dafarko dai yar’uwa kisani auren namiji ko mace mazinaci ,bashi da wani alkairi ALLAH SWT YANACEWA BA MAI SON YA AURI MAZINACIYA SAI DAI MAZINACI KUMA BA MAI SON TA AURI MAZINACI SAI DAI MAZINACIYA. KUMA ALLAH SWT YA HARANTAWA MUMUNAI YIN HAKAN. sai dai in antuba an dena aikata zinar.
Sannan in kin auri mazinaci zakigamu da wadannanmatsalolin:
1- ZAI SHAFI MUTUNCINKI: dazarar mijinki mazinaci ne to kekam baki da wata daraja a idon mutane ,da qawayenki dan ansan mijinki bamutumin kirkibane kuma kike zaune dashi.
2- JIFANKI DA HABAICI KE DA YAYANKI. imma agidan buki ko a taron mata baki isa kiyi tunqaho ba ke da yayanki dan yanzu ayimiki habaici keda yayanki,SUKAN IYA CEWA AI YAYANKUMA AHAKA AKA SAMESU YAYAN GABA DA FATIHANE MUSAMMAM YAYAN KU,NA FARI ,AIKEMA KINA BUDURWA MAZINACIYA IMBA HAKABA ME ZAISA KI AURI MAZINACI. haka za aitaimiki habaici ke da yayanki har zuriyarki andinga yimuku gori kenan.
Ko yayanki akwararo za anace musu babankudinnan da akakama da wance kaza da kaza.
3- DAUKAR FANSA AKAN YAYANKI MATA: kisani matuqar mijinki bai dainaba tozinabashice kuma yaya mata sune suke biya (inji imamu ahmad dan hanbal).
Imam shafi’i yace in kabada dirhami goma kayizinato yarka kyauta za ayi daita.
DANHAKA YAYANKI NACIKIN HATSARI.
4- RASHIN SAMUN INGANTACCIYAR TARBIYYA GA YAYANKI:domin zasu raina ubansu suki karbar umarninsa su tsaneshi ,shikuma bazai iyabasu tarbiyya ta kirkiba domin yasan yayansa sunsan bana garine ba shima.
In ba aisa’aba dasu girma suma mazan ko matan su gaji ubansu dan bai isa yahanasu ba.
5- SHIGOMIKI DA SHEGE CIKIN YAYANKI: in akai rashin sa’a za ki iya rainon dansa ko yarsa shegiya ta wata matar dayaizinada’ita tasami ciki tahaifu.KINGA YABATA MIKI ZURIYA .
6- RASHIN SAMUN GAMSHAS SHIYAR SOYAYYA. domin shidai bazai ce yana sonki 100% dan aikinsa yanuna qarya yake bakuma zaice kekadaice mace a ransaba ko yadogara da itaba kinsan qaryane kawai.
7-RASHIN GAMSAR DA JUNA A RAYUWAR AURE:
shida bai gamsuwa dake sakamakon yasabazinadamata kala kala wasu sunfiki komaI kinga ke SAI DAI YAIMALEJI DAKE KAWAI AMMA BA WAI DAN GAMSUWABA.
sannan kekuma aduksadda yake saduwa dake ko bayan kinbiya buqatarki dashi to BAQINCIKI NE ZAIRUFEKI DA HAUSHI AZUCIYA .dan zakina tuna yanzufa haka yakewa wata wacce baniba ba matarsaba kuma a daki kamarnawa akan gado yacirekaya kamar haka ZAKIJI BACIN RAI DABAKITABA JINSABA A RANKI ZAKIYI NADAMA DA DANASANI DAKIKA AURESHI.
8- ZAMA CIKIN ZARGI: kullun idonki nakansa kina zarginsa ,bakiso kiyi baqin yanmata ,bakiso kije unguwa kibar baquwa ko kiyi baquwa ,bakison akawo miki yar aiki ,inkin ganshi damace koda yar’uwarsace ranki abace.
9- BARAZANA GA LAFIYARKI:
kullun kina cikin taradadi da kada yakwaso miki wata cutar kamar hiv,ciwon sanyi da shauransu.
10- zama cikin fargaba.domin iyayen yaya zasu na zuwa gidan kasheji,WATARANA MA KARUWANSANE ZASU ZO HAR GIDANKI NEMANSA, WATARANA SHI ZAKI TARAR DAWATA A DAKINKI danhaka kotafiya kikayi kina fargaba da Allah Allah kidawo gida. Ko maikuma zaki tarar agidan.
Yar uwa wasu daga cikinmatsalolinda zaki fuskanta game da auren mutum MAZINACI.
SHAWARATA GAREKU YANMATA KOME MUTUM YAMALLAKA KOMAI IYA SOYAYYARSA DAKULAWARSA GAREKI KARKI SAURARESHI BALLANTANAMA KI AURESHI. DAN ZAI CUTAR DAKE DA ADDININKI,DA LAFIYARKI DA MUTUMCINKI DA ZAMANTAKEWARKI CIKIN AL’UMMA:
DAN ALLAH YANA FUSHI DA MAZINACI .
ALLAH YASHIRYA MASUYI YAKUMA KARE ALUMMAR MUSULMI DAGA SHARRINZINA
Dr-Nuraddeen katsina
08068962793