya tafiya.”

Tashi tayi ta shiga gidan,bata k’arasa shigaba Daddy ya k’araso wajan da Baba babba yake zaune.

Sallama Daddy yayi masa yana mai mik’a masa hannu dan su gaisa.

shima hannu yaba Daddy sukayi musabaha, kana yanunama Daddy wurin zama, bayan Daddy yazauna.

Sai Daddy yace, dama nazo na d’auki su Zainab ne akace sunanan”.

Sai da Baba babba ya numfasa kana yace,”eh sunanan ko kiramaka Zainab d’in za’ayi?”.

Sai Daddy yace, eh akiramin su dan gobe ne zasu koma makaranta”.

Sai Baba babba yace, a’a kayi hakuri bada Fatima ba, dan yanzu ko ina bazata koma tafiya ba, saboda data kammala makaranta aure zanyi mata”.

Arazane Daddy yad’ago idonsa ya kalle Baba babba, Daddy yace, “aure”.

Kai Baba babba ya d’aga masa, alamar eh, sai Daddy yace, “dama ammata miji ne?”.

Sai Baba babba yace, “a’a yanzu dai nakeson takawo mijin.”

yakara da cewa, inma bata kawo ba ni zan had’ata da wanda yadace da ita”.

Sai Daddy yace, “da anbarta takawo wanda take so
zaifi”.

Sai Baba babba yace, “intakowa dan kanta inma bata kawo ba ni ina da wanda zanbata”.

Sai Daddy yace, “miyasa bazakubarta tayi karatun taba, inyaso, koda tana cikin karatune idan tasamu wanda takeso, sai ayima ta auren”.

Baba babba yace, “bamuyi tun farko ba, dan haka bazamu fara akanta ba.saidai indai tayi aure mijin ta yabar ta, to wannan kam bazamu hanaba”.

Daddy babu yadda bai nunama Baba babba sai yace, “a’a.”

Jikinsa amace yayi mishi sallama yayi tafiyar sa,dan bai ma tsaya aka kira masa Zainab saboda cikin tashin hankali yake.

Daddy nashiga mota yatada bai tsaya ko inaba sai gidan babban abokinsa Alhaji Aminu.

Yana yin picking din motar sa kai tsaye parlour dayasan zai sameshi yaƙarasa.

yana shiga ko ya sameshi, yana kallon news hausa.

Dashigar sa firij yaÉ“uÉ—a ya d’auki ruwa masu sanyi yakifa abakinsa sai da yasha sosai sannan ya aje.

Tunda yashigo Alhaji Aminu yake kallon sa, yana mamaki yanayi da yashiga.

saida yabari yagama shan ruwa, ya kalleshi da kyau yace, Alhaji Mansur, lafiya naganka a haka kuwa?”.

sai da Daddy yayi ajiyar zuciya kana yace, iyayin Fatima aure zasuyi mata” yana faÉ—a kamar yayi kuka.

Sai Alhaji Aminu yace, “to miyasa zaka damu, bayan na gaya maka mafita amma kak’i yarda”.

Sai Daddy yace,” ba nak’i yarda bane, a’a ina dubin yadda zan aure abokiyar É—iyata kuma É—iya a gareni”.

Daddy yakara da cewa wallahi nayi nayi nafiddata araina amma nakasa, kamar ma ina kara cusata ne a zucuya ta”.

Alhaji Aminu yace, “kayi yadda nace ma,dan bari kaji,shi so idan bai shiga zuciya ba ne akecewa abarshi, amma da zaran kabari yashiga to fitar dashi abune mai wahalar gaske, dan haka kaje kanemi magani kafin yayimaka illah”.

Daddy yace, “to naji katayani addu’a, dan na sanar da Gwaggo tace Mani na hak’ura.kuma naje na faÉ—ama yaya tah.

Ni ina ma tsoron karta ce bazata samin hannu ba, tunda kasan yadda mukayi abaya”.

Alhaji Aminu yace, “Insha Allahu komai zaizo da sauÆ™i”.

Alhaji Aminu yakara da cewa,”ina son ka auri yarinyar nan ko dan ka kuÉ“uta daga hannun Hajiya Kulu, kada kaman ta, yanzu kashiga harkar siyasa abu kaÉ—an kayi sai duniya taji ka dan haka kakare mutuncin ka dana iyalinka”.

Sai da Daddy yayi ajiyar zuciya, kana yace, wallahi har da Æ™arin abunnan yasa nakeson nakara aure dan abun nadamuna, yakara dacewa,”insha Allah da komai yadawo dai-dai zanje na gaya ma yayata Hajiya Sa’a.

kai kuma abunda kaÉ—ai nakesu da kai ka tayani addu’a”.

Alhaji Aminu yace, “kada kadamu insha Allah zan tayaka komai, har sai kasamu abinda kakeso”.

Haka sukaci gaba da hira daga baya Daddy yayimasa sallama yayi tafiyar sa.

Bayan sun shirya da Gwaggo Maryam,ya fad’a ma Hajiya Sa’a tace,” yabar komai ahannuta.”

Bayan kwana biyu shiryawa tayi taji gidan su Fatima.

Koda taje akayi rashin sa’a Ummar Fatima batana be Nan ta tafi Unguwa. Kakar ta kaÉ—ai ce agidan.

Da fara’a Kakar Fatima ta tarb’e Hajiya Sa’a, badai kamar data ga yanayin shigar ta.

Bayan sun gaisa, Kakar Fatima tace, “
naso naganeki amma banganeki ba”.

Sai Hajiya Sa’a tayi murmushi tace,”Inna bazaki gane ni ba, dan koni bantaÉ“a zowa gidan nan ba sai yau”.

Sai Kakar Fatima tace,”to lafiya dai ko?”

sai Hajiya Sa’a tace, “lafiya Æ™alau, kodama alfarma nazo nema, akan yariyar da Æ™anena yagani a gidan nan, yace, yanaso”.

Sai Kakar Fatima ta gyara zama tace, “wacece, acikin su, ko ad’auku miki hotonan su dan ‘yan matan suna da yawa”.

Sai Hajiya Sa’a tace, “basai an dauko hoto ba”.

Dan Kaka Amo ta matso taji ko wacece, saboda y’an matan suna da yawa.

Sai Hajiya Sa’a tace, “sunan ta Fatima, dafatan dai ba’ayi mata mijiba”.

Sai Kaka Amo tace, “a’a ba’ayi mata mijiba, duk da dai shi Baban ta yace, zai samar mata miji cikin satin nan, amma tunda kinzo ai shikenan sai ayi daku d’in.”

Sai Hajiya Sa’a tace, “nagode sosai, sai dai shi Æ™anin nawa fah ba saurayi ba ne, yanada mata har ma da yara biyar”.

Sai Kaka Amo tace, “ai albarka akeso bawani zancen saurayi ba, dan haka kamar zuwa gobe sai kidawo.don kiga Shi baban nata da yamma.”

Godiya Hajiya Sa’a tayima Kaka Amo, jikar ta ta É“uÉ—e kuÉ—i masu yawan gaske Hajiya Sa’a ta ajema Kaka Amo, tace, “gasunan, asai goro”.

Aikowa Kaka Amo bakinta kasa rufuwa yayi, É—aukar kuÉ—in nan tayi tanata juyawa, tana cewa, “kunga rabo ko. arziki yazo maka har gida.

kana tamaida kallon ta ga Hajiya Sa’a wadda itama ita take kallo, tace, “gobe kidawo in dai aure ne babu fashi. nice nan kakar yarinya sai yadda nace za’ayi”.

Hajiya Sa’a godiya tak’arayima Kaka Amo kana tayi mata sallama tawuce tace Sai zuwa goben.

Muje zuwa

Comment
Nd
Share
1/23/20, 11:48 AM – +234 706 211 8047: 💦💦💦💦💦💦💦
💦💦💦💦
💦💦

 *KAWAR* *'YATA* *CE* 

®�
GASKIYA WRITERS ASSOCIATION�
{ Gaskiya É—aya ce daga Æ™inta sai É“ata, burinmu mu faÉ—akar da al’umma domin ribantar duniya da kuma lahira. }

     🎐 ```G•W•A```🎐

GASKIYA DOKIN ƘARFE•🏇🏼

Story & written
By
Sumy✍�

Bismillahi rahamanir rahim`

My baby inatayaki murnar fara sabo book dinki mai suna lZZAR SARAUTA Allah yabaki ikon kammala shi lafiya

Page 2�0�

Da yamma Kaka Amo tashirya taje gidan Baba babba, dan a lokacin ne takesa ran dawowar sa gida.

Aikowa tana zuwa ta same shi a gida. Bayan sun gaisa da matar sa, tashi tayi tabasu wuri dan tasan halin lnna Amo sarai.

Fitar ta keda wuya, Baba babba yace, “Inna lafiya kika zo da kanki ai da aikowa kikayi kira na da yafi.”

Inna Amo tace, “a’a magana ce mai muhimmanci, dan shi yasa kaga nazo da kana”.

Yace,”wace magana ce lnna?”.

Tace,” kan maganar minjin Fatima, ko ka tsaida wanda zaka bata ne? ko Kuma ita takawo wanda take so,?”.

Baba Babba Yace,” a’a lnna ko d’aya ba’ayi ba, dan ita wannda tace tana so ma karatu yakeyi, mu kuma bazamu tsaya jiranshi har ya kammala karatunshi tana gida zaune ba.”

Kaka Amo tace, “a’a baza mu jira sa ba kam.

sai kuwa Inna Amo ta gyara zamanta, ta kwashe duk yanda suka yi da Hajiya Sa’a tagaya masa.

Takara da cewa, “kuma daganin ta matar y’ar babban gida ne,dan har kud’i tabani akalla zasu kai dubu dari.

Da karfi Baba Babba yace, “dubu dari fah kika ce lnna? “.

Tace, “sosai kuwa,don shiyasa ma nazo dasu dan kagan su”.

Jikkar dake sanye ajikin ta taÉ“uÉ—e ta É—auko masa kuÉ—in tace,” gasu ka Æ™irga kagani”.

KarÉ“a yayi hannusa na karkarwa yace, “lnna duka tabaki?”.

Tace, “sosai kuwa, kaga abin “arziki har gida ko?”

Inna Amo ta numfasa sannan ta k’ara da cewa,”ni tsoron da nike yarinyar nan kada tayi mana tsiya”.

Da sauri Baba Babba ya É—ago kai ya kalli lnna Amo yace, “lnna bari ma wannan zancen, dan indai naga shi wannan daki kace yayimin to ita Fatimar ko bayyi mata ba baruwana, kuma yadda nace haka za’ayi da ita,ko uwar ta tayi kaÉ—an ta canja abinda nace”.

Numfasawa Yayi sannan yaci gaba da cewa, “badai kince gobe ita Hajiyar zata dawo ba?”.

Inna Amo tace, “tabbas gobe zata dawo.

Sai Baba Babba yace, “zan tsaya na jira ta ma”lnna Amo tace, hakama zaifi kyau,don gaskiya ayi komai a gama”.

Haka sukaci gaba da fira sai da akayi kiran sallah, Baba babba yatashi yaje masallaci, itama Kaka Amo takoma gida.

Koda ta koma Umma dasu Fatima duk sun dawo, amma komai bata ce wa mahaifiyyar fatimar ba.

Koda gari yawaye Kaka Amo tashirya tanajiran zowan Hajjiya Sa’a, kusan sha biyu na rana, sai ga Hajiya Sa’a tashigo da sallamar ta.

Da fara’a Ummar Fatima ta amsa ma ta, aikuwa Kaka Amo da sauri tafito daga d’akin ta, dan har Hajiya Sa’a zata shiga É—akin mamar Fatimar,sai Kaka Amo tafito tana cema, “mamar Fatima bafa wajenki tazo ba,ehe wajena tazo kisani”.

Sai Ummar Fatima tace, “lnna kiyi hakuri naga kar a bar ta a tsaye ne shiyasa nace, ta shigo, kuma bansan wajenki ta zoba dana kai ta wajenki”.

Hajiya Sa’a ita dai kallon ikon Allah take yi.

Inna Amo tace, “Hajiya mutafi can gidan yayan Babanta”.

Hajiya Sa’a tace “to lnna muje”.

Inna Amo tana gaba itako Hajiya Sa’a nabiye da ita har suka kawo gidan Baba babba.

Da shigarsu kai tsaye d’akin Baba Babba lnna Amo takai Hajiya Sa’a.

Da sallama ta shiga, ya amsa mata da fara’a afuskar sa.

wajen zama ya nuna musu suka zauna. Bayan sun zauna ne lnna Amo tace ma Baba Babba,”ga fa Hajiya nan tazo”.

Baki ya washe ya gaishe ta ta amsa.

Baba Babba yace,”ai lnna ta faÉ—a min abunda ke tafe dake.”

Sannan yaci gaba da cewa,” toshi k’anin naki yafaÉ—ama ita Fatimar ne?”

Hajiya Sa’a tace, “nidai yace ya faÉ—a mata amma bansani ba ko da gaske ne? amma zaku iya tambayar ita Fatimar kuji”.

Sai Baba Babba yace, “a’a ai tunda ya gaya mata bakomai, kawai ko aiko da magaba tan ku”.

Abun yaba Hajiya Sa’a mamaki taga babu wani bincike sai kawai aturu.

Numfasawa tayi sannan tace, “to ai bakusan waye mijin ba kuma naji har kunce muturo, kodai yazo ne bansani ba?”.

Baba Babba ya shiga mazurai Saboda Shi kanshi yasan abinda sukayi ba Haka ya Dace ba,don haka Sai cewa yayi,”a’a bai zoba, Amma dai mun san zai zo kafin auren”.

Hajiya sa’a tace, “insha Allah”. Sannan ta kallesu gaba d’aya tace, “amma fa kusani, kar kuce kun bamu kuma daga baya ku ce kun fasa.K’ara ku fad’a mana gaskiya.”

Sai su lnna Amo sukace, ba komai indai tasan Æ™aninta mutumin kirki ne, to babu matsala”.

Hajiya sa’a ta girgiza Kai tace “a’a wannan ba hujja ba ce gaskiya”.

Takara da cewa,” amma, gaskya zan faÉ—a muku,kuma amatsayina na uwa mace gaskya zan iya bashi aure amma fa gamai irin ra’ayina, dan kaga shi ba yaro ne ba, saboda yace min ita Fatima abokiyar diyarsa ce, Zainab”.

Kaka Amo tace,” ai mutunci yafi komai tunda yanada mutunci ai babu matsala”.

Godiya Hajiya Sa’a tayi musu, sannan tayi musu alhairi mai tarin yawa wanda yasa Baba Babba rikice wa, har yanace wa yaushe magabatan sa zasuzo?”

Sai Hajiya sa’a tace, “dana koma gida munyi magana da Baba duk, yadda yace, zan faÉ—a muku”.

Sai Kaka Amo tace, “ba komai ai mun gode, haka suka rakota su nayi mata godiya, har tashiga mota ta wuce, tabar su nan baki yaki rufuwa.

Aikuwa cikin sati d’aya akayi komai amma, babu wanda suka gayama wa.

ko mahaifin ta kayan da aka kawo nasa ka rana suka gwada masa.

Sukace masa ga kaya nan, dan nan da sati uku masu zuwa za’ayi auren Fatima.

komai bai ce musu ba, addu’a yayi mata kana yawuce gida, badan yasan waye ne mijin taba.

Haka akayi ta shirye shiryen bikin Fatima, amma ko ita Fatima har yanzu bata san waye mijin taba.

Dan lokacin da Daddy, yake gaya mata yana son ya aureta bata fahimci mi yake nufi ba, ita dai abinda ta fahimta shine yana son yak’ara aure.

Haka abubuwa sakayi ta tafiya biki yarage saura sati d’aya Daddy yazo ya gaida Baba Babba shi da abokin sa Alhaji Aminu.

Bayan sun gama gaisawa, Alhaji Aminu yaga batar masu da kansu.

Kana yayi musu kyautar, kujerar Hajji da Umura.

Hmm zokaga murna wajen lnna Amo da Baba Babba, dan har makota sai da sukaji Mijin Fatima yabiya musu kujerar hajji.

Koda Ummar Fatima da Baban ta sukaji suka taya su murna.

Amma duk da haka Kaka Amo sai da taje har d’akin mamar Fatima taci mata mutunci, wai tayi bakin ciki, dan bada ita akace za’a ba.

Ita dai Ummar Fatima batace, mata komai ba, har ta gama tayi tafiyar ta.

Ai babu babban tashin hakali daya wuce Zainab, data kira Fatima take Mata,”Fatima Wai da gaske ne Daddy ke zai aura?”.

Fatima tana kwance ta mik’e zumbur ta tashi zaune tace,
“Zainab, wannan wace irin magana ce haka?”

“Daddy fa ki kace? to ko hauka nayi na warke bazan aure Daddy ba, danni uba yake gareni kamar yadda yake uba a wajen ki”.

Zainab tace,” naji to yanzu wanene mijin naki?”.

Sai Fatima tace duk jikinta Yayi sanyi”koni Zainab, bansan waye ba, dan bana bukatar na sani tunda ba shine zab’i na ba”.

Zainaba tace, duk da haka kije kiyi bin ciken waye mijinki”.

Bata bari tayi magana ba, Zainab ta yanke wayar.

Sai da ta gama nazarin maganar Zainab kana ta tashi tayi wajen Ummar ta.

Koda taje a d’aki ta same ta zaune tayi tagumi kamar mai tunani..

Muje zuwa

Comment
Nd
Shere
1/23/20, 11:48 AM – +234 706 211 8047: 💦💦💦💦💦💦💦
💦💦💦💦
💦💦

 *KAWAR* *'YATA* *CE* 

®�
GASKIYA WRITERS ASSOCIATION�
{ Gaskiya É—aya ce daga Æ™inta sai É“ata, burinmu mu faÉ—akar da al’umma domin ribantar duniya da kuma lahira. }

     🎐 ```G•W•A```🎐

GASKIYA DOKIN ƘARFE•🏇🏼

Story & written
By
Sumy�

BISMILLAHI RAHAMANIR RAHIM

DEDICATED To
ALL GASKIYA WRITER’S
Aysher Aliyu Humaira (INNARO)💞💞💞💞
Marubuciyar
AISHATUL MUWAFAQA

   *Page* 2�1�

Da sallama tashi ga sai da ta samu wuri ta zauna takalle Umma ta wanda itama ita take kallo.

Tace, “Ummah” kuma sai tayi shuru.

Sai Ummah tace, “Fatima lafiya kowa?”.

“Gayamin mike da munki”.

Sai da tayi k’asa da kanta tace, “Ummah wai wane-ne su Baba Babba, suka tsayar min?”.

Sai da Umman ta kallata tace, “wallahi koni Fatima ban sani ba dan ni ba abunda nasani game da aurenki”.

Ido tad’ago ta kale Umma ta.

Umma tace, mi yasa naga yanzo kin damu keda bavkisa damuwa a ranki ba kuma yanzo naga kina son kisa?

Tace, “Ummah dole nasa, yanzu Zainab takirani take cemin wai da gaske Daddyn su zan aure,da sauri Umma ta É—ago kai ta kalle ta! tace, “shiyasa nake son nasani kuma kinsan ba yarone zan aure ba koda ganin irin kuÉ—in da yake sakar musu”. tana mai fashewa da kuka.

Umma ta saida tayi ajiyar zuciya.

Kana tace, “kidana kuka Fatima ba kuka ne mafita ba, komai lokaci ne dashi kiya hak’uri da duk in da kika samu kanki kikasance mai hak’uri da godema Allah, ina ce kinga yadda sukayi ma Yayarki kuma tayi hak’uri ta zauna dan haka kema kiyi hak’uri”.

Kuma kinga magana ce a keson nayi suci min mutunci dan haka ko inane za’a kaiki kiyi hak’uri dan Allah, nasan kome nene wata rana sai labari dan haka tashi kije ki cema Kakar ku taba ki number ango kina son kuyi magana da shi kin ga tanan zaki san waye ango” tace, “tau Ummah” Ummah tace, “yauwa y’ar albarka tashi kije”.

Tashi tayi ta tafi bata tsaye ko inaba sai É—akin Kaka Amo.

Kwance, tasame ta tana saurarin radiyo sai da tayi sallama da k’arfi! sannan Kaka Amo tasan da shigo war tah.

Tashi tayi da alamun fitina a fuskar tah. Tace, “lafiya kika zomin kamar wata muna fuka, ko sautin tafiyar ki mutum bayaji”.

Sai Fatima tace, “yaza’ayi ko kiji tunda ida kina sau raren radiyo har muÆ™ofta sai sun sani”.

Sai Kaka Amo tace, “ko Uwarki kaji bai dameni ba”.

Ta kuma cewa, “me kika zomin a É—aki ko ajiya kika bani”.

Fatima tace, “ko É—aya, nadai zone kibani numbar wanda zaku aure min ne”.

Sai Kaka Amo tayi mata kallon k’asa da sama kanan tace, “muna fukar banza wadd tayo gadon munafur ci, duk waya dakukeyi nina baki numbar sa ne?”.

Sai Fatima tace, “wace waya na taÉ“ayi dashi! ni wallahi bama san shiba bale nayi waya dashi”.

Ai kuwa wata kuru-ruwa! Kaka Amo tayi tayo cikin Fatima tana nuna ta da yatsa tana huci, tana cewa, “kun jimin muna fukar yarinya salon ace auren dole ne zamu yima alhali keki ka turu su wajan Baban ki?”.

Sai Kaka Amo ta k’ara da cewa, “dan ubanki jiyama bashi ne naga yazo ba har da kaya yakawo muku keda muna fukar uwarki?”.

Tsawa! tadaka mata tace, ko bashi ba ne?”.

Sai Fatima tace, “Kaka kinsan kowa ye yazo jiya, Daddy su Zainab ne fa”.

Kaka Amo tace, ko dai uban kine fa”.

“Dan haka ba gudu ba jada baya sai kin aureshi”.

Kaka Amo bata kai da rufe bakin ta ba, su kaji ana cewa “ina shigiyar take ita da uwar ta?”.

Wa zasu gani in ba momy ba ita da kawar ta Hajiya Safa .

Da k’arfi! Fatima tace, “Momy lafiya wani abu ya faru ne?”.

Momy tace, “yau sai naci uwarki, niza kici amana ki auremi miji, wallahi kinsha k’arya da ke har muna fukar uwarki?”.

Haniyar da Ummar Fatima da ta jiyo ne yasa ta fitowa daga d’akin ta.

Momy naganin mamar Fatima tafi to daga É—aki ita ko tak’arasa tana nunin ta da yatsa tace, “kece uwar ta to bari kiji da ke har ita ni ba sa’arku bane dan haka tun wuri kujan ye wan-nan zancen aure tsakanin ku da mijin na ko kuyi mamaki na”.

Tana ce musu haka suka juwa suka fita suka bar gida.

Har zasu fita sai ga Hajiya Sa’a zata shigo cikin hanzari.

Kallon-kallo, suka farayi tsakanin su da su momy, amma bawan da yayi ma d’an uwansa magana hakan kowanin su yayi gaba yana ta sake- sake aran sa.

Fitar su keda wuya Fatima ta É—ora hannu akai ta fashe da kuka tana cewa,wallahi bazata aureshi ba sai dai akashe ta”.

Sai Ummah Fatima tace, “Fatima daina kuka, dan bawan da zaiyi miki wanna auren dan wallahi bazan bari ba”.

Aikuwa Kaka Amo da sauri tak’arasa wajan da Ummar Fatima da take nunan ta da d’an yatsa tana cewa, “wallahi bari kiji ko gawar Fatima ce sai ankai ta gidan Alhaji Mansur”.

Suna ciki haka Hajiya Sa’a ta k’araso da sauri tayi wajan su, tana tambayar su meyake faruwa?

Kaka Amo tayi sauri tace, “baki ga wasu mata biyu ba yanzo da zaki gashigo”.

Hajiya Sa’a tace, nagansu, wani abu sukayi muke ne?”.

Sai Kaka Amo tace, “basu yi mana komai ba sun dai yi mana bara zanar kada musake ayi wannan aure”.

Ajiyar zuciya Hajiya Sa’a ta sauke kanan tace, “lnna ku k’yalesu ba a bunda zasuyi ku dai kawai ku cigaba da shirye- shiryen biki”.

Sai Ummar Fatima tace, gaskiya Hajiya bawani shirye -shirye da za’ayi dan y’ata baza tayi wan nan auren ba”.

Aikowa karkusu ku ga yadda Kaka Amo tayi cikin Mamar Fatima tana masifa.

Ita Fatima ba’a bunda takeyi sai kuka dan k’ar Hajiya Sa’a ta shawo kan Kaka Amo tak’yale Ummar Fatima ita ko ta wuce gida.

Aikuwa Baba Babba, nada wowa gida shida Baban Fatima tatashi.

Baban Fatima nadawo wa gida Bayan ya huta sai Ummar Fatima ta fad’a masa duk abunda a ke ciki, yace, “gaskiya wannan abun baiyi ba amma bari naje wajan Yaya muyi magana dashi”.

Sai Ummar Fatima tace, “gaskya katashi kaje kuyi magana”.

tashi yayi yaje wajan Yayan nasa koda yaje ko a can yasame Kaka Amo suna magana da shi.

Bayan yashigo ya zauna ya gaishe su cikin ladabi.

Kowanni su ya amsa ciki-ciki bayan sun amasa sai yace, “Yaya wa nene kuka tsai damma Fatima a ma tsayin miji”.

Ai bai kai da rufe baki ba Kaka Amo tayo cikin sa da masifa.

Tace, to bari kaji wallahi idai ina raye sai Fatima ta aure shi,bari kaji kona mutu wannan auren ba fashi”.

Sai Baban Fatima yace, lnna dan Allah kuyi hak’uri wannan mutum ba tsarar auren ta ba ne, kuma kinga ita d’iyar sa abokiyar ita Fatima ce fa”.

Sai da Kaka Amo tanumfa sa kanan tace, “kai bari kaji kowaye yake awajan ta in dai addini ya yadda Fatima ta aureshi to sai ta aureshi”.

“Tak’ara da cewa, kasan asbar akace za’ayi wannan auren ko to bari kaji ta kai dubanta ga Baba Babba, tace, kaima kanajina” yace, “eh lnna”.

Tace, “kira Alhaji kace, ni Kakar yarin ya nace, gobe za’ayi d’aurin auren shi da Fatima kuma idan ya wuce gobe to nafasa bashi ita”.

Da sauri suka d’ago kai suka kalle ta.

Har zasuyi magana da sauri tada ka musu tsawa! tace, “duk wannda yayi musun wan- nan magana tawa to ban yafema saba, abunda nace kawai nakeson ayi”.

Tana kaiwa nan tatashi tafice tabarsu d’auke da mamaki!.

bayan fitar ta sunjima bawan da ya sake magana.

Sai can Baban Fatima yace, “Yaya kayi yadda lnna tace, nidai ina mata fatar Allah yasa hakashi ne mafi alhairi gare ta”.

Yana kai wa nan yatashi yafice a d’akin.

Ko Baba Babba dake son auren nan yajima yana mamaki lamarin lnnar tasu sai da yagama tunani yadda zaiyi, kana yad’auko wayar sa yakiri Alhaji Mansur ya fad’ama abun da a keciki.

Daddy yace, “bakoma duk da bana ma gari amma zan kir Yayana ya wakil ceni dan ni sai zuwa yamma zan dawo”.

Sai Baba Babba yace, “bakomai amma kafad’a masa kar fe biyu ne za’ayi”.

Daddy yace, “ba komai nagode” kanan sukayi sallam.

Koda Baban Fatima yakoma gida yafad’a musu abinda a keciki Ummar Fatima har da kukan ta, da k’yar Baban Fatima ya la-lashewa ta tayi shuru yace, “kawai muyi hakuri musa mata albarka”.

Ita kam Fatima yadda taga dare haka taga rana, dan cikin dare har da kayan ta tahaÉ—a dumin tabar gari da wannan bakin ciki da abin kunyar da zasu sata har tafi to cikin sanÉ—a har taka wo tsakar gida takama hanyar da zata sada ta da k’ofar fita, ita kuma Kaka Amo tafi to daga toilet, innuwar mutum kawai tagani aikowa tasake butar dake hannuta tana faÉ—in, kufito ga barawo aikowa Baban Fatima da Umman ta da sauri suka fito suna faÉ—in,” lnna nayake?”.

Jikin ta na karkawa tanuna musu hanyar fita waje.

Fitilar dake hannu Baban Fatima ita suka haska a wajan dumin sugani ko za su ganshi aikowa suna haska wa mizasu gani inba Fatima ba jikinta na karkarwa dan itama
Kaka Amo taba ta tsoro.

Fatima suka gani da jikar ta kuma dagani almun fita zatayi.

DaÆ™ar fi Baban ta yace, “Fatima! mi kikeyi anan?”.

Aikowa Kaka Amo najin ance Fatima da hanzari taje k’afafun ta tak’arasa wajan su.

Tana zowa taga Fatima É—auke da jakar ta.

Kaka Amo tace, “nashi ga uku ni Amina to mizan gani haka, ashe shirin da uwarki tashirya miki jiya ko shiyasa naga kuna kus-kus ko tana mai É—ura hannu saman kai tana mai fashewa da kuka.

Aikowa Baban Fatima a fusace yakal-le wajan da Ummar Fatima take.

Yace, “nizakiwa haka duk hak’urin da nabaki ashe bakiyi ba, to bari kiji in har ita Fatima batabar gidan-nan ba to ke yanzo zaki barshi”.

Cikin razana da maganar sa tace, “wallahi Baban Fatima bani nashirya Fatima tatafi ba dan Allah kayi hakuri”.

Tsawa! yadaka mata yace, “wallahi duk bakije ba yanzo zan katse igiyar aurena akanki “.

Bashiri ta É“uÉ—e k’ofa zata fice.

Sai Kaka Amo tace, “a’a babu inda zataje dan yanzu da taje gidan su k’arya da gaskiya zata faÉ—a musu suku ma su yad-da a dinga watsamu a gari”.

Amma tun da karan tse, ta kai duban ta ga Ummar Fatima”ke kifita idan kika kai wuri can da nanu na miki sai kidawo kinga ran tsowar sa ta fice kuma daga inda nace sai kidawo, haka kowa akayi tana fita tadawo.

Baiwar Allah

Kaka Amo tak’ara da cewa kodai bata fice ba idan na tambaye malam sai na san abunyi”.

Ita ko Fatima yana kowo wa wajan datake.

YaÉ—auke ta da wani marin dayasa ta dai na gani nawa ni É—an lokaci, sannan ya wul-lata tsakar gida.

Ya k’ara da cewa, “indai aure ne ba fashi”.

Tofah wannan kakar da rigema take

Comment
Nd
Shere
1/23/20, 11:48 AM – +234 706 211 8047: 💦💦💦💦💦💦💦
💦💦💦💦
💦💦

 *KAWAR* *'YATA* *CE* 

®�
GASKIYA WRITERS ASSOCIATION�
{ Gaskiya É—aya ce daga Æ™inta sai É“ata, burinmu mu faÉ—akar da al’umma domin ribantar duniya da kuma lahira. }

     🎐 ```G•W•A```🎐

GASKIYA DOKIN ƘARFE•🏇🏼

Story & written
By
Sumy�

DEDICATED To…
Maman Ammar💕💕

~Vote & Follow 4Wattpad @ GaskiyaWritersAsso.~

BISMILLAHI RAHAMANIR RAHIM

        *Page* 2�2�

__📖 Safiya na wayewa Kaka Amo tashirya taje gidan Baba Babba, taga yama sa abunda yafaru.

Yace, “ai yau duk wadda a ke ita ce, dan yau zata bar gidan taje can, inta iya ta gudu “.

Kaka Amo tunda tazo gidan Baban Babba.

Bata koma gida ba sai da aka É—aura auren Daddy da Fatima kana tayi godiya ga Allah sannan tace,

“tatafi tagaya ma k’wayen ta da dare suzo akai amarya É—akin ta.

(Kunji fah za’a kai amarya bashiri ba komai) to Allah ya kyau ta.

Tunda su Momy suka bar gidan su Fatima basu tsaya ko ina ba sai wajan sha hararen Malamin su.

Suna zowa bayan sun shiga wajan sa.

Sunyi masa kirarin da suka sabayi masa kana suka É—ura da maganar abunda yakawo su.

Sai daya É—an jima kaÉ—an kana yaÉ—ago kai ya kalle su yace, “subari aduba musu”.

Bayan yagama Æ´an surku llensa.

kana yace, “musu da matsala.

YaÆ™ara da cewa, amma zan baku wani abu ayi masa hayaÆ™i dashi da zaran yashaÆ™i hayaÆ™in to koda saura awa É—aya ne baza’ayi auren ba”.

Duk da momy taji tsoro amma kuma da yace, za’afa sa sai taji na tsowa.

Karɓa tayi tana mai yi masa godiya kana suka tashi zasu fita.

Har zasu fita yaÉ—ago kansa yallesu yace, kutabbar da yasheÆ™i haÆ™in kafin É—auren auren. yak’ara da cewa, “dan in bai she Æ™a ba ba abunda zai hana yayi wannan auren”.

Momy tace, “a dole yasha Æ™a dan gobe daya cemin ya sauka kafin ya Æ™araso zan tirari gidan dashi”.

Yace, “to kuna iya tafiya”.

Momy haka suka dawo gida ciki da farin ciki, dan yanzo dawowar Daddy kawai takeji ra.

Haka Momy ta kwana cikin farin ciki dan koda wuraren azzahar sai da takira Daddy yaƙara sheda mata zuwa yamma zai dawo.

Zuwa k’arfe huÉ—u na yamma sai ga Hajiya Shafah tazo gidan Momy cikin da tashin hankali.

Koda Momy tagan ta ita ma sai tashiga tashin hankali.

Sai da Hajiya Shafa ta zauna kana ta kalle Momy tace, “kin san abunda ke faruwa kowa?”.

Momy ciki da tashin haka tace, “a’a wallahi bansani ba Hajiya Shafa, mike faruwa hala?”.

Dan gabanta sai dukan uku-uku yakeyi.

Hajiya Shafa tace, “to bari kiji wallahi anyi ta taÆ™are, anwa mai dame d’aya sata”.

Momy tace, “dan Allah kifid-dani a duhu”.

Sai Hajiya Shafa tace, “yanzu Alhaji ya dawo gida yana ta fara’a, na tambaye shi ko kasuwa ce tayi daÉ—i yake fara’a?

Sai yace, “saÉ“anin haka, yak’ara da cewa É—aurin auren nan ne ya burgeni”.

Nace, “wani É—aurin aure?.

Yace, “na Alhaji Mansur”.

Ban san lokacin da namiki tsaye ba.

Amma daga baya sai nawa yince masa nace, shin ba assabar bane”.

Yace, “a’a yau suka maida shi”.

Hajiya Shafa Kallon Momy tayi domin tabata shawar ta yanda abun zai kasan ce Aikowa Momy tagani ta zube tafaɗi ƙasa sumam miya.

Ai kowa Hajiya Shafa ta saka ihu!

Taje ta É—auko ruwa masu sanye ta watsama ta.

Ajiyar zuciya Momy ta sauke, kana Hajiya Shafa ta Æ™araso wajan data ke zaune tada fa kafaÉ—ar ta tace, “kiyi hak’uri kinji ai insun san wata basu san wata ba”..

Nan dai Hajiy Shafa tayi ta kwan tar ma Momy da hakali har tasamu taÉ—an na tso san nan tace, “kuma kishirya dan naji yace, yau za’akawu amarya.

Momy har zata É—aga hankalin ta Hajiyan Shafa tace, “kada ki soma dan gobe zamu haÉ—u metting”.

Dan haka ki tashi ki gyara jikinki kinsa mijinki nabi sa hanya kuma ba musan yasan kina ciki wani hali tace, “to zan kiyaye”.

Haka ko akayi dare nayi aka kawo amarya duk waÉ—an da suka kawo ta babu yaro dukan su tsofaffine.

Koda suka zo kawo amarya Daddy yadawo.

Hajiya Sa’a ita-ta kaisu wajan da za’akai Fatima, dan koda ma Daddy yajema da kyaran sa.

Aikowa Momy naji hayaniyar ƴan kawo amarya hankalin ta yaƙara tashi bata ma fito ba har suka bar gidan.

Sai da Hajiya Sa’a taga komai ya kammala sannan tayi musu sallama ta wuce gidan ta.

Momy ko sai data ji alamun kowa yafice a gidan san nan tashirya kamar ba abun da keda mun ta taje É—akin Daddy tace, yatashi tara kashi É—akin amarya cikin wani irin salon ta.

Yace, “a’a ta dai kawo masa abinci yaci yunwa yakeji.

bayan ta kawo masa yaci yak’oshi.

Yace, “ta tashi tazo yara ka ta”. tace, “a’a sai tara kashi. daÆ™yar ya samu ta yarda yara kata.

sai da yakai ta har É—akin ta yayi mata sallama san nan shima ya wuce É—akin amaryar sa.

Cigaban labari

Muje zuwa

Comment
Nd
Shere
1/23/20, 11:48 AM – +234 706 211 8047: 💦💦💦💦💦💦💦
💦💦💦💦
💦💦

 *KAWAR* *'YATA* *CE* 

®�
GASKIYA WRITERS ASSOCIATION�
{ Gaskiya É—aya ce daga Æ™inta sai É“ata, burinmu mu faÉ—akar da al’umma domin ribantar duniya da kuma lahira. }

     🎐 ```G•W•A```🎐

GASKIYA DOKIN ƘARFE•🏇🏼

Story & written
By
Sumy�

Dedicated to..
Masoyiya NANA Aysha💕💕

~Vote & Follow 4Wattpad @ GaskiyaWritersAsso.~

BISMILLHI RAHAMANIR RAHIM

     *Page* 2�3�

__📖 Sai da tagama tunanin ta tagama rera kuka, tashi tayi taje ta gyara gidan duk da bashi da wata ƙazan ta.

Sai da taga komai yayi dai-dai, tayi wanka tashiriya tagabatar da sallah.

Bayan ta kammala sallah ta É—auko alÆ™ur’ani tafara karantawa cikin muryar ta mai daÉ—in saurare.

Sallamar da Daddy yayi ne yasa tana kai aya tasha fa.

Tashi tayi tazo har wajan dayake ta duƙa ciki da ladabi ta gaishe shi.

Sai da yaÉ—ago kai ya kalle ta san nan ya amsa ciki da kulawa ya Æ™ara dacewa, “Naga fusakar ki kamar ta kunbura miyasa meta, ko kuka kiyaye ne?”.

bata ce masa komai ba yace, “to kiyi hakuri nasan kaÉ—ai ce ne kuma zaman kaÉ—ai ce ba daÉ—i”.

Sai da yaÆ™ara mata kallo sosai kana yace, bari nasa akawo mana abinci nasan akwai yauwa a tari dake, dan nasan ko É—azo bakici wani abun Æ™irki ba dan ina sauri ne shiyasa na kyaleki”.

Bai tsaya jin mizata ce ba, yadanna wata ƙararrawa bai jima da dan nata ba sai aka fara yi musu knocking.

Damar shigowa yaba da sai ga wata mata tashigo É—auke da kayan abinci, saman dinning takai taje ra.

Kana ta ƙarasu wajan da suke tana mai gaishe su cinki har shin turanci

Daddy ya fara amsa mata sannan Fatima taÉ—ago ta kalle ta sannan ta amsa mata ciki da kulewa, kana tafice warta.

Sai da ta fita Daddy ya kalle Fatima yace, “taso muje kici abinci dan nima yauwa nakeji”.

Bai tsaye jin miza tace ba yatshi yayi wajan dinning yaje kujera ya zauna.

Tana ganin yatashi itama tabi bayan shi, tazo itama taje kuje har zata zauna yace, “a’a wadda ke kusa dashi yanuna mata yace, ta zauna”.

Haka tazo ta zauna ba dan ran ta yaso ba, tayi saveg din su kana suka fara ci.

Daddy shi kaÉ—ai keci ita ko ba ci takeyi ba dan inban da tsa korar sa ba abunda takiyi kuma Daddy duk yana kule da ita.

Sai da yaji cikinsa ya É—auka san nan yakalle pelat É—in ga ban ta.

Komai bata ciba dan haka spoon din hannu ta ya ƙara ɓa.

Kallon sa tayi abinci yaÉ—ebo zai kai bakin ta.

Da sauri ta kauce fusakar ta “tana faÉ—in Daddy na koshi fah”.

Kallon ta yayi yace, “naji amma ki karÉ“a wan nan kici”.

Tace, “to Daddy bani zan ci da kai na”yace, a’a ni zan baki da kai na”.

Bata iyayi masa musu dan haka sai da ta kulle idon ta sannu a hankali tafara buÉ—e bakin ta yafara ciyar da ita har sai da yatabbar da ta koshi san nan ya kyaleta.

Har zata tashi tabar wuri yayi sauri yace, “kije kishirya zamu fita zaga gari”.

Kamar baza tayi magana ba tace, “to”.

Kallon sa tayi tana son tayi masa magana kuma tafa sa.

Har tafara tafiya sai yace, “Fatima mikike son kice kinyi shuru please kifaÉ—a min”.

Kamar bazayi magana ba tace, dama-dama kuma sai tayi shuru.

Yace, “dama me? kifaÉ—a mana”.

Tace, “wayar da kace sai kadawo kabani nakira Ummah na”.

Yace, “oh sorry naman tane” wata waye
sabuwa yamiÆ™a mata yace, gata nan har da number Hajiya Sa’a tana ciki sai ki kira ta dan tana son magana da ke”.

Ba musu ta karɓa tayi masa godiya tayi tafiyar ta ɗaki.

Sai da ta zauna, kana tane mu number Ummah ta takira ba jimawa aka É—aga.

Ajiyar zuciya tasauke kana tayi mata sallama.

Ummah ta najin muryar Fatima ta faÉ—a-É—a fa’ar ta tace, “Fatima kece?”.

Tace, “Ummah nice, ya kuke da fatar duk kuna lafiya”.

Ummah tace, “lafiya kalau muke, ina fatar lafiya kuka sauka”.

Bayan sun gama gaisawa suka cigaba da fira, Ummah taƙara mata har da nasiha akan tayi biyayya ga mijin ta, haka tayi-tayi mata nasiha daga baya sukayi sallama.

Kiran Hajiya Sa’a tayi itama sun jima suna fira kana tayi sallama da ita kafin suyi salama sada ta cema Fatima takira Hajiya Ummu su gaisa tace, “yanzo kowa”.

Bayan sun gama waya da Hajiya Sa’a.

Kiran Hajiya Ummu tayi suka gaisa kana itama taƙara mata wani ƙarin bayani sosai tayi mata jan kunne akan tayi wa mijin ta biyya.

Suna gama waya tana cikin tunanin maganar da Hajiya Ummu tayi mata ta ƙarshe.

Sai ga Daddy yashigo yana faÉ—in kin shirya muta fi”.

Tace, “Daddy kayi hakuri bari na shirya yace, to ina falo ina jiran ki”.

Bayan ta shirya tafito tasa meshi zaune yana jiran ta .

Tunda tafi to yakife ta da ido yana kallon ta, da wani irin kyau ne taƙara yimasa.

Kallon da yake mata ne yasa taki ƙarasa tafiyar da takeyi.

Saboda wata kunya takeji idan yana mata wannan kallo.

Dan ita bata son wannan kallon da yake ma.

Tana cikin wannan tuna nin sai jinshi tayi kusa da ita yana yacewa, “kinyi tsaye kizo mutafi ko baki zowa mufa sa ? “.

Tace, a’a Daddy mutafi”.

Hannu ta yariƙa suka fara tafiy, haka tafara tafita ya kamar wadda kwai yafashe ma ciki.

Haka sukaci gaba da tafiya har suka kawo wajan da motar sa take.

BuÉ—ema ta yafarayi tashi ga kana shima yadawa zaman direba yazauna, kana yaje mota suka tafi.

Sunyi yawo sosai yakai ta wurare wasan ne da na shaƙa tawa da dama, tun bata saki jikin ta har tafara sake.

Sai da dare yayi san nan suka dawo gida.

Yana yin picking tabuÉ—e mota zata fita.

Hannu ta taji yari Æ™e kallon sa tayi taga ita yake kallo yace, mikikewa sauri ne?”.

Kamar baza tayi magana ba tace,

“Daddy bacci nake ji” tana magana kamar zatayi kuka.

Yace, “to muje kiyi bacci sai da yabaÉ—e yafito san nan yazo yabuÉ—e mata tafi to kana su shiga tare.

Da shigar ta ka tsaye bedroom ta wuce ta rage kayan jikin ta San nan ta shiga toilet tayi wanka tafi to.

Bayan ta gyara jikin ta kayan bacci tasa ka masu kauri har zata kwanta ta tuna alƙawarin da tawa Hajiya Ummu inza ta kwan ta zata sha fa turin da ta bata.

Har tasu ta barshi kuma sai tadawo taÉ—auka tasha fa.

Tana ɓuɗe kulbar taji ƙamshisa yayi mata daɗi sosai dan shi tafara shife jikin ta da shi.

Tana gamawa ta bi lafiyar gado ta kwan ta bacci.

Bata jima da kwan ciya ba Daddy yashago É—akin.

kallon ta yayi yaga har tafar bacci dan haka shima yaje yayi wan ka yafito.

bayan yagama gyara jikin shi yabi lafitar gado ya kwanta.

Yana kwantawa wan sihirttacin ƙamshi ne ya bige hancin sa wanda yafara jansa tun shigo warsa ɗakin.

Haka ya kwanta jikin sa duk yayi sanyi yarasa yazai yi yaji daÉ—i.

Ahankali yafara jawo ta jikin sa, aikowa jikin su na haÉ—uwa waji daya, wata irin ajiyar zuciya ya sauke.

Yana mai ƙara sanya ta a jikin sa kamar zai madata aciki.

dan ita har bacci yayi awon gaba da ita.

Kamar a mafarki taji kamar ana shafar jikin ta.

Idon ta ta buÉ—e taji abunda taji da gaski ne, aikowa jinkin ta ne yafara karkarwa bashiri tasan ya mishi kuka.

Yayi nisa cikin abun da yake mata dan haka bai masan ta farka ba, kukan ta dayaji ne yasa shi dakatawa dan gabaki É—aya jikin sa yayi sanye yarasa me zaiyi.

Yana cikin wan nan tunani ne yaje zata tashi tabar wajan.

Da sauri ya janyo ta jikin sa, aikowa takara sanya masa kuka tana cewa,

“Daddy dan Allah kara budani zan koma parlour na kwan ta”.

Komai bace mata ba dan ko magana ya kasa.

Ita ko sai famar kuka take masa.

Kukan nata yaji yayi masa yawa dan haka bai san lokacin da ya haÉ—e bakin su waje É—aba, sai da yayi kiss din ta sun ran shi san nan yabar.

Tashi yayi yaje toilet yawa tsa ruwa kana ya É—uru alwala ya koma falo yashin fiÉ—a sallaya yafar gabatar da nafila.

Tunda yatashi yabar ta take kuka tana mai dana sanin zowa ta wan nan ƙasar.

Sai datayi mai isar ta tatashi taje tolit ta watsa ruwa kana tazo ta kulle dakin san nan tayi addu’a kwanciya takwan ta bacci ba tajima da kwanciya ba bacci yayi awun gaba da ita..

Muje zuwa

Comment
Nd
Shere
1/23/20, 11:48 AM – +234 706 211 8047: 💦💦💦💦💦💦💦
💦💦💦💦
💦💦

 *KAWAR* *'YATA* *CE* 

®�
GASKIYA WRITERS ASSOCIATION�
{ Gaskiya É—aya ce daga Æ™inta sai É“ata, burinmu mu faÉ—akar da al’umma domin ribantar duniya da kuma lahira. }

     🎐 ```G•W•A```🎐

GASKIYA DOKIN ƘARFE•🏇🏼

Story & written
By
Sumy�

Dediceted to
Miss xerks🌺

~Vote & Follow 4Wattpad @ GaskiyaWritersAsso.~

BISMILLAHI RAHAMANIR RAHIM

       *Page* 2�4� 

__📖 Gari Yana waye Daddy da zazzaɓi mai zafi ya tashi dan ko bacci bai samu ba, danshi baya son yashi ga irin wannan yanayi dan da bai samu biyan buƙata ba sai ya ƙwanta ciyo na kwana biyu.

Ita ko batama sani ba dan tana tashi tayi sallah tayi azkar É—in data saba kana ta koma baccin ta.

Sai datayi baccin ta mai isar ta, kana ta tashi saboda yanwar da take ji.

Da sauri tazo taɓuɗe ƙofa dan a tunanin ta Daddy yasa an kawo breakfast yaci yafi ta.

Aikowa tana ɓuɗe ƙofa taga Daddy kwance, a yadda ta ganshi ne hankalin ta ba ƙaramin tashi yayi ba.

Da hanzari taÆ™arasa wajan da yake kwance, tana kiran Daddy meya sameka?”.

Da taga yaki bata amsa,aikowa hankalin ta ya Æ™ara tashi tafara yimasa kuka tana cewa, “Daddy dan Allah katashi.” tana girgizar masa jiki.

Kukan ta da yaji yayi yawa ne yayi karfin halin cewa, “Teema ki daina kuka,wannan ai Æ™aramin ciyo ne kinji kidai na”.

Tace,”to Daddy kakira doctor Yaduba ka Mana, please Daddy.” tana mai Sanya masa kuka.

Kukan nata yayi masa yawa dan haka waya yayi mata nuni data É—auko masa.

Da sauri ta É—auko masa wayar takawo masa.

FaÉ—a mata numbar da zata kira yayi, tana kira doctor ya É—aga tafaÉ—a mishi abinda ke faruwa

Ba’a d’auki lokaci ba Docter d’in yazo.

Kwocking yayi musu, tashi tayi zata je taɓuɗe masa ƙofar.har ta juya zata tafi taji Daddy yariƙe mata hannu.

kallon sa tayi tace, “Daddy doctor ne zai duba ka”.

Sai da ya kara duban ta da kyau kana yayi karfin halin cewa, “badai haka zakije ba, kije kisa hijab d’in ki.”

Dubin yadda take tayi dan ita sam ta manta yadda take.

Tashi tayi taje ta sanya hijab nata kana taje taɓude masa ƙofar.

Doctor na shigowa bayan sun gaisa tanuna masa wajan da Daddy yake.

Duba shi ya farayi yana tambayarsa, haka har yagama dubashi yabashi magani kana doctor yace, “kona baka magani bashi zaisa kaji sauki ba,a’a zai dai rage maka zafin zazzaÉ“i ne kawai.”

sai da ya dubi Daddy da kyau kana yaci gaba da cewa, “idan kana son kasamun sauÆ™i to ga madam nan yanzu zaka samu sauki”.

Yana murmushi yana faÉ—in haka kana yayi musu sallama ya wuce.

Bayan ya fita Fatima tazo ta sanya aka kawo musu breakfast. daƙer tasamu yaci kaɗan yasha magani ya kwanta.

Sai da taga komai yayi dai-dai har yasamu yayi bacci taje tayi brekfast ta gyara gidan kana tazo ta gyara jikin ta tazauna jiran tashin shi.

Haka dai tayi ta jinyar Daddy har yasamu sauƙi sosai dan har aiki yafita yau.

kwance take tagama aikin ta, da ba abinda takeyi inba gyaran gida ba dan koshi ita tace tafi son tayi da kan ta.

Wayar ta ce tafara ruri duba screen É—in wayar tayi sunan Hajiya Ummu dataga yana yawo yasata yin tsaki kaÉ—an, sai da takusan tsinkewa kana taÉ—auka.

Sallama Fatima tayi bayan takarÉ“a suka gaisa da ita kana Hajiya Ummu tace,”Fatima shine kika daina kirana dan kar nace kima mijin ki biyyaya ko?”.

Fatima tace, “a’a wallahi ba haka bane.”

Hajiya Ummu tace, “ba haka bane?to miye dalilin ki? ke tsaya kiji Fatima, ko minene yanzu Shi mijinki ne, kuma ki sani ke dashi Babu Mai raba ku sai mutuwa,dan haka ki natsu kiriÆ™i mijinki kodan kisamu rabauta duniya da lahira.”

Sai da tayi mata nasiha sosai kana ta É—ora dacewa, “kin yi affani da kayan da nabaki kuwa? kuma wallahi kada kimin Æ™arya kinji ko”.

Fatima tace,”gaskya Hajiya wannan na shafawar kawai nashafa shima sau É—aya”.

Hajiy Ummu tace, “Fatima wai miyasa ba kijin magana ne? dan Allah kinsa konawa Hajiya Sa’a ta kashe kuwa?”

Fad’a tayi Mata sosai sannan daga baya tadawo tana rarrashin ta.

Bayan ta gama yi Mata fad’an cikin dubara tasa Fatima tayi mata alÆ™awarin yau zatayi duk abinda tace tayi”.

Bayan sunyi sallama tashi tayi taje taÉ—auko duk abinda Hajiya Ummu taba ta.

Zama tayi taci wannan taci wancan,amna dataji akwai daci Sai ta ajiye shi.

haka dai tayi-tayi har wasa-wasa taci Mai yawan gaske.

Turarurrukan ta É—auko ta shafe duka jikinta dasu.

Nan da Nan gidan ya d’auki k’amshi gaba d’ayanshi,saboda turarurrukan suna da mugun k’amshi.

Sai da akayi i’sha Daddy yadawo tunda ya shigo falo yaji wani kamshi mai sanyin daÉ—in gaske sai tashi suke acikin gidan.

parlour ya zauna yana shaÆ™ar Æ™amshin wani daÉ—i nashigar shi azuciya gaba É—aya jikin sa yaya sanyi danshi yakasa Æ™arasawa cikin d’akin dan ita bata masan yadawo ba.

Tagama shirin ta tayi kyau sosai wayar ta ta fito ta d’auka.

Tana fitowa taga mutum zaune dan har yaso yabata tsoro, tsaye tayi takasa ƙarasawa taɗau wayar kuma takasa komawa.

Kamar mutsi yaji ya juwa dan yaga ko miye, ita yagani tsaye kamar wadda aka dasa waje É—aya.

Murmushi yayi Mata,sannan ya zuba Mata dukkan idanuwanshi Saboda ba karamin kyau tayi masa ba.

Riga da siket ne sanye ajikin ta pink colour kayan sun karɓeta.

A hankali yafurta tare dayin k’asa da muryarshi yace,”kizo mana”.

Yi tayi kamar bata ji shi ba, sai da ta d’anyi seonds sannan tafara takawa a hakali har takawo wajensa.

Durkusawa tayi cikin ladabi ta gaida shi.

Ajiyar zuciya yayi Sannan ya amsa acan kasan mak’ogwaran Shi,sautin muryarshi ya nuna shauk’in tsananin sonta a bayyane.

Tashi tayi taje takawo masa ruwa masu sanyi.

Tana ajiye masa yajawo ta jikin sa. Æ™oÆ™arin tashi ta rink’ayi amma ya hanata.

Rungume ta Yayi a jikinsa yana shaÆ™ar kamshin jikin ta yace,”duk ni akayi wa wannan kwalliyar? gaskiya na gode sosai”.

Ƙokarin ture shi ta rink’a yi tana cewa, “Daddy dan Allah kabar ni naje sallah zanyi”.

Akasalance yace, “bakiyi sallah bane?”

Fatima K’ara marairaice wa tace, “eh banyi ba”.

Daddy ya numfasa Yace, “to kije kiyi kizo kibani abinci naci kinji.”

Fatima jiki na rawa tace, “to sakeni natashi”.

Bayan ta tashi yabi ta da kallo har sai da yabar ganin ta kana ya sauke ajiyar zuciya yace, “my teema inasonki dayawa” maida idanuwansa Yayi ya lumshe Yana aiyano ta ajikinsa.

Har tagama abunda takeyi tadawo a inda tabarshi anan tasame shi zaune.

Kallon ta yayi yace, “teema inason nayi wanka ki haÉ—amin ruwa please”.

Tace, “to tashi tayi taje ta had’a mashi ruwan wanka. tana cikin haÉ—amasa sai ganinshi tayi ya shigo a toilet É—in.

Da sauri ta kama hanya zata fito aikowa ya riÆ™eta yace, “tazo suyi wankan tare.”

aikuwa kuka ta sanya mashi dolen shi yabar ta ta fito.

Tana fitowa tana share hawaye tana faÉ—in,”wai shi Daddy nan ko kunya ta bayaji ni fah Æ´arsa ce”

Bayan yayi wanka ya fito takawo masa abinci yaci.

Bayan yagama ci yazo wajan datake ya zauna aikuwa yana zama ta miÆ™e zata tafi riÆ™eta yayi yace, “ina zakije ki tsaya muyi fira please”.

Tace, “a’a Daddy bacci nakeji kabari sai gobe zamuyi fira”.

Yace, “to sai da safe tace, “to Daddy”.

Tana shiga bedroom É—inta har da sanya key ta rufe kana tayi wanka tazo tayi addu’a ta kwanta.

Shiko Daddy sai da yagama kallon da yakeyi yatashi dumin yaje ya kwanta yana tura ƙofa yajita rufe key din sa yaɗauko yazo yabude yashiga kana ya kulle.

Saida ya canja kayan sa zuwa kayan bacci kana yazo yayi addu’a shima ya kwanta dan ita tajima dayin bacci.

Yana kwantawa yajawo ta jikin sa turarin da tasanye ne yadaki hancinsa aikuwa ya rikice don bai san lokacin da yafara wasa da ita ba.

Cikin bacci taji abinda takeji ba shiri ta tashi zata gudu. domin abinda yake Mata yafi na sauran Rana ku.

ƙoƙarin tashi take amma takasa dan gabaki ɗaya yasanya ta cikin jikin sa dan yanzu burinshi kawai ya rabata da kayan jikin ta.

Da taga abun nashi da gaske yakeyi aikuwa tafara kuka, shiko bai masan tanayi ba dan haka ya cigaba da wasa da ita son ran shi, bakin kukan nan ma ya haÉ—eshi danashi hmmmm daÆ™ar tasamu ya sakar mata baki ta fara wani irin kuka mai tada hankalin mai saurare.tana faÉ—in “Daddy nifa Æ´arka ce ka taimakamin dan Allah.”

shi kuwa ma gabaki d’aya baya cikin hankalinsa dan yau ji yake idan bai samu biyan buÆ™ata ba zai iya mutuwa…

To fah Su Daddy🤔

Muje zuwa

Comment
Nd
Shere
1/23/20, 11:48 AM – +234 706 211 8047: 💦💦💦💦💦💦💦
💦💦💦💦
💦💦

 *KAWAR* *'YATA* *CE* 

®�
GASKIYA WRITERS ASSOCIATION�
{ Gaskiya É—aya ce daga Æ™inta sai É“ata, burinmu mu faÉ—akar da al’umma domin ribantar duniya da kuma lahira. }

     🎐 ```G•W•A```🎐

GASKIYA DOKIN ƘARFE•🏇🏼

Story & written
By
Sumy�

BISMILLAHI RAHAMANIR RAHIM

Dediceted to..
Aunty Binta 💕💕
Marubuciyar
CIN AMANAR ƘUNA

~Vote & Follow 4Wattpad @ GaskiyaWritersAsso.~

        *Page* 2�5� 

_📖 Kuka take babu ƙau-ƙau tawa shiko bai masan tana yi ba
dan yayi nisa.

Dan har yayi nasarar raba ta da kayan jikin ta, da taga yayi nisa baya jin kira, ta koma addu’a Allah kasa kada yara bata da abinda take ma masoyin ta tanadi.

Tana cikin wannan tunanin ne taji ya fara addu’a saduwa da iyali, aikowa wata irin kururuwa k’ara ta sanya masa tana faÉ—in.

“Wayyo Daddy dan Allah kada ka illatamin rayuwa ka kyaleni dan Allah”.

Bai masan tanayi ba a hankali ya bida ita har ya rabata da farin cikin ta.

Aikowa wani zafi ne ya ratsa sassan jikin ta yazo har ƙwaƙwalwar ta wata ƙara mai ciki da dana sanin zowan ta wannan ƙasar tasanye.

Wadda da ace a gidan su Momy ne da babu abinda zai hana sujita.

Sai da yaɗan samu biyan buƙata sannan ya ƙyaleta amma badan ya gaji ba.

Sai daya sauke ajiyar zuciya kana yayi ma Allah kirari yayi masa godiya sosai.

Kana ya jawota jikin sa yana saukar da ajiyar zuciya, wani son ta na k’ara shigarsa, sosai ya sanyata jikinsa ya rasa sama mezai ce mata yayi dan wani farin cikine ke ziyartar zuciyar shi wanda baya misaltuwa.

Kukan da take ne ya dawo da hankalin sa daga tunanin da yake, wanda baya fita sosai saboda kuka har muryar ta dushe.

Tashi yayi yaje toilet ya haÉ—a mata ruwa masu zafi yadda zasuyi mata maganin abinda yayi mata.

Zuwa yayi ya É—auke ta bai tsaye ko ina da ita ba sai cikin ruwan,da ya haÉ—a mata aikowa wata irin k’ara ta sanya wadda ta tsora tashi.

Sai da ya gasa ta sosai kana ya kyaleta.

Dan har yaso yayi mata wanka amma tak’i bari tace, ita zatayi da kanta dole yabar ta.

Yana bakin ƙofar toilet a tsaye har sai da ta gama wankan ta fito da ƙir take tafiya.

Yana ganin ta fito da sauri ya ƙarasa wajanta dan daƙir take tafiya.

Yana ƙarasuwa wajan ta bai tsaye komai ba ya ɗauke ta kamar wata ƴar tsana.

Bai tsaye da ita ko inaba sai sama gado yaje ya É—auko mata magani zazzaÉ“i dana bacci ya kawo mata da ky’ar ya samu tasha kana ta kwanta.

Sai da ya tabbatar da tayi bacci ya gyara mata kwanciya kana yasamu natsowa.

Toilet ya shiga yaje yayi wanka kana ya ɗuru alwala yazo ya tada sallah nafila yana ƙara godema Allah daya nuna masa wannan ranar.

Koda safiya ta waye Daddy ya fara tashi har yayi sallah bata ta shiba kuma yana son ya tashe ta amma ya kasa.

Yana cikin tunanin ya zaiyi ya tashe ta sai gashi ta farka da kanta.

Tana buÉ—e idonta sukayi 4 eyes dashi ba tasan lokacin da ta jawo bargo data yi rufa dashi ba ta rufe fusakar ta.

Kuka tasan ya mishi tace, sai ya madata gida, hakuri yayi t abata da ƙir yasamu ta ɗan hakura yace,.

“To tashi kiyi sallah gari ya waye kinga kada rana tafito bakiyi ba”. Amsa ta bashi da cewa.

“To amma sai ka fita zanyi”. Ya ce, “zaki iya tashi kowa”?. tace, “eh zan iya” dan a yanzo ko magana bata so ya nayi mata.

Sai da ya fita kana ta tashi da ƙir ta fara tafiya, sai taji ta daina jin ciyo ba kamar jiya ba.

Da haka taje tayi wanka saida taƙara gasa jikin ta kana ta ɗuru alwala tazo ta gabatar da sallah.

Bayan ta kammala tazo takoma tayi kwanciyar ta bata jima da kwanciya ba bacci yayi awun gaba da ita.

Haka dai Daddy yayi tajinyar ta har tasamu sauk’i dan ga baki d’aya ya daina fita ko wajan aikinsa waya yayi musu bazai samu fita ba na kwana biyu.

Aikowa tun tana jin haushi Daddy har tazo ta daina ta fara sakin jikin ta dashi har da Daddy yayi mata wayo sai da aka koma ruwa..

Kuyi hakuri da wannan

Comment
Nd
Shera
1/23/20, 11:48 AM – +234 706 211 8047: 💦💦💦💦💦💦💦
💦💦💦💦
💦💦

 *KAWAR* *'YATA* *CE* 

®�
GASKIYA WRITERS ASSOCIATION�
{ Gaskiya É—aya ce daga Æ™inta sai É“ata, burinmu mu faÉ—akar da al’umma domin ribantar duniya da kuma lahira. }

     🎐 ```G•W•A```🎐

GASKIYA DOKIN ƘARFE•🏇🏼

Story & written
By
Sumy

Dediceted to..
Family 💕💕💕💕

~Vote & Follow 4Wattpad @ GaskiyaWritersAsso.~

BISMILLAHI RAHAMANIR RAHAM

       *Page* 2�6�

__📖 Tun bata saki jikin ta dashi ba har ta dawo ta saki, tana yi wa Daddy biyya dai-dai gwar-gwado, dan yanzo idan kan gansu ita da Daddy sai karan tsa auren soyayyane sukayi.

Saboda Hajiya Ummah da Umman ta, akai-akai suna kiran ta suna bata shawara akan ta yiwa mijin ta biyya hardai ta amince zatayi masa biyya koda ran ta bai soba.

Dan yanzo ta saki jiki dashi sosai dan har sunyi sabon komai zasuyi a tare Wata rana ko aiki zaije da ita yake zuwa sosai sukayi sabo.

Dan Hajiya Sa’a har kiran shi tayi tace, ya dawo an kusa bikin Sulaiman Da Abdallahi, Amma yace, mata tayi hak’uri har yanzo bai gama aiki ba da Æ™yar ta yadda a kan cewa, bayan biki da sati zasu dawo.

Kuma gashi Momy tada meshi a kan sai yadawo dan ita hankalin ta yaki ya kwanta dan ta san daya dawo dole ko ina suka kai Fatima su mai data.

yau ma kamar haka suna kwance suna bacci safe dan yanzu Daddy ya gama a kin da ya kawo shi ƙasar hutan sa kawai yakeyi shida abar son shi.

Wayar sace ta fara ruri cikin bacci yaji kamar wayarsa na ƙara, sai da ya gyara kwanciyar sa kana yayi picking.

Sallama tayi masa ya amsa tama bata ma bari suka gaisa ba ta sanya mishi kuka ciki da kissa.

A razane yatashi daga kwanciyar da yake yace, “Hajiya lafiya miyasa meki? please ki gayamin”.

Ba tace masa komai ba kuka kawai take masa, duk inda hankalin shi yake yatashi rasama mizai yi yayi sai can tace masa,

“Ba dole nayi kuka ba tunda nake da kai baka taÉ“a tafiya kajima kamar wannan ba”.

Sai da yayi ajiyar zuciya kana yace,

“Wallahi naÉ—auka wani abu yasa meku, duk kin tadamin da hankali”.
tace

Hmmmm ciki da son taji ina Fatima take, tace,

“Ya za’ayi hankalika ya tashi tunda Hajiya Sa’a ta turu maka Fatimar ka, ta Æ™arasa zancin tana murmushi mai sauti.

Tana faÉ—ar haka sai da gabansa yafaÉ—i, amma dayake namijin duniya ne sai ya basar yace,

“Hajiya Sa’a ce ta faÉ—amiki Fatima na wurina ne?”.

Momy tace, a’a nasan dabata wajanka da kajima da dawowa, to koma tana wajanka aini zanfi samu kwanciyar hankali dan bana sun abarmin kai ka zauna kai kad’ai ba mai kulada kai, tak’ara da cewa,

“Ni kabani ita mu gaisa in tana kusa dan munyi kewar ta da yawa, musamman Zainab da kulsum”.

Murmushi yayi mai sauti yace “tana bacci amma idan ta farka zanki kiraki”.

Aikowa yana cewa haka gaban ta yayi mumunar faÉ—uwa wadda yasa kar mata jiri lokaci d’aya, cikin ranta tace, “ashe da gaske suna tare”.

Shurun dayaji tayi ne yace, “Hello ko bakijina”.

Cikin da kisar ta tace, “kayi hakuri network É—in ne ba kyau shiyasa amma dan Allah idan ta farka kabata waya muyi magana najita ko naji sanyi, Idan kuma kana bata wuya naji dole naje na faÉ—ama Hajiya Sa’a kamai muna ita”.

Dariya yayi yace, “to nama fasa bata bale ta gayamiki É—in.

Akowa magiya taringa yi masa sai da ya amince zai bata wayar kana sukayi sallama, dan ƙarfin hali ne kawai yasa takeyin magana dan neman take sugama wayar tasan abinyi.

Aikowa suna gama wayar ta É—au key É—in motar ta, Allah ne kawai yakai ta gidan Hajiya Shafa, tana shiga tasa meta zaune ita da Hajiya Binta sana magar yadda wannan auren kezo musu bazata

A harge tse ta ƙarasu wajan da suke ta zauna, kuka tasan ya musu.

Hankalinsu inyayi dubu ya tashi da ƙyar suka samu tayi shuru tafaɗa musu abunda ke faruwa.

Sai Hajiya Binta tace, “ni wallahi tun wan can lokacin nakeji a jikina tare da ita yatafi amma saboda hankalina ba kwanciba shiya sanya ban ce komai ba”.

Sai da Hajiya Shafa ta nisa kana tace, “ku kwantar da hankalinku, jiya an faÉ—amin wani shahararrin boka a wani Æ™auye kuma aikinsa kamar yankan uÆ™ane dan haka ku kwan, da shiri gobe ita ce ranar da a kezowa wajan sa dan haka inkun shirya sai muje É—in”.

Gaba É—ayan su suka haÉ—a baki wajan cewa ko yanzu a kezowa zasuje dan haka gobe da safe za suzo sutafi.

Haka sukayi tafirar su kana sukayi sallama akan sai gobe.


Tana cikin bacci taji kamar Daddy na waya kuma kamar ba lafiya ba irin yadda taji yana magana.

Dan haka yana gama wayar tace, “Daddy lafiya kowa?”.

Juyuwa yayi ya kalle ta kana yace, “ashe kin tashi?”. Tace “eh yanzo na tashi naji kana waya da Æ™arfine”.

Sai da ya janyu ta jikin sa kana ya faÉ—ima ta yadda sukayi da Momy.

A d’an razane ta tashi daga jikinsa tace, “Daddy da gaske Momy Mufida ce ta faÉ—a mata?”.

Daddy yace, “itace mana inba itaba wazai faÉ—amata dan ni bangaya mata kinzo ba”.

Fatima tace, abinda yasa nayi mamaki ita tace, ko Zainab kada na fadama.

Yace kila tafisun ta gaya musu dakan tane shiyasa ta hanaki fada musu.

Tace kuma haka ne shiyasa ta hanani faÉ—a.

Tashi tayi domin taje tayi wanka, har tashiga toilet zata fara wanka kawai ta ganshi yashigo wai suyi a tare.

Ai kuwa yana shigowa da sauri tajawo towel dan ta rufe jikin ta da hanzari yakar É“e towel din aikowa tasanya mishi kukan shagwaÉ“a tace, “Daddy dan Allah kabarni nayi wanka na”.

Komai bai cemata ba kallon ta kawai yakeyi cikin da so da ƙauna, tana cikin yimasa magiya bashiri taji yasun gumeta sai cikin bahon wanka aikowa bashiri tasan ya masa kuka gaske da ƙyar ya rarrashe ta tabari ya wanke ta tas.

Haka sukayi ta soyewar su ko wajan shiri shiya shiraya ta tun bata so har takai da ta sakar masa jikin dan ita fitinar Daddy har tsoro take bata.

Bayan sun gama shiryawa sukayi breakfast yace, suje suga gari haka kowa sukaje sukayi ta yawo wararn hutawa da warin wasan ni duk sai da ya kaita, har mota sai da ya fara koya mata sai da dare yayi sosai kana suka dawo gida.

Suna shiga kai tsaye bedroom É—inta ta wuce kayan jikin ta ta rage ta shiga wanka, bayan ta fito turaruka masu kamshi ta shafe jikin ta dasu kana ta sanya kanyan bacci marasa nauyi tayi addu’a kwanciya ta kwanta bacci.

Sai da tayi bacci Daddy ya shigo bayan shima yayi wanka yayi addu’a ya kwanta.

Jikinsa ya jawota kana ya fara lalubar ta yana wasa da ita cikin bacci taji sak’on da Daddy ke aika mata a hankali tace,

“Daddy dan Allah ka bari ni wallahi a gajiye nake please” Daddy kafin ta Æ™arasa zancin ya haÉ—e bakin su waje daya, danaga almun Daddy bazai k’yale taba bashiri nikam nafito na jawo musu kofa.

Tunda sassafe Momy ta shirya dan ko breakfast bata tsaye ba ta kira driver tasa shi yakai ta gidan Hajiya Shafa.

Koda tazo itama har ta shirya itama Momy bata jima da zuwa ba Hajiya Binta tazo basu É—au lokaciba suka É—au hanya.

Basu tsaya ko inaba sai wani mugon daji dan idan kaga wannan dajin baza kaci akwai wata bil adam a cikin sa ba.

Parking sukayi kana suka fito suka cigaba da haurawa a k’afa dan wajan mota bata shiga sai da sukayi tafiya mai nisan gaske kana suka fara hanko wata bukka wanda aka zagaye ta da wani bak’in kyalle.

Tun basu ƙarasa wajan ba suƙa fara jin kamar ana kuka, Momy ta kalle Hajiya Shafa tace, wajan nan kowa lafiya naji kamar ana kuka, sai Hajiya Shafa tace, kiyi shuru dan yanzo haka yana jinmu, bashiri Momy tasa hannu tariƙi bakin ta, a haka har suka kawo wajan sa.

Sai da suka ciri takalman su suka shiga cikin bukkar, aikowa mutum suka gani bak’ik’irin kamar ba mutum ba, aikowa haka suka dake suka Æ™arasu wajansa.

Dariya ya sanya musu mai sauti wadda tayi sana diyar bayyanar da hak’uransa baÆ™aÆ™e kamar jikin shi dan kosu ba alamun haske a tare dasu.

Kallon Hajiya Shafa yayi ita da Hajiya Binta, kana yace, “so kuke alata zaman amaren da aka kawo muku san nan daga baya ayi musu sakin walak’anta ko?”.

Kai suka girkiza alamar “eh haka mukesu”.

Kollon sa ya maida ga Momy yace, “ke kuma aikin ki bazai yiba dole sai ammasa akin da zai dawo Æ™asar nan sai muyi aki akansa.

Dan haka yau komai dare zai kiraki yace, miki zai dawo dan haka gawan nan daya ce zai dawo kije kiyi wanka dashi, inyaso daya dawo sai muyi aiki akansa”.

Godiya sukayi masa kana suka aje masa kuÉ—i masu tarin yawa suka fito, suka kamu hanya suka dawo gida ciki da farin ciki.

Yau sun makara basu tashi da wuri ba saboda basu kwanata da wuri ba dan haka suka makara.

Ita ta fara tashi kana ta tadda Daddy tace, “yatashi sun makara da Æ™yar yatashi, sukayi sallah kana sukayi breakfast.

Bayan sun gama breakfast ya kalle ta da kulewa yace, “my Teema kishirya yau nake sun mukuma gida dan akwai abunda zanyi mai muhinmanci”.

Kallon sa tayi kana tace, “Daddy bakace, sai wani sati ba”.

Yace, “eh amma yanzo akwai aikin da nake sun nayi tace, “to Daddy Allah ya kaimu lafiya” yace, “ameen yace, “tashi kishirya kafin na karÉ“o mana visa.

Tace, “to Daddy dan ita gaba É—aya hankalin ta bai kwantama wannan. tafiyar ba.

Ba jimawa ya dawo yace, “ta fito su tafi dan anyi sa’a ai yanzo jirgin zai É—aga.

Tace, “Daddy tun yanzo bashirin komai?”.

Yace, “dan Allah ki fito mu tafi dan na matso nabar Æ™asar nan”.

tace, “to Daddy d’an bari na shirya”.

Ba jimawa suka haɗa komai nasu suka kamu hanyar filin Jirgin ƙasar.

A filin jirgi ya kira Momy da Hajiya Sa’a yaÉ—a musu gasu nan zowa.

Hajiya Sa’a tayi mamaki wannan zowan nashi dan tasan sunyi dashi sai sati na gaba, fatan sauka lafiya ta musu kana sukayi sallama.

Ita ko Momy har da rawa sai da ta taka kana sukayi sallama, taje tayi wanka da abinda aka bata.

Ko minti goma basu yi da zowa ba jirgin su yaÉ—a zowa Æ™asar su ta haihuwa Nigeria….

Muje zuwa

Amma idan banji comment sosai ba gaskya zan dakata da rubuta wannan novel

Comment
Nd
Shere
1/23/20, 11:48 AM – +234 706 211 8047: 💦💦💦💦💦💦💦
💦💦💦💦
💦💦

    *KAWAR 'YATA CE* 

®�
GASKIYA WRITERS ASSOCIATION�
{ Gaskiya É—aya ce daga Æ™inta sai É“ata, burinmu mu faÉ—akar da al’umma domin ribantar duniya da kuma lahira. }

     🎐 ```G•W•A```🎐

GASKIYA DOKIN ƘARFE•🏇🏼

Story & written
By
Sumy

Dedicated to.
Maman Aysar 💕💕 marabuciyar KISAN GILLAH

BISMLLAHI RAHAMANIR RAHAM

        *Page* 2�7� 

__📖 Koda suka shiga jirigi jikinsa ya sanyata sosai kamar wanda za’a ‘kwace masa ita, ko tari tayi sai ya tambaye ta lafiya, haka dai har jirginsu ya sauka.

10:pm jirginsu yasauka, tunda jirginsu ya sauka gaban Fatima ya fara dukan uku-uku addu’a tarinÆ™a karantawa har taji sau’kin abunda takeji.

Momy yakira yace mata sun sauka tace masa, “driver ya jima da zuwa É—aukarsu”.

Har zaiyi magana yafasa, dan driver yagani yana tunkarusu da saurinsa shiyasa yace mata, ” gamashi nan nagansa”.

Jikar dake gabansu yaɗauka kana yayi musu sannu da zuwa, yana mai ƙarasawa wajan da yayi parcking ɗin motarsa.

Hunnunta Daddy yariÆ™o, kallonsa tayi yace, “mutafi ko” yana mai kashe mata ido É—aya.

Komai batace masaba suka fara tafiya dan ita gaba ɗaya jikinta ba daɗi, suna ƙarasowa driver ya buɗe musu suka shiga ya kulle motar.

kana yaja motar, basu tsaya ko ina ba sai bakin gete É—in gida, horn yayi cikin sauri mai gadi yazo ya buÉ—e musu suka shiga kana ya maida gate ya kulle.

Aikuwa Momy ita da yaranta suna jin anyi honrn sukayo waje wajan tarbunshi suna murna, dan tunda yace ya sauka suka dawo babban falo suna jiran k’arasowarsa.

Ita ko Fatima tunda suka shigo gidan gaban ta kefaman dukan uku-uku cike da tsoron abunda zata tarar.

Har ya buÉ—e yafito bata sani ba, saida yariÆ™o hannuta yace, “my Teema kifito mushiga daga ciki”

sannan tasan sun ƙarasa fitowa ,kuma fitowarta tayi dai-dai da fitowar su Momy da yaranta.

Kallo É—aya sukayi mata suka É—auke fuska, irin kallon da suka jefa mata ne yasa gabanta ya sake dukan uku-uku tsoro da bargaba duk suka taru suka haÉ—e mata lokaci É—aya, musamman kallon da Zainab tayi mata.

Kulsum ce tazo da gudun ta tafaÉ—a jikin Daddy tana cewa “oyoyo Daddy” hannunsa ya ware tashiga jikinsa yana dariyar jin daÉ—i.

Suma suna Æ™arasuwa suka faÉ—a jikinsa sunayi masa barka da zuwa, da Æ™yar yasamu suka bar jikin shi, kana Momy ta Æ™araso tanayi masa wani kallo mai ciki da ma’anoni da dama, wanda shi kansa yarasa gane ma’anarsa kuma ba shakka saÆ™on ya isa zuwa gangar jikinsa dan take jikinsa yayi sanyi.

Ahankali take takowa tana sakar masa murmushi, wanda yayi sanadiyar É—aukar hakalinshi har takowa wajan da yake shida yara, cikin dabara irin tata tatura yara zuwa cikin gida, sai da tabari sun Æ™arasa ciki kana tafara takuwa har ta Æ™aresa jikinsa ta rugumeshi tana faÉ—in, “l miss you dear”.

Aikowa tana faÉ—awa jikinsa wata sassanyar ajiyar zuciya ya sauke kana yace, “nima haka”.

Fatima kam tunda sukayi mata wannan kallon tayi tsaye kamar wadda aka dasa ta a wajan, tsaye tayi tana kallon su har suka shaga cikin gida, sai da Momy tafaɗa jikin Daddy ne sannan tafarga kunya ta kamata bata san lokacin da taja ƙafafunta zata shige cikin gidan ba.

Motsin da yajine da sauri yajanye Momy daga jikinshi, juyawa yayi dan yaga ko waye, Fatima ya gani sunye da kanta ƙasa.

Kafin yayi magana Momy tace, “sorry k’anwata duk ban lura dakeba” tana mai janyota jikinta.

Daddy yace, “Fatima mike damunki ko duk gajiya ce?”

Murmushi kawai tasakar masa batace komai ba.

Yace, “to kizo muÆ™arasa daga ciki” ya faÉ—i yana mai dubanta.

Momy hannun Fatima tariƙo har suka kawo Babbab falo, Daddy ne yafara zama saman kujera Momy taje takowa masa lemu mesanyi, kallon Fatima yayi yace,

“kinyi tsaye ki zauna ga lemu kisha”

kamar mejin tsoron wani abu sai tace, “a’a Daddy ina son naje na watsa ruwa ne”.

Yace, “ok”.

Key ɗin part ɗinta ya ɗauko yamiƙa mata, karɓa tayi tafara tafiya kamar wanda ƙwai ya fashema aciki.

Tana bada baya suka faki idon Daddy suka antaya mata harara Musamman Zainab dan ita a yanzo wata tsanar Fatima takeji aranta.

Ahankali take hawa step step har takawo cikin parlour, zama tayi saman É—aya daga cikin kujerun parlour tana tunani abunda Zainab tamata nako inkula, sai can tace,

“Æ™ila fushi takeyi dani dan ban faÉ—amata inda najeba, amma kuma ai ba laifinaba ne Hajiyar Mufidace tace kada nagayama kowa acikin su amma bari da safe naje nabata hakuri dan nasan Zeey nada sauÆ™i”

ita É—aya tai maganarta ahaka tasamu natsuwar abunda takeji aranta.

Fatima bata jima da tafiya ba shima Daddy ya tashi yace, “zaije ya watsa ruwa”.

Yana shiga Momy tabi bayanshi, suma yara suka tashi suka tafi mukwancinsu.

Toilet Mommy taje tahaÉ—amasa ruwan wanka sannan tace, ga ruwa na haÉ—amaka kaje kayi yi wanka.

Yace, “to” tashi yayi yaje yayi wanka yafito.

Yana fitowa bayan yashirya Momy takawo masa abincinsa, da kanta tayi serving nasa, “to Alhaji bismillah kafara ci”

har yazauna zai faraci ya tashi yace, “sorry Hajiya bari nakira k’anwarki please”.

Wani baƙin cikine ya tukare mata zuciyar amma komai bata cemasa ba har tafita.

Koda yaje bai sameta parlour ba dan haka ya ƙarasa bedroom ɗinta.
Motsin ruwan da yajine ya tabbatar masa da wanka takeyi dan haka yatsaya jira har tafito.

Bai jima da zama ba tafito, daga ita sai wani ƙaramin toilet iya cinyarta, batama kula da mutum ba dan haka wajan mirrow taje tafara shirinta.

turarukka masu ƙamshin gaske tabi jikin ta dasu, tana gamawa wata rigar bacci ta ɗauku ta sanya wadda da ita da babu duk ɗaya.

kallon da Daddy ke mata baki ɗaya sai ya daskare dan tin fitowarta ya kafeta da ido, so yake yatashi yaƙarasa gareta amma yakasa saboda shika ɗai yasan me yakeji gashi kuma ta sanya wannan rigar wadda tatafi da imaninsa, bashiri yatashi domin yaƙarasa gareta.

Tana cikin saka rigar kawai sai ji tayi anjawota, aikowa bashiri tabuÉ—e baki dan tasaka Æ™ara, da sauri yarufe mata baki yana faÉ—in, “haba Faty na nine fa”.

Ajiyar zuciya ta sauke sannan tace, “Daddy yaushe kashigo ban saniba?”.

Bai bata amsaba bakinsa ya haÉ—e danata yafar kissing É—inta kamar ya haÉ—iyeta aikowa itama tafara mayar masa da martani aikowa Daddy gaba É—aya yafita hayyacinshi, yamanta ma inayake ,tsayuwar yaga tanane man tagagaresu dan haka cak yaÉ—auketa sai saman gado, abun na Daddy taga yanane man ya wuce wuri dan haka tafara yimasa magana tace,

“Daddy dan Allah ka Æ™yaleni wallahi agajiye nake inason na huta” yi yayi kamar bai jitaba sai can cikin kasalaliyar murya yace,

“Ko yanzo hutuwa zamuyi, dan Allah kiyi haÆ™uri bajimawa zamuyiba please Teemana”.

Tace, “amma Daddy ba nan ya dace ka kwanaba wajan Momy” baima tsaye saurarin taba yaci gaba da abunda yakeyi mata, bashiri tabada kai.

Momy ko tunda taga Daddy bai dawo ba tafara safa da marwa, dan har zata zo part É—in Fatima ta fasa, ta cika tayi fam jira kwai take safiya tawaye taje wajan bokansu tafaÉ—a mishi Daddy ya dawo.

Kiran Hajiya Shafa tayi tafaÉ—amata duk abunda yafaru tace, ” Æ™yalesu in ya kwana yau ai gobe bazai kwana ba dan haka ki kwantar da hankalinki kinji zuwa gobe da kaina zanje wajan boka nagaya masa abunda ake ciki” sai da taga Momy ta É—an natsu kana sukayi sallama.

Daddy koda yadawo daga duniyar taurari kasa tashi yayi ya koma part ɗinsa, duk da Fatima taso yakoma amma ya ƙyaleta dan haka itama ta ta ƙyaleshi.

Kiran sallah farin suka tashi shida Fatima, tashi yayi ya koma part É—insa wanka yayi ya É—auro alwala yazo yayi raka’atanil fajar sannan yazo part É—in Momy domin yatashe ta amma yaji Æ™ofar akulle dan haka bai tsaye komai ba ya wuci masallaci.

Ita ko Fatima tana gama wanka tazo tayi sallah bayan takammala tajima zaune tana tasbihi kana tatashi ta koma bacci.

Shiko Daddy bai dawo gidaba sai da gari yayi haske kana yashigo gida, kai tsaye part É—insa ya wuce yaje ya kwanta dumin akwai gajiya atare dashi.

Momy ko data farka gari ya waye sosai dan har rana tafara fitowa, tashi tayi taje tayi wanka sannan tazo tayi sallah ta tashi, taɓata lokacin sosai wajan yin kwalliyar, tayi kyau sosai shadda ce ta sanya ash color sannan tafeshe jikin ta da tirare mai ƙamshin gaske, sannan tafito taje part ɗin yara ta tatashesu kana tayo part ɗin Daddy.

Koda taje Daddy baccinsa yake cikin kwanciyar hankali, tajima zaune kafin Daddy yafarka yana buɗe idonsa wani ƙamshine yaziyar ceshi aikowa baisan lokacin da ya ida tashiba.

Momy tana gani ya tashi taje tahaÉ—a masa ruwan wanka tazo tace, yatashi yaje garuwa can tahaÉ—a masa.

Tashi yayi yaje yayi wanka yafito, koda yafito tafitar masa da shadda kalar tata, sai da tagoge masa jikinsa da ƙaramin towel ɗin dake riƙe a hannusa kana tashafesa da mayuka masu ƙamshin gaske.

Sai data taimaka mashi yasaka kayansa kana suka jero zowa falo domin suyi breakafast.

Koda suka fito gaba É—aya yaransu sunfito falo, suka É—ai sukejira, Kulsum tana gani sun fito tatafi da gudunta tafaÉ—a jikin Daddy tana masa barka da safiya.

Karɓawa yayi yana maiɗagata a sama yana murmushi.

Sai da suka kawo wajan dinning Momy taje masa kujera ya zauna.

Zainab da Nabila da Ummi sukazo suka fara gaidashi, ammasawa yayi ciki da nuna farin ciki, Momy tayi seving É—insa kowani su suka zuba zasu fara ci, sai Daddy yace, ” oh, bari naje nakira Fatima nasan har yanzo bata tashiba”.

Har zaya miÆ™e sai Momy tayi sauri tace, “a’a Alhaji bari Kulsum taje takira ta tunda gasu ba sai kaje ba”.

Bai musa ba ya koma ya zauna.

Yace, “ok kulsum jekikira Auntyn ki Fatima”

aikowa da gudonta tatashi dan taje, koda ta ƙarasa part ɗinta parlour tashiga bata nan dan haka kai tsaye bedroom tashiga.

Gaban mirrow tasameta, Æ™arasuwa tayi wajan ta tana faÉ—in, “Aunty Daddy yace kizo muyi breakfasat”

sai data dubeta da kyau kana tace, “Kulsum bako sallama, bare gaisuwa”.

Murmushi tayi mata tace, “to Aunty kiyi haÆ™uri bazan sake ba please”.

Tace, “to naji jekice ganinan zuwa”

tace, “Aunty karki jima fah”.

Tace, “to Kulsum”.

Kulsum natafiya tashi tayi tasanya tufafinta riga da sikrt na atamfa, tayi kyau sosai dan kayan sun karɓeta, mayafin ta taɗuko tayafa kana takama hanyar sauka ƙasa.

Tunda tafara saukowa ya É—ago ido yana kallonta, murmushi yasakar mata saboda tayi masa kyau sosai.

a hankali take takuwa har takowo wajan da suke, kujerar da tagani kusa da Daddy wanda ita kaÉ—ayce bakowa a sama, koba a faÉ—amata ba tasan a nan zata zauna.

Sai da tazauna ta gaida Momy, ciki-ciki Momy ta amsa mata, sannan ita kuma ta gaishe da Daddy shima ya amsa cike da kulawa, haka ma su Zainab duk suka gaisa koshi dan sunga idon Daddy ne da ko magana ba zasuyi mata ba….

Wai🤦‍♀nagaji da typing, bari nabarshi a haka gashi ma nayi ya goge😢

By Sumy�

Comment
Nd
Shere
1/23/20, 11:48 AM – +234 706 211 8047: 💦💦💦💦💦💦💦
💦💦💦💦
💦💦

ƘAWAR ‘YATA CE

®�
GASKIYA WRITERS ASSOCIAT
{ Gaskiya É—aya ce daga Æ™inta sai É“ata, burinmu mu faÉ—akar da al’umma domin ribantar duniya da kuma lahira. }

     🎐 ```G•W•A```🎐

GASKIYA DOKIN ƘARFE•🏇🏼

Story & written
By
Sumy�

Dedicated to..
My lovely Sister
Shema’u💋💋🥰
💕

BISMILLAHI RAHAMANIR RAHAM

    *Page* 2�8�

~Vote & Follow 4Wattpad @ GaskiyaWritersAsso.~

__📖 Bakajin motsin komai sai na spoon ko wane a nutse yake cin abinda ke gabans a, tunda ta zauna ba wani abun kirki take ba daga baya tashi tayi tana faɗin Alhmdullah.

Daddy ne ya kalleta yace.
“badai har kin tashi ba?”.

murmushi tayi masa tace. “eh Daddy na koshi”.

plate É—in dake gabanta ya kalla yace. “mikika ci ne?, da zakice kin Æ™oshi?”. Ba abinda tace masa ba.

Ita kowa Momy duk haushi ya cikata meye tasa a ciki dan bata ciba, tana faÉ—i ne a cikin ranta.

Komai bai ce mata ba, da taga haka itako ta fara tafiya, tako É—aya tayi domin takoma part É—in ta magana yayi mata yace.
“Fatima kije part É—ina ki jirani yanzu zanzo”.

Gaban tane yayi wani mummunar faÉ—uwa, kanta ta É—ago takalli wajan da su Momy suke zaune aikowa wata muguwar harara suka an taya mata wadda ta saka jikinta karkarwa lokaci É—aya.

Tashi Daddy yayi yana mai kallon wajan da take yace.

“ko bakiji me nace ba?, muje ko”. yana mai takawa zuwa part É—insa.

Tsoro da fargaba suka taru suka haÉ—e mata lokaci É—aya, kamar mai koyon tafiya haka ta fara tafiya har ta kawo hanyar da zata sadata zuwa part É—insa.

Zaune ta sameshi a parlour yana jiranta tana ƙarasuwa ya kalleta yace.

“Fatima hala baki da lafiyane?,naga ko breakfast É—in kirki ba kiyi ba, to meke damunki?”.

Kamar wadda bata son magana a hankali ta ɓuɗe baki tace.

“A’a Daddy lafiyata Æ™alau gajiya ce dai har yanzu bata sakeni ba”.

Yace. “to naji ta sakeki kafin Monday dan Monday zaki fara fita school dan haka ki zama cikin shiri”.

Kallonsa tayi da kyau hawaye ne masu dumi suka zubu mata, saboda wani abu dat aji ya zo mata a zuciya amma sai ta dake tana maiyi ƙasa da kanta ta ɓuɗe baki tace.

“Daddy nagode Allah ya Æ™ara arziki”.

Sai da ya kalleta da kyau ciki da sanyen jiki yace.

“Ameen”.

Key ɗin mota yamiƙamata yace ta karɓa.

kallon sa tayi ciki da mamaki tace.

“Daddy meye wannan?”. kallonta yayi yace
“kiÆ™karÉ“a motarki ce wadda zaki fara zawa makaranta da ita, duk da nasan baki Æ™ware sosai ba, amma nasan Zainab zata cigaba da koya miki”.

Godiya tayi mishi sosai, sannan yace mata shi zai fita office. addu’a tayi masa sosai sannan ya tashi ya fita.

Har yakai ƙofa kuma ya dawo kallonta yayi yace.

“Fatyna mezan sayo miki idan zan dawo?”.

arasiwa yayi gareta jikinsa ya sanyata aikowa kamar jira takeyi tasan yamishi wani kuka mai cin zuciya dan ko dama tana danne zuciyartane wani abinda take masa badan taso ba sai dan tana son tayi biyayyane ga Ummah ta.

Gaba ki É—aya Daddy ya rikice,rarrashinta yake yi amma kamar bata san yana yiba da k’yar ya samu ta daina kana yace.

“Me ake yi miki Fatima?, ko school É—ine bakison zowa?”.

Da sauri ta girgiza kanta tace.

“A’a”.

Yace, “to me kikeso?”.

Tace. “wurin Ummana nake so”.

Yace, kiyi hakuri gobe sai kije kinga yanzo jirana akeyi a office”.

Kallonsa tayi tace.

“to gobe zaka kaini?”.

Yace, “sosai kowa da kaina zan kai ki”.

sannan taÉ—an saki jikinta yana ganin ta saki jikinta yayi mata sallama ya fice warsa.

Koda yazo wajan dasu Momy suke yasu tazo suyi sallama amma taki tace yaje kawai bata jin daÉ—in jikin ta badan ya yaddaba haka yafi cewar sa.

Ita kuwa Momy badan komai tak’i zuwa suyi sallama ba sai dan yadda zuciyarta ke mata zafi dan ko taje bazata faÉ—a masa magana mai daÉ—i ba.

Itako Fatima tana nan a zaune ta kasa fita saboda tsoro, dataga zaman bazai k’aremata ba yasa ta tashi ta fara tafiya har takawo wajan da suke zaune kamar wata É“arauniya haka take tafiya slow-slow.

Nabila ce tayi mata magana a tswa ce tace.

” ke munafuka! Ke munafuka!”.

Jikin tane ya fara rawa da sauri tayi Æ™asa da kanta ta k’asa komai dan ba abinda ke mata zuba inba hawaye ba.

Zainab ce ta tashi ta fara tako d’aya bayan d’aya wajan da Fatima take taÆ™arasu ga banta sai data yi mata kallon sama da Æ™asa kana tace.

A rayuwata ban taÉ“a ganin jaka kamar kiba inba da kike jaka ace ki rasa wa zaki aure sai mahaifina, kece k’arya wadda aka haifa ba jini aji kinta sai da a kasa mata manja to bariji”.

Har zatayi magana Momy ta É—aga mata hannu tace. “Zainab k’yaleta dan yanzu fita zanyi dan haka kuje ku nuna mata aikin dake garemu kada rana tayi”.

Tana kaiwa nan ta yafa mayafin ta tace musu tafi.

Sai da suka saka k’yayarta gaba suka bata aiki mai woya sannan suka barta, tanayi tana kuka..

Momy na fita driver ta kira tace ya kaita gidan Hajiya Shafa, koda suka isa gidan har Hajiya Shafa ta fito da nufin tafiya, sai ga Momy tazo dan haka tace to suje, haka ta shiga mota Hajiya Shafa taje suka tafi.

Basu tsaya ko ina ba sai wannan mogon daji, sai da suka aje motarsu wani wajan kana suka Æ™arasa da Æ™afa kamar yadda suka ji kuka wancen lokaci ko yanzo haka sukaji amma saboda taurin zuciya irin tasu haka suka k’arasa.

Suna Æ™arasawa cikin wannan bokkar tasa yasa kar musu dariya mai ban tsoro, saida ya gama dariyarsa kana ya haÉ—e fuska kamar bai taÉ“a dariya ba, wani Æ™ullin magani ya mik’ama Momy yace, gashi ki tabbatar da ya shiga gida da hayakin maganin zai fara cin karo, sannan ya bata wani k’ulle yace.

“Wannan kuma a zuba masa cikin ruwan lipton masu zafi a zuba wannan maganin a ciki, yana shigowa gida bayan yaci karo da wannan haÆ™in kafin wannan abinda zaiji ya sakeshi sai ki bashi wannan ruwan lipton É—in. yadda yaji bata son haÆ™in, haka zaijin bata son komai kama da ita, kuma yadda yasha ruwan lipton masu kunar masa zuciya haka zaiji zafi idan ya tuna komai kama da ita kuma ko bai sake taba zai manta da ita har abada, da fatan dai koyi yadda a kace kuyi dan haka ku tashi ku tafi”.

KuÉ—i masu yawan gaske suka ijje masa kana suk afito cike da farin ciki.

By Sumy ✍✍

Comment
Nd
Shere
1/23/20, 11:48 AM – +234 706 211 8047: 💦💦💦💦💦💦💦
💦💦💦💦
💦💦

 *KAWAR* *'YATA* *CE* 

®�
GASKIYA WRITERS ASSOCIATION�
{ Gaskiya É—aya ce daga Æ™inta sai É“ata, burinmu mu faÉ—akar da al’umma domin ribantar duniya da kuma lahira. }

     🎐 ```G•W•A```🎐

GASKIYA DOKIN ƘARFE•🏇🏼

Story & written
By
Sumy

Dedicated to…
My sweet Shemah❣❣💖

BISMILLAHI RAHAMANIR RAHAM

~Vote & Follow 4Wattpad @ GaskiyaWritersAsso.~

         *Page* 2�9�

__📖 Haka suka dawo gida ciki da farin ciki.

Shiko Daddy yana fita daga gida bai tsaya ko inaba sai gidan yayarshi Hajiya Sa’a.

Koda yaje tayi murna sosai da ganin sa, bayan sun gaisa take tambayar shi ina Fatima yace,

” gobe zankawo miki ita kiganta, dan gobe koda nace ki araman ita zaki bada”.

dariya tayi irin tasu tamanya kana tace, “nasa kana kulada ita dan gashi kaima naga kayi Æ™iba tubari kallah”.😃yace,

“Yaya sai ma kinga Æ™anwar taki zakigane ina kula da ita”.

Tace, “gashi yau zanyi tafiya zowa germany, kasan Abban su Mufida za’ayima aiki shiyasa yau zanje”. yace,

“Yaya abun har ya kai haka to Allah yabashi lafiya, ta amsa da “ameen”.

ya kara da cewa idan kin sauka zan ga yamiki lokaci da zamu zo dubashi.” tace,

“to yayi sai nakiraka. tambayar sa tayi tace, kaje wajan Gwaggo kowa? yace, “yanzo dana fita wajan ta zanje”.

Tace, to ka gaidamin ita nima zan biyo kafin na wuce. haka dai sukaci gaba da fira tana bashi labarin auren Æ´an uwanshi da ikayi bayanan, daga baya yayi mata sallama ya wuce gidan Gwaggo.

Koda Gwaggo ta gansa tayi murna sosai daganin É—an nata, bayan sun gaisa take tambarsa ya gida dasu Fatima. yace, “duk lafiya qlau suke”fira sukayi sosai kana yayi mata sallama yatashi zai fice bayan yasa asauke kayan daya zo mata dasu tayi murna sosai kana yayi mata sallama ya fice.

Da fitarsa bai tsaya ko inaba sai gidan iyayin Fatyna shi.

koda yaje Kaka Amo yasa aka kira masa tayi masa jagora har gidan Baba Babba.

bayan sun gaisa yayi musu shatara na arziki, dan mafi yawan dangin Fatima saida yayi musu alhairi, dan har Ummata da Babata wannan lokacin saida yabiya musu umura, sannan yayi musu sallama yawuce office.

Har yafara aiki yaji yana sun yaji Fatyn shi, wayar sa ya É—auko yakira ta, tana ringing ba’ayi piking ba har sada yayi miss call fiya da goma ba’a É—a gaba, kana ya iji wayar zuwa ajima yakoma kira yaga ko zata dauka.

Ita ko bata masan yana yiba dan tana can tana É—awainiya da aikin da suka sata tanayi tana hawaye tana tuna zakin da Zainab tayi mata.

Ita ko Momy tunda tadawo gida tafara shiri yadda komai zai kasance mata cikin natsowa, lokaci-lokaci sai takira Daddy tana tambayar sa karfe nawa zai dawo, hardai taci riba yafaÉ—a mata yanzu zaI dawo dan gashi nan ma ya kamu hanyar gida.

Itako Fatima saida tagama Ai kin dasuka sakata kana takoma part É—inta, wanka tayi tayi sallah, bayan tagama ta shitayi domin ta gyara jikin ta, wayar tace tafara ruru sunan da taga yana yawo saman screen É—in wayar ne yasa da sauri tayi pinkig.

Sallama tayi tari da faÉ—in, “Ummata yakike.saida ta amsamata kana tace, “lafiya Æ™alau Fatima, ya gidan naku inafatar kuna lafiya?Fatima tace, “lafiya muke Ummu bayan sun gama gaisawa Umma tace, “Fatima baji mawaba Mijinki yazo ya gaishe da iyayyinki har yayi muna abin arziki dan har Umura saida ya biya muna nida mahaifinki, dan haka nace bari nak’iraki na gayamiki kimasa godiya sosai kinji, kuma kiyi ta hakuri da yadda kika samu kanki kinji”.

saida ta numfasa kana tace, “tau Umma insha’Allahu zan masa”. saida suka sha fira daga baya sukayi sallama.

Har cikin ranta taji daɗin abinda yawa iyayyin ta, dan haka tayi ƙudirin sai ta faran ta masa.dan haka cikin hanzari ta ƙarasa jikin mirrow ta ɗanɗasa kwaliya daba ta taɓa irinta agidan ba, kana ta murje dukkan jikin ta da turarukka masu kamshi gaske.

dogowar riga tasanya ta materi, rigar ta karɓe jikinta gashi taɗeme mata jikin sosai tyi kyau, gashi abuga mai kyau, ɗaurin ɗan ƙwali ta murza gashi ita gwanace a wajan, ita kanta tasan tayi kyau bana wasaba.

sai da tagama koma tafara tunani yadda zata fita taje part É—in Daddy a haka, tunani tashigayi can dai tace, “tasan zaizo dan haka ko sauka ba zatayiba bare suyi mata kallon banza, tana wannan magane ita kaÉ—ay. dan haka tasamu waje ta zauna kafin ya Æ™arasu.

Momy ko tana jin yace ya kama hanyar gida tazo tafara turarin ta sai da ta turare gida gabaki ɗaya, kana tahaɗa ruwan lipton tasaka wannan magani kana takuma wajen harabar gate ta zauna, tana jiran ƙarasu war sa.

Ba jimawa da zaman ta sai gashi inayi horn, da sauri maigi yaje yawan game gate ɗin, hanci motar driver yasanyo ciki harabar gidan, wajan da aka tanadar domin picking ɗin moto nan yazo yayi picking, Momy ko tana ganin sun ƙarasu da sauri tayo wajan da suke, ƙarasuwar ta tayi dai-dai da fitowar Daddy a cikin Mota, yana fitowa yaji wani baƙon alamari yazo masa tari da wani ɗuwi da bai taɓa jin irinshi ba, aikowa kakarin amai yafari kamar zai amaye ƴan cikinsa.

yana cikin haka Momy ta ƙarasu gareshi da sauri tana faɗin,

“Alhaji lafiya? komai bai cemataba dan haka taÉ“uÉ—e cup É—in da tazo dashi na ruwan lipton tace, Æ™arÉ“e kasha zaka daina”.

Ba musu ya Æ™araÉ“a ya kai bakinsa, hankali yafara zuwa makoshin sa har ya kai zuwa Æ™irjinsa har yazo zowa zuciyar yarsa, aikowa yana kaiwa ga zuciya yarshi sada yasaki wata Æ™ara tari da faÉ—in, “ya Allah”.

Sai da ya shanye shi tas kana ta janye cup ɗin daga bakinsa, hannusa tariƙa ta ƙarasa dashi part dinsa. sai da ya zauna yajima kansa na kasa, ahankali yafara ɗago kansa yasauke gareta.

Ido ya kefeta dasu yana kallon ta, dan wani kyau ne yaga tayi masa wanda bai taɓa gani haka ba sai a yau, har wata yarinya yaga takoma mishi, gawani sonta da yaƙara zomasa wanda bataɓa jin hakaba atari da shi ba.

Tunda taga ya kifeta da ido tafara sakar masa murmushi maita yar da hankalin Æ´an maza slow-slow tafara takonta har takawa gareshi, jikinsa ta faÉ—a tana faÉ—in,

“dear nah sannu da zuwa”

sai da ya ƙarasanya ta jikinsa sannan yace,

“yauwa sweet heart É—ita, ya gida”.

Tace, “lafiya Æ™alau”.

Tashi zatyi yakara sakata jikinsa, murya Æ™asa-Æ™asa yake faÉ—in ina zakije? “.

A hankali ta furta cewa, “ruwan wanka zan hadama sai kayi wanka kaci abinci dan nasan akwai gajiya atari da kai”.

Ba musu yace, “tau Hajiya tah duk yadda kikayi dai-dai ne”.

Wani daÉ—in ya ziyarcr Momy wanda ba tasan lokacin da ta rungumeshi ba tana fad’in I love Alhaji nah”.

Haka dai sukaci gaba da soyewar su suyi wanna suyi wancan har dai yayi wanka yaci abinci ya kwanta, amma koda wasa baiyi tunani wata Fatima aranshi ba.

Itako tanan zaune tana jiran Daddy har magarba ta gabatu ba Daddy babu alamunshi.

By Sumy �

Comment
Nd
Shere
1/23/20, 11:48 AM – +234 706 211 8047: 💦💦💦💦💦💦💦
💦💦💦💦
💦💦

 *KAWAR* *'YATA* *CE* 

®�
GASKIYA WRITERS ASSOCIATION�
{ Gaskiya É—aya ce daga Æ™inta sai É“ata, burinmu mu faÉ—akar da al’umma domin ribantar duniya da kuma lahira. }

     🎐 ```G•W•A```🎐

GASKIYA DOKIN ƘARFE•🏇🏼

Story & written
By
Sumy

Dedicated to…..
My family 💖🥰

~Vote & Follow 4Wattpad @ GaskiyaWritersAsso.~

     *Page* 3�0�

__📖 Tana gama sallah tunani tashigayi ko dai Daddy bai dawo ba.

Har taso taje part É—inshi tagani ko ya dawo amma tana tsoron abunda zata tarar, haka ta hak’ura badon taso ba tace bari ta É—au waya ta gwada kiran sa taji ko lafiya.

Waya ta É—auka domin ta kira shi amma sai taga miss call d’in shi kusan har goma, dan haka cikin sauri tadanna masa kira, tana ringing amma ba’ayi picking ba. Saida tayi mishi kusan miss Call uku ba’ayi picking ba dan haka tace bari ta dakata zuwa anjima Æ™ila baya kusa da wayar.

Har goma ta kusa ta kuma kiranshi, Amma abin mamaki yanzu wayar ma akashe take.

hankalinta ya soma tashi, don bai taɓayi mata haka ba, kuma tana son ta fito amma ta kasa.

dan haka ta hak’ura tace inbai zoba da safe taje tagani ko lafiya.

Da haka ta hak’ura taje ta kwanta.

Momy ko tana ganin ya samu bacci takoma part É—inta ciki da farin ciki.

Tana ƙarasawa wayarta ta ɗauka takira Hajiya Shafa.

Ringing da bai wuce uku ba ta É—aga.

bayan sun gaisa Momy ke faÉ—amata abinda yafaru, aikuwa murna awajanta ba’acewa komai, dan har rawa saida ta taka kana tace, “gobe insha Allahu a gidanki za’ayi meeting, dan haka kisa ta haÉ—a mana lunch mai kyau”.

Momy tace, “angama Hajiya tah kada kidamu tunda safe zata tashi ta É—ora”.

Haka nakeso kafin itama tabar gidan taci ubanta,gobe ko wani taga zai auri É—aya daga cikin mazajenmu nasan bazata bashi shawara ba”.

Momy tace, “sosai kuwa, ko Zainab da take goyon bayanta yanzu ko ta daina dan haka sai gobe ma idan kunzo”.

Tace, “ba damuwa sai munzo”.

Sallama sukayi Momy tayi wanka ta koma part É—in Daddy.

Koda gari ya waye da zazzaɓi ta tashi dan ko baccin kirki bata samu ba dan sai gaf da asuba ta samu bacci mai ƙarfi ya ɗauke ta.

Tana cikin bacci ta mai daÉ—i dan ko sallah asuba bata samuyi ba,cikin barci taji anayi Mata knocking da Æ™arfi kamar za’acire Æ™ofar.

Tashi tayi da addu’a abakin ta, yadda take jin jikin ta kamar ba zata iya tashi ba amma saboda bugun Æ™ofar yayi yawa dan haka tayi Æ™arfin hali ta tashi ta fara tafiya ahankali har takawo Æ™ofar dan har jiri take gani.

A hankali ta murɗa handle ta buɗe ƙofar, Momy ta gani tsaye fuskar ta haɗe, jikinta ne yaɗau karkarwa batasan lokacin da ta furta cewa,

“Momy dan Allah kiyi hakuri wallah yanzu na farka daga barci”.

Sai da Momy tayi mata kallon sama da ƙasa kana ta yatsine fuska sannan tace,

” haÉ—a mana breakfast yanzu, indan kuma kika gama ki maida sanwar Rana saboda muna da baÆ™i yau agidan, Kinji ko bana son asamu matsala don haka tun yanzu kije kifara”.

Cikin muryar masu zazzaÉ“i tace, “to momy bari nayi sallah dan yanzu na tashi”.

Momy tace, “ba ruwana kije can idan kin gama sai kiyi dan mijina yanzu zai fita dan haka kiyi sauri ki haÉ—a mana breakfast kafin ranki ya É“aci”.

Ba musu ta raɓa ta gyafin Momy ta wuce kitchen.

Momy sai da taga ta shiga kitchen kana ta koma É—akin Daddy ta kwanta suka cigaba da barcin su.

Ita ko koda taje kitchen rasa abinda zatayi tayi,duk tunanin ta Yana Kan Daddy,watau jiya gida ya kwana,to amma me ya hana shi zuwa dubata? kodai dan ya kira ne banyi picking ba? Tambayoyi take tayi barkatai acikin zuciyar ta.

Sallah ta farayi kana ta fara haɗa breakfast tanayi tana zama tana hutawa dumin yadda takejin jikinta ba ƙarfi, saida ta kammala sannan ta jera saman dinnig sannan ta wuce part ɗinta. tana zuwa saman gadu ta faɗa saboda yadda jiri ke ɗibarta ko gani batayi sosai dan haka ta kwanta domin ta huta.

Momy ita da Daddy sune basu farkaba sai 10:am, kana sukayi komai atare sannan suka fito domin suyi kalaci.

A falo suka same su Zainab, dan Ummi da Kulsum su sunje school tun safe.

Zainab ce ta fara gaishesu sannan Nabila, zama sukayi sukayi breakfast É—insu cikinsu babu wanda yayi maganar Fatima har shi kansa Daddy haka sukayi breakfast É—insu su kaÉ—ai bayan ya kammala yafita ba tare da ya nemi Fatima ba, dan shi a yanzu gabaki daya ya manta da ita.

Haka momy tayi masa rakiya har wajan motar sa,sai da driver yaje sannan tadawo tasame Su Zainab suka cigaba da firarsu.

Momy ta dubi Zainab tace,”kije kitchen ki duba man ko yariyar can tayi akin dana sata”.

Zainab tace, “to Momy bari na duba”.

Tashi tayi taje kitchen taga bata nan dan haka tazo ta faÉ—ama momy bata kitchen.

Momy tace taje part É—inta tagano ko tana can? tashi tayi ta tafi a hankali take tafiya har takai part É—inta,knocking tayi mata jin ba’ayi magana ba yasa ta tura Æ™ofar ta shiga ciki.

Cikin bargo ta sameta tayi rufa dashi tana makyarkyatar sanyi.

A hankali take takowa har tazo gab da ita, tsawa ta daka mata “tace hala bakiji ana knocking bane kinyi banza da mutane eh? “.

A hankali taÉ—ago kanta ta kalle Zainab tace, “haba Zeey kiyi hakuri wallahi banji ba kuma ko naji ba iya tashi nakeba”.

Zainab tace, “ba ruwana da baki iya tashi dan haka ki tashi kije ki Æ™arasa aikin da aka saki kinji ko”.

Komai batace mata ba dan ko magana bata sonyi, da Zainab taga bata ce komai ba dan haka taje ta gayama Momy wai tace baza tayi ba dan ita ta gaji, aikuwa ba shiri Momy tacema Nabila taje ta gayamata duk ta yadda tasame ta sai tayi dana sanin zuwan ta gidan.

Kafin momy takai ƙarshen zancen tuni Nabila ta fara tafiya.

Tana zowa da Æ™arfi ta buga Æ™ofar ta shiga bako sallama ba komai, yadda Zainab ta barta haka itama tazo ta sameta, da zuwanta bata tsaya komai ba tayaye bargon da ke rufe ajikinta, ido Fatima ta É“ude tace dan Allah Aunty Nabila kuyi hakuri wallahi banda lafiya”.

Aikuwa bata kai da rufe bakinta ba taji saukar mari har guda biyu hago da dama.

Kallon ta Nabila tayi tana huci kana tace, “har kin isa momy tasaki abu ki k’iyinsa? to wallahi bari kiji ko mutuwa zakiyi sai kinyi aikin da aka saki dan haki tun ranki bai b’aci ba kitashi kije ki Æ™arasa”.

Tana riƙe da kuncinta komai bata ce mata ba,tashi tayi tafara bin bango tana tafiya har ta kai bakin ƙofa jiri ya samu ɗibarta har zata faɗi tayi sauri ta riƙe ƙofar.

sai da taji dama-dama kana taci gaba da tafiya har ta Æ™arasa kitchen d’in.

Nabila ko tana ganin ta shiga kitchen taje ta gayama momy ta tashi har ta fara aikin sannan itama momy ta koma part ɗinta dan ta shirya tarbar baƙinta.

Ta jima zaune tana nishi kana tayi ƙarfin hali ta tashi ta kunna gas ta fara haɗa musu abinda sukace.

Tunda ƙamshin girkin da takeyi ya dake hancinta ba shiri zuciyar ta tafara tashi aikuwa tafara ƙoƙarin tayi ammai, amma ta kasa dan ba komai acikinta.

Tajima kafin abun ya saketa dan ta wahala sosai kana ta tashi taci gaba da aikin da suka sata.

Bayan ta kammala girki, tana cikin tsaftace kitchen sai ga Momy tazo tace mata taje ta gyara gida dan baƙin ta na kan hanya. To Fatima tace mata.

Sai da tagama gyaran kitchen kana ta taje ta gyara dukkan gida tanayi tana share hawaye tana tunanin ina Daddy yaje mi tayi masa da ko wayar ta bai kiraba. Haka dai tayi ta magana a zuciyar ta har ta gama ta koma part É—inta.

Wanka tayi da ruwa masu É—umi ko zataji Æ™arfin jikinta haka kuwa ya kasance da taji jikinta ya mata sauÆ™i sosai dan haka ta shafe jikinta da mayuka masu k’amshi kana ta kwanta.

Wayarta ta É—auka tadanna kira Daddy tana ringing amma ba’ayi picking ba, har saida tayi mishi kusan miss call biyar bai É—agaba. wayar ta tayi jefa da ita tana Mai fasa kuka cicin k’arfnta,kukan da takeyi irin kukan Nan ne Mai cin zuciya.

Tana kuka tana faÉ—in, “Allah kabani ikon cin wannan jarabawar daka É—oramin”.

Shiko Daddy koda ta kira bai ma saniba dan baya cikin hayacinsa, dan yau yafaÉ—a kaidin Hajjiya kulu.

dan baijima da zuwa office ba Hajjiya Kulu tazo wajansa taci kwalliya sosai gwanin ban sha’awa gawani Æ™amshi mai sanyaya zuciya tare da sanya nishaÉ—i musamman ga wanda yaji Æ™amshin.

Knocking tayi masa,aka bata damar shiga.

ahankali ta turo Æ™ofar ta shiga, cikin ta kunta mai jan hankalinsa ta Æ™arasa ciki, tun batayi sallama ba k’amshin ta yayi masa sallama,take yaÉ—ago kansa ya kalleta, aikowa wani shu’umin murmushi ta sakar masa wanda yayi sanadiyar kashe masa duk wani Æ™arfi dake jikinsa.

Idonsa ya kifeta dasu nan take yaga ta koma mishi wata irin kyakyawa, aikuwa bashiri yataso zuwa gareta.

A hankali yake tafiya har yazo wajan da take tsaye kamar wanda aka dasa waje É—aya tana aika masa da shu’umin murmushi mai birkita Æ™waÆ™walwa.

Yana ƙarasowa gareta jikinsa ya sanyata aikuwa tanajin ta jikinsa ta sauke wata ajiyar zuciya mai ƙarfin gaskiya, dan rabonta data jita jikinsa tun lokacin da ya fara neman auren Fatima.

Shiyasa duk duniya yanzu ba abinda ta tsana kamar Fatima, dan taso ya aureta amma yace a’a Fatima yakeso dan haka ita zai aura.

Hajiya kulu ba inda bataje ba dan kada ya auri Fatima amma da yake Allah ya ƙaddara ba wanda ya isa ya hana, dan haka taci alwashi duk yadda zatayi sai taraba shi da Fatimar shi. Ko yanzu atunanin ta abinda akayi mata ne yafara aiki dan haka tayi ƙudurin sai ta rabashi da duk wani wanda ke raɓarsa. Badan komai yasa tasa bokanta yayi mata aiki ba sai dan yazama mallakinta ita kadai.

Tunda taga yanayin da yashiga tafara jin wani sanyin daÉ—i ya rufeta.

Aikuwa tana gani haka ta janye shi daga jikinta cikin murya mai jan hankali da iya bariki tace, “sakeni koda ma nazo ne mu gaisa kawai, kuma gashi natarar aiki kakeyi”.

Cikin muryarsa data fara dushewa yace, “kiyi hakura zan ajiye aikin har kitafi, kibarni mu gaisa please “.

Kamar baza tayi magana ba tace, “a’a bazan tsaya ba sai dai kazo muje gidana”.

Ba musu yace, “muje to”.

Wani farin cikine ya lubeta bata san lokacin da takai masa kiss a lips ba, shiko kamar jira yake yafara mayar mata da martani da ƙyar tasamu ya barta.

ÆŠaya daga cikin ma’aikatan shi kira yace zaifita. adawo lafiya sukayi masa kana suka wuce shida ita.

Tunda suka shiga gidan ta tafara rikitar dashi gabaki É—aya ya manta da kowa bare wata mai suna Fatima.

Dan koda ta kirashi bai masan a ina wayar take ba.

Bata jima da kwanciya ba barci yayi awon gaba da ita, dan ko dama har barci akwai acikinta.

12:pm dai-dai motocin group7,suka fara shigowa gida kowanin su cikin shiga ta alfarma suka fara shigowa, inda aka tanadar musu Momy ta nuna musu suka zauna d’aya bayan d’aya suka fara zuwa har suka kai su bakwai.

Ko wacce daga cikin su idan zata shigo sai ta rangwaÉ—a guÉ—a, Hajiya Hafsa ta dubi Momy tace, Hajiya Hadiza naga har Æ™iba kinya fah mi yabaki daga jiya zuwa yau”tana mai sanya dariya.

Saida suka tafa kana tace, “komai ma yabani tunda yanzu sai yadda nace”.

Aikuwa gabaki d’ayansu suka tafa sukayi wa kansu kirari suna faÉ—in, sai mu group7 bamu ba kishiya duk wanda yace zai ja damu yayi k’arya. amma idan zaka iya kazo ka gwada.

Haka dai sukayi tayiwa kansu kirari, daga baya sukaci suka sha har da taka rawa sannan sukace akira musu Fatima su ganta.

Momy Kulsum takira tace taje takira Fatima.

Koda Kulsum taje kwance ta sameta tana bacci dagani ba barcin daÉ—i ne takeyi ba.

Sai data Æ™araso gabanta tafara faÉ—in, “Aunty, Aunty, kitashi Momy na nemanki”.

A firgece ta farka tana faÉ—in, Kulsum ina Momy take?”.

Kulsum tace, “tana parlour tana jiranki”.

Fatima tace, “to je yanzu zanzo”.

Har Kulsum zata tafi sai kuma tadawo tace, “Aunty hala baki da lafiya ne”?

Har taso tace eh kuma tafasa tace, “lafiya ta Æ™alau bacci daine bai ishe niba”.

Kulsum tace, “to Aunty idan kika dawo sai kiyi ta barcin ki”.

Gajiya tayi da maganar kulsum dan haka tace, Kulsum je kice mata gani nan zuwa kinji”.

Aikuwa da gudunta tafice.

Itama Fatima tana ganin tafita tashi tayi da ƙyar ta saka hijab nata kana ta safko, tun bata karasa ba tafara jin hayaniya aikuwa ba shiri gabanta yafara duka uku-uku.

A hankali take tafiya har takawo cikin falon.

Tunda ta tunkaro su suka fara antaya mata harara,nesa dasu ta durÆ™usa tace, “Momy gani”.

saida ta aikamata kallon banza sannan tace, “hala jakar uwarki bata koya miki yadda ake gaida mutane ba? “.

Idon ta tap da hawaye tafara girgiza kai hawaye na zuba a idonta.

Gaishe su ta farayi amma ba wanda ya ƙarɓa mata.

Hajiya Binta cikin tsawa tace, “kitashi kibamu wuri dan ni ko ganinki bana sonyi”.

Jikinta na karkarwa ta miÆ™e zata bar wurin cikin sauri Hajiya Hafsa tace, “ke zonan nagani naga kamar cikine da ita”.

A firgice Momy ta mik’e tsaye tana faÉ—in, “ciki kuma?????”

Sai Hajiya Shafa tace, “ina wadda ko kusantar ta bai ta bayiba ina wani zancen ciki sai dai in wani taje yayi mata amma ba Alhaji ba, dan Malam yace bazai iya kusantar taba har su rabu kunga ko ba wani ciki bakin ciki ne dai zai kasheta”.

Sai a lokacin Momy ta saki wata ajiyar zuciya mai Æ™arfi kana tace, wallah yau dana ci ubanta kuma da yanzu zanje a zubar dashi, dubanta ta kai ga Fatima da jikinta ke karkarwa tace bazaki bar wurin nan ba ko sai na ci ubanki”.

Aikuwa bata bari ta ƙarasa zancen ba ta tashi da gudunta tabar wajan.

Haka dai sukayi ta k’ullawa da warwarewa har dai suka samu mafita sannan kowa cikinsu ta kama gabanta.

Haka dai rayuwa taci gaba da tafiya, dan Fatima kullum sai abunda yayi gaba ga ciyo ga wahala gashi rabon da taga Daddy har ta manta.

Kuma ko wayar da take kiransa da ita tunda Nabila ta ganta ta ƙarɓeta shiyasa yanzu kowa batada labarinshi.

Dan shima Daddy yanzu yana kwana biyu bai kwana gida ba, yana can ya tare gidan Hajiya Kulu.

Ita ko Momy ko ajikinta dan yanzu taga ko maganar Fatima ba yayi gaba d’aya ya manta da ita……

By Sumy�

Comment
Nd
Shere
1/23/20, 11:48 AM – +234 706 211 8047: 💦💦💦💦💦💦💦
💦💦💦💦
💦💦

typing✍�.

ƘAWAR ƳA TA CE

®�
GASKIYA WRITERS ASSOCIATION.�
{ Gaskiya É—aya ce daga Æ™inta sai É“ata burinmu mu faÉ—akar da al’umma domin ribantar duniya da kuma lahira.}

    ```🎐G•W•A🎐```

GASKIYA DOKIN K’ARFE•🏇ğŸ?

Story & wrtten
By
Sumy�

Dedicated to
Khausar😍

~VOTE & FOLLOW 4 Wattpad~@
~GaskiyaWritersAss~.

BISMILLAH RAHAMANIR RAHIM

        *Page* 3�1� 

_📖 Yau ma kamar kullum tana gama sallah asuba ta maga azkar ɗin da takeyi, tashi tayi taje kitchen domin ta fara haɗa musu breakfast.

Tana fitowa falo taga gabaki É—aya ya yamutsa kamar ba jiya da yamma tayi gyara shiba.

Dan haka sai da ta gama gyaran shi sannan ta wuce kitchen ta haÉ—a musu breakfast takai dinning ta jera.

Tana cikin jera abinci saman dinnig, sai ga Daddy ya shigo falon, dan sai yanzu ya dawo daga masallace.

Tunda ya fara shigowa parlour ya kejin wani ƙamshi mai daɗi ya fara ziyar hancinsa.

Ta kunsa ya ƙara domin ya ƙarasa parlour ya zauna ko new ɗin safe ya kalla.

A hankali yake tafiya har ya kawo cikin falon, har zai zama bisa É—ayan kujerun da ke falon, sai idon shi ya kai gareta tana tsaye tana jera abinci saman darning.

Ido ya zuba mata yana kallonta, tunani ya shiga yi ina yasan wannan?har yaso ya tuni nan take zuciyar sa ta fara yi masa zafi sosai, bashiri ya kauda wannan tunanin.

Parlour ma ga baki É—aya yaji bazai iya zama ba, dan haka ya tashi domin ya koma part É—insa ya kwanta koda zai ji damar zuciyar sa dake masa zafi.

Mutsen da taji ne yasa ta É—ago kai ta kalle taga ko Momy ce dan tunda ya shigo bata ma sani ba dan gabaki É—aya ta maida hankalinta ga aikin data keyi.

Aikuwa tana É—ago kanta suka haÉ—a ido dashi gabanta ne ya faÉ—i, dan rabun da ta sanya shi a ido tun lokacin da yace zai kaita gidan su.

Gaba d’ayan su kowane kallon É—an wun sa yake, ita tana mishi kallon, Daddy mena maka,shiko yana yi mata kallon ina ya santa.

A hankali ta buÉ—e baki dan tayi masa magana, har zatayi taji mutsi kamar za ashigo dan haka da sauri ta koma kitchen.

Momy ce ta fito daga part ɗinta, Daddy ta gani tsaye da haka da hanzarinta ta ƙarasu gaban sa tana faɗin.

Alhaji ka dawo ne? Kallon ta yayi fuskar sa É—auke da murmushi yace, “eh yanzu na dawo kuma yanzu nake son nafita dan akwai wani meeting É—in da zamuyi yanzu, dan haka ki haÉ—a min breakfast ki kamin É—akina dan yanzu wanka zan shiga”.

Tace, “to Alhaji”.

Wanjan dinning ta Æ™arasa domin ta had’a masa abinda yace har ta fara haÉ—awa sai ga Fatima ta fito daga kitchen zata koma part É—inta.

Momy ce ta kalleta a ya tsane tace, “kizo ki had’a ma mijina breakfast dan waya nake so nayi dan haka kiyi sauri ki haÉ—a ki kai masa part É—inshi dan haka kiyi sauri bana son shiriri ta”.

Tana gama faÉ—in haka ta wuce zuwa parta É—inta.

T ajima tsaye kafin ta ƙaraso wajan dinnig, ta fara haɗa masa duk abinda tasan yana da buƙata, kana ta ɗauka zuwa part ɗinsa.

A hankali take ta fiya har takai falon sa, kuma shigar ta tayi dai-dai da fitowar sa bedroom É—insa.

ido ya kife ta dasu ya fara tunani ina yasanta? Kayan dake hannu ta ta aje kana tafara taku a hankali har ta kawo gabansa.

Durkusawa tayi hawaye na zuba a idon ta, kana tafar faÉ—in.

“Daddy dan Allah idan wani laifi nama maka dan Allah kaya feni please”. tana mai sanya masa kuka mai cin zuciya.

Shi dai sai kallon ta yake kamar ya santa amma ya kasa ganu ina ya santa, dan haka yace, “ke waya baki damar shigowa part É—ina a matsayiki na yar akin?”.

Kuka data takeyi tada kata kanta É—ago ta kalle shi tace.

“Daddy nice fah Fatima? Duba kagani ba tar aiki ceba”.

Ai bata kai da ƙarasawa ba ya daka mata tsawa mai ban firigi ta wanda tasa jikinta ya fara karkarwa lokaci daya.

Bashiri ta mike tsaya, Hanyar fita ya fara nuna mata dan ko magana baya son yayi mata dan haka da hannu yayi mata nuni da tafita.

Da gudu ta tabar É—akin tana mai zubda hawaye, part É—inta ta wuce ta faÉ—a kan gado tafara sabon kuka mai ciki da kunar zuciya.

Ta jima tana kuka, kukan da take taga ba shine mafita ba dan haka bashiri ta tashi, hijab É—inta ta tasaka tafito.

A hankali take tafiya har ta kawo parlour.

Tayi sa’a kowa babu dan haka cikin sauri tafit harbar gidan.

Tana kawo wa geta mai gida ya gaidata kana ya ɓuɗe mata tafice.

Tana fita ta fara tafiya har ta kawo bakin titi kuma kawo war ta yayi dai-dai da zowan mai adedeta, taran sa tayi sai da ta shiga take faÉ—a masa uguwar da zai kaita.

Kana yaja suka tafi……

   *Sumy*�

Comment
Nd
Shere
1/23/20, 11:48 AM – +234 706 211 8047: 💦💦💦💦💦💦💦
💦💦💦💦
💦💦

typing✍�.

ƘAWAR ƳA TA CE

®�
GASKIYA WRITERS ASSOCIATION.�
{ Gaskiya É—aya ce daga Æ™inta sai É“ata burinmu mu faÉ—akar da al’umma domin ribantar duniya da kuma lahira.}

    ```🎐G•W•A🎐```

GASKIYA DOKIN K’ARFE•🏇ğŸ?

Story & written
By
Summy�

Dedicated to
My daughter🥰
(Zainab)

~VOTE & FOLLOW 4 Wattpad~@
~GaskiyaWritersAss~.

BISMILLAH RAHAMANR RAHAM

       *Page* 3�2�  

_📖 Tafiya sukeyi basu tsaye ko ina ba sai wata ungowa mai Æ™arancin jama’a.

Bakin wani k’ofar gida tace ya sauke ta,fita tayi ta bashi É—ari biyar, ko canji bata tsaya karÉ“a ba ta Æ™arasa cikin gidan.

Da sallama tashiga gadan, matar gidan ta amsa mata, kana tace ta wuce ta zauna.

Sai da ta zauna kana ta gaishe ta tana cewa, “Fatima yau kece a gidan mu dafan dai lafiya kuke?”.

Fatima sai da tayi k’asa da kanta tace, “Lafiya Æ™alau muke mama, inasu Nafisa?”.

Tace, “duk sunje makaranta”.

Shuru ya biyo baya, sai da Fatima ta nunfasa kana tace, “Mama malam baya nan ne?”.

Sai da ta kalle Fatima tace, “wallahi bai jima da fita ba, amma bari na kira shi in bai yi nisa ba nace mishi gaki kinzo”.

Fatima tace “tau Mama nagode”.

Waya ta É—auko takira shi ta faÉ—a masa ga É—alibar shi Fatima tazo neman sa.

Yace ta jira shi gashi nan zuwa. Mama kallon Fatima tayi ta faÉ—amata yadda yace.

Tace, “tau mama nagode”.

Ba tajima da kiran sa ba sai gashi yazo cikin hanzarin sa.

Da sallama yashiga gidan. Sai da suka amsa kana ya shigo.

A hankali Fatima ta kai duban ta gare shi ido suka haÉ—a, yace, “Subuhanallah, Fatima hala baki da lafiya ne?”.

Aikuwa ba kai da rufe baki ba ta sanya mishi kuka mai tsoma zuciya.

Ido ya kifeta da su, dan ko magana ya kasa.

Mamace tayi ƙarfin halin ta fara rarrashi Fatima da ƙyar tasamu tayi shuru.

Sai da yaga tayi shuru kana yace.”Fatima meke damun ki?”.

A hankali ta fara buÉ—e baki ta faÉ—a masa duk abunda ke damun ta.

Aikuwa tana kai Æ™arshe Mama ta fara salati tana faÉ—in, “duniya ina zaki damu kalli ji har gani”.

Sai da malam ya numfasa kana yace. “Fatima kiyi hak’uri ko wane bawa da inda Allah ke jarbtarsa, dan haka ki kara hak’uri kinji, kuma sai kin tashi tsaye sosai wajan namen tsarin jikinki ki nutso sosai ki dage da addu’a, kuma insha Allahu muma zamu ta yaki kuma duk wanda ya shiga tsakanin ki da mijinki Allah ya fishi, dan Allah baya kwana dan hakk’in wani akan wani kici gaba da rok’on Allah sauki kuma ki nace da rok’on Allah, duk abinda yayi tsanank yana tare da sauki kinji”.

“Badan koma muka baki shawara kiyi wannan auren ba sai dan ki samu ki gama da iyayenki lafiya dan haka kiyi hak’uri, yanzu zan haÉ—a maki magani da zaki affani dasu insha’Allahu lokaci kaÉ—an ko meye zai sake shi amma fah, sakin dage da addu’a”.

Tashi yayi yaje É—akinsa.ya jima kafin yafito, sai da ya zauna, ya kalleta kana yace.

“ga wannan maganin keje ki fara aikin da shi muga abunda Allah zaiyi”.

Man zaitu da habbatus sauda ya fara bata kana yace, “kisan yadda zakiyi ki haÉ—e masa su cikin man da yake shafawa a jikin sa , ki Æ™oÆ™ar ta kada kisa wasa”.

Wani É—aurin magani ya bata yace. wannan ko ki samu lemu ki haÉ—a masa yasha kuma ki tabbatar da yasha kinji”.

Sannan ya koma bata wani yace, ga wannan turare ne sai ki haÉ—a shi da turare mai kamshi sai kirinÆ™a yima gidan hayaÆ™i da shi”.

Kuma kema idan zaki kwanta ki shafe kirjinki da man zantun dan yana kariya sosai”.

Yace,” insha’Allahu idan kin kiyaye abunda nace to komai zai dawo kamar ba’ayi ba”.

Dan haka ki tashi ki koma gidanki Allah yayi miki abarka ya k’ara baki hak’uri, Allah kasa adace kuma idan kena neman Æ™arin bayani sai ki gaya man”.

Godiya tayi masa sosai kana tasoma tashi, sai mama tace Fatima zonan kiji”.

Kallon ta malam yayi yace. “Dan Allah ki barta ta tafi kinga kilama bada izinin shi tazo ba”.

Mama tace, “malam kayi hak’uri ba jimawa zamuyi ba”.

Yace, “to kuyi sauri gani ina jiran ku”.

Tashi Fatima tayi ta same mama a É—aki, wajan zama ta nuna mata ta zauna, kana ta kalleta da kyau tace.

“Fatima ki buÉ—e kunneki da kyau kijini, dan naga ba ainkin sihiri kaÉ—ai ke cin kiba har da tsoro”.

Dan haka, bari kiji koda malam ya baki magani karya wannan sihiri bashi zai sa ya karye ba sai kin cire tsoron su a zuciyar ki. Dan haka kiyiwa mijinki biyayya, in har kina son kema ki zama mace kamar kowa ce a gidan mijin ta. Dan haka Tashi kije malam najiran ki a waje”.

Wani kullin abu ta É—auko ta bata tace, gashi duk lokacin da kika ga abun yayi sauki ga mijinki to kisa madara kisha, duk da naga alamun ba ke kaÉ—ai kike ba, amma zaki iya sha”.

Karɓa tayi tana godiya, dan ita bata san me take nufi da ba ita kaɗai take ba.

tashi kije ga malam can ya fara magana.

Tashi tayi tana mata godiya.

Koda ta fito gaba yasa kata sai data shiga adedeta sahu kana ya hucewar sa wajan aiki.

Tunda ta fita daga cikin É—akinsa yake tuna ne wai a ina yasanta dan shi gani yake ya santa amma ya manta inane?.

Yana cikin wannan tunanin Momy ta shiga ta same shi tace,

“Alhaji yana ganka a tsaye ko har ka fito?”.

Kallon ta yayi yace, “nafito yanzu nake son nayi wuce jira na akeyi”.

Har zai sake magana wayar sa ta fara Æ™ara, sunan da yaga yana yawu saman sereen É—in wayar shi ne yasa da sauri yayi pinkig, yana faÉ—in “ganin zuwa”.

Momy data ke tsaye ya kalla yace, “Hajiya ni zan wuce office dan jirana akeyi”.

Yana faÉ—in haka ya kama hanyar fita.

Tace, “Alhaji ko breakfast baka tsaya yi ba”.

Yace, “ba komai idan naje can zanyi”.

Sai da ta mishi rakiya har wan motar sa, driver yaje mota tadowa ta wuce part É—inta.

Dai dai kofar gida mai adai-daita ya tsaya tafita. knocking tayi mai gida ya zo ya buÉ—e mata ta shiga ciki.

A hankali take tafiya har ta kawo parlour, ko yanzu tayi sa’a ba kowa dan haka da sauri tayi hanyar part É—inta, saida ta shiga ta dafe kirji tana fitar da numfashin É—aya bayan É—aya.

Bedroom É—inta ta Æ™arasa ta kai kayan ta aja waje daya kana ta kwan ta ta fara tunanin yadda za’ayi taje É—akin daÉ—i.

Can tayi wani tunani dan haka da hanzari ta tashi ta sauko ƙasa.

Kitchen taje ta É—ura sanwar rana, sai da ta kammala ta kai dinning ta jera kana ta fara tsaftace gidan gabaki É—aya.

Turukan ka aka bata taje ta dauko ta haÉ—asu da masu kamshi ta fara turare gidan dasu har parta É—in Daddy sai da taje ta turare shi da turare kana ta ko ina na gidan dan har wajan part É—in Momy sai da tayi karfin halin kaiwa can, cikin lokaci kaÉ—an gida ya É—auke da kamshi ma haÉ—e da turarin isaka na kaya sihiri.

Har ta gama bawan da ya fito, Aikuwa da taga haka da sauri taje ta É—auko man zatun da man habba tayi dakin Daddy, wajan mirrow ta Æ™arasa duk man da ta gani sama sai da ta zoba man habba da man zaitun a cikin sai da ta kammala tafito tana tafiya kamar wata É“arauniya, tana fitowa ta fara faÉ—in “Alhmdllah”.

Dan ita kanta yau tasan tayi na mijin ƙoƙari duk da bama wata lafiya ce da itaba.

Har zata shiga part ɗinta momy ta fito kalon sama da ƙasa ta jefa mata kana tace.

Kije part É—in baki ki gyara shi dan yau Maram zata zo ita da yaran ta”.

Aikuwa taji dad’in faÉ—in wadda zata zo saida gabanta ya faÉ—in dan tasan kowa ce ce Aunty Maram dan tafi Aunty Nabila fitina.

Tsawar da Momy tayi mata ne yasa ta dawo cikin hankalin ta.

A hakali ta fara tako har ta kai part É—in baki.sosai ta gyara shi sai da ta gama shima ta sanya mishi turare kana ta kulle shi sannan ta fito.

Part É—inta ta koma sai da tayi wanka tayi sallah kana ta kwanta, bata jima ba bacci yayi awun gaba da ita dan yau iya gajiya ta gaji.

Tana cikin bacci taji hayani sama-sama, idon ta ta buÉ—e dan tasan Aunty Maram ce ta iso tashi tayi taga har huÉ—u tayi dan haka tayi sallah.

Ta jima zaune kan sallaya kafin ta tashi.ko fitowa batayi ba dan tasan ba abunda fitowar ta zata tsina na mata sai zagi dan haka tayi zaman ta tana karatun husnul musulim.

Sai daf da magarb ta sauko koshi alamun dawowar Daddy taji dan haka da sauri ta fito ta ƙarasa Kitchen.

Lemun abarba ta haÉ—a masa mai sanye kana ta É—auko wannan kulle maganin da aka bata ta zuba.

ÆŠauka tayi dan ta kai masa, tana fitowa ta haÉ—u da Kulsum.

Da gudu Kulsuma tazo gare ta tana faÉ—in “Aunty kinsan Momy su Afra tazo kowa?”.

Fatima tace, “a’a yaushe tazo?”.

Kulsum tace, “koda na dawo school sun zo”.

Sai Fatima tace, “to bari naja na gaishe ta, amma ga lemu kije ki kaima Daddy, kuma kar ki fito sai ya shanye sai kizo na baki naki kunun aya da na haÉ—a miki”.

Aikuwa da murna ta karÉ“a tana faÉ—in, “yauwa Aunty bari naje na kai masa yanzu ma yadawo”.

Fatima tace, yauwa autar Momy”.

kulsum na fitayi ita ko Fatima ta koma kitchen dan ta haÉ—ama Kulsum kunun ayar ta…..

By Summy�

Comment
Nd
Shere
1/23/20, 11:48 AM – +234 706 211 8047: 💦💦💦💦💦💦💦
💦💦💦💦
💦💦

 *KAWAR* *'YATA* *CE* 
         *1441H/2019M.*

®�
GASKIYA WRITERS ASSOCIATION�
{ Gaskiya É—aya ce daga Æ™inta sai É“ata, burinmu mu faÉ—akar da al’umma domin ribantar duniya da kuma lahira. }

     🎐 ```G•W•A```🎐

GASKIYA DOKIN ƘARFE•🏇🏼

Story & written
By
SUMY✍�

Dedicated to..
Gaskiya writers 🥰

~Vote & Follow 4Wattpad @ GaskiyaWritersAsso.~

        *Page* 3�4�

__📖
Har Daddy ya É—auko wayar sa yakira doctor,amma ba wanda ya tashi a cikin su Momy.

Daddy bai jima da kiran doctor ba ya ƙarasu.

Sai da ya koma part É—inta yace ta gara ga doctor yazo,kuka ta sanya masa tana faÉ—in, “Daddy nifa na warke”.

Ko ta kanta bai biba yaje yakira doctor suka ƙarasu part ɗinta.

Da ƙyar tabari doctor ya dubata da kuka da komai saida yayi rarrashin ta kana tayi shuru.

Bayan doctor ya gama duba ta yayi Æ´an gwaje-gwajen da zai mata yace, ma Daddy “ajima zai kawo saka mako”.

Godiya Daddy yayi masa kana yara kashi har wajan motor sa,sai da yaÉ—aga sannan Daddy ya koma cikin gida.

kwance ya same ta, ta kife kai da gado tana kuka.

Da sauri ya ƙarasu ga reta yana faɗin,

“Dan Allah Fatyna kiyi hakuri,dan lafiyar ki tafiye man komai a wajena”.

Kamar ba tasan yana yiba ta share shi taci gaba da kukan ta.

Rasa me zaiyi yayi dan a duniya, ba a buda ya Tswana duk bai wuce yaji tana kuka.

Ganin yadda ya koma kalar tausai yasa ta rage sautin kukan ta ta kalle shi kana tace,

“To zaka kai ni gida anjima daga can naje na gaida Gwaggo?”.

Sai da yasau ke ajiyar zuciya kana yace,

“eh zan kaiki amma sai na dawo wajan aiki zuwa yamma sai muje”.

Da hanzari ta tashi daga kwance da take ta faÉ—a jikin sa ta fara murna.

Jikinsa ya ƙara sanya ta sosai kana tace,

“yauwa Daddy na na gode Allah yabar minin kai”tana faÉ—a tana shafar gyamun fuskar sa.

Fuskar ta yaÉ—ago suka haÉ—a ido kana yace, Ameen Fatyna”.

Har zatayi magana ya haÉ—e bakin sa da nata yafara kissng É—inta kamar zai cinye ta.

Ita kuma batayi ƙo ƙarin hanashi ba.

Wayar sace da ta fara rura tadawo dasu cikin hankalin su.

Gabaki É—aya jikin Daddy yayi sanyi ya kasa tashi,wayar sace data cigaba da rura dan haka Fatima ta tashi daga jikinsa taje ta É—auko.

Sunan da ke yawo saman screen É—in wayar ta bi da kallo, Hajiya My D.

Haka yafito ɓaru-ɓaru saman screen ɗin .

sunan ta mai-mai ta har sau uku kana ta kalle shi,dan har yanzu yana nan inda ta barshi ya kasa tashi.

A netse ta ƙarasu gare shi tace, My Daddy,ahankali yaɗa go idon shi wanɗan da suka canja launi ya kalle ta,amma ya kasa magana.

Cikin muryar ta mada É—in sauraro ta fara faÉ—in, “Daddy katashi kayi picking call É—in da ake maka”.

A hankali ya ɗago kai ya kalle ta ido ɗaya ta kanne masa,ta fara magana cikin muryar ta mai kashe masa jiki mai haɗi da ƴar shuguɓa tace,

“Daddy hala waye Hajiya My D? Ƙo Momy ce ke neman ka?”.

A razane ya tashi daga kwanci yar da yayi, kallon ta yayi sai yace, ina wayar take?”.

Miƙo masa tayi tana mai ƙara kwanciya saman ƙirjin shi.

Bai jima da ƙarɓar wayar ba akasa ke kira.

Rasa yadda zai É—au wayar yayi dan haka sai ya tsinci kansa da tsinki kiran batari da tagani ba.

Ita koma duk abunda ya keyi tana kule da shi sai dai tayi kamar bata gansa ba,dan tunani take wacece Hajiya my D.

Kauda tunani da takeyi tayi dan haka tayi yunÆ™urin domin tashi daga jikinsa,maida ta yayi yana mai faÉ—in My Baby tah ina zakije?”.

Zan haÉ—a maka abun karyawa ne dan nasan yanzu zakaje wuce office?”.

Kallon ta yayi ciki da mamaki kana yace,

“keda baki da lafiya mezaki iya haÉ—awa bana so ki daina ga su Zainab kuma ga Æ´an aiki dan haka bana so kibari suyi”.

Cikin murya kamar tayi kuka tace,

“Daddy dan Allah kabarni na haÉ—ama idan ma ina kwance nakejin zazzafi ya tasoman, amma idan ina aiki sai naji da sauki”.

Badan yaso ba haka yabar ta tayi amma yace kaÉ—an zatayi.

Tashi yayi yace” “bare yaje yayi wanka.

tace, “to Daddy”

tana ganin yatashi ita ma tashi tayi taje kitchen ta fara haÉ—a masa breakfast.

Agurguje ta haÉ—a masa breakfast.

part ɗinta ta koma tayi wanka ta shirya cikin riga da sikt na ataffa ɗukin ya karɓe ta sosai.

Sai da ta feshi jikinta da turare kana ƙarasa kitchen ta ɗau breakfast ta wace part ɗin Daddy.

A parlour ta aje masa breakfasat ta ƙarasa bedroom ɗinsa.

Shigar ta tayi dai-dai da fitowar sa daga toilet.

Da sauri ta ƙarasa ga reshi ta ƙarɓe towel ɗin da ke hannusa ta fara goger masa jikin sa dashi.

Ahankali take gogar masa jiki har ta kammala,mayukan da ke gaban mirrow ta É—auko ta shefe shi dasu cikin wani salo data ke masa wanda yasa gaba ki É—aya jikin sa yayi sanyi.

Saida ta kammala shirin sa kana ta je hannun sa kamar raƙumi da akala , har wajan da breakfast yake, zaunar dashi tayi ta haɗa masa tea tazo har gaban sa ta fara bashi yana sha.

Ahankali take shayar da shi har ya cika cikin sha sosai dan badan komai yasha sosai ba dan kada ya daina kallon ta dan ba karamin kyau ta masa ba.

har zata tashi ta maida kayan da suka É“ata ya jawota jikin sa yana faÉ—in kema sakin yi naki braekfast kafin natafi dan nasa ba abunda ke cikin nan nake”.yana faÉ—a yana lalubar cikin ta.

Wanda ta haɗa ya ɗuko ya fara bata. ba musu ta karɓa saida yaji cikin ta ya ɗago kafin ya kyale ta.

Tashi yayi yace, “shi zai tafi jiran sa ake office”.

Addu’a tafara yimasa sosai dan haka yaji daÉ—i aran sa.

basan lokacin da ya jawota jikinsa ba ya fara bata kissing son ran shi .

Saida taga abun na Daddy zai wuce wuri dan haka tayi hanzarin ƙwatar kanta.

Zama yayi itama ta zauna kusa dashi. suna cikin dai-dai ta numfashin su sai ga Momy ta shigo É—akin É—auke da sallama abakinta.

Ai wadda tagani zaune kusa da Daddy ne yasa takasa ƙarasa sallamar.

Ita ko Fatima gabanta ne yafara dukan uku-uku amma sai ta dake.

Ahankali ta É—ago kanta ta ta kalle Momy wadda ita ma ita take kallo,tana mata kallon mamaki.

Ahakali Fatima ta buÉ—e baki tace, “Momy ina kwana?”.

Sai alokacin da tayi magana Daddy ya É—ago kai ya kalle ta dan shi bai ma san ta shigo ba.

Kallon da taga Daddy yayi mata yasa ta gane cewa ba wancan Daddy data sani ba ne, dan haka ta amsa mata ba yabo ba fallasa.

Dubanta ta maida ga Daddy ta gaisheshe.

Amsa mata yayi yana mai meƙiwa tsaye yana faɗin,

“ni yanzu zan wuce dan jirana akeyi a office”.

Momy kallon sa tayi tace,

“yanzu zaka fice ko braekfast bakayi ba?”.

Yace, “kina can kina barci ina kika san nayi braek.ai kanwarki tabani nayi dan haka ni zan wuce” yana mai kallon Fatima.

A dawo lafiya ta ƙara yi masa.

Momy ita tama kasa magana sai can tayi masa adawo lafiya.

Tana mai bin bayan sa dan tayi masa rakiya.

Har ya kai Æ™ofa ya juwu ya kalle Fatima yace,”Fatyna”.

Gabanta ne yasake dukan uku-uku,Momy da ke tsaye ta kalle aikuwa kallon da taka watsa mata yasa cikin ta murÉ—awa .

Yace, “taso muje kimin rakiya ba musu tazo suka tafi har wanjan motar sa.

Har ya shiga mota driver ya kunna zasu tafi da sauri ta ƙarasu jikin motar tafara faɗin,

“Daddy dan Allah kafin kaje office kafara zuwa wajan Kawo Gwaggo”.tana faÉ—a kamar zatayi kuka.

Sai da ya laÆ™ace hancin ta kana yace,”kada ki damu inasha’Allahu daga nan can zan wuce fatana dai kitana dar min gift É—in da zaki bani kafin na dawo”.

Sai da ta shafe gyemun fuskar sa kana tace,”baka da matsala Daddy fatana dai ka kulamin da kankai.

Yace,”insha Allah” driver na mai jan mota suka É—aga.

Gabaki É—aya ta manta da Momy na wajan tsaye sai da suka É—aga tajuya domin ta tafi suka haÉ—a ido……

#Comment
#Vote
#Share

Sumy✍�
1/23/20, 11:48 AM – +234 706 211 8047: 💦💦💦💦💦💦💦
💦💦💦💦
💦💦

*ƘAWAR ƳA TA CE*
        *1441H/2019M.*

®�
GASKIYA WRITERS ASSOCIATION.�
{ Gaskiya É—aya ce daga Æ™inta sai É“ata burinmu mu faÉ—akar da al’umma domin ribantar duniya da kuma lahira.}

    ```🎐G•W•A🎐```

GASKIYA DOKIN K’ARFE•🏇ğŸ?

Dedincanted
to Family🥰🥰

~VOTE & FOLLOW 4 Wattpad~@
~GaskiyaWritersAss~.

INAMA WRITTENS ƊIN GASKIYA WRITTENS BARKA DA DAWOWA HUTON ƘARSHIN MAKO🥰

BISMILLAHI RAHAMANR RAHIM

         *Paga* 3�3�

__📖 Koda ta shiga ɗakin Daddy Yana zaune saman kujera yana hutawa dan yau a gajiye ya dawo.

Da murnar ta ta ƙarasa gareshi tana faɗin.

“Daddy sannu da zuwa ga lemu na kawo maka ka sha”.

Dariya yayi mai É—an sauti kana yace, “yau autar Momy ke tarbana?”.

Tace, “aikuwa Daddy dan yau Momy ta Aunty da É—iÆ´an ta take shine nace bari nazo wajan Daddy na”.ta Æ™arasa zancin ta mai zubu masa lemu ta miÆ™i masa ya Æ™arÉ“a ya sha.

Tunda ya fara sha ya fara jin wani sanyin daÉ—i na ziyar tar zuciyar sa, dan haka yasha da yawo kana ya aje yace, amma Kulsum kin taimawa Daddy ki dan haka, keje ga chocolate can ki ďauka ke kaďai”.

Aikuwa tun bai kai ƙarshin zan cin ba ta antaya da gudu taje ta ɗauku.

Jug,É—in da ke gaban Daddy ta É—auka tana faÉ—in Daddy nagode,naje naci abuna bada Ummi ba bada Afra ba”.

Shi dai Daddy kallon ta yake yana murmushi har ta fice.

Kitchen ta koma wajan Fatima da murnar ta, Daddy ya bata chocolate.

Ko kunun ayar bata tsaya karɓa ba, ta aje jug ɗin hannu ta ta fice da da gudu.

Ita dai Fatima da kallo ta bita,jug É—in da ta aje ta d’auka ta buÉ—e kaÉ—an ne ya rage,aiÆ™uwa wani daÉ—i ne taji, lokaci É—aya ta fara faÉ—in, “alhmdullah”.

Tana gama haÉ—a kunun ayar ta É—abi wanda zata sha saura tasa a fridge.

Part É—inta ta koma taje tayi wanka ta shirya ta É—auko husunil musulm ta fara karantawa kafin atada sallah.

Daddy ko tunda Kulsum ta fice,tashi yayi yaje toilet domin yayi wanka.

har ya fara wanka yaji zuciyar sa ta fara tashi,k’ok’arin amai ya fara aikuwa ba bata lokaci ya fara amai,saida ya yi amai sosai kana ya É—ago kansa dumin yasa karma wajan da yayi aman ruwa,aikuwa wani baÆ™in abune yaga shine ya amayar,abun ya bashi mamaki dan shi bai san yaci komi ba tun safe sai yanzu da Kulsum ta kawo masa lemu yashi.ruwa ya zubama wajan kana ya fara wanka dan jikin sa duk yayi masa ba daÉ—i.

Koda yafito wanka mam shfawarsa da ke saman mirrow ya É—auka waÉ—an da ta haÉ—e su da man habba,su ya É—auko yashe jikin sa da su kana ya kwanta saboda gaba ki É—aya jikinshi yayi sanyi.

Bai jima da kwanciya ba bacci ya É—auke shi.

Momy ko tana can ɗakin baƙi ita da yaran ta suna fira dan yau babbar ɗiyar ta tazo gida wadda ke aure abuja,wato Maryam(maram).

Tana da yara biyu Affan, Afar,.yau suka kawo ma su Momy ziyara dan sunjima basu zoba.

Fatima ko sai da aka tada sallah,tashi tayi tayi sallah.bayan ta kammala tajima tana azkar kana ta tashi.

Zama kaɗai ce taji ya ishe ta dan haka ta taso ta sauka ƙasa.

Koda ta sauk ba kowa har zata zauna wani tunani ya faÉ—u mata,part É—in Daddy ta kama hanya dumin taje duk a tsorace take amma ta dake ta kama hanyar ta tafi.

A hankali take tura ƙufar shiga,koda ta ƙarasa Parlour baya nan dan haka ta ƙarasa bedroom ɗinsa.

Kwace ta same sa yayi nisa cikin bacci,a hankali ta ƙarasu har ta kawo wajan da yake kwance.

Kallon sa tayi da kyau,cikin ranta tace ƙila ko sallah Daddy bai yiba.

Dan haka a hakali ta zauna saman gadon da yake kwance.

Tunanin yadda zata tadashi ta fara yi domin yatashi yayi sallah.

Hannuta ta ɗura saman ƙirjin sa tafara shafawa a hankali,a hankali ya fara ware idon sa,itako tana ganin haka duk da a tsorace take tafara sakar masa wani ƙayataccin murmushi.

Ido ya kife ta daso, tunani yafara ina yasan ta?aikuwa lokaci É—aya ya tashi zaune.

Kallon ta yakeyi kamar bai taɓa ganin ta ba.ita ko duk tsoro ya rufeta dan haka tayun ƙura dumin ta tashi.

Cikin hanzari yajawo ta jikin sa yana cewa.

“Zainab ina kikaje na daina ganinki,me namiki kike guduna,wallah da gaske sonki nake yi bazan iya rabuwa dake ba”.

Ajiyar zuciya ta sanya mai sauta kana ta farawa Allah Kirari. kana tace,”Daddy yanzu katashi kayi sallah daga baya mayi magana”.

Tana mai tashi ta bar part É—insa.

Da ido ya bita har taɓa ce ma ganin sa kana ya tashi domin yayi sallah.

Alwala yayi yafice zuwa masallaci.

Ita ko tana ƙarasawa part ɗinta ta faɗa saman gado ta fara kukan.

Dan ita bata san kukan me zatayi ba,amma tayi godiya ga Allah sosai da ya fara karkatu mata da hankalin mijin ta gare ta.

Ƙuma ta ɗau ɗanmar yaƙi da duk wani wand ke son rabata da mijin ta.kuma zata tayi masa biyayya kamar yadda tasan zatawa wanda ta keso idan ta aure shi,dan haka duk wata kunya da tsoro zata ajesu waje ɗaya ta yima mijin ta biyayya kamar yadda ya kama ta.

Dan haka ta shi tayi taje tayi wanka tayi sallah isha’i.

Bayan ta kammala,tashi tayi tayi taje wajan mirro ta fara shefe jikin ta da mayuka masu Æ™amshi,bata tsaya wata kwalliya ba,gown ta atamfa ta saka tayi mata kyau sosai dan haka ta É—an zauna ta idar karatun addu’ao in ta,sai ta sauka Æ™asa.

Shiko Daddy tunda ya fita bai dawo gida ba saida akayi sallah isha’i,kana ya dawo.

Ana gama sallah ko gasai wa da mutane bai tsaya yiba ya fice domin burin shi ya dawo gida ko zai ganta.

Cikin sauri yake tafiya har kawo gida .

Yana ƙarasu wa falo tsaye yayi dan Momy ita da yaran ta yanzu sun dawo nan falo suna fira.

Afra da Affa ne suka zu da gudu wajan Daddy suna faÉ—in,oyoyo “Daddy Aunty Kulsum”.

Hannu sa ya ware suka shiga yana mai jin daÉ—in ganin su.

Zama yayi yana mai dura afra aciyar sa.

Maram ta tasu har wajan da yake ta duƙa ta gaidashi,amsawa yayi yana mai farin cikin ganin su.

Ya tambaye ta gida lafiya tace eh duk lafiya suke.

Fira suka fara yaushe gamo,amma rabin hankalin sa yana kan Fatyn shi.

Har sha biyu saura bai samu tashi yaje wajan ta ba, kuma gashi bacci yaji dan yau ya kwaso gajiya a wajan aiki,dan haka part É—insa ya wuce yaje yayi wanka kana ya kwanta bacci ciki da tunanin ta.

Ita ko tunda taga bai zoba har tasu taje wajan sa kuma ta fasa dan haka tayi shirin kwanciya ta kwanta bacci.

Itama Momy da yaran ta suka tashi wukaje ma kwancin su kana ita ko ta wace part na Daddy.

Ba wani bacci kirki tayi ba dan ƙarfi biyun dare ta farka ta fara na filfili,tana kai kukan ta ga Allah.

Sai da akayi sallah asuba kana tayi sallah ta É—an kwanta.

Shiko Daddy yau koda ya tashi ya makara shiyasa bai samu yaje ya tasu taba.

Amma yana dawowa gida bai tsaya ko inaba sai part É—inta.

Ita koma lokacin ta samu ta kwan ta, a hankali yake tafiya har ya kwao part nata,ko knocking ba tsaya yi ba, key ɗinsa yasa ya buɗe ƙofa ya shiga.

Tundan ya kama hanyar part ɗinta wani ƙamshi turare mai daɗi ya fara ziyar tar sa,uwa uba bare yanzu da ya shigo parlour ta .

Wata sanyayar ajiyar zuciya ya saukar,zama yayi sama ɗaya daga cikin kujerun parlour ,sai da yayi ƴan secnds kana ya tashi ya ƙarasa bedroom nata.

Koda ya Æ™arasa kwance ya same ta, a hankali ya futa cewa,”kardai ace bata yi sallah ba”.

Dan haka da suri ya ƙarasu gare ta,zama yayi ƙusa da ita a hankali ya kai hannusa ga reta,ya fara tashinta.

Da yake bacci nata baiyi nisa sosai ba,dan haka a hakali ta fara buÉ—e idon ta,ta sauke su akan shi.

Yana ga ta buÉ—e ido cikin muryar mai kama da rarrashi yace,”tashi kiyi sallah har angama sallah baki tashi ba”.

A hankali ta buÉ—e baki ta fara magana tace, “nayi sallah yanzu ma na kwanta”.

Yace, “to shine zaki kwan ta baki san ba kyau ba”.

Bata ce da shi komai ba.jin shurun da tayi ne yasa ya Æ™arasu gareta,jikin sa ya sanya ta kana yasuma faÉ—in My teema na, ina kika je na daina ganin ki? kuma kinsan ba zan iya ruwa baki a tari dani ba ko?”.

Koma bata ce masa ba inba hawaye da ke zuba a idon taba,tunda ya fara magana.

Aikuwa gaba ki É—aya ya rikice yafara rarra shin ta,irin yadda taga ya rikice ne yasa ta daina kukan da takeyi.

A hankali ta É—ago ido ta kalle sa kana ta furta cewa,”Daddy da gaske kana sona?”.

Saida ya ƙara matseta ajikin sa kana yace.

“Fatima ko ban faÉ—a ba duk wanda ya kalleni yasan akwai sonki maitarin yawa atari dani”.

Tace,”to Daddy amma inson ka nemi tsarin jikin ka,kuma ka Æ™ara dagewa wajan tsayuwar dare,in har kana son muci gaba da zama cikin kwanciyar hankali,kuma da ka ke faÉ—in ina naje,niba inda naje ina nan dan kona je É—akin ka korata kakeyi shiya na dana dan naga yanzu ga daina sona”.

Bai bari ta kai Æ™arshin zancin ba ya rufe mata baki tare da faÉ—in,dan Allah kada ki faÉ—a haka wallahi ina meki son da baki bazai iya faÉ—a ba,kuma bam masan kin taÉ“a zowa na Æ™ureki ba.amma dan Allah kiyi hakuri kuma kada ki faÉ—ama yaya Sa’a,kuma insha Allah zan Æ™ara neman,anjima ma zanje wajan kawo Gwaggo”.

Tace,”kada kada mu Daddy kowa ma bazan gayama ba bare Hajiya”.

Idonsa yasa cikin nata yana mata kallon da gaske?kai ta girgizamasa alamar eh”.

Yace,”ya akayi naji jikinki da zafi ko baki da lafiya ne?”.

Idonta suka suma kawo ruwa a hankali ta buÉ—e baki tace. “na kwana biyu banda lafiya dan ko aiki da Æ™yar na keyin sa”.

A razane ya furta aiki! to waya saki aiki ne?,to bari kiji ban yadda ki sake É—aukar koda wani tsinke ba da sunan aiki, ni bari ma nakira doctor ya dubamin ke, dan inson naje gida Kowa Gwaggo”.

Tashi yayi domin yaje part É—insa ya d’auko wayar sa.

Har zafita ta kira shi tace, “Daddy ina zuwa” .
tsayowa yayi yana jiran ta,wata kwalbar zuma ce ta ɗauƙo ta ɓuɗe ta zuba a cokali ta fara bashi yana sha sai da ta bashi kosan cokali biyar kana ta aje.

Kallon ta yayi yace,”bata isan ba aÆ™a ramin”.

tace,”a’asai anjima zan Æ™arama Daddy”.

Yace,to abu biyu zaki bani anjima ko?”.

Tace, “meye É—aya?”.

Ido É—aya ya kanne mata.

Kuka taso mayi tana faÉ—in Allah ban yadda ba Daddy”.

Dariya ya sanya yana mai buɗe ƙofa yafita.

By Sumy�

Comment
Nd
Shere
1/23/20, 11:48 AM – +234 706 211 8047: 💦💦💦💦💦💦💦
💦💦💦💦
💦💦

 *ƘAWAR ƳATA CE*                                                          *1441H/2019M.*   

®�
GASKIYA WRITERS ASSOCIATION.�
{ Gaskiya É—aya ce daga Æ™inta sai É“ata burinmu mu faÉ—akar da al’umma domin ribantar duniya da kuma lahira.}

    ```🎐G•W•A🎐```

GASKIYA DOKIN K’ARFE•🏇ğŸ?

Story & Written
By
SUMY✍�

Dedicated to..
Family🥰🥰🥰

~VOTE & FOLLOW 4 Wattpad~@
~GaskiyaWritersAss~.

Congratulations Mrs Basakkwace, ina tayaki murnar kammala novel É—ikin me suna Samha,faÉ—a karwa dakikayi akansa Allah yabaki lada,kuskure Allah yaya femiki.kuma ina tayaki murnar fara sabon novel É—inki mai suna WATA KISHIYA BATAYIBA
Allah yasa anfara asa’a

Page 3�5�

__📖 Wani kallo Momy ke binta da shi gabiki ɗaya tsoro ya bibiye ta, amma sai ta tuna maganar da matar Malamin su ta faɗa mata, dan haka ta dake zuciyar ta, ta fara ta fiya domin ta koma part nata.

Har zata wuce Momy tayi saurin cin gaban ta,kallon Æ™asa da sama tayi mata kana tace, “ni zakima rashin kunya?kice zaki raÉ“i mijina ko? to bari kiji, ba’ayi wata É—iya mace wadda zata raÉ“ar mijina ta zauna lafiya ba, dan haka sai naga wanda ya É—aure miki Æ™afa da har zaki É—au shegiyar Æ™afar ki kije part É—in mijin har da haÉ—a masa breakfast,kece tsowar munafuka É—iyar matsiya ta”.

sai da tayi mata tas kana ta kyale ta.

Ita ko Fatima ko É—aga kai batayi ta kalle ta ba bare tasa ran zata tanka mata.

sai da tabari tagama zubar ta kana ta raɓe ta gyafinta ta wuce war ta ba tari data kalle Momy ba.

Haka data yi ba ƙaramin ɓata ma Momy rai yayi ba dan haka da hanzari ta bi bayan ta.

Koda Fatima ta ƙarasa parlour duk sun nan zaune suna fira,amma tayi kamar bata ga wata halitta a wajan ba,dan haka ta kama hanyar da zata sada ta sa shen ta .

Aikuwa Nabila naga nin haka cikin É—aga war murya ta daga mata tsawa,tari da faÉ—in, “ke!”

Tafiyar ta taci gaba dayi kamar bata san da ita take ba.

Momy da taga Fatima batada alamun tsayowa, dan haka itama ta daka mata tsawa tari da faÉ—in,”marar mutuncin yarinya hala bakiji ana miki magana ba”.

Sai da Momy tayi magana yasa tayi tsaye cak, batari da ta juyu ta kalle suba,duk da atsora ce take amma tada sosai.

Abunda tayi ya ɓata musu rai sosai,dan haka cikin han zari Nabila ta zo ga banta hannu ta ɗaga dan ta mare ta, ita ko Fatima cikin da dakewar zuciya ta riƙi mata hannu kallon-kallon,suka fara yi tsaka nin su.

Ahankali Fatima ta buÉ—e baki tace,”Nabila me namiki zaki mareni?”.

Iya saÆ™owa Nabila tasaÆ™o dan haka hunnu ta ta fizge domin ta kai mata mari,sai Momy ta É—aga mata hannu tare da cewa, “Nabila bar ni da ita,kishi zatiyi dani,to kijira dan wallahi ko uwarki sai tayi kuka bare ke” Momy na faÉ—in haka tayi Æ™faci ta kama hanyar part É—inta da sauri batari da tace musu komai ba.

Itama Fatima ta raɓa ta gyafin Nabila ta koma part ɗinta.

Momy na shiga É—ikin É—inta wayar ta ta É—auko,kiran number Hajiya Shafa tasa.

ringing da ba wuce biyi ba akayi picking, sai da suka gaisa Momy ta Æ™ara da cewa,Hajiya inaga fah kamar aikin nan ya karya”.

Hajiya Shafa tace, “a’a gaskya aiki na nan,ta Æ™ara da cewa me kika gani da zaki ce haka”.

Momy tace,”komai nagani Hajiya”.

Nan Momy ta shiga faÉ—ama Hajiya Shafa duk abunda ta gani har ma da wanda bata gani ba.

Sai da Hajiya Shafa ta numfasa kana tace,”kada kisa damuwa aranki,kinga jebi sai mukoma mugaya masa abunda ake ciki,dan kinga yau bara nar zuwane wajan saba sai jibi muyi samma ko sai muje wajan sa”.

Momy tace,”to Hajiya zanyi iya hakuri har jibi? dan wallahi ni ka dai nasan me nakeji a zuciya ta”.

Hakuri Hajiya Shafa ta shiga bata, da nuna mata wannan karun É“atar da ita za’ayi babu mai saki ganin ta kuma babu mai saki maganar ta har abada.

Aikuwa Momy ba ƙaramin daɗi tajiba dan haka tasaki jiki suka cigaba da fira har daga baya sukayi sallama.

Parlour tadawo ta sa mesu zaune.

sai da ta zauna Maram ta kalle ta kana tace,”Momy haka kuke fama da yarinya Æ™arama tana muku rashin mutun ci kuma baku É—au mataki ba?”.

sai da Momy ta numfasa kana tace,”Maram yarinyar nan shegiya ce, duk abuda kayi mata sai ta kwance shi,amma nasan wannan karun tayi Æ™aÉ—an ta kunce shi”.

Maram tace,”haka yafi dan na tsane na ganta agidan nan. Momy ni gani nake kamar ciki ne da ita”.

Momy tayi saurin faÉ—in, “a’a Maram bata da komai”.

Tace, “Allah Momy haka nake gani,amma zan sa ido akanta kafin na bar gidan nan”.

Sai Momy tace,”to kisa dan wallahi in shine sai naci ubanta kafin na zubar da shi”.

Haka dai suka cigaba da firar su,Zainab kam ko mai bata ce musuba duk abundan da suke iya kar ta kallon su.

Dan yanzu ta rage jin tsanar Fatima a ranta.

Ita ko tunda ta shiga ɗaki ta faɗa saman gado ta fara kuka mai tada hankalin mai sauraru kamar wadda aka niƙama duka.

Sai da tayi mai isar ta,kana ta tashi taje toilet tayo alwala ta zo ta fara sallar walha.

Bayan ta kammala tajima tana addu’a kafin ta shafa,ta É—auko husunl musulima ta fara karan tawa,har sai da akayi sallah azahar tayi sallah kana ta kwanta bacci.


Daddy ko tunda ya fita daga gida gida Kawo Gwaggo ya fara zuwa,bayan sun gaisa,Daddy ya faÉ—a masa abunda ya kawo shi.

Sai da yayi ma Daddy faɗa mai haɗi da nasiha kana ya haɗa masa magana ya bashi,man habba ya ɗauko ya bashi yace ya tabbatar duk zai kwanta barci ya shefe ƙirjin sa da shi,dan yana kariya sosai koda an jefeka acikin barci da ikon Allah ba abunda zaiyi ta siri akan kai.

Ya Æ™ara dace masa kuma ya dage da azkar safe da yamma insha’Allahu ba abunda zai same shi.

Godiya mai yawa yai masa,kana yayi mishi alhairi sannan ya wuce gidan Gwaggo ya gaisheta kana ya wace office É—insa.

Bai jima da zama office ba doctor ya kirasa yace, “gashi nan zuwa ya kawo saka makon abunda ke damun Fatima”.

Daddy yace, “sai dai kasameni office dan yanzu nafita daga gida”.

Doctor yace, “oky ganinan zuwa”.

Daddy yace, “tom yana mai aje wayar.

Bai sujima da yin wayar ba.doctor ya ƙarasu.

Damar shiga ya bashi sannan ya shigo.

Sai da suka ƙara gaisawa sannan doctor ya fara yiwa Daddy bayani.

Yace, “da farko dai congratulations,ina tayaka murnar matar ka na dauke da cikin wata biyu da sati uku”.

Daddy ba abunda yake faÉ—a sai “Almhdullah”lokaci É—aya farin ciki ya mamaye fuskar sa.

Doctor ya Æ™ara da cewa, kuma abar barin ta tana shiga damuwa saboda haka kan iya haifar da illa sosai ga abunda ke cikin ta”.

Ta kardar magani ya ba Daddy yace, “sai ta rinÆ™a sha insha’Allahu zata samu Æ™arfin jiki,kuma zata daina zazzafin da takeyi akai-akai.

Godiya Daddy yayi masa sosai kana yayi masa alhairi mai tarin yawa.

Shima doctar godiya yawa Daddy kana yayi masa sallama ya wuce.

Tunda doctor yatafi Daddy yasu ya koma gida amma aiki ya riƙi shi,dan ko kiran da Hajiya Kulu kema sa baibi ta kan saba,daga ƙarshe ma da yaga ta dameshi da kira kashe wayar yayi yaci gaba da aikin sa.

Itace bata farka ba sai da akayi sallah la’asar, tashi tayi tayi sallah kana ta sauka Æ™asa domin ta shiga kitchen.

Har ta É—ura sanwa tana cikin yin blending É—in kayam miya,sai ga Nabila ta shigo ita da yayar su Maram.

Ko kallon inda suke batayi ba taci gaba da aikin ta.

Tunda Maram ta shigo takefe Fatima da ido tana su ta gane gaskiyar lamarin.

Itako bata ma kula dasu ba dan aikin ta takeyi.

Tana cikin haka Nabila ta zo har wajan da take tana leƙin me take girka wa.

Kallon ta tamaida ga Fatima kana tace,ke idan kin gama ki haÉ—a mana kun aya dan yau shi muke son shi”.

Kamar bata san da halitta awajan ba haka tayi musu.

Maram ce ta daga mata tsawa tana faÉ—in, “ke bakiji ana miki magana kinyi banza da mutane”.

Sai alokaci ta É—ago ta kalle su,kana tace,”kuyi hakuri ban É—auka dani kuke ba”.

Har Maram zatayi magana Momy ta shigo tace,”wai me kukeyi ne naji kamar hayani ya”.

Nabila ce tagaya mata ƙarya da gaskiyar abunda ya faru.

Momy tace, “ku kyale ta, bana son kuna haÉ—a baki da É—iyar ta lakawar nan,dan haka kuje idan tagama girki dole ta ta kawo kuci”.

Duk abunda suka ce ko kallon su bata yiba, bare har su sa ran zata tanka musu.

Suna fita taci gaba da aikin ta,ƙarfi biyar,ta kammala,sai da ta haɗa komai ta koma part ɗinta,wanka tayi kana tazo gaban mirrow ta fara ɗan-ɗasa kwaliya tayi kyau sosai bayan ta shirya ta kashe ɗauri ba shakka tayi kyau sosai,turaruka masu kamshi ta ɗauko ta feshe jikin ta dasu,kana ta ije ta zauna jiran dawo warsa.

Oyoyo, dataji Kulsum nayi yasa tasan Daddy ne ya dawo dan haka,takalma masu tudu ta sanya kana tafara saukowa ƙasa.

Ahankali take tafya har ta kawo setop ɗin ƙar she,lokacin ita ma Momy tafito cikin shirin ta dan ko ita ba laifi tayi kyau.

Yana ƙara suwa parlour da Momy yafara cin karo,sannu da zuwa ta masa kana ta ƙarɓe jikar dake hannusa,yana mai ƙarasuwa cikin parlour.

Su Zainab gaisheshe suka farayi,ya amsa ciki da sakin fuska.

Momy ta dube shi tace,”mu Æ™arasa daga ciki sai ka É—an huta”.

Ba musu yace, to muje”.

part ɗin Fatima ya kalla,aikuwa tsaye ya ganta tana sakar masa murmushi mai ƙara mata kyau.

Alama yayi mata da hannu tazo.

Bamu ta fara tako ahankali har ta ƙarasu wajan da yake.

Durkusawa tayi, tayi masa sannu da zowa.

Amsawa yayi ciki da fara’a afuskar sa, tari da faÉ—in, “ya jikin naki”.

Sai da tayi Æ™asa da kanta kana tace, “Ahmdllh”.

Tashi tayi domin ta koma part É—inta.

Kallon ta yayi yace,”Fatima ki kawomin ruwa na sha”.

Ahankali tace, “to Daddy”.

Wani kallo ne Momy ke aika mata wanda bana ko mai bane sai na tsana.wanda ita ko Fatima bata masan tanayi ba.

Fatima tafiya tayi, ta dauko masa ruwa masu sanyi da lemun kwa-kwa,ta kawo masa,yana zaune a parlour shi shi da Momy.

Ajewa tayi domin ta tayi fiyar ta, amma yace ta zuba masa ya sha.

Ba musu ta zuba masa ta bashi ya karɓa.

Lura da kallon da Momy keje far ta dashi ne yasa ta tashi domin ta koma.

Har ta kai Æ™ofa fita daga parlour Daddy yace,Fatima ina zakije ki tsaye muyi fira mana”.

Tace,”a’a Daddy idan kayi wanka zan dawo”.

Yace,”to yanzu ko zanyi”.

Tana fita Daddy ya kalle Momy yace,”ki haÉ—amin ruwan wanka”.

tashi tayi ta haÉ—a masa ta dawo tace masa ta haÉ—a tashi yayi yaje yayi wanka ya fito.

Sai da ya kammala shirin sa sannan ya fito parlour inda ya bar Momy anan yazo ya sameta.

Zama yayi ta haÉ—a masa abinci ya É—an ci bada yawa ba, tashi yayi yana faÉ—in,”Alhmdullah”.

Momy tace, “ba dai har ka kushi ba yace,na kushi Hajiya,fita ma nakeson nayi dan jira na akeyi”.

Momy tace,”haba Alhaji yaushe ka dawo da har zaka fita”.

Yace,kiyi hakuri ba jimawa zanyi ba”.

Adawo lafiya tayi masa kana yasa kai ya fice.

Da fitar sa part ɗin Fatima ya ƙarasa zaune ya sameta,riƙi da lattafi tana karan tawa.

Sallama yayi yana mai ƙarasuwa gab da ita.

Amsawa tayi ta mai ƙara gaida shi.

Kallon ta yayi yace,”kin ci abinci kowa?”.

Kasa tayi da kanta kana tace,”a’a yanzu zanci”.

Yace,”to zo muje kici sai kasha magani, dan doctor ya kawa maganin ki”.

Rau-rau tayi da ido kana tace,ni fah nawarke Daddy”.

Jikinsa ya jawo ta sai da ya kai bakinsa dai-dai kunne ta kana yace,baki son kije ki gada Ummah da Gwaggo,ko?”.

Kallon sa tayi cikin muryar shagoÉ“a kana tace,”Daddy kai fa kace zaka kaini”tana matsar hawan shagoÉ“a.

Yace,”eh zan kai ki amma saikin ci abinci kin sha magani da”.

Da hanzari ta yunkura zata tashi saman jikin sa sai ya riÆ™ita kana yace,”so kike kiman É“arna ko”. Yana mai lalubar cikin ta.

Bata bi ta kan magar da yayi ba dan burita yanzu taje gida.

Kamar zatayi kuka tace, “Daddy sakeni naje naci sai mutafi”.

Yace, “naji amma kitafi ahankali”.

Tace, “to” dan ta Æ™agar yasake ta.

Tashi tayi taje ta É—auko abinci taci, kana ya bata magani ta sha, sannan yace taje ta canja kaya jikin ta waÉ—an da kejikin ta turare ne dasu,kuma tasan ba kyau saka turare ga macci idan zata fita.

Dan haka taje ta canza ta É—auku faya finta ta fito tasa meshi parlour zaune yana jiranran ta.

Sai da ya kalle shigar yaga tayi mai kana yace,”su tafi”.

Ahankali suke taka setop É—in har suka sauka.

Alokacin Momy na zaune ita da yaran ta Zainab ce kawai bata wajan.

Momy kallan Daddy tayi tace,”aw bakaje ba?na É—auka katafi”.

Yace,”aa yanzu zanje”yana mai takawo dan ya fita.

Momy kallon ta ta maida ga Fatima wada kebin sa a baya kana tace,”ke ina zaki ne?”.

Daddy ya juyu ya kalle Momy yace,”tare zamu fita”….bai tsaya jin me zata ceba suka Æ™ara gaba.

Suna kaiwa wajan da mota take driver ya buÉ—e musu suka shiga kana yaje suka wuce.

Momy ko har suka fita bata sani ba,dan sun barta da baki buÉ—e tana mamaki tare zasu fita…..

#Comment
#Vote
#Share

Sumy ce
1/23/20, 11:48 AM – +234 706 211 8047: 💦💦💦💦💦💦💦
💦💦💦💦
💦💦

ƘAWAR ƳATA CE
1441H/2019M.

®�
GASKIYA WRITERS ASSOCIATION✍�
{Gaskiya É—aya ce daga Æ™inta sai É“ata burin mu faÉ—akar da al’umma domin ribantar duniya da lahira}

 ```🎐G•W•A🎐```

GASKIYA DOKIN ƘARFE�

Story & Written
By
Sumy✍�

Dedicated to..
Gaskiya writers

~VOTE & FOLLOW 4 [email protected].~

Page 26

_📖 Maram ce tadube Momy tace, ” wallah tun wuri ki ta kama yariyar nan birki dan inba haka ba kinaji kina gani komai na gidan nan zai dawo hannun ta”.

Nabila tace, “kema kya faÉ—a Aunty Momy ko naci zan yima yarinyar nan hukunci sai tace kada nayi amma wallahi wannan karun ko Momy ta hana sai nunci uban ta”.

Ita dai Momy ta kasa cewa komai dan ita kadai tasan me takeji a zuciyar ta.dan haka tashi tayi ta koma É—aki dan surutun su ya nasu ya hai far mata da matsale a zuciya.

Bin Momy da kallo sukayi kana Nabila tace, “Aunty ba zamu zuba ido akan wannan Æ™aramr yariya tayi yadda take so ba a gidan nan”.

Maram tace, “bani kwana biyi kafin natafi zan san abunyi”.

Basuyi nisa da tafiya ba Daddy ya kalle Fatima yace, “ina zamu fara zow gidan su Umma ko gidan Gwaggo?”.

Ahankali taÉ—ago kai ta kalle sa kana tace,”gidan Gwaggo zamu fara kaga ban taÉ“a zowa na gaishe taba”.

Sai da yaja hancin ta kana yace, “duk yadda kikace haka za’ayi” yana faÉ—a yana murmushi.

Driver Daddy ya faÉ—ama wurin da zai kai su.

Basu tsaya ko ina ba sai gidan Gwaggo.Daddy ya fara fita daga motar kana ya buÉ—e mata ta fito.

Hannusa ya sakala anata kana yace, “muje ko”.

Kallon sa tayi tare da saka masa kukan shagwaÉ“a kana tace, “Daddy sake min hannu kaga shiga zamuyi kuma ni kunya zanji idan muka shiga ahaka”.

Yace, “meye na kunya tunda mijinki ne ba kowa ba”.

Tace, “eh Daddy duk da haka kayi hakuri har mu fito”.

Yace, “to naji”…yana mai sakin hannun ta.

Ahankali suke tafiya har suka ƙarasu paulour Daddy na gaba tana biye.

Sallama sukayi ma Gwaggo.

Amsawa tayi tana mai tashi daga shingi É—in da take.

Yana shigowa Fatima ta shigo,aikuwa Gwaggo naganin Fatima ta fara murina tana faÉ—in,

“Yau baki ne damu agida? sanunku da zowa”.

Cikin na tsowa Fatima ta ƙarasu wajan da Gwaggo take ta durƙusa har ƙasa ta gaishe da Gwaggo cikin mutunci.

Amsawa Gwaggo tayi tana mai faÉ—in ya gidan duk lafiya kuke?”.

Sai da tayi Æ™asa da kan ta kana tace, ” “lafiya Æ™alau muke Gwaggo”.

Bayan sun gama gaisawa Gwaggo ta dube shi tace, “Mansur kaje su Sa’adatu sun dawo kowa?”.

Da kamar mamaki ya É—ago kai ya dube ta kana yace, “yaushe suka dawo Gwaggo ?”.

Tace, “to baka ma sani ba ai na É—auka daga can kuka fito ashe baka masani ba,dan haka ku tashi tun yanzu kuje duk Æ´an uwa nata zuwa yi mata sannu dan haka ko tashi kuje can kuma kace ina gaishe ta da jikin mijin nata”.

Kallon Gwaggo yayi yace, “to” yana mai tashi dumin su tafi.

Kallon Fatima yayi yace, “tashi muÆ™arasa wurin yaya babba ta dawo mu gaisheta”.

Sai da ta Æ™arayi Æ™asa da kanta kana tace,”to.”

Jikar ta ta buɗe ta ɗauko wata bakar leda ta aje gaban gwaggo tana mai meƙiwa tsaye.

Kallon ta Gwaggo tayi tace, “Fatima har da wata É—a wai niya?”.

Tace, “a’a Gwaggo kiyi hakuri ba yawa”.

Gwaggo tace, “ba komai na gode sosai Allah yayi albarka”…addu’a tamu su sosai kana ta rakasu har suka shiga mota suka suce.

Sai da suka kama hanya Daddy ya jawo ta jikinsa kana yace, “me kika kaima Gwoggo shine baki gwada min ba ko”.

tace,” “dan zanba mahaifiya ta abu sai ka gani”.

Sai da ya ƙara matsa ta ajikin sa saboda wani daɗi ne da yaji har cikin zuciyar shi da takira Gwoggo mahaifiyar ta.

Yace, “naji mai mahaifiya nima zan rama”.

Murmushi tayi bata reda ta ce da shi komai ba.

Dai-dai lokaci kuma suka ƙarasu bakin gate ɗin gidan.

Horn driver yayi,mai gida yazo da sauri ya boÉ—e musu,hanci motar sa yasaka aciki kana yasa mu wuri yayi packing.

Kallon ta Daddy yayi kana yace, “ki Æ™arasa daga ciki dan kinsan ni mai laifi ne,idan kin bata hukuri sai ki kirani na Æ™arasu”.

Kallon sa tayi tace,”Daddy wani laifi kuma kayi mata?”.

Yace,”kije kiyi yada nace”.

Kallon sa tayi tace, “to Daddy tana mai buÉ—e mota ta fita.

Har tafita ta juyo ta kalle Daddy cikin muryar me taushi tace,”Daddy to da wace waya zan kira ka? koda wayar ta?”.

Kallon ta yayi kana yace, “ke ina wayar ki?”.

Tace, “kasan yanzu bani da waya”.

Kallon ta yayi har yaso yayi magana kuma ya fasa.hunnusa yasa aljihu ya ɗauko wata haɗaɗiyar waya ya miƙi mata yace,

Ta kirashi da wannan”.

Ƙarfa tayi tana mai ƙarsawa cikin gidan.

Ahankali take tafiya har ta kai paulour da taji kamar hayani ya na tashi.

Dan haka sallama tayi ta shiga.

Amsa mata suka.Hajiya Sa’a ta É—ago kai ta É—ube ta fuskar ta É—auke da murmushi kana tace,wanake gani kamar Fatima”.

Murmushi itama tayi a dan kunya ce sai da ta duka har ƙasa kana ta gaishe ta da tambayar ya mai jikin.

Amsawa tayi tana faÉ—in, ” jiki Alhmdullah”.

Sai da suka gama gasaiwa kana tace, “ina shi mijin naki ko batare kuke ba?”.

Fatima tace, “a’a tare muke amma bari nace ya Æ™arasu” tana mai danna kiranshi tace ya Æ™arasu.

Ba tajima da kiran shiba ya ƙarasu har cikin paulour ya shiho dauke da sallama abakin sa.

Amsawa sukayi kana ya fara gashe da Hajiya Sa’a Amsawa tayi tare da jefar sa da kallon mai haÉ—e da tuhuma.

Matan dake zaune a wajan suka gaisheshi ya ammasa tare da faÉ—in amaryar Yaya kuke?”.

Amsawa tayi tare da faÉ—in,wannan ce amaryar ka?”.

Yace, “eh tace”.

Sai Hajiya Sa’a tace, “hala baki santa ba?”.

Sai ita amaryar Alhaji Sulaiman wato kishiyar Hajiya Binta,tace, ba wanda taje wurin sa muma shiyasa bamu je wajan ta ba”.

Daddy yayi saurin faÉ—i,kuyi hakuri laifi nane da ban kai taba amma yanzu zan rinÆ™a kai ta”yana mai tashi soboda anfara kiran sallah.

Sai da yafita Hajiya Sa’a ta kalle su tace, “ya kamata kuma ku haÉ—e kanku sai kuji daÉ—i zaman ku tunda su waÉ—an can sun haÉ—e kansu kuma me zai hana ku haÉ—e naku,duk da nasan sunfiku sanin komai amma kuma idan kuka haÉ—e naku zaku jidaÉ—in rayuwa kuma za suji shakkar taÉ“a É—aya daga cikin ku”.

Kallon ta ta maida ga Fatima kana tace, “ya zaman naku yake duk da nagan ku atare amma ban sani ba ko da wata matsala?”.

Fatima tace, “a’a wallahi Hajiya komai Alhmdullah”.

Tace, “kai masha Allah, gaskiya naji daÉ—in haka”.

Kallon ta ta maida ga matar Alhaji Abdullah wato kishiyar Hajiya Shafa tace, “kefa Maryam ya zaman naku?”.

Sai da ta numfasa kana tace,”wallah Hajiya sai godiyar Allah dan dani da babu duk É—ay take a wajan sa,inba ita tace ba baya komai dani da Amina duk haka muke agida ba mai jin daÉ—i mijin sa”tana faÉ—a tana zubda hawaye.

Ajiyar zuciya mai karfi Hajiya Sa’a ta sauke kana tace,”kuyi hakuri kubani kwana biyu dai-dai mutane sun rage zuwa dubiya sai nasan abunya inshaAllahu,komai zai wuce”.

Gabaki É—ayan su sukace Allah yayar da.

Musayar number waya sukayi suda Fatima,suka ce mata bayan kwana biyu zasu kai mata ziyara.

Godiya tayi musu sosai,kana suka cigaba da fira kamar sun san juna.

Suna cikin haka Daddy ya dawo yace, “tazo su tafi,sallam yayi da yayar shi da matan yayan sa kana suka fice sai da sukayi musu rakiya har mota kana suka dawo.

Suna kama hanya ta kalle Daddy sai da taÉ—an kwanta saman kirjin sa kana tace,”Daddy dan Allah ina so naje gida Æ™awata Nafisa na gaida ta please Daddy love”…Tana Mai nar kema masa ajiki.

Sai da ya shafe fuskar ta kana yace, ba jimawa zakiyi ba ko? kinga dare yayi”.

Tace,”dana shiga zan fito suna uguwar yace ta gaya masa.

Tana gaya masa ya faÉ—ama diriver.

Basu tsaya ko inaba sai wani bakin ƙofar gida Malamin su na islamiya.

#Vote
#Shere
#Comment

Sumy ce
1/23/20, 11:48 AM – +234 706 211 8047: 💦💦💦💦💦💦💦
💦💦💦💦
💦💦

ƘAWAR ƳATA CE
1441H/2019M.

®�
GASKIYA WRITERS ASSOCIATION✍�
{Gaskiya É—aya ce daga Æ™inta sai É“ata burin mu faÉ—akar da al’umma domin ribantar duniya da lahira}

 ```🎐G•W•A🎐```

GASKIYA DOKIN ƘARFE�

Story & Written
By
SUMY M NA’IGE🌸

Didicated to
My Nusaiba😘

Congratulations Ummu Nabil ina tayaki murnar kammala novel É—inki me suna,SANAU’L HUSNA,abunda kika faÉ—a dai-dai Allah ya baki lada kuskure Allah yaya femiki kuma sabon novel É—in da kika fara Allah kasa kin fara asa’a.

~VOTE & FOLLOW 4 [email protected].~

      *Page* *37*

_📖 Cikin gidan ta Æ™arasa cikin sa’a tasamu malam yana gida.

Sai da suka gaisa da matar shi kana ta Æ™arasu wajan da yake ta gaishe shi amsawa yayi tare da sakin fuska kana ya tambaye ta gidan ? tace, “lafiya Æ™alau”.

Shuru ya biyu baya sai daga bi sani yake tambayar ta taga canji kowa?sai da ta numfasa kana tace,

“Alhmdullah”agugoje tayi masa bayanin komai ta Æ™ara da cewa “shima ya kowa ni”.

Sosai malam yaji daɗi dan haka ya ƙara bata wani magani karya kana ya ɗura mata da cewa ta tsare karatun suratul baƙara a koda yaushe koda aya biyar ne a rana.

Tace, “insha’Allahu zata kiyaye” godiya tayi masa sosai kana tayi masa alhairi mai yawa shida matar sa.

Suma godaya sukayi mata kana tayi musu sallama tafice war ta.

Da sauri ta ƙarasa wajan da sukayi packing ɗin motar su buɗe wa tayi ta shiga.

Kallon sa tayi tari da sakar masa murmushi mai Æ™ara mata kyau tace,”My Daddy da fatar ban jimaba ko?”.

Kallon ta yayi tare da maidar mata da marta nin murmushin datayi masa kana yace,”a’a Fatyna saura Æ™an dai”.

Driver yaje mota suka tafi.

Suna cikin tafi ta kalle Daddy tace,”Daddy yanzu ina zamuje?”.

Kallon ta yayi kana yace, “gida zamu koma kiyi hakuri gobe sai muje gidan Umma mu gaishe ta”.

Kallon sa tayi da Æ´ar shagwaÉ“a kana tace,”kamun alÆ™awari ko?”.

Yace, “insha’Allahu indai nada wo aiki sai mutafi”.

Ciki da murna tace, “Allah ya kaimu”haka suka cigaba da fira har suka Æ™arasu gida .

Koda suka ƙarasa paulour ba kowa dan haka kai tsaye part ɗinta ta ƙarasa.

Tana shiga ta rage kayan jikin ta toilet ta karasa tayi wanka ta fito ta shafe jikin ta da turarukka masu Æ™amshi kana ta shafa man habba aÆ™irjin ta tasaka kayan bacci tayi addu’a ta kwanta barci.

Bata jima da kawan ciya ba Daddy ya shigo cikin shirin sa na kwanciya.

Glove É—in da ta kashe ya kunne Æ™arasuwa yayi saman gadon ya kwanta tare da kashe glove kana jawu ta jikin sa yana faÉ—in, “ba dai kinyi bacci ba”.

Komai bata ce masa ba tashi tayi ta ɗauko man habba ta zaba hannuta ta zo wajan sa ta fara shafa masa aƙirji.

To daga shafa man wasa ta sauya Dan Daddy ya Nuna mata yayi missing ďinta over.

Dan haka ba ƙaramar wuya ta sha ba awajan Daddy dan da ƙyar ta samu ya ƙyaleta amma ba dan ya gaji ba.

Tashi tayi tayi wanka dan bata sun kwana da janaba ajiki dan yana ba sheÉ—an damar shiga jikin ka domin ya cutar da kai.

Shiya sa ake sun mutum ko bai samu yayi wanka ba to yayi alwala idan yana tare da janaba kafin ya kwan ta barci.

Tana cikin wanka Daddy ya zo sukayi wanka tare.

Bayan sun kammala suka yi shirin bacci suka kwan ta.

Basu jima da kwanciya ba barci ma daÉ—i yayi awun gaba da su.

Ƙiran sallah farin ne ya tashe su da ita har Daddy.

Alwala sukay kana suka zo suka tada sallah na fila can daga baya Daddy ya tashi domin zuwa masallace.

Yana fita part É—in Momy yaje ya tashe ta kana ya wuce masallaci.

Tana gama sallah bayan ta gama azkar tayi kartun Æ™ur’ani tashi tayi taje kitchen agurgoje ta haÉ—a mishi breakfast tana kammala wa ta dawo part É—inta tayi wanka ta É—an-É—asa kwaliya ta sauÆ™o Æ™asa ta É—au breakfast ta je part É—insa ta zauna tana jiran dawo war sa.

Bata jima da zama ba Daddy ya dawo, dan yau so yake yafi ta da wuri dan yana da metting a office.

Kai tsaye part É—insa yaje domin yayi wanka.

Ƴana shiga yafar jin kamshin turare me daɗin shaƙa,zaune yagan ta riki da littafin husunil musulin tana karan tawa.

Sai da yayi sallam ta san ya shigo.

Kanta ta dako tari da sakar masa murmushi me Æ™ara mata kyau kana ta zo gare shi ahankali take tako har ta Æ™arasu jikin sa ta faÉ—a kana tace,”My Daddy nah antashi lafiya?”.

Sai da ya sauke ajiyar zuciya kana yaÆ™ara matse ta ajikin sa sannan yace,”lafiya Æ™alau,kema in fatar haka”.

Kanta ta girgi za masa alamun “eh”.

Ruwan waka yace ta haɗa masa saboda sauri yake dan metting ne da shi ƙarfi ta 8:.

Bari jikin sa tayi taje toilet ta haÉ—a masa ruwan wanka kana tafito.

Har zai shiga yace, “dear nah ba zaki tai makamin nayi wankan ba?”.

Kallon sa tayi a É—an marai ce kana tace, “a’a Daddy sauri kakiyi kaje kayi niko nafitar da kayan sa warka.

Ba musu yace, “to” tare da shiga toilet dan ya fara wanka.

Koda yafito tagama fitar masa da kayan sawar sa.

Taima kamasa tayi ya shirya ya fito domin yin breakfast .

sai da ta cika masa cikin sa kana itama yaci kama ta nata kana ya tashi domin ya tafi .

Jikarsa ta ɗauka domin ta rakashi,koda suka ƙarasa paulour lokacin ita ko Momy zata fito domin taje part ɗin sa.

Kallan- kallon saka farayi tsakanin su duk mugun kallon da Momy ke aikama Fatima yau bai sa taji tsoron ta a zuciyar taba dan haka tayi kamar bata san tanayi ba.

Sai da Momy ta gaishe da Daddy kana itama Fatima ta gaishe ta.

A ya tsane ta karÉ“a gaisuwar kana Momy taÆ™ara da cewa, “ba dai har zaka fitaba?”.

Yace, “yanzu zan fita saboda metting garemu yanzu”

yana mai takawa dan ya fita saida sukayi mishi rakiya har sai da motar shi ta É—aga suka dawo ciki.

Duk kallon da Momy kema Fatima baisa yau taji tsoron ta ba dan haka kai tsaye part É—inta ta koma ta kwanta da bacci ba wani isar ta yayi ba.

Momy ko tana ganin yara duk sun tafi school bata tsaya koma ba ta yafa mayafin ta ta fita domin zuwa wanjan bokan su.

Dan ko gayama Maram bata yi tafiba,dan sauri take taje ta dawo.

Direba ta kira ta gaya mishi ida zai kai ta mota ya ja yakan ta gidan Hajiya Shafa.

Suna zowa ita ma Hajiya Shafa ta gama shirin ta dan haka taje mota suka tafi.

Koda suka je suka faÉ—a masa aikin ya karya shi kansa yayi mamaki sosai dan haka yace, “kada su damu komai zai dawo dai-dai dan wannan aikin mai tsaneni za’ayi”.

Godiya sukay mishi kana suka zuba mishi kuÉ—i masu tarin yawa,sukafice tare da zomar cewa su zuba idao suga me zai faro.

Tana cikin barci taje anta sallama dan haka ta tashi ta zo tagani wake sallama.

bakin part É—inta suke,aikuwa tana ganin su ta sakar musu murmushi tari da faÉ—i,”Aunty Maryam da Aunty Amina kone tafe?”.

Wato kishiyar Hajiya Shafa da Hajiya Binta.

Tace, “sannuku da zowa ku Æ™arasu ciki dan Allah”.

Ƙarasuwa sukayi suka zauna kana taje ta kawo musu kayan motsa baki ita ma ta zauna tace,ashe zaku zo?”.

Sai Maryam tace, “to mu irinki muke da bata sun shiga cikin mutane”.

Murmushi Fatima tayi kana tace,”wllahi Aunty ba haka ba kawai yanzu bana jin daÉ—in jiki nane?”.

Sai Amina tace, “aike Fatima kin more kina samu yana kulaki tunda gashi har rabu ya kuka,amma gamu muda babu duk É—aya dan nibada Hajiya Sa’a ba da tafiya ta zanyi wannan wahala har ina kai ne kome gaka ka koma kamar Æ´ar aikin gida”.

Sai da suka gama nasu kana Fatima tabasu labarin inda ta fito kuma tace suje wajan malamin isilamiyar su da ikon Allah zai basu taimako ko meye zai kwanci.

Godiya sukayi mata sosai kana ta basu number wayar sa.

Sai da suka yi fira sosai kana sukayi mata sallama akan sai sunyi waya.

Har suka fito Momy bata dawo ba.

Maryam ta dube Fatima tace,”Hajiyar ki da tawa yau fah tun safe suka fita gashi har yanzu basu dawo ba”.

Fatima tace,”ni bamma san bata gidan ba”.

Sai Amina tace,”Maryam zo muje firan ba zata Æ™araba gwara muje wurin malamin kafin wani lokaci mu koma gida”.

Sallama sukayi ma Fatima suka fice.

Ita ko bata koma É—aki ba kai tsaye kitchen ta wuce.

Bata jima da shaga kitchen ba taji hayani ya dan haka tasan da Æ´an boko sun dawo suda Momy.

Sai da ta kammala aikin ta ta fito.

Tana fitowa part É—in Daddy takama hanyar zuwa dan ta gyara shi, yi tayi kamar bata ga kowa a paulour ba.

Tafiya take bata masan da damai zuwa ba jitayi sunyi kara da wani abu kuma kafin ta ankara an wanke ta da kykyawan mare.

A razane ta É—ako kai ta kalle waya mare ta.

Nabila tagani dan haka itama cikin zafin nama ta wanke ta da mari har biyu tana huci kamar kumur cin macije.

Nabila ita ma hannu ta ɗauka dan ta ƙara kai ma Fatima mari amma sai Fatima ta riƙi hannu ta kana ta fara faɗin,

Haba Nabila da hankalinki da tunanin ki zaki É—au hannu ki ki mare matar ubanki?”tare da sakir mata wani murmushi me biÆ™ita Æ™waÆ™waliwa.

Aikuwa tana cewa haka ba Nabila ba har Momy da ke wuri zaune tana kallon su sai da ta miÆ™e tsaye har su Maram da Zainab Kalaon-kallon suka farayi tsakanin su….

#Vote
*Comment
Shere

Sumy M Na’ige ce✍ğŸ?
1/23/20, 11:48 AM – +234 706 211 8047: 💦💦💦💦💦💦💦
💦💦💦💦
💦💦

KAWAR ƳATA CE
1441H/2019M.

®�
GASKIYA WRITERS ASSOCIATION✍�
{Gaskiya É—aya ce daga Æ™inta sai É“ata burin mu faÉ—akar da al’umma domin ribantar duniya da lahira}

 ```🎐G•W•A🎐```

GASKIYA DOKIN ƘARFE�

Story & Written
By
SUMY M NA’IGE✍ğŸ?

Didicated to..
Gaskiya writers

~VOTE & FOLLOW 4 [email protected].~

*Page* *38*

_📖 Ƙarasuwa sukayi har suka kawo wajan da suke.

Momy ce tayi magana ciki da É—aga murya.

Tace, “sannu matar uban su bari yanzu nasa ta mare ki sai naga uban da zai rama miki kuma wallah ki-kiya yeni kinji ko”.

Kallon Maram Momy tayi tace, “rama ma Æ´ar uwarki marin da tayi mata naga meza tayi”.

Cikin hanzari Maram ta É—au hannu zata kai ma Fatima mari taji an daka mata tsawa mai ban firgi ta.

Da sauri ta sauke hannun ta, dukan su suka juyu domin suga kowa ye.

Kallon-kallon suka farayi tsaka nin su,dan ba suyi zaton ganin shi a wannan lokaci ba.

Shi kuma tunda suka gama metting Hajiya kulu tazo wajan sa tana masa magiyar yazo su tafi gidan ta dan wallahi tana da buƙata da shi tayi-tayin masa magiya amma ko kallo bata ishe sa ba.

Dama yaga zata dame shi ya haÉ—a kayan sa ya dawo gida duk da bai gama aki ba haka ya dawo gida.

Ita ko tana ganin ya rufe office ta É—auka tafiya za suyi sai da taga ya shiga motar shi driver yaje kana ta cije yatsa ta fara faÉ—i, “dole gobe na kuma wajan malam dan wallahi ba zan iya barin ka ba wan’nan karon dole sai ka aureni” tare da yin kwafa ta kama hanyar gidan ta ciki da baÆ™in cike.

Tunda Nabila ta mare Fatima dai-dai lokacin ya ƙaraso paulour yana tsaye kumai ya faru ya ɗauka Momy zatayi magana amma yaga ita ce ki sa suyi ran shi inyayi dubu to yau ya ɓaci.

Yaci ka yayi fam ahankali ya fara ta kowa domin ya ƙaraso gare su.

Duk kan su son tsora ta daga nin yanda fuskar sa ta sauya lokaci É—aya,ko Momy sai da Æ´an cikin ta suka kaÉ—a saboda yanda taga ya sauya lokaci É—aya.

Nabila guduwa taso yi tsawar da ya daga mata yasa jikin ta ya fara kar-karwa lokaci É—aya.

Yana Æ™arasowa wajan da suke ya wanke ta da mari har sau biyu kana ya dubi Maram zuciyar shi na huci yace,”minti 30 nabaki ke haÉ—a kayan ki driver ya mai daki gida,kuma kisani zamu huÉ—e nida ki”tare da yin Æ™wf ya kama hanyar É—akin sa.

Har ya tafi ya dawo yaje hannu Fatima ya ƙarasa da ita part ɗinsa,ya bar su tsaye suna kallon ikon Allah.

Itako Nabila na kuka.

Wani baƙin ciki ne ya rufe Momy wanda ta kasa cewa komai.

Har ya kai part É—insa ya dawo inda ya bar su anan yasa me su duban sa ya kai ga Momy kana yace,”nan da minti ashirin ina sun nagan ku a Babban paulour dan magana zamuyi”.

Yana kai karshe ya koma ciki batari da ya tsaya jin me Momy zata ce ba.

Wurin da ya barta tsaye anan ya dawo ya same ta.

Ahankali yake tafi har ya kawo wajan da take,jitayi ya rungume ta ta baya sosai ya matse ta jikin sa kana ya juyar da ita ta gaban sa.

Idon sa ya kefe akan lipss ɗinta ahankali ya fara ɗukar da fuskar sa,idon ta tare rufe sai ji tayi lips ɗinsa akan nata kissing ďinta ya shigayi sosai, kodan yarege jin raɗaɗin da zuciyar sa ke masa.

Tsayuwarce ta gagare su dan haka ciƙ ya ɗauke ta ya ƙarasa bedroom ɗin shi da ita.

Kayan jikin ta ya fara ƙoƙari rage mata tayi sauri ta cire bakin ta cikin nashi kana ta fara magana can ƙasan maƙoshi tace,

“Daddy dan Allah kayi hakuri har ajima wallahi aiki…bai bari ta Æ™arasa ba ya haÉ—e bakin ta da nashi.

Sai da ya cire mata kayan jikin ta ya fara wasa da ita sosai musan-man boobs ɗinta da suke mutuƙar ɗaukar hankali sa.

Sai da yayi wasa da ita son ranshi kana ya fara aikin a kan ta sosai ya bata wuya dan har sai da takai ga saka masa kuka ya ƙyeta.

Dan shi idan ran she ya ɓaci in bai kasan ce da mace ba komai zai iyayi dan shi kafin ya yan ke hukunci ya rage zafi da Faty shi rabin ranshi.

Jikin sa ya matseta sosai kana ya fara bata hakuri sai da yaga ta hakura kana ya tashi yaje toilet da kansa ya haÉ—a musu ruwan wanka kana ya zo ya É—auke ta yaje suka yi wanka a tare sai da suka shirya suka fito paulour lokacin duk su Momy sun fito zaman jira fitowar su.

Sai da ta kawo masa abinci yaci, kana ya zo ya zauna kusa da su.

Sai da yayi gyaran murya kana yace,”yanzu Hadiza keda nake gani mai hankali ashe ba haka kike ba,ace wai kece ke tura yaran ki su mari mata-ta kuma kina amatsayi na mahaifiya mai bada tarbiya wallahi ko da ace wani ya gaya min haka da ba zan yarda ba wai kisa yara su mare matar da nake aure,wai kuma tarbiya ce kike koyar da su amma laifi nane dana Æ™yale Æ™i na zuba miki ido dan atunani na ki mai kular min abinda na wo ce to.. ashe ba haka ba amma wallahi da kunya ace kana kishi da Æ´ar cikn ka”.

Sai da yayi musu tas kana ya numfasa tare da duban su yace,”kuma daga yau waÉ—an nan yaran ya nuna Zainab da Nabila yace, “naba ko wata biyu kuka wumin mijin da zaku aura kuma inba ku kawo ba ni da kaina zan baku wanda nake su na aure muku dan haka ku tashi kubani waja kuma ga Fatima nan idan nafita na dawo natarar da gawar ta agidan nan”.

Kallon sa ya maida ga Maram yace, “ke kuma ki tashi ki koma gidan ki in kin gama dukan mata-ta ga driver can najiran ki.

Har ta buÉ—e baki dan tayi masa magana ya É—aka mata hannu tare da nuna mata ta tashi.

Momy ko ita har zata yi masa magana ya tashi ya bar wajan tare da ce ma Fatima taje ta shirya zasu tafi”.

#Vote
Comment
Shere

Sumy M Nai’ge🌸
1/23/20, 11:48 AM – +234 706 211 8047: 💦💦💦💦💦💦💦
💦💦💦💦
💦💦

ƘAWAR ƳATA CE
1441H/2019M.

®�
GASKIYA WRITERS ASSOCIATION✍�
{Gaskiya É—aya ce daga Æ™inta sai É“ata burin mu faÉ—akar da al’umma domin ribantar duniya da lahira}

 ```🎐G•W•A🎐```

GASKIYA DOKIN ƘARFE�

Story & Written
By
Sumy M Na’ige

Dedicated to
MRS BASAKKWACE🥰🥰

Congratulations Maman Muhammd, ina tayaki murnar kammala book É—inki JUYIN RAYUWA Allah ya baki ladar fadakar wa kuskure Allah yayefe ameen.

~VOTE & FOLLOW 4 [email protected].~

     *Page* *40*

_📖 Yau ma kamar kullum tana idar da sallah asuba Bayan ta gama azkar ɗin da ta saba, tashi tayi taje kitchen dumin ta haɗa musu breakfast duk da yanzu akwai masu aiki amma ita tafi su ta haɗa mishi breakfast da kan ta.

Da yake yau weekend ne Daddy bada wuri zai fita ba dan haka ta tsaya ta b’ata lokaci wanjen haďa masa breakfast.

Duk da yau ba itace da duty ba amma ta tsaya ta bata lokaci sosai wajen haÉ—a masa abun karyawa.

Tare da Æ´an mutuna ta gama,komai sai da ta kai dinning kana ta bar ma Æ´an aiki saura tafice zuwa part É—inta dumin tayi wanka duk da yau bata jin wani daÉ—in jikin ta dauriya ce kawai take har ta samu tayi wannan aikin.

Toilet taje domin tayi wanka sai da ta haÉ—a ruwan wanka kana ta É—auko turarin ta na wanka mai masifar Æ™amshi tare da wata powder mai fitana nin Æ™amshi ta zuba aruwan aikuwa suna haÉ—uwa waje É—aya wani k’amshi ne ya tashi mai san yaya zuciyar duk wanda ya shaÆ™e sa.

Wanka ta tsaya tayi kana tafito daga cikin toilet É—in.

Shiko Daddy yana tashi yayi wanka ya fito parlour.

Koda ya tashi Momy ta koma part É—in ta dumin tayi wanka ta shirya.

Paulour ba kowa dan haka ya haura sama dumin ya gani ko teemar sa ta tashi.

Shigowar sa paulour n ta yayi dai-dai da fitowar ta daga toilet.

Wani ƙamshi ne ya dake ancin sa,aikuwa bai sai lokacin da ya sauke wata sa sanyar jiyar zuciya tare da kai zaune cikin ɗaya daga cikin gujerun paulour.

Ga ban merrow ta zauna ta fara shefe jikin ta da mayuka masu ƙamshi haɗe da humra masu daɗin shaƙa.

Ta jima tana kwalliya kana ta tashi domin ta saka kayan ta.

Gown ɗin shadda tasa ash color ɗinki ya karɓe ta sosai saida ta kashe daure kana ta feshe jikin ta da turare ta ɗauko ta kalme masu tudu tasa kana tafito dumin ta sauka ƙasa.

Shiko tunda ya zauna ya kasa tashi har ta gama shiri.

Kamshi turaren ne ya dake hancin sa dan haka ya tashi dumin ya ƙarasa cikin bedroom ɗin ta.

Itako zata fito karo da juna sukayi ido ta ɗago suka kalle juna,wani ƙaya taccin murmushi ta sakar masa wanda ke ƙara mata kyau.

Ido ya kefata dasu ya kasa koda mutsa ƙafar shi saboda tunda ya sheƙi wannan turarin jinki sa yayi sanyi sosai dan haka bai san lokacin da ya jawo ta jikin sa ba.

Ahankali ya ke sauke nun fashi kana ya sunkuyar da kansa wajan wuyan ta ya fara shaÆ™ar Æ™amshin jikin ta ahakali ta buÉ—e bakin ta cikin kasalaliyar murya tace, “Daddy ina kwana?”.

Bai samu damar karɓa bata ba, idon sa ya dago ya kalle ta ba shiri ya haɗe bakin sa da nata yafara kissing ɗin ta sosai tare da shaƙar ƙamshin jikin ta.

Bakin gado ya Æ™arasa da ita wasa ya shigayi da ita sosai Æ™uÆ™arin cire mata kaya kijin ta ya fara,ba shiri ta cire bakin ta ana sa ta tashi zaune cikin yane yi kamar zatayi kuka tace, “Daddy kamanta ne yau bani ce da duty ba”.

Kamar ba zaiyi magana ba, saboda ga baki É—aya jikin sa yayi sanyi sosai ya ma kasa magan.

Sai da ya dai-dai ta na tsowar sa kana ya É—ago kai ya kalle ta yace,”ina sane kuma ke É—in ce dai ke sani shiga wani hali”yayi maganar tare da tashi ya shiga toile.

Kallon sa tayi tace, “Daddy ni me nayi?”.

Bai bata amsa ba kuma da ya fito bai tsaya komai ba yace ta zo suyi breakfast.

Kallon sa tayi tace, “gata nan zowa”.

Bai tsaya jiran ta ba ya fice dan yasan da ya tsaya wani abu zai iya shaga tsaka nin su shi ina yana tare da teema gaba ki É—aya baya da na tsowa sai yaji shi ajikin ta.

Sai da ta koma gyara jikin ta kana ta fito.

Koda ta sauko ita kadai suke jira dan har sun zauna saman dinning.

Kamar bata son tafiya haka take ta fiya har ta ƙarasu ga resu Momy ko inban da aka mata harara ba abunda takeyi.

Shi ko Daddy tunda ta fito ya kefi ta da ido kamar bai taɓa ganin ta ba.

ÆŠayan kujer ta je ta zauna kana ta dube Momy ta gaishe ta.

Sai da Momy ta watsama ta harara kana ta amsa da “lafiya Æ™alau”.

Bawan da ya sake magana da Nabila da Zainab duk suna wajan amma sun kasa gashe ta bare su Ummi, Kulsum ce ta buÉ—e baki tace,

“Aunty Fatima “ina kwana?”.

Sai da Fatima tayi murmushi kana tace,”Kulsum kin tashi lafiya?”.

Tace, “lafiya Æ™alau Aunty”.

Daddy har zai fara break ya kai duban sa ga su Nabila,sai da ya haÉ—e fuska kana yace, “kuba baku iya gaisuwa ba ne?”.

Kasa da kansu suka yi aÉ—an tsawa ce yace, “baza ku gaishe ta ba ne, Kulsum ta fiku ahankali gashi ita ce Æ™ara ma”.

Zainab ta buÉ—e baki tace, “Daddy kayi hakuri baza mu sake ba.kana ta kai du ban ta ga Fatima tace,”Aunty Fatima ina kwana?”.

Sai da ta É—ago kai ta kalle ta kana tace, “lafiya Æ™alau Zeey”.

Nabila ko ciki-ciki haÉ—e da ya tsane fuska kana tace, “ina kwana?”.

Amsa mata Fatima tayi haÉ—e da sakin fuska kana suka cigaba da break É—in su.

Gaba ki É—aya baka jin mutsin komai sa na cokali.

Bata wani ci da yawa ba taji zuciyar ta ta fara tashi har ta so ta daina ci amma kuma ta ciga ba da cusawa aikuwa ta na kai spoon ɗin bakin ta ta fara kakarin amai da sauri ta tashi dumin ta ƙarasa waja amma saboda ya zo mata bata san lokaci da ta durkusa ba ta fara fesu shi kamar zata amaye ƴan cikin ta.

Da sauri Daddy ya taso ya ƙara so gare ta bai damu da aman da take fesawa ba da sauri ya jawo ta jikinsa Ga baki daya aman ya wanke masa jikin sa.

Bai ma damu da aman da ya ɓata masa jiki ba ya taso da ita daga durƙushen da take ya na fadin,

“Fatima dama baki da lafiya ne?” Ita bata masan ya na yi ba Because duk ta fita hayyacin ta Jikin ta ga baki daya duk ya saki.

Shi kuwa gaba ki daya hankalin shi ya tashi ya rasa ya zaiyi da ita
Ita kuwa mummy tana gefe tana kallon shi ta kai cin shi ya kamata sosai ji take kamar ta naÉ—a mishi É—an banzan duka.

Gashi Shi kuma ya rasa yanda zaiyi da ita duk Tausayin ta ya kamashi ji yake kamar yayi kuka.

Zainab ce da taga mom ba ta da alamar tashi dan haka cikin hanzari ta miƙe ta ƙarasa gare su tana faɗin,

” Daddy muje akaita hospital” dan a lokacin ita ba ta masan ida kan ta ya keba Daddy shi gaba d’aya ma ya manta da wani zancen Asibiti saboda tsabagen ruÉ—ewa.

Da sauri cikin hanzari ya ƙarasa part din shi rigar da ke jikin shi kawai ya canja ya fito falo.

Ko da ya ƙaraso falo zainab ta taima ka mata ta kaita toilet Tare da taimakon Ladidi yar aiki suka gyara mata Jikin ta .

Suna fitowa daga toilet da sauri ya ƙarasu garesu cak ya dauketa bai tsaya da ita ko ina ba sai harabar gidan tare da kwallawa direba kira

Cikin hanzari gudu-gudu ya Æ™araso yana fad’in Alhaji ranka yadade gan…… Baima Æ™arasa maganar ba saboda halin da ya ganshi ciki da hanzari yaje ya tada mota Suka nufi hospital

Ita kuwa mummy mutuwar zaune tayi saboda ganin yanda Daddy ya dauki Fatima agabanta kuma duk ya wani bi ya ruÉ—e Kamar bai taÉ“a ganin ana amai ba Sai da tayi Æ™waf tace, “hmmmm tama mutu ni ina ruwana”.

Sai Nabila Tacce, “Nifa mummy gani nake fa kamar Zanci Anty Maram gaskiya ne yarinyar nan ciki ne da ita” .

Tana faÉ—in haka Sai da Gaban mummy ya faÉ—i yayi wani duuuuuuuuummm Sai tace, “koni kamar haka na ke gani Amma wallahi tayi kaÉ—an ta haifeshi agidan nan ko da kuwa cikin ne bare ma bashi ba ne”.

Sai da ta numfasa tace, “Ƙo miye gama Æ™aryar iskancin ta take yi wlh kwanan nan sai ta bar gidan nan ko da mi take taÆ™ama da shi”.

Ita kuma Nabila ta ce, “wallali kuwa Mummy dan ni na tsani ganin ta agidan nan”.

Mummy komi ba ta ƙara cewa ba tashi kawai tayi ta wuce part dinta

Ita kuma zainab tunda suke wannan maganar ko mi bata ce musu ba kallon su kawai takeyi dan ita duk tausayin Teema ya cika mata zuciya.

Suna ƙarasawa Hospital Emergency room Suka karɓeta Likitoci suka Fara bata taimakon gaggawa

Tunda aka shiga da ita Daddy sai safa da marwa yake yi zufa sai tsayaye yake masa ajiki.

Yana cikin haka likita ya fito da sauri Daddy ya ƙarasa gare shi yana tambayar sa jikin ta.

Sai da likita ya dube shi da kyau kana yayi masa maga cikin kwantar da murya yace, “ya biyu shi office…

#vote
Comment
Shere

Sumy M Na’ige🌸
1/23/20, 11:48 AM – +234 706 211 8047: 💦💦💦💦💦💦💦
💦💦💦💦
💦💦

ƘAWAR ƳATA CE
1441H/2019M.

®�
GASKIYA WRITERS ASSOCIATION✍�
{Gaskiya É—aya ce daga Æ™inta sai É“ata burin mu faÉ—akar da al’umma domin ribantar duniya da lahira}

 ```🎐G•W•A🎐```

GASKIYA DOKIN ƘARFE�

Story & Written
By
SUMY M NA’IGE✍ğŸ?

Didicated to... My Family 🥰

~VOTE & FOLLOW 4 [email protected].~

Page 41

_📖

Koda suka isa office kujerar zama doctor ya nuna masa,sai da ya zauna kana ya fara yi masa baya nin abun da ke damun ta.

Doctor yace, “yanzu komai ya dawo dai-dai sai dai aÆ™ara kula da ita sosai dan bata yawan cin abinci ko abu mai gina mata jiki dan haka a kula sosai”.

Sai da Daddy ya numfasa kana yace, “insha’Allahu doctor zan Æ™ara kula sosai ya Æ™ara da cewa yanzu ya jikin nata?”.

Dactor yace, “yanzu jikin ta ya dawo dai-dai nan da awa É—aya zata farka insha’Allah kuma idan na Æ™ara dubata naga ba wata matsala sai na salame ta”.

Godiya sosai Daddy yayi masa kana doctor yayi masa jagora har É—akin da aka kai ta.

Suna shiga ɗakin da sauri Daddy ya ƙarasa gareta.

Kwance take saman gadu da ƙarin ruwa ahannun ta.

Ahankali Daddy ya ƙarasu ga ban gadon da take kwan ce ya zauna yana kallon ta lokaci ɗaya har tayi rama.

Daddy ya nan zaune har awa É—aya ta ciki ,cikin ikon Allah sai gashi ta buÉ—e idon ta,da sauri Daddy yazo ga reta yana faÉ—in, “ya jikin”.

Komai bata ce masa ba,dan haka da sauri yaje yakira Doctor.

Tare suka shigo Dactor ya cire mata ƙarin ruwan kana ya fara duba ta.

Sai da ya duba ta sosai sa’anan ya ruÉ“uta mata magani kana ya rubuta musu ta kardar sallama.

Sai da Daddy yasai magani kana suka shaga mota driver yaja suka wuci gida.

Sunayi parking Daddy da hannuta ya riƙo saboda jirin da bai gama sakin ta ba.

Ahankali suke tafiya har suka ƙarasu paulour dai-dai lokacin da Zainab ta fito a ɗakin su.

Da sauri ta Æ™arasu garesu tana faÉ—in,”Daddy ya jikin ta?”.

Yace, “da sauki Zainab”yana mai Æ™arasawa da ita part É—in ta.

Zainab taje ta gayawa Momy sun dawo.

Sai da tayi mata wani kallo kana tace, “to meya dameni aciki da dawo warsu da rashin da wowar su da zaki zo ki gaya min eh?”.

Tace, “Mumy kiyi hak’ur idan nayi laifi” tana mai ficewa daga É—akin.

Sai da Zainab tajima da fita Momy tashi tayi ta fito bata tsaya ko ina ba sai part É—in Fatima.

Koda ta shiga bata same su paulour ba dan haka kai tsaye ta wuce bedroom É—in ta.

Sai da ta shiga tayi sallam gaban ta ne ya faÉ—i irin yadda taga Daddy rungume da Fatima lokaci É—aya fuskar ta ta sauya amma sai ta wayin ce tayi kamar abun bai dame ta ba.

Bayan Daddy ya amsa sallama ta ƙarasa gabansu tana faɗin,

“Ashe kun dawo gashi har na shirya nasa drivir ya kaini sai Zainab ke cemin kun dawo”..tana magana tana ya mutsar fuska kamar da gaske.

Daddy yace, “koda ma aman ne ya wahal da ita amma yanzu da sauki”.

Tace, “masha’Allah,Allah ya Æ™ara sauÆ™i,taÆ™ara da cewa to Daddy su zainab meke damun ta?”.

Yace, “ba komai bane sai matsalar ciki ce”.

Ganban momy ne yayi mum-munar faÉ—uwa amma ta dage tace,

Tace, “kamar ya?ko ciki ne da ita?” ta faÉ—i haka muryar ta na rawa amma sai ka natsu za ka gane haka.

Cikin rashin damuwa Daddy yace, “ciki ne da ita har na tsawon wata uku”.

Gaban mumy ne yayi dummmmm amma da yake Æ´ar duniya ce tace, “amma shine baka gaya mun nasamu Æ™aruwa ba sai yanzu ” tafaÉ—a aÉ—an shagwaÉ“an ce.

Hakuri Daddy ya bata da ƙyar ta hakura kana tace, bari taje ta haɗa ma Fatima koda tea ne ta sha.

Godiya Daddy yayi mata kana ta fice.

Da ƙyar ta ƙarasa part ɗin ta dan gabaki ɗaya tafiya gagarar ta tayi.

Tana isa ciki da ta shin hankali ta É—au waya takira É—iyar ta Maram ta faÉ—a mata abunda ke faruwa.

Sai da tagama faÉ—a mata kana tace, “amma yanzu zan haÉ—a mata tea sai na zuba wani magani wanda ko cikin ya zube baza a gane meyesa cikin zubewa ba.

Maram tace, “haka yayi Momy kiyi sauri kiyi”.

Suna yin sallama bata tsaya ko ina ba sai kitchen,ruwan tea ta haÉ—a da madara kana ta É—auko wani magani ta zuba a ciki sai da ta juya shi sosai ya haÉ—e da madara kana ta É—auko ta kawo musu.

Sallama tayi kana ta shigo ko yanzu yadda ta barsu haka ta same su.

Ƙarasuwa tayi gaban su tace, “gashi ta tashi tasha sai ta sha magani zata ji daÉ—in jikin ta.

KarÉ“a Daddy yayi tare da yima Mumy godiya yace, “Fatima tashi ki sha”.

Ba musu ta tashi dan koda ma yunwa take ji kofin yami Æ™a mata ta Æ™arÉ“a yace, “ta sha”.

Kofin ta É—auka zata kai bakin ta tare da faÉ—in bismillah….

#Vote
Cmment
Shere

Sumy M Na’ige🌸
1/23/20, 11:48 AM – +234 706 211 8047: 💦💦💦💦💦💦💦
💦💦💦💦
💦💦

ƘAWAR ƳATA CE
1441H/2019M.

®�
GASKIYA WRITERS ASSOCIATION✍�
{Gaskiya É—aya ce daga Æ™inta sai É“ata burin mu faÉ—akar da al’umma domin ribantar duniya da lahira}

 ```🎐G•W•A🎐```

GASKIYA DOKIN ƘARFE�

Story & Written
By
SUMMY M NA’IGE✍ğŸ?

Didicated to..
My Shemah🥰

~VOTE & FOLLOW 4 [email protected].~

Page 42

_📖 Har ta kai bakin ta sai taji ƙarnin madarar ya dake hancin ta aikuwa lokaci ɗaya ta fara kakarin amai.

Amayar da wanda ta kurɓa tayi tare da aje kofin dan jin take zuciyar ta na tashi sosai.

Shi ko Daddy duk rikicewa yayi yana ta faÉ—in,

“Sannu ,meke damunki Fatima?”.

Ita ko Mumy ranta ne ya ɓaci sosai gani tabbas Fatima bata sha tea ɗin da ta kawo mata ba.

Sai da aman ya lafa Daddy ya jawo ta jikin tari da faÉ—i,

“Mekike ji yanzu?”.

Ahankali tace, “komai banji Daddy”.

Momy ko cikin ranta faÉ—a takeyi yariyar nan munafukace fah ji yadda ta wani shige masa ajiki wai ita bata da lafiya wai me ciki.

Ƙaraso wa tayi gaban su kana tace ma Daddy, “tunda aman ya lafa kabata ta sha sai tasha magani kaga zata ji daÉ—in jikin ta”.

Ba musu Daddy ya É—auko kofin tea É—in ya miÆ™ata yace, ” “sha Fatima”.

Kai ta girgiza masa kana tafara magana a hankali tace, “Daddy bana son madara amai zanyi”.

Sai da Momy ta fake idon Daddy ta wanka mata hara-ra kana tace, “to me kike su sai akawa miki?”.

Sai da Daddy ya mai-mai ta mata kana tace,”fura nake su”.

Faɗima Momy yayi abunda tace dan ƙasa-ƙasa tayi maganar dan Mumy bata fahin ta ba sai da Daddy ya faɗa mata.

Momy tace, “to bari na kawo mata” tana faÉ—a tana aikama teema hara-ra.

Tana fita Daddy da kansa ya kai Fatima toilet ya taima ka mata ta gyara jikin ta kana ya fito.

Kuka ta sanya masa tace sai ya kai ta gida.

Da ƙyara ya samu ta haƙura zuwa ajima zai kaita kamar yadda yace.

Mumy ko kitchen ta koma ta É—auko fura ta sake zuba wannan maganin kana tafito domin ta kai mata.

Salamar da akayi ce ya da katar da ita daga saurin da take.

Kallon-kallon suka fara yi ma juna kana Mumy ta Æ™aÆ™alo murmushin karfin hali tace, “yau wa muke agani agida”.

Ita ma Hajiya Sa’a martanin murmushin da tayi mata ta mai da mata.

Gaisawa suka fara yi kana Hajiya Sa’a ta tambaye Mumy yara da kuma Fatima.

Sai da Mumy tayi ajiyar zuciya kana tace, “yara duk suna É—akin su,Fatima ko batada lafiya dan yanzu itace ma zan kai ma fura tashi”.

Hajiya Sa’a tace,”ash-sha meke damun ta?”.

Mumy tace, “lamarin ciki ne”.

Sai da Hajiya Sa’a ta dube Mumy da kyau kana tace, “tana ina yanzu?”.

Sai Mumy tace, “tana É—akin ta”.

Hajiya Sa’a bata sake yiwa Mumy magana ba ta haura sama,Mumy ita ma tana bin bayan ta har suka karasa ciki.

Ko yanzu kwance take shiko Daddy na gefe ta yana jera mata sannu.

Sallama sukayi kana suka shigo .

Aikuwa yana ganin Hajiya Sa’a ya faÉ—a-É—a murmushin sa kana yace,”Babbar Yaya kece agidan?”.

Tace, “nice tunda ku baku neman ba aigwara na zo na-nemeku naji ko lafiya”.

Sai da ya sosa kai kana yace, “Hajiya Babba hak’uri zaki Æ™ara yi damu yanzu ayuka sun muna yawa sasai”.

Tace,hmm “ko bada aiki ba haka kuke Allah dai ya kyau ta.

Fatima ko tana jin muryar Hajiya Sa’a taji wani daÉ—i sosai dan haka tayun Æ™ura ta tashi zaune dumin su gaisa.

Fatima gaida Hajiya Sa’a tayi itama ta amsa ciki da sakin fuska haÉ—e dayi tamata yajikin?”.

“Da sauÆ™i tace mata”.

Mumy ta miÆ™o mata fura tace, “gashi ta sha sai ta sha magani dan yau kome babu acikin ta”.

Hajiya Sa’a ta karÉ“e furar ta buÉ—e sai da tayi mata kallon tsaf kana ta rufe ta aje aÆ™asa batare da tace komai ba kuma bata ba Fatima ba.

.
Bata cema kowa komai ba suka cigaba da firar su game da yadda bikin zai kasan ce na sauran ƙannen ta.

Mumy na tsaye komai bata ce ba da taga alamun ba furar zata bata ba dan haka ta fice zuciyar ta na zafi dan a duniya bata ga abunda ta fi tsana ba irin Hajiya Sa’a,saboda tana mata shi-shige ga lamarin ta.

Sai da sukayi fira sosai kana Hajiya Sa’a tayi musu sallama dan tafiya zatayi.

Aikuwa Fatima nagani tafiya zatayi lokaci É—aya tayi rau-rau da ido ba shiri sai ga hawaye sun fara zuba sai tafara sha-shekar kuka .

Hajiya Sa’a ta juyu ta kalle ta tace, “Fatima lafiya meke damun ki?”.

Ai kamar kada tace haka ta fashe da kuka mai tsuma zuciya.

Kallon-kallon aka fara yi tsaka nin Hajiya Sa’a da Daddy.

Jikin shi amace yace, “wallahi ba abunda na mata Yaya”.

Komai bata ce mishi ba ta ƙarasa wajan Fatima,kan ta taɗago tare da kura mata ido.

Jikin ta aÉ—an sanyaye tace, “Fatima me akayi miki lafiya ki gaya min kinji?”.

Sautin kukan da takeyi ne ta rage kana tace,”ni zanbiki bani da lafiya”.

Sai da Hajiya Sa’a ta sauke ajiyar zuciya kana tace,”to dai na kuka da ke zanje kinji”.

Tace “to na daina tana mai ciki da farin ciki”.

Tashi Hajiya Sa’a tayi ta fara haÉ—a mata kayan ta.

Da sauri Daddy ya Æ™arasu gaban ta yana faÉ—in, “dan Allah Hajiya kada kitafi da ita wallahi komai ban mata ba kiyi haÆ™uri Hajiya.

Kallon sa tayi da kyau kana tace, “ai bance kayi mata wani abuba zan dai je da ita sai taji É—an sauÆ™i”.

Ruk’un ta ya ciga ba dayi ta bar masa matar sa amma tayi kamar bata ji shi ba.

Sai da tagama haɗa mata kayan ta kana ta bata hijab tasaka tari ƙi hannu ta suka tafi.

Haƙuri Daddy yaci gaba da bata amma taki saurarin sa har suka kawo babban paulour.

Mumy suka tarar zaune ita da yaran ta,gashe da Hajiya Sa’a sukayi kana tayi wa Mumy sallama taje hannu Fatima suka wuce.

Aikuwa Mumy naganin da Fatima za’aje wani tashin hankali ya Æ™ara ma-maye zuciyar ta kuma bata da halin maganar kada aje da Fatima dan tasan Hajiya Sa’a wuta ce idan aka taka ta akwai bila’i, kuma idan tayi niyar abu ba mai hanata sai Allah.

Aikuwa Daddy nagani da gaske Hajiya Sa’a keyi ya kama bakin sa yayi shiru dan yasan halin ta sarai,amma zuciyar shi ba daÉ—i.

Akuwa tunda ga wannan lokacin Daddy kulum yana hanyar gidan Hajiya Sa’a kuma ta hanashi ya ga Faty shi yayi magiya har ya gaji har Æ™ara ya kai ta ga Gwaggo amma suna magana da Gwaggo tace abar ta har taÆ™ara jin sauki.

Shi wallahi ya gaji matar sa yake buƙata dan yanzu ƴar nacin can ta dawo masa kuma baya sun yana biye mata kuma gashi sun riƙi masa matar shi.

Koda Mumy nanan amma ya fisun ya haÉ—a biyu bare ma teemar sa ta daban ce agun sa.

Dan haka yaje ya sanar da Hauwa ƙawar Fatima a yanzu.

Bayan kuwa biyu Hauwa Ta shirya taje gidan Hajiya Sa’a bayan sun gaisa take tambayar ta Fatima.

ÆŠakin da Fatima take Hajiya Sa’a ta kai ta.

Sai da Hajiya Sa’a ta fita kana Hauwa ta matso kusa da Fatima bayan sun gaisa Hauwa ta dube Fatima da kyau kana tace,

“Ke yanzu teema kina jin daÉ—in zama haka ba mijinki tari dake?”.

“Wai ma me kika gaya ma Yaya Babba da har zata hana masa ganinki?”

Fatima tace, “ba abunda nace mata kuma dakika ce bana jin daÉ—i zama haka to bari kiji wallah ni nafi jin daÉ—in zama haka dan ba mai ta kuramin shi kuma Daddy ya fiye ta kurama mutum dan shi ban wani da muba”.

Wani kallo Hauwa ta watsa mata kana tace,

“Sai kiyi ta zama wata rana sai akawo miki labarin zai aure Hajiya kulu”.

Gaban tane ya bada dumm! kana tace,

Waye Hajiya kulu kuma?”.

Komai bata ce mata mayafin ta ta yafa zata fice.

RiÆ™e mata maya fi Fatima tayi tace, “haba Aunty Hauwa kin san bama haka dake dan Allah ki gaya min” tana magana kamar zatayi kuka.

Kallon ta Hauwa tayi tace, “ni dai nafaÉ—a miki kiyi yadda nace dan inba haka ba hmmmmmm taÆ™ara da cewa yanzu mijin ki ko gida baya zama ya can…bari nayi shuru amma inkin tashi komawa gidan mijikin to ki kirani a waya” tana faÉ—in haka ta fice war ta batari da ji abunda Fatima zata ce ba.

Jikin Fatima ne yayi sanyi sosai kuma lokaci É—aya taji tana son ganin Daddy ko jinsa dan tunda tazo ko wayar sa bata É—auka ba bare ma taji wani hali yake…..

#Vote
Comment
Shere

Sumy M Na’ige🌸
1/23/20, 11:48 AM – +234 706 211 8047: 💦💦💦💦💦💦💦
💦💦💦💦
💦💦

ƘAWAR ƳATA CE
1441H/2019M.

®�
GASKIYA WRITERS ASSOCIATION✍�
{Gaskiya É—aya ce daga Æ™inta sai É“ata burin mu faÉ—akar da al’umma domin ribantar duniya da lahira}

 ```🎐G•W•A🎐```

GASKIYA DOKIN ƘARFE�

Story & Written
By
SUMMY M NA’IGE✍ğŸ?

Didicated to..
My Hafsa😍

~VOTE & FOLLOW 4 [email protected].~

Page 43

_📖 Jikin ta a sanyaye ta jawo wayar da ke gaban ta ta dan na masa kira tana ringing ba’a ďauka ba, har sai data yi masa kusan miss call biyar amma ba’a É—auka ba.

Gabanta ne ya fara dukan uku-uku saki kira tayi ko nan ba’a É—auka ba.

Ai bata san lokacin da hawaye suka fara tsiyaya a idon ta ba.

Lokaci É—aya ta shiga rera kuka mai tsuma zuciyar mai sauraro.

Shi ko Daddy lokacin da ta kira bai ma san takira ba dan yanzu ba ita ba ko Mumy ta daina ganin shi kuma da Mumy ta tambaye shi sai yace mata aiki ne ke re ƙishi.

Dan yanzu ga baki É—aya ya tare gidan Hajiya Kulu sai yadda tayi dashi.

Ita ko Mumy ta ɗauka da gaske aikin ne ke riƙeshi dan haka bata sake maganar ba,bata san Hajiya Kulu ce ta sashi agaba ba.

Wace ce Hajiya Kulu?

Hajiya Kulu gogagayar Æ´ar duniya ce ta bugawa a jari da,tunda mijin ta yarasu bata sake aure ba sai taci gaba da harkokin ta na bariki, tana da yara biyu Salim, Naja’atu,naja tayi aure har da yara biyu shi ko Salim na Dubai yana karatu.

Ita ko Hajiya Kulu bata da wani aikin da ya wuce shiga cikin Æ´an siyasa da Æ´an kasuwa da manya mutane data ji za’ayi wani taro ko metting to babu abunda ke hana mata zuwa ko dan ta samu wanda ya kwan ta mata arai idan taga namiji ya kwan ta mata to fah duk yadda zatayi sai tasa ya kula ta ko baya so.

Haka tafaru haÉ—uwa su da Daddy wata rana sun yi metting suna fitowa shi kuma yana sauri ya tafi gida dan Mumy ta kirashi tace mishi Kulsum ba lafiya har sun kaita asibiti.

Karu yaji yayi da mutum dan bai masan da mutum ba.

Kansa ya É—ago ya kalle ta, hak’uri ya bata ba tare da ya tsaya ba ya wuce war sa.

Ita ko tunda ta ganshi taji ya kwanta mata arai aikuwa tunda ga lokaci tabi duk wata hanya da zata bi har ta samu ya fara kula ta.

Taso ya aure ta amma yaki amma wannan lokaci kuma tace dole sai ya aure ta kuma da alamu zai amince.

Hankalin Fatima ya tashi sosai,bata tsaya wani abu ba tafito falo zaune ta same Hajiya Sa’a tana kallo dan haka ta Æ™arasu wajan da take, zama tayi tare da gaishe ta.

Bayan sun gama gasaiwa Fatima tana son tayi mata magana kuma tana jin nauyi abunda zata faÉ—a É—in.

kula da haka É—in da Hajiya Sa’a tayi dan haka ta kalle Fatima da kyau kana tace,

“Fatima ko kina buÆ™atar wani abune?”.

Tana son tace eh kuma da kunya ta faÉ—a mata abunda take su.

Mai-mai tama ta Hajiya Sa’a ta koma yi,amma sai tayi Æ™arfin halin cewa “a’a ba komai Hajiya”.

Bata yadda da abunda tace ba dan haka tace,

“Fatima ni aganina ni dake ba wani abin boye-boye in har kin É—auke ni amatsayin Yaya kuma uwa ina son ki gayamin meke da munki?”.

Shuru Fatima tayi sai can ta numfasa kana tace,

“Dama ba komai ba ne Daddy ne naga ya bar zowa gidan nan kwana biyu”…tana faÉ—a tanayin Æ™asa da kanta muryar tana rawa.

Sai da Hajiya Sa’a tana numfasa kana tace, “kada ki damu anjima zan neme shi naji ko lafiya” daga haka bata sake magana ba dan ta kula Fatima tana son ta kuma gidan mijin ta kuma ita bata son ta koma yanzu sai taji sauÆ™i laulayin da take yi.

Ita ko Fatima duk kunya ta bi-biye ta saboda abunda ta faɗa gani take bata yi dai-dai ba da ƙyar ta tashi ta kuma ɗakin ta.

Bayan magarb Hajiya Sa’a takira Daddy tace gobe yazo ya d’au Fatima.

Sosai Daddy yaji daÉ—in abunda ta cemasa kuma wani gefe fargaba yake yadda zai tun kare Fatima da Hajiya Sa’a da maganar auren Hajiya Kulu,duk da shi har yanzu baya jinta aran sa amma gani yake gwara ya aure ta zaifi.

Washi gari da kusan Æ™arfe goma sai ga mai gyaran jiki da Hajiya Sa’a takira ta zo.

Bayan sun gaisa da ita Hajiya Sa’a ta kai ta É—akin Fatima tace mata ga mai gyaran jiki za’ayi mata har kitso da lalle.

Shuru Fatima tayi tana tunanin gyaran jikin me za’ayi mata.

Kamar Hajiya Sa’a ta san me take tunani sai tace, “Fatima da taga ma miki sai ki shirya dan mijinki zai zo ya É—auke ki kinji” bata bari taji me Fatima zata ce ba ta fice warta aÉ—akin.

Binti da kallo Fatima tayi aikuwa ba bashiri sai ga hawaye sun fara zuba sai kuka.

Wayar ta ta É—auko ta kira Hauwa ta ta faÉ—a mata yadda sukayi da Hajiya Sa’a.

Haƙuri Hauwa ta bata kana tace ta daina kuka yanzu ga tannan zowa gidan.

Koda Hauwa ta Æ™arasu har in fara mata gyaran jiki tana zowa tafara kiran “amaryar Daddy yau kam ba zai gane ki ba haka” tsaya kala-kala ta dan ga yi mata bayan ta gama zama tayi suka fara fira.

Sunan ta ta kira har sau uku tace, “Fatima ina son ki bani arun hankalinki idan kin koma ki Æ™ara saka mijinki ajinki sosai,dan gaskya bazan É“oye miki ba aikawai aiki ga banki amma idan kika Æ™ara saka shi jikin ki ko meye zai zo miki da sauki insha Allah”.

Haka dai suka cigaba da fira har aka gama mata gyaran jikin,Hajiya Sa’a tazo tace tayi sauri ta shirya dan ga Daddy nan ahanya.

Hauwa kayan da tazo mata dasu na ƙamshi da gyaran jiki ta bata kanan tayi mata sallam ta wuce war ta.

Hauwa na fita Fatima ta shiga toilet tayi wanka bayan ta fito daga wanka sosai ta ɓata lokaci wajan kwalliya tayi kyau sosai bare gashi ta sha gyara kuma abu ga mai ƙaramin ciki.

Ƙofar da aka turuce yasa ta ɗago da kan ta.

Hajiya Sa’a ce ta shigo tace, “Fatima inkin gama ki fito yana jiran ki kuma dan Allah ina son ki Æ™ara da gewa da addu’a sosai kuma idan kinga abunda bai miki ba to ki kirani ki faÉ—amin dan haka tashi muje kada yaga kin daÉ—e”.

Komai Fatima bata ce ba dan ita bata ta so ta koma yanzu ba tadai mata magana ne dan ta ganshi.

Mayafin ta ta yafa ta fito ahankali take tafiya har ta ƙarasu parlour .

Zaune yake yana fira da Hajiya Sa’a har ta Æ™arasu wajan da suke .

Tashi yayi yana cewa, “Hajiya mudai zamu wuce dan yamma tayi”.

Tace, “to Allah ya Æ™iyaye ya kaiku lafiya kuma dan Allah arinÆ™a kula da ita kasan yanzu ba ita kaÉ—ai take ba”.

Sai da ya dobe Fatim kana yace, “kada kidamu Hajiya tah insha’Allahu zan Æ™ara kula ta sosai”.

Rakiya ta musu har wajan da sukayi parking ďin motor su.

Sai da suka shiga driver yaje san’nan ta dawo ciki da kewar Fatima dan kwana biyu ďin da tama ta har ta Æ™ara shiga ranta dan ta fahince ta tana da saukin kai.

Tunda suka shiga mota Daddy bace mata komai ba abun ta kaice ko kallon ta yaƙi yayi dan ko fuskarsa juyar da ita yayi gefe ɗaya.

Abun ya bata mamaki sosai amma sai ta ƙyale shi har suka kawo gida.

Driver nayin parking Daddy ya fito bai ma bari ta fito ba yayi tafiyar sa ya barta.

Sosai abun ya ƙara ɗaure mata kai amma sai tafi to ta ƙarasa daga ciki.

Ba kowa afalo dan haka ka tsaye ta karasa part É—in ta.

Kiran sallah aka fara dan haka tashi tayi ta gabatar da sallah azakar taci gaba dayi har akayi isha’i tagabatar da ita bayan ta kammala tashi tayi ta sake wanka tasa ka wasu figagin kayan bacci wanda dasu da babu duk É—aya bayan ta gama ta feshi jikin ta da turare kana ta É—auko wani zumbulelen hijab ta saka ta kulle part É—in ta ta sauko Æ™asa.

Koda ta sauko Mumy suna falo zaune tafiya taci gaba dayi har ta ƙarasu wajan da suke.

Mumy ta kalla ciki da ladabi da sakin fuska ta gashe ta.

Kallon Æ™asa da sama Mumy tayi mata kana tace, “munafuka kin gama muna furcinki kin dawo”.

Murmushi Fatima tayi batace da ita komai ba.

Duban ta tamaida ga Zainab tace, “Zeey kina lafiya?” wai dan Allah inasu Maryam da Aysha ga baki É—aya na daina ganin su nace lafiya dai ko?”.

Zainab tace, “lafiya Æ™alau suke amma nasan satin nan zasu shigo kin san za’akawo kayan auren mu”…..bata Æ™arasa faÉ—a ba Mumy ta bugar mata baki ta dinga zakin ta tana faÉ—in,

Wan’nan muna fukar zaki tsaya kina faÉ—a ma abunda ya shafeki salon taje ta bi-biya taga waza ki aure ta aure shi”haka Mumy tayi ta masifar ta amma Fatima ba abunda tace mata dataga abun Mumy sai karuwa yake taja Æ™afafunta ta wace É—akin Daddy.

Tana shiga daga ciki ta zare hijab ɗin da ta saka kana ta ƙarasa bdroom ɗinsa.

Zaune yake yana waya da Hajiya Kulu da ta dame shi akan yazo wajan ta amma yace mata sai gobe haka dai taci gaba dayi masa naci har tayi nasarar yace mata gashi nan zowa.

Yana aje waya Fatima na shigowa dan har ya fara shirin fita.

Ahankali take ta kawa har ta ƙarasu cikin ɗakin tsaye tayi tana kallon sa dan shi bai ma san ta shigo ba ƙamshi turarin da yajine yasa ya ɗago kansa ya kalle ta ba shiri suka haɗa ido murmushi tayi masa mai ƙara mata kyau, ga bansa ne ya faɗi irin yadda ya ganta dan gabaki ɗaya ta can zama sa kamar ba itaba, lokaci ɗaya ya taso gare ta,da sauri ta faɗa jikinsa sosai ya ma tsata jikinsa yana saukar da numfashi da sauri da sauri.

Bai cemata komai ba bakin su ya haɗe waje ɗaya ya fara kissing ďinta kamar ya cinye ta gabaki ɗaya ya ma manta da wata Hajiya Kulu bare alƙawarin da yayi mata na ga shinan zowa.

ÆŠaukar ta yayi caÆ™ ya karasa saman gado kayan jikin ta ya cire mata ya fara wasa da ita son ran shi duk da ita baso take ba amma saboda abunda Hauwa tace mata yasa tabiye mishi.

Sosai ya bata wuya a wannan daren dan ji yake kamar ya shekara bai gantaba haka yake ji.

Sai da komai ya lafa su kayi wanka sukayi addu’ar barci suka kwan ta.

Koda gari ya waye tana idar da sallah da azkar ɗin da ta saba har taso tafice amma yariƙi ta yace,

“Fatima ina zakije?”.

Kallon sa tayi tace “zanje É—akina na shirya”.

Duban ta yayi da kyau kana yace, “Fatima mena miki yasa ki ke guduna ne?”.

Tace, “komai baka mun ba Daddy kai É—an ne ke shareni” tana faÉ—a tana cinnu baki gaba.

Yace, “ai dole na share ki tunda kinje wajan Hajiya kin barni.

Bai bari tasake magana ba ya haÉ—e bakin sa da nata daga nan labari ya sauya,…sune basu fito ba sai goma saura

Parta É—inta ta koma tayi wanka ta fito,koda ta fito ita kaÉ—ai suke jira zama tayi suka fara bearkfasat bayan sun kammala Daddy duban Mumy yayi yace, “ki gayama Æ´an uwanki ranar da za’akawo kayan auren yaran nan”..yana faÉ—a yana tashi domin ya fita saboda Hajiyar sa ta dame shi da kira gashi har Fatima ta fara zargin wani abu akai.

Mumy ba tare da ta dube shi ba tace, “zan gaya musu”.

Har ya kai baki ƙofa Fatima takira shi,tashi tayi ta ƙarasa wajan da yake kana suka cigaba da tafiya har wajan motar sa.

Kallon sa tayi tace, “Daddy lafiya naga sai sauri kayi kafita?”.

“Lafiya Æ™alau yace da ita ya Æ™ara da cewa jirana akeyi shiya sa”.

Tace, “yau Æ™arfe nawa zaka dawo?”.

Sai da ya duba agogon dake hannun sa kana yace, “Æ™arfe biyu insha Allah” tare da shiga mota driver yaja suka wuce ita ko ta dawo daga ciki.

Tana shogo wa Mumy ta kalle ta tace, “wai me kike taÆ™ama dashi ne da zaki ce kiyi masa rakiya bata re dana baki dama ba “.

Fatima bata cemata komai ba ta haura sama ta barta tana kumfar baki.

Ba ita ta sauko ba sai wajan ƙarfe biyu na rana ta sauko kitchen ta shiga koda taje ƴan aiki sun gama komai dan haka ko mawa tayi domin tayi wanka.

Bayan tayi wanka ta shirya wayar ta ta ɗauko domin ta kira Daddy taji lafiya har yanzu bai ƙarasu ba gashi har huɗu saura.

Kiran sa tayi amma tana ringing ba’ayi picking.

Sai da takira har sau uku aka É—auka ajiyar zuciya ta sauke kana tayi sallama mai-mai kon taji muryar Daddy sai taji ance, “ke Æ´ar jagaliya…. kin dame mu dakira fah,hala baki san yana tare da amaryar sa bane da zaki dame mutane to wallahi kikiyaye ni dan ni ba tsarar yinki ce ba,kuma zamu haÉ—u dake lokaci kaÉ—an zan shigo gidan kuma zaki kuyi dana sani keda waccan tsohowar”….tana kaiwa nan ta katse kiran batari da taji me Fatima zata ce ba.

Mamaki ne ya rufe ta ga baki É—aya ta kasa koda sauke wayar akunne ta tama rasa me zatayi taji daÉ—i ba abunda zuciyar ta ke tuna mata inba maganar Hauwa ba.

Ita ko Mumy tunda Daddy ya fita ta yafa mayafin ta taje wajan Malamin ta ya bata maganin da zata zuba ma Fatima cikin ta ya zobe.

Shiko Daddy bai masan tayi wan’nan wayar ba dan lokaci bacci ya keyi,Kuma bai dawo gida ba sai da akayi sallah magarb kana ya dawo…..

#Vote
Comment
Shere

Sumy M Na’ige🌸
1/23/20, 11:48 AM – +234 706 211 8047: 💦💦💦💦💦💦💦
💦💦💦💦
💦💦

ƘAWAR ƳATA CE
1441H/2019M.

®�
GASKIYA WRITERS ASSOCIATION✍�
{Gaskiya É—aya ce daga Æ™inta sai É“ata burin mu faÉ—akar da al’umma domin ribantar duniya da lahira}

 ```🎐G•W•A🎐```

GASKIYA DOKIN ƘARFE�

Story & Written
By
SUMMY M NA’IGE✍ğŸ?

Didicated to..
Neat lady 🥰🥰

~VOTE & FOLLOW 4 [email protected].~

Page 44

__📖 Hawaye masu zafi suka fara zuba a idon ta,wayar dake gaban ta ta É—auko takiri Hauwa tana É—auka ba tace da ita komai ba saboda zuciyar ta dake ma ta zafi sai da ta fitar da isaka mai zafi kana tace, “Aunty Hauwa nikam gida zan koma dan ba zan iya ba wallahi koda ma iyaye ne nake ma biyayya to a gaskiya yanzu bazan iya ba”.

Hauwa tace, “me yafaru teema?”.

Tace, “komai ya faro”nan ta kwashe duk abunda ya waka na tsakanin ta da Hajiya Kulu ta faÉ—a mata.

Sai da Hauwa tayi ajiyar zuciya kana tace, “Fatima tafiyar ki gida ba itace mafi taba,shawara da zan baki ita ce ki tsaya ki taimake Daddy ki dan wallahi ya faÉ—a tarkon Hajiya Kulu tun da jimawa kuma shi kansa baya sun zaman sa da ita amma yarasa ya zaiyi saboda Hajiya Kulu shu’umar mace ce ban san yadda zan baki labarin ta ba dan haka kiyi affani da son da Daddy kemi ki ki haÉ—a da addu’a ki raba shi da ita dan Allah Fatima kada kije ko ina, ko Alhajina yasu yara bashi da ita amma ya kasa please Fatima ki tsaya ki cece uban É—anki ko Æ´arki kuma uba ga masoyiyar ki ke ko ba komai tsakanin ku to zaki samu lada sosai a wajan Allah”.

Haka tayi taba Fatima shawara har ta yarda zata tsaye tayi yadda tace amma da sharÉ—in itama zata sama ta hannu,daga baya sukayi sallama akan sai sun haÉ—i.

Suna gama wayar ta É—an ji sanyi abunda ke damun ta, kusan magarb ta sake wanka taje ta shirya cikin wata riga da sikt na atamfa, sosai suka karÉ“e ta jikin ta ta feshe da turari tayi sallah har isha’i sai da tayi kana ta sauko kasa.

Koda ta ƙarasu parlour su Mumy suna nan zaune suna kallo.

Ƙarasuwa tayi ta zauna kana ta ɗago da kanta ta gaishe da Mumy.

Ƙarɓawa Mumy tayi ciki da sakin fuska haɗe da ƙaƙalo murmushi da bata shirya ba.

Fira ta fara jan Fatima da ita,abun ya ba teema mamaki sosai amma sai ta basar suka cigaba da firar su har su Zainab.

Suna cikin fira Mumy ta tashe taji kitchen ta haÉ—u kunun aya tara dara bashi gida biyu É—aya ta zuba wani É—aurin magani ta juya har sai da magani ya haÉ—e da kunun ayar kana ta É—auko ta fito dash parlour.

Wajan da Fatima take zaune ta Æ™arasu É—aya kofin ta miÆ™a mata tace “gashi ki sha ke kaÉ—ai nasan idan na haÉ—eki da na su Zainab za su shanye su barki”.

Godiya Fatima tayi mata tana me karɓar kofin da ta bata.

Ɗaya ko ta miƙa ma yaran ta suka fara sha.

Fatima É—auko wanda Mumy tabata tayi ta zoba a kofi dani yar ta sha sai sukaji salamar Daddy.

Da sauri Kulsum ta miÆ™e zowa gare shi tana faÉ—in “oyoyo Dadddy ” tare da karÉ“ar kayan dake hannun sa.

Kayan da ya sayo musu ita da Ummi ya miÆ™a mata tare da faÉ—in “ke da Ummi” ya wuce warsa É—aki tari da kira Fatima ta kawo mishi ruwa.

Har zata tashi taji Mumy tace, “kiyi zaman ki bari na kai masa”.

Komai Fatima bata ce ba Mumy taje ta kai masa ruwa.

Mumy na tafiya Nabila na fitowa daga É—akin ta,zama tayi kusa da su sai Kulsum tace “Aunty kina can kina waya muka sha kunun aya bada ke ba”…ta Æ™arasa maganar tana mata dariya.

Har zatayi magana idon ta ya kai ga wanda Fatima ta zoba domin ta sha ta tashi ta É—auko batare da tace ma Fatima ta bata ba ta É—auko kofin gabaki É—aya ta fara sha.

ita dai Fatima ko mai batace da ita ba dan ita yanzu duk abunda ya shafe madara ba sun shi takeyi ba.

Daddy yace da Mumy takira masa Fatima.

Koda ta fito har Nabila ta gama shan kunu ayar har an mai da kofin kitchen.

Mumy na faÉ—a mata tashi tayi taje É—akin Daddy.

Koda taje yana parlour zaune zama tayi nesa da shi ta fara gaisheshi.

Kallon ta yayi yace, “dawo nan mana Fatyna”.

maganar da sukayi da Hauwa ta tuna dan haka bamu su tazo gare shi.

Jikin sa ya jata yace “yau nasan fushi akeyi dani ko? to kiyi haÆ™uri nima wani aki ne yari Æ™eni” tare da kai hannun sa yana shafe cikin da ke jikin ta.

Kauda abunda takeji tayi a zuciyar ta kana ta kwantar da kanta Æ™irjin sa san’nan tace “to Daddy amma gobe idan zaka jima tare zamuje sai nataya ka aikin “.

Murmushi yayi mai É—an sauti kana yace “insha’Allahu ba zan sake jimawa ba”.

Bai bari tayi magana ba ya haÉ—e bakin sa da nata ya shiga wasa da ita son ran shi.

Shi kadai yake abunsa amma ita ko kukan zuci takeyi dan jitake kamar ta naÉ—a masa É—an bazan duka.

Fatima na tashi Mumy ta kalle Zainab tace “ina kofin da Fatima ta sha kunun aya?”.

Kulsum ce tayi saurin tace “ai bata sha ba Aunty Nabila ce ta shanye shi gaba ki É—aya…..ai bata kai karshin zan cin ba Mumy ta fara salati tana ihu…..

Ita ko Nabila tunda ta sha kunun ayar ta fara jin cikin ta na juya mata kaÉ—an-kaÉ—an aikuwa Mumy na fara salati taji cikin ta yayi wani masifar juya mata kamar Æ´an hanji cikin ta sufito.

Wani uban ihu ne ta zuba tare da faɗuwa ƙasa sume.

Ai ba Mumy ba har Zainab sai da hankalin su ya tashi haÉ—e da saka nasu nasu ihun.

Gabaki É—aya Mumy ta rikice tarasa ya zatayi inba safa da marwa ba ba abunda take.

Jinin da suka ga yana fita ta ƙasan Nabila yasa suka ƙara wani ihu,ita ko Mumy inaba kuka da zakin Fatina ba ba abunda take .

Zainab ce taje da gudu part É—in Daddy domin ya fito aka Nabila asibiti.

Shiko gaba kiÉ—aya ya burki ce burin sa ya kawai yaji ya afka aciki…..

Bugun ƙofar da Zainab keyi ne yasa Fatima tayi masa magana dan shi bai masan tanayi ba.

Sai da tayi masa magana har sau uku kana ya gane me take nufi.

Ba dan ranshi ya soba ya tashi ya sanya jalabiyar sa itama tasaka kayan ta suka fito.

Zainab ya gani nan take faɗa masa abunda ke faruwa,ihun da yaji Mumy nayi ne yasa ya ƙarasa parlour da gudun sa.

Abunda yagene yayi matuƙar razana shi dan haka bai tsaya komai ba ya ɗauke ta suka wuce asibiti shida Mumy da Zainab,aka bar Fatima da Kulsum da Ummi.

Koda suka isa asibita karɓar ta sukayi aka fara bata taima kon gaugawa.

Likitoci sun sha wahala kafin su samu jinin ya daina zuba.

Bayan komai ya dai-dai ta suka fito Daddy ya tambaye su mike damun ta suka ce su basu gane komai ba amma idan ta farka zasu ƙara binci ke akai.

Godiya Daddy ya musu kana yace ma Mumy shi zai koma gida sai da safe tare da cema Zainab ita ma tazo su tafi gobe sai tazo da safe.

Haka akayi suka bar Mumy ita kadai tana zubda hawaye da ƙudurun ramuwa akan Fatima.

Yana dawo yaje É—akin teemar sa suka cigaba da baccin su.

Har akayi kwana biyu Nabila bata farka ba abun yaba likitoci tsoro sosai, Mumy ko in ba kuka ba ba abunda take dan ko lokacin da Fatima tazo da banda Daddy da ta haÉ—e ta duka.

Ita ko Fatima tunda taga abunda Mumy ta mata bata sake zuwa duban Nabila ba.

Mumy na asibiti jinya shiko Daddy yana gida tare da teemar sa ba abunda ke fitar da shi sai aki kuma da ya gama zai dawo gida wajan Fatyn shi.

Ita ko Hajiya Kulu kwana biyu ta daina ganin Daddy sosai hankalin ta ya tashi dan haka ta koma wajan malamin ta ta faÉ—a masa abunda ake ciki.

Yace mata mundin yana tare da yarinyar nan Fatima to koda ansakeyi masa aiki zai kara,kuma lokaci kaÉ—an zata rabaki dashi mudin baki tashi tsaye ba.

Sosai hankalin ta ya tashi dan yadda takejin Daddy aran ta to komai zata iyayi kuma ta ɗau alƙawari sai Daddy ya rabu da Fatima cikin satin nan..

Ita ko Fatima tama manta da wata Hajiya Kulu harkar gaban ta takeyi sai neman kariya daga Allah….

#Vote
Comment
Shere

Summy M Na’ige🌸
1/23/20, 11:48 AM – +234 706 211 8047: 💦💦💦💦💦💦💦
💦💦💦💦
💦💦

ƘAWAR ƳATA CE
1441H/2019M.

®�
GASKIYA WRITERS ASSOCIATION✍�
{Gaskiya É—aya ce daga Æ™inta sai É“ata burin mu faÉ—akar da al’umma domin ribantar duniya da lahira}

 ```🎐G•W•A🎐```

GASKIYA DOKIN ƘARFE�

Story & Written
By
SUMMY M NA’IGE✍ğŸ?

Didicated to
Mumy Kulsum
Mumy Abdullah

~VOTE & FOLLOW 4 [email protected].~

Page 45

_📖 Nabila sai da tayi sati biyu a hospital suka dawo gida, bayan sun gama yimata binci ke amma ba’aga nu komai ba.

Duk yadda Hajiya Kulu taso tara ba Daddy da Fatima amma abu bayi ba, dan shi kamar lokaci ake ƙara saka masa son ta azuciya.

Ba inda bata jeba amma bata ci nasara ba amma tayi alƙawari ko wane lokaci ne sai ta rabasu.

Suku sauran ‘yan group7 ankawo musu amare, duk abunda sukayi bai yi ba awannan lokaci, dan amare sun tare ba yadda suka iya haka suka zoba ido suna kallon baÆ™in ciki dan ita Hajiya Hafsa har kwanciya sai da tayi hospital satin ta uku aka sallame ta.

Lokaci yata fi abubuwa sun sauya na daɗi da rashin sa babban tashin hankali a wajan su alokacin Allah yayi ma Gwaggo Maryam rasuwa mutuwar tayi matuƙar raza nasu, sunyi kuka har sun gaji sun barma Allah ikon sa.

Ita kuma Fatima yanzu cikin ta ya kai watan haihuwa dan ko yaushe ina saran haihu warta.

Gidan su sun so Daddy ya kawo ta ta haihu a can amma yace a’a sai ta haihu zai kawo ta,dan ko Hajiya Sa’a taso ya mai da ta amma yace a’a tayi hakuri har ta haihu, ba yadda ta iya dan haka ta kyale shi.

Dan yanzu sosai take samun kulawa wajan Daddy da Hajiya Sa’a da sauran Æ´an uwansu har ma dana ta dan Kaka Amo koda yaushe tana bisa hanyar gidan Fatima.

Kuma yanzu amaren da aka kawo sun haÉ—e kansu da Fatima sosai suka samu fahin tar juna danshi yanzu ko su Mumy da Hajiya Shafa sunyi wani aiki baya ta siri, dan dawani abu yasa mu É—ayan su to zama zasu sugano me yasa meshi, in wanda baza su iya magan ce shine ba da kansu sai su faÉ—a ma Malamin su Fatima na islamiya.

Ga Hauwa ita ma ba’a bar ta abaya ba wajan kula da Fatima, dan yanzu cikin yayi girma sosai.

Mumy ko tana ganin cikin yaki zube wa ta koma wajan malamin ta ya bata magani yace da Fatima ta fara na ƙuda azoba aruwa abata tasha, yace mata koda ta haihu komiye to bazai zo da rai ba.

Tundaga lokacin Mumy ta fara sa Fatima jikin ta sosai har ta É—an saki jiki da Mumy dan ta É—auka cewa abun na Mumy ya sauya ne.

Itako Mumy yanzu abunda bata so duk bai wuce zowan da Hajiya Kaka keyi lokaci-lokaci ba,dan ko tana son tayi abu to idan Hajiya Kaka na nan baza ta samu damar insa ba.

Yau ma kamar kullum suna gama bearkfast Daddy ya fice yaje wajan aiki,ita ko tana gamawa ta koma part É—inta ta kwanta dan yau haka takejin jikin ta duk ba daÉ—i.

Ita ko Mumy na kule da ita, dan haka itama tashi tayi taje É—akin Fatima taga ni ko da gaske bata da lafiya .

Tana shiga ta same ta kwance tana ta ya tsane fuska.

Ƙarasuwa tayi wajen da take kwance kana tace, “Fatima baki da lafiya ne?”.

A hankali ta É—ago kanta murya a dashe bata fita sosai tace “eh Mumy ban da lafiya”.

Tambayoye Mumy tayi mata ita ko ta bata amsa,Mumy naji duk alamun haihuwa ne tace “Fatima bari nazo kin ji Allah ya sauke ki lafiya”.

Fita tayi taje ɗakin ta ta ɗauko wannan ƙullin maganin da malamin ta ya bata ta haɗe da ruwa ta zo wajan Fatima ta domin ta bata tasha.

Koda ta koma Fatima ta fara fita daga haiya cin ta, da sauri ta ƙarasu wajan da take tana yi mata sannu.

Ruwan magani da ke cikin Æ™ofin ta É—auko ta ce “KarÉ“a kisha Fatima zaki samu sauÆ™i yanzu……

Kunsan abu ga mai na Æ™uda kome ye aka bashi Æ™arÉ“a yake yi, in har ance za’a samu sauÆ™i..

#Vote
Comment
Shere

Summy M Na’ige🌸
1/23/20, 11:48 AM – +234 706 211 8047: 💦💦💦💦💦💦💦
💦💦💦💦
💦💦

ƘAWAR ƳATA CE
1441H/2019M.

®�
GASKIYA WRITERS ASSOCIATION✍�
{Gaskiya É—aya ce daga Æ™inta sai É“ata burin mu faÉ—akar da al’umma domin ribantar duniya da lahira}

 ```🎐G•W•A🎐```

GASKIYA DOKIN ƘARFE�

Story & Written
By
SUMMY M NA’IGE✍ğŸ?

Didicated to
Family😘

~VOTE & FOLLOW 4 [email protected].~

Page 47

_📖 Kafin suyi mata magana tace, kone Æ´an uwan Fatima ?”.

Kaka Amo tayi sauri tace ta haihune?”.

Sai nurse É—in tace “eh ta haihu amma bazan faÉ—e me aka samu ba sai kun ban goron albishir”.

Rigan-gan akayi wajan bata Daddy da Hajiya Sa’a,Daddy kuÉ—e ya bata masu yawan gaske wanda shi kansa bai san yawan su ba.

Hajiya Sa’a ma haka,ita kanta nurse É—in abun ya bata mamaki sosai godiya ta musu kana tace musu “an haife kyawa-wan twins maza gasu can ana gyaransu bari na É—auko muko ku gani”.

Ai tun bata rufe bakin ta ba Daddy ya fara yiwa Allah kirari yana masa gode akan kyautar da ya bashi.

Itako Hajiya Sa’a har da biye ma Kaka Amo tayi wajan rawa sunayi suna godeya ga Allah da ya sauke ta lafiya.

Hajiya Sa’a kiran Æ´an uwa da abukan arziki tayi ta faÉ—a musu suma sun taya su murna sosai.

Suna cikin haka sai ga nurses sun fito kowace É—auke da daya ahannun ta.

Da sauri suka ƙarasa garesu suka karɓe yaran suna murna.

Sai da suka gama gani Daddy ya karɓa yayi musu huɗe kana yasama rayuwar su albarka ciki da so da ƙaunan yaran.

Nurse É—in ya kalla yace “ina ita Mamar su?”.

Sai nurse É—in tace “tana É—aki tana hutawa amma zaga iya shiga ka ganta”.

Tun bata refe baki ba Daddy yace “muje ki kaini”.

Suma su Hajiya Sa’a da Kaka Amo bin su sukayi É—akin da Fatima take.

Kuda suka shiga tana zaune saman gado kamar ba ita ce Daddy ya É—auko ba rai a hannun Allah.

Ƙarasuwa sukayi wajan ta suka fara yimata yajiki .

Bayan ta amsa suka bata yaran da ta haifa tagani amma saboda kunya cemusu tayi ta gansu.

Da ƙyar suka samu ta karɓa yaran.

Bayan awa biyar aka sallame ta dan ba abunda ke damun ta sai rashi ƙarfin jikin da bata da, koshi sunce zowa wani lokaci zataji ta dai-dai.

Gaba ki É—aya Daddy ya manta bai kira Mumy ya faÉ—a mata ba.

Hajiya Shafa ce ta kira ta dan suma har sunji labarin haihuwar Fatima ransu baiyi daÉ—e ba dan ba haka suka so ba.

Dan kishayar ta Nafisa har rawa sai da tayi ita da sauran amaren saboda murna.

Sai da takira har sau biyu kana Mumy ta É—auka dan tana É—aki tana bakin cikin zowan Daddy gida dan son tayi abar ta har ta gama shan woya kafin akai ta hospatal kafi wani lokaci komeye acinkin ya mutu.

Tana cikin haka wayar ta ta fara rura har taso taƙi ɗagawa amma data ga andame ta dakira dan haka ta ɗauka.

Sunan Hajiya Shafa tagani dan haka tayi sauri ta kara akunnen ta.

Bayan sun gaisa sai Hajiya Shafa tace “ko har dake kuna hospatal?”.

Sai Mumy tace “warin me?”.

Sai Hajiya Shafa tace, “au baki masan ki shiyarki ta haihuba kenan dan naga ko kiran mu bakiyi ba”.

Tana cewa haka sai da gaban Mumy ya faÉ— baki na karkarwa Mumy tace “yaushe ta haihu kuma me ta haifa, taÆ™ara da cewa nasan kome ta haifa ya mutu”.

Sai da tagama jerama Hajiya Shafa tambayoye kana ta buÉ—e baki tace “ko É—aya dan niman yanzu naji mutumi yar ta ta fito tana guÉ—a tana rawa wai anhaifar musu Æ´an biyu kuma gaba É—ayan su maza ne”.

Ai tun Hajiya Shafa bata kai Æ™arshin zancin ba Mumy ta sake waya ta faÉ—i Æ™asa tace tas…

Tan gaɗi ta farayi kamar zata faɗi,kujerar dake kusa da ita tariƙe kana ta fara magana cikin wata muryar kamar ta ƙatti.

Tana faÉ—in wallahi Æ™arya ne ba wata wadda zata haife É—a namiji a wannan gidan ta zauna lafiya matuÆ™ar ina raye”.

Hauka Mumy ta farayi har da cewa ba jinin Daddy ne ba in ma da gaske anhaihu É—in.

Tana cikin wannan haukar Daddy ya shigo da sauri ta Æ™arasa gareshi tace “Daddy Zainab ina Fatima É—in? tunda har zaka É—auke ta amma baka sanar dani ba”.

Yace “albishirin ki
kin samu yara biyu dukan su maza”.

Wannan karun Mumy ta sauya ba kamar da ba dan Æ™iri-Æ™iri tace “da gaske ko É—iyan kane? kodai wani wajan tasa musu ta Æ™aÆ™abamaka kai ko ido rufe zaka karÉ“a”…..bai bari ta kai Æ™arshin zancin ba ya wanke ta da mari har bayu.

Yana huci yana nunin ta da É—an ya tsa kana yace “kin san me kika faÉ—a kowa, yaran nawa zaki fara sheganta su kuma ina raye”.

Ba’abun da bai ce mata ba itama haka daga bisani yaga abun nata kamar da taÉ“in hankali dan haka yafice yabar mata gidan gabaki É—aya.

Duk abunda akeyina hidamar suna Mumy bataje taga yaran nan ba kuma ta hana yaran ta zowa Zainab ka dai ce taje amma batare da sanin Mumy ba dan tace duk wanda yayi mata maganar Fatima sai ta illatashi.

Mumy takoma kamar sabon kamun hauka dan bataji bata gani ko ina zowa takeyi dan akashe yaran ita dai burin ta su bar numfashi.

“`(Allah sarki su yara mesuka sani ko me suka yamata.

Dan Allah ƴan uwana mu daina ƙazamin kishi dan bashida anfani wallahi wani kishi illah ne ga remu.

Kowa na dakishe amma kada kishi yasa muhaÉ—a Allah dawani,dan haka mukeyaye Æ´an uwana.

Allah yasa mufi Æ™arfin zukatan mu kuma ya kare mu daga Æ™azamin kishi ameen. “`)

Inyi shagalin wajan sunan yaran inda Daddy yace ba zai sauya musu suna ba haka zai a barsu.

Sosai nera tayi kuka dan ba abunda Daddy bai yi mata ba, har sauyama iyayen ta gida yayi kuma yaba mahaifin ta mota har Æ™anwar ta sai da yaba mota itama Kaka Amo sai da yayi mata kyau ta mai girma Hajiya Sa’a ma tawa Kaka Amo, aikuwa Kaka Amo kamar tayi hauka dun daÉ—i.

Duk hidamar da akeyi ta sunan su alhasan bawan da group7 suka je kuma basuyi murna ba.

Watan Fatima É—aya da haihuwa akayi auren su Zainab da Nabila,anyi shagalin biki sosai anka kashe nera Mumy ma ta narke nara sosai.

Bayan bikin su Zainab da sati uku Daddy yama tsama Hajiya Sa’a amaidam masa da Fatima.

Ba yadda ta iya tashirya taje gidan iyayen ta ta faÉ—a musu saÆ™on Daddy kafi kowa yayi magana Kaka Amo tace wani sati da kanta zata maida Fatima ita kam Ummah bata so haka ba, dan taso abar Fatima har tayi arba’in biyu amma ga yadda Kaka Amo tace kuma yadda tace haka za’ayi dan haka bata ce komai ba tayi shuru dan bata iyawa da yayyaÆ™ar da zata mata.

#Vote
Comment
Shere

Summy M Na’ige🌸
1/23/20, 11:48 AM – +234 706 211 8047: 💦💦💦💦💦💦💦
💦💦💦💦
💦💦

ƘAWAR ƳATA CE
1441H/2019M.

®�
GASKIYA WRITERS ASSOCIATION✍�
{Gaskiya É—aya ce daga Æ™inta sai É“ata burin mu faÉ—akar da al’umma domin ribantar duniya da lahira}

 ```🎐G•W•A🎐```

GASKIYA DOKIN ƘARFE�

Story & Written
By
SUMMY M NA’IGE✍ğŸ?

Didicated to..
My lovely Aunty🥰🥰🥰🥰🥰�

~VOTE & FOLLOW 4 [email protected].~

Godiya mai tarin yawa ga hasken gaskiya Writers,ina matuƙar jinjina a gareku da godaya agareku sarakan haƙuri da kawaici da yafiya, ina ƙara godiya gareku na yadda kuka fara fitar da tauraruwa ta social media har take haskawa banda kamarku My Aunty nah (Mrs xerks) &Ummu Nabil�

Ina sonku
irin sosai ɗin nan Allah yabar min ku😘

Duk inda kuke inanan liƙe daku koda zakuyi min gore bazan barku ba bare nasan ba halinku bane yima mutum gore😁

Allah ya baku nasarar abunda kuke nema duniya da lafira Allah ya ƙaramuku basira mai yawa wadda zaku anfanar da dubban mutane da ita sabida Allah👌 Ameen ya Allah.

Ina ƙaunarku all gaskya writers😘

Masu iya magana sunce, da wasa da yaro gwanda kwana da yunwa👌

Page 48

_📖
Bayan sati ɗaya da dawowar Fatima Kulsum taje ta karɓo Husaini tazo da shi wajan Mumy aikuwa Mumy naganin tazu da shi ta karɓeshi cikin mutumci tace ma Kulsum taje ta karɓo ɗaya.

Da gudun ta taje dumin ta karɓo Alhasan.

Tana fita Mumy tayi sauri taje ta É—auko wani fauzin tahaÉ—a shi da madara ta fara bashi.

Suna cikin haka sai ga Kulsum ɗauke da ɗayan,da sauri Mumy ta karɓeshi tace mata ta ɗauke Husaini ta maida ita ko ta karɓi Alhasan.

Haka kowa akayi Kulsum ta É—auke shi ta maida tana fita Mumy ta É—auko Alhasan ta bashi wannan madarar mai haÉ—e da fauzin.

Ko da Kulsum ta dawo Mumy na bashi madara tace “Mumy ashe ya iya shan madara” tana faÉ—a tana dariya jin daÉ—i.

Mumy tace, “eh ya iya mana ba gashi yana sha ba”.

Mumy sai da taga ya sha madara sosai kana tace ma Kulsum ta maidashi wajan Mamar sa kuka yakeyi.

Kulsum ko ta dauka ta maida shi wajan Fatima.

Tana zuwa tace ma Fatima Mumy tace na maida shi kuka yakeyi dan har madara ta bashi yaki ya daina kuka.

Karɓar sa Fatima tayi tayi masa wanka ta kwantar da su.

Bayan minti ashirin da maida su sai ga yara sun fara fitar da kumfa abaki suna yin wata irin miƙa kamar zasu mutu.

Aikuwa Fatima na gani hak lokaci É—aya ta riki ce tama rasa me zatayi sai can dabara ta faÉ—u mata ta É—au waya ta kira Daddy tana kuka ta faÉ—a masa abunda ke faru.

Baƙara min ta shin hankali ya shiga ba lokacin da tafaɗa masa haka da sauri ya bar abunda yakeyi ya zo gida.

Koda ya ƙarasu bai tsaya komai ba ya ɗaukesu hankali ta she ya kai su hospatal ɗin dake kusa da su.

Taimakun gwagawa likitoci suka fara basu.

Shiko Daddy sai safa da marwa yakeyi a hospatal.

Ita ko Fatima na zaune kamar ba abunda ke damun ta, amma azuciyar ta tafima Daddy shiga tashin hankali.


Ita ko Hajiya Kulu tunda Daddy ya dai na kulata taje wajan Malamin ta akace sai ya rabu da Fatima zai dawo dai-dai,to tayi yawo wajan Malamai har tagaji amma bata samu nasara ba acan ne garin yawon ta tahaÉ—u da wani Alhaji tundaga wannan lokaci suke tare ko ina zaije da ita yake zowa.

Bayan wata uku da haÉ—uwar ta da shi har tafara tunanin yadda zata dawo wajan Daddy sai ciyo ya kamata ba sauki har sai da akaje hospatal.

Ana mata gwajin farin sai aka gano tana dauke da cuta mai karye gargowar jiki ajikin ta.

Tashiga tashin hankali sosai kuma taneme wannan Alhajin ƙasa ko sama amma bata ganshi ba tayi kuka har ta gaji ba dan son ranta ba ta fara shan magani dan lokaci ɗaya jikin ta ya sauya kowa ya san halin da ta ke ciki har yaran ta sunyi kuka har sun gaji sunyi tir da hali irin na mahaifitar su.

Daga baya da suka ga yadda ta koma lokaci É—aya dan haka suka sauko daga fushin da sukeyi da ita suka fara bata kulawa.

Amma lokaci-lokaci take zuwa kaɓar magani amma kamar bata sha dan har yanzu jikin nata bashi da kyau gani.

Sunfi awa biyu kafin likitoci su fito.

ÆŠaya daga cikin Doctors É—in da suka fito yace ma Daddy ya sameshi office dan haka ba musu suka biyu bayan shi har ita Fatima.

Bayan sun zauna dactor kewa Daddy bayani kan yaran yace, “ba komai aka basu suka sha ba sai guba mai illah acikin É—an adam yace amma sunyi Æ™oÆ™ari wajan dawo da lafiyar su amma yanzu muna jiran farfaÉ—owar su lokaci kaÉ—an amma kuyi addu’a dan koshi abune mai wuyar gaske”.

Hankalin Daddy sosai ya tashi lokaci É—aya ya dawo da kallon sa ga Fatima.

Tambayar ta ya farayi waya ba yaran sa guba.

Irin yadda yake mata magana yasa ta rikice tama rasa me zata ce masa.

Magana yake mata amma takasa koda mutsa baki bare yasa ran zata ce wani abu.

Ai da zuciyar sa ta rufe basan lokacin da ya kai mata mari har biyu ba.

Itako tana can tana tunanin yadda zatace masa tasan komai basa sha inba nonoba sai madarar da Kulsum tace Mumy ta basu É—azo kuma tana gudun tace Mumy ta basu madara wata rigima ta tashi dan yace ko ruwa kada abasu sai sun kai wata bakwai.

Tana cikin wannan tunanin taji saukar mari har biyu alokaci É—aya.

#Vote
Comment
Shere

Summy M Na’ige🌸
1/23/20, 11:48 AM – +234 706 211 8047: 💦💦💦💦💦💦💦
💦💦💦💦
💦💦

ƘAWAR ƳATA CE
1441H/2019M.

®�
GASKIYA WRITERS ASSOCIATION✍�
{Gaskiya É—aya ce daga Æ™inta sai É“ata burin mu faÉ—akar da al’umma domin ribantar duniya da lahira}

 ```🎐G•W•A🎐```

GASKIYA DOKIN ƘARFE�

Story & Written
By
SUMMY M NA’IGE✍ğŸ?

Didicated to..
All Gaskiya writers😘

~VOTE & FOLLOW 4 [email protected].~

A RAYUWA ILIMI NA DA DAƊI IDAN KASAMU ƘARAN CIN ƊAYA DAGA CIKIN BIYU NAN RAYUWA BAZATAYI DAƊI BA, AllAH KABAMU IKON NEMAN ILIMIN DUNIYA DA LAFIRA
AMEEN YA AllAH.🙏

Page 49

_📖 Kanta ta É—ago ta kalleshi shiko inba huci ba ba’abunda ya keyi.

Nunin ta ya keyi da É—an yatsa kana yace “kigaya min me kika ba yarana wanda ke neman ya ka shesu”.

Komai bata ce masa ba dan irin yadda taga yana magana ba ƙaramin ɗaga mata hankali yayi ba.

Tashi tayi taje nesa kaÉ—an dashi ta kira Hajiya Sa’a ta faÉ—a mata abunda ke faru.

Bata jima da kiran taba sai gata tazo .

Yadda taga Daddy ko ita hankalin ta ya tashi amma ta dake ta fara bashi haƙuri da nuna masa cewa yaran zasu ta shi.

Cikin ikon Allah yaran na cika awa uku suka fara mutsawa.

Doctor suka kira ya ƙara duba yaran ya tabbatar musu da lafiyar su sannan Daddy ya samu natsowa.

Daddy ko ya nace sai Fatima ta gaya masa me taba yaran shi.

Badan taso ba tayi masa bayani tace bata basu komai ba inba Kulsum da tace Mumy ta basu madara ba.
.

Ai tun bata Æ™arasa faÉ—a ba ya kama hanyar fita Hajiya Sa’a na kiran sa amma bai san tanayi ba.

Sosai yasa direba gudu basu ɗau wani lokaci ba suka ƙarasu gidan.

Kafin driver yayi packing Daddy ya buÉ—e murfin mota yafito.

Ba kowa a parlour dan haka da sauri ya ƙarasa part ɗin Mumy .

Koda yaje har zai ƙwalamata kira sai yaji tana waya haɗe da wata irin dariya .

Bai ce komai ba dan abun mamaki ya bashi na wannan dariyar da takeyi.

Wayar ta taci gaba da yi ita da Hajiya Shafa tana bata labarin yadda akayi taba yaran poisen suka sha har yadda taje wajan wani Malami wanda yace a cikin satin nan Daddy sai ya sake Fatima kome suke ta ƙama da shi .

Firar su suka cigaba dayi sai da suka gama kana suka aje wayar Mumy tayi haka ta É—ago kanta suka haÉ—a ido da Daddy aikuwa ba shiri ta tashi zaune tana burin kunya.

Shiko Daddy gaba ki É—aya yarasa me zai ce mata abun duniya ya taru yayi masa tsaye azuciya .

Mumy ko gaba ki É—aya jikin ta yafara karkarwa harda kukan munafurci ta farayi.

Har ta buÉ—e baki dumin tayi masa magana amma ya daka mata tsawa yace “duk abunda zaki faÉ—a bana son ji,dan haka kitashi kibarmin gidana na sakeki saki biyu, kuma kisani komai kikayi min na barki da Allah kuma kanki kika cuta bani ba”.

Yana kaiwa anan ya ficewar sa zuciyar sa na ƙuna dan ji yake kamar ya faɗi, ikon Allah ne ya kaishi ɗakin sa ya samu ya zauna kana ya ɗauko magani ya sha sannan ya ɗan kwanta.

Ita ko Mumy ba Æ™aramin tashin hankali ta shiga ba dan bata taÉ“a tunanin akwai lokacin da Daddy zai’ayi furta kalmar saki agare ta ba.

Sosai ta shiga tashin hankali waya ta É—auko dan ta kira Hajiya Shafa ta gaya mata abunda ake ciki.

Kiran ta tayi amma har ta tsinke bata ɗauka ba har sau biyar ta kira batayi picking ba sosai hankalin ta ya ƙara tashi.

Itako Hajiya Shafa koda Mumy ta kira itama tana cikin nata tashin hankali dan Alhajin Aliyu yazu wucewa yaji tana waya tana dariya abunda ta faɗi ne yayi matuƙar bashi tsoro da mamaki hankalin sa ya tashi dan haka bai san lokacin da yaki feta da mariba har sau uku lokaci ɗaya, sai da yaci mata mutunci sosai kana ya bata takardar sakin ta itama biyu yace ko minti ɗaya kada ta ƙara ta bar masa gida sa.

Tana kuka tana bashi hakuri amma kamar cemasa takeyi ya kara,da taga yana nema ya illata ta bata san lokacin da tafito daga gidan ba.

Gidan Mumy ta nufa dan ta faÉ—a mata abunda ake ciki tana bisa hanyar tafiya ne Mumy ta kira ta.

Koda ta isa gidan Mumy itama har ta fara haÉ—a kayan ta dan ta tafi gidan.

Tanaa cikin haka taga Hajiya Shafa hankali ta she Mumy tambayar ta ta farayi lafiya, nan Hajiya Shafa ke faÉ—a ma Mumy abun da ake ciki.

Itama Mumy gaya mata nata tayi nan suka haÉ—e suna kuka gwanin ban tausai.

Shiko Daddy sai da yasamu kwanan awa É—aya yaji zuciyar sa ta É—an rage yimasa zafi.

Dan haka wanka yayi ya dawo hospatal.

Koda ya dawo fuskar sa bawani annashawa dan daka gansa kasan yana cikin damuwa .

Kiran Hajiya Sa’a yayi gyafe É—aya ya faÉ—a mata abunda yake ciki yana faÉ—a kamar yayi kuka.

Duk da taji daÉ—in hukunci da yayanke amma sai ta nuna masa ba ayanke hukunci cikin fushi sosai taÉ—an jamasa kunne haÉ—e da bashi kuri har ya É—an sauko.

Suna cikin haka Alhaji Aliyu shima yakira ta ya faÉ—a mata abunda ake ciki.

Shima kamar yadda tawa Daddy haka ta masa haÉ—e da basu hakuri har suka É—an sauko.

Bayan sati biyu da faruwar haka aka sallame Æ´an biyu suka koma gida.

Kwanan su ɗaya da dawowa Daddy yayi musu bisa suka wuce ƙasar germany.

Ummi da Kulsum ya kaisu gidan Hajiya Sa’a.

Ita ko Mumy da Hajiya Shafa ba inda basuje ba da mazan su su maida su amma kamar yi suke dan sukara nisa dasu.

Da suka ga abun yaÆ™iyi dan haka suka turu iyayen su gun Hajiya Sa’a.

Haƙuri taba iyayen nasu kana tace bayan kwana biyu zatayi magana da mazan su dai-dai sun huce.

Suko sauran koda suka ji abunda ya same Æ´an uwansu suka shiga tai-tayin su dan kowace bata son ta koma gida zawarci da tsofan ta.

Bayan sati biyu da ta fiyar su Daddy sai ga Maram ta dawo gida wai mijin ta ya koron ta dan zai ƙara aure ita ko ta tada hankalin ta, da yagaji shine ya turuta gida.

Shiko Daddy shida abar sonshi sai soye warsu sukeyi sunyi ɓul-ɓul dasu sunyi gwanin kyau musamman ƴan biyu.

Lokacin da Maram ta dawo gida sosai hankalin Mumy ya tashi.

Dan da tazo gidan iyayen Mumy itama taje, yanzu Mumy kuka takeyi na gaske dan abubuwa sun haÉ—e mata musmman rashin sahibin ta kusa da ita.

Wannan lokacin da kanta taje tagaya ma Hajiya Sa’a abunda ake ciki, kuma ta bata hakurin abunda tayi musu.

Hajiya Sa’a karÉ“ar Maram tayi ta maidata É—akin ta kana ta shirya ta da mijin ta.

Bayan ta maida Marma ita ko Mumy kulum tana saman hanyar gidan Hajiya Sa’a dan ita burin ta Daddy ya maida ta yanzu har wani ladabi suke yawa Hajiya Sa’a ita da Hajiya Shafa kamar ba suba…..

Dan yanzu Mumy taga ta kanta da ko gidansu ba mai kulata dan haka ta koma kamar wata marainiya.

Zaman data keyi agidan ta gaji da shi dan haka ta samu wata islamiya ta shiga kuma Alhamdullah dan yanzu tana ganewa sosai kuma tayi tana nadamar abunda ta aikata dan yanzu haka neman Daddy da Fatima takeyi sama ko ƙasa dan tabasu haƙuri amma bata gansu ba ko wayar su taso ta samu amma bata samu ba tayi kuka har tagaji dan yanzu Mumy tauhidi ya shige zuciyar ta sosai.

Ita ko Fatima da Daddy tunda suka tafi basu dawo ba har Fatima tasake wata haihuwa ta samu Æ´an biyu mace da namiji….

“`Amfa nin zuwa Makaranta kenan yana da kyau komai mukeyi mu keÉ“e lokacin da zamu je makaranta neman ilimin da zamu bauta ma ubangijin mu.

Sai kaji mutane da dama suna faɗin zasu kuma makaranta amma bazaka ji sunce zamu koma isilamiya ba musamman ga matan aure kuma annabi Muhd (S W A) yace duk wanda yaje neman ilimin har ƙura ta bice masa ƙafafuwa to fah kasani wutar jahannama baza taci kaba.

Mudubi wannan falalar ƴan uwana👌

dan Allah mukula mu tsaya muneme ilimin da zai affanemu duniya da lafira.

Annabi yace idan kanason ka gane cewa kanason Allah da manzon sa to katsaya ka duba da kyau me kafi kusanci da shi aryuwar ka.

Ilimin addini ko me.

Namanta karshin hadisin wallahi🙈😥

Amma mukula sosai idan nafaÉ—i abunda mutum yaji zafi akansa dan Allah ya yafemin.“`

#Vote
Comment
Shere

Summy M Na’ige🌸
1/23/20, 11:50 AM – +234 706 211 8047: 💦💦💦💦💦💦💦
💦💦💦💦
💦💦

ƘAWAR ƳATA CE
1441H/2019M.

®�
GASKIYA WRITERS ASSOCIATION✍�
{Gaskiya É—aya ce daga Æ™inta sai É“ata burin mu faÉ—akar da al’umma domin ribantar duniya da lahira}

 ```🎐G•W•A🎐```

GASKIYA DOKIN ƘARFE�

Story & Written
By
SUMMY M NA’IGE✍ğŸ?

`Didicated`to..

~VOTE & FOLLOW 4 [email protected].~

Page 50

_📖 Ko Zainab yanzu tana da yara biyu dayeke haihuwar zamani ce tayi.

Nabila ce dai ko ɓatan wata bata taɓayi ba,sunyi yawun zuwa hospatal har sun gaji amma har yanzu baa dace ba.

Ƴan uwan mijin ta har sun fara yimata ƙurafi akan haka,ko mijin wata rana yakan nuna mata shi aure zai ƙara dan haihuwa yake su.

Tayi kuka har ta gaji tayi yawo hospatal har ta gaji amma ba’agane komai.

Daddy har wajan germany sai da ya kaita aka duba ta amma baaganu komai ba.

Daddy da Fatima sai da suka shekara huÉ—u suka dawo da Æ´an yaran su gwani ban sha’awa.

Bayan sun dawo da ɗan lokaci kaɗan sai Maram da Nabila da Zainab da Ummi da Kulsum suka zo wajan Daddy suka bashi haƙuri akan ya maida Mumy ɗakin ta har da kukan su,kuma suka ba Fatima hakuri akan sukayi mata.

Tace babu komai kuma har da ita ta tayasu ba Daddy haƙuri amma yayi kamar bai san sunayi ba daga baya ma tashi yayi ya bar musu gida.

Abu kamar wasa ba irin magiyar da baayi ba Daddy ya maida Mumy amma yaƙi dan yanzu har da Hajiya Saa tayi masa magana amma yaƙi ko ya saurare ta inda akan maganar ne.

Itako Mumy ba wanda bata aiko masa ba amma yaƙi ya saurare shi ba irin magiyar da bata yi ba.

Fatima ce data Daddy bashida niyar maida Mumy dan haka itama ta bar masa gidan sa tace bazata dawo ba har sai ya maida Mumy É—akin ta.

Dan yanzu Mumy abar tausayi ce dan yanzu idan ka ganta sai kayi mamaki sosai ta sauya dan a islimiya ta haÉ—u da Æ™awaya masu É—aura ta kan hanya sosai take jin dadin mu’amala dasu.

Ko da Fatima ta koma gida da ƙyar aka samu Daddy ya aminta zai maida ta amma da sharaɗi daya ga abunda bai yadda dashi ba zai kura ta.

Kuma ta yadda da abun da yace.

Ba aÉ—au lokaci ba Mumy ta koma amma yanzu ba gida É—aya suke da Fatima ba,dan ita Mumy wancan gidan ta koma ita ko Fatima ya kata wani fantamemin gida da yagina mata da farko tace bata yadda da haka ba gwanda ya game su amma daga baya da yace inta aminta da haka zai maida Mumy inko bata yarda ba to sai da Mumy tayi tazama agida.

Da haka Fatima tabyadda ta zauna a wannan gidan.

Mumy ta dawo kamar wata malama dan Daddy har gwada ta yayi tayi har kawo mata yaran yake suna zomata lokaci-lokaci sosai Mumy take sasu ajikin ta dan yanzu Hasan da Husaini sun fin son zama wajan Mumy dan haka Fatima ta haÉ—e musu kayan su suka dawo nan da zama kuma idan ga gansu ayanzu zaka ce Mumy ce ta haifesu.

Abun Nabila yaƙi ƙarewa dan yanzu mijin ta aure zai ƙara Nabila tayi kuka har ta gaji.

Lokacin da suka je gidan Fatima suna fira har suka bata labarin abnda ake ciki sosai ta nuna rashin jin daÉ—in ta akan haka.

Shawara Fatima ta basu tace abari agwada na hausa ko Allah nasa adace ,sosai suka ji daÉ—in shawar ta.

Koda suka faÉ—a ma Mumy itama tayi na’am da haka Fatima ta shirya taje ita dasu wajan Malamin su na isilamiya ta faÉ—a masa abunda ake ciki.

Magani ya haÉ—ama Nabila yace taje tayi affani dashi bayan kwana biyu ta dawo.

Haka akayi kafin ma tagama anfani da shi aljanin dake jinkin ta ya bayya na.
1/23/20, 11:50 AM – +234 706 211 8047: 💦💦💦💦💦💦💦
💦💦💦💦
💦💦

ƘAWAR ƳATA CE
1441H/2020M.
RABI’U II/JAN.

®�
GASKIYA WRITERS ASSOCIATION✍�
{Gaskiya É—aya ce daga Æ™inta sai É“ata burin mu faÉ—akar da al’umma domin ribantar duniya da lahira}

 ```🎐G•W•A🎐```

GASKIYA DOKIN ƘARFE�

Story & Written
By
SUMMY M NA’IGE✍ğŸ?

Alhmdulillahi,Alhmdulillahi, hausawa sunka ce laihin daÉ—i Æ™arewa, kamar yau ne anka fara labaringa na ƘAWAR ƳATA CE amma gashi yau ya Æ™are, LABARI daya zo mana akan MOMMY,FATIMA, da DADDY….. wato har yau mata da yawa saboda ZAFIN KISHI sukan kasa yarda cewa shifa AURE lamari ne na ubangiji bana É—an adam ba, abu ne wanda tini ubangiji ya rigada ya rubuta shi sai anyi, idan ya nufi mijinki da yayi to tabbas babu tsuminki babu dabararki sai anyi auren nan, mijinki na halin Æ™ari baki isa ki hanasa ba tinda Allah ya umarce dayi, mace tayi ta faman tada hankali tana shiga malamai ta maida kanta mushirika saboda kawai miji zai Æ™ara aure, Æ™arshe duk abinda kika aikata ya zama a banza a wofi dan auren da ubanigiji ya shirya bashi da fashi, tsabagen son zuciya mace ta manta da faÉ—in ubangiji da yace yana yafe kowanne kuskure da bawansa ya aikata a garesa matsawar ya nemi gafararsa amma banda abu guda wato SHIRKA ,amma akan wata banza kishiyar da idan tazo ba zama zatayi akanki ba, ba Æ™wace miki miji zatayi ba sai dai idan ke kika so, kije ki jefa kanki ga HALAKA kina aikata saÉ“on Allah kina SHIRKA, mai-makon mace ta kawai Allah kukanta wato ta dage da ADU’A shine kawai zai zamar mata mafita saboda babu wani abinda ya gagari adu’a wlh sai dai idan baki yi ba, Æ™arshe kizo kina dana sanin da bashi da amfani saboda bazaki taÉ“a tashi ganewa ba sai lokaci ya Æ™ure maki, muna mantawa da mutuwa, muna mantawa da mutuwa,waya izubillah,duniya tana ruÉ—armu mu mance da abu uku da suke GASKIYA muna mance faÉ—in Allah mu É—auki huÉ—ubar sheÉ—an, ƘAWAYE suyi mana banzar huÉ—u ba, MUTUWA, ZAMAN ƘABARI da HISABI sun zama dole amma RUÆŠIN DUNIYA da SON ZUCIYA suke mantar damu su, a banza ilimin da tinanin mata ya gushe, idan kin hana mijinki aure a nan duniya ai baki isa ki hana shi a ALJANNAH ba, gidan da za’a bashi HURUL-EN.

ga dai yanzu darasi mun ɗauka akan Mommy, duk yanda taso ta raba tsakanin Fatima da Daddy amma haƙarta taƙi cimma ruwa, hakan ya nuna mana kenan matsawar ba aikin ƙwarai kasa a gaba ba to hanya bata taɓa ɓulle maka indai akan na sharri ne,Allah yasa mu amfana da wannan faɗakarwar taki Sumayya.

Sumy Nah ina mai tayaki murna tare da farin cikin kammalla wannan NAGARTACCEN labari naki mai cike da É—umbin DARASI tare da FAÆŠAKARWA na rayuwa, Allah ya baki ladan faÉ—akarwar da kika yi ya kuma yafe maki kuskuren da kika aikata aciki,sai mun sake jinki a sabon novel naki na gaba mai Æ™ayatarwa wanda zai nusar da al’umma zuwa ga amfana,muna godia sose da sose sakillahu biljanna,Allah ya raya zuri’a ya kuma Æ™ara danÆ™on Æ™auna ga tsakani ga mai gida._

MISS XERKS✍️.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button