Hausa Novels

DARAJAR ‘YA’YANA PART ONE 1

DARAJAR ‘YA’YANA1-01
Posted by ANaM Dorayi on 11:41 PM, 08-Mar-16
Under: DARAJAR ‘YA’YANA
__________________NA ___________HALIMA K/MASHI Cikin sauri sadiya take yin komai dan bata son mai gidanta ya dawo ya sameta ba yanda idonsa yake bukata ba.Tuwon (semo) tayi mashi miyar kubewa danya, sai farfesun kafar sa, sanan ta tanadifura da nono, tasa a cikin fridge don tana bukatar yayi sanyi.Ta share ko ina na gidan fes ta wada tashi da kamshi turare, taje ta fesa wanka sanan ta bata lokaci a gun kwalliya.Kankwasa kofar da taji ne ta tuna da ‘yan yaranta, da sauri taje ta bude musu, kai tsaye ban daki tace su nufa.Wanka ta sake yi musu sanan ta shirya su cikin sababin kayansu masu kyau ta feshesu da turaruka.Ta dawo dakinta inda ta rasa wane kayane ma zata saka, a karshe ta yanke shawarar saka wani jan material riga da siket.Ta dubi kitsonta kanana da ta yarfa a madubi, sanan ta kashe daurin dan kwali. Tasan yau zata burge mijinta, musanaman da ta kalli lallen hannunta na fulawa da aka zana mata.Ta kalli agogo karfe shida da kwata, wayarta wadda ta dauke saboda rashin chaji, ta jonata chaji.Ashe garin sauri bata sa dai dai ba, don haka bata samu chajin ba har aka dauke wuta. banda haka da taji yanzu mijinta yana dai dai ina?Kwnkwasa kofar ne ya dawo da ita daga haushin rashin cajin da wayarta bata da shi, ita da yaranta suka diba da gudu don taryo mijinta.Tana bude kofar shine tsaye, sanye cikin kayan yansanda, daga ka ganshi kasan babban jami’ine, ta fada jikinshi tare da rumgume shi, amma me?Sai taga ya sabule tare da cewa sannu da gida.Cikin mamaki ta amshi ledar hannunsa tare da jakarshi, ya tsugunna yana sha kan yayan sa cikin jin dadi da kewa, sadiya ta tsaya cike da mamakin saboda al’amari da take gani a gurin me gidan nata.Abin da tasani a duk lokacin da ya dawo yakan iso ne a marmatse cike da kewarta, da ya shigo burinsa kawai ya rungumeta tsam a jikinsa kafin yaran, amma yau sai taga ita ce ta rumgume shi har yana sabulewa, lallai wanan sabon al’amarine a gurinta.To ko dai gajiya ce take damunsa?Kokuma fushi yayi ya gaji da kiranta bai samu ba?Ta dubi kanta, kokuma kwaliyarta ce batayi ba?Ta sake wai wayawa ta kale su inda yake rungumarsu daya bayan daya.Da kausar ya soma, sanan Al’amen, sai mama ta tuno yanda yake mata a duk juma’ar da yazo, ya kamata ya fi dokinta a wanan karon da ya hada saty biyu bai zoba.Abin duk ya dameta, tana tsoron kada wata masifa ko annoba ta ratso cikin kyakkawan zaman nasu, tana tuna da yadda take makale a gefen damansa sannan ya dauki mama da hannun hagunsa har cikin falonsu.Yanxu dai ba zatace ganin yara bane, domintasan yaransu sun taso sun samesu cikin wata rayuwa da suka shinfida ta shakuwa da kaunar juna.Sun saba ganinsu rungume da juna, sun saba ita da yaran suyi ta kokuwa a jikinshi, basa yin wani abu da zai kawo matsala ga tarbiyar yaransu, amma sukan rungumi junako yin falo da junan ana hira.Sun rigata shiga falo, ta shigo nan ma ta sake kallonshi, mamaki ganin ya zauna shi da ke zarcewa dakinsa, can suke zuwa ya basu tsarabarsu. Sanan ya basu ta iya ya ce su kai mata, sanan kada kudawo in na huta zanzo in gaidata, sai mu dawo tare.Su ce to Abba, su tafi suna tsallensu.Shi kuwa suna fita wata ran ko wanka baya yi zai rungumota ya ce Dear my choice a matse nake.Ya wancin lokacin sai ya samu natsuwa kafin ya ci abincin ba yan yayi wanka.Dan Aliyu mutum ne mai matsanan ciyar bukata.Cikin damuwa ta isa kusa dashi.Yaya Ali yau kagaji sosai ko?Ya dubeta me kika gani?Ta ce, baka saba zama cikin falo ba.Ya miko hannu bani ledar nan in sallami yaran nan.Ya fada ba tare da ya bata waccen amsar ba.Ta miko masa kanta daure ta nufi dakinsa da jakarsa, ya ba yaran tsarabarsu, kayan ciye ciye ne da na wasa, sanan ya mike ya nufi dakin sa.Kausar tace, abba yau ina tsarabar iya?Sadiya daga cikin dakinta ta kaso kunne taji amsar da zai ba da.Ba tare da ya waiwayo ya dubi kausar ba, yace kinga magariba ta kusa, bari in anyi sallah sai muje ko?Ya shiga daidai lokacin ta shiga ban daki dan hada masa ruwan wanka.Ta fito yana zaune bakin gado yana kwance igiyar takalminsa ta iso gurin.Da sauri ta tsugunna tare da cewa abba kausar yau kuma harda aikina zaka shigar min?Ta ci gaba da kwance takalmi tana cewa, yau duk na ganka wani iri daban, ko duk gajiyar ce?Ya ce gajiya saikace ba jami’in tsaro ba?Ta soma balle masa maballen riga, to baka jin dadin jikinka ne ko? Yaja tsaki, dan Allah ki bar ni da tambayoyinnan naki please, gabanta ya fadi, ta dubeshi da gaske yake yi fuskarshi daure.Jikinta yayi sanyi, ta gama balle botiran, ya mike ya nufi ban daki ta mike zata taimaka mashi kamar yadda ta saba, ya shiga sai ya banko kofar zata tura sai taji karar makulli yana kulle kofar.Cike da tsoro taje dakin tana kallon kanta a madubi, ko dai batayi kyau ba ne yau?Ta duba ba wata makusa, ta kara jan baki da turare sanan ta fito ta same shi yana shafa mai,ta isa gurinshi, ta ciro masa kaftani da wando na shadda mai ruwan sararin samaniya, ta ciro hular da zata dace da kayan ta ajeye masa, amma sai taga ya janyo jallabiya mai dogon hannu fara sol ya saka.Daga nan sai ta koma ta jingina da bango dan jiran ganin sarautar Allah.Ya fita, ta bishi ganin zai fita waje ta ce, tabban kausar abincin fa?A sanyaye tayi maganar.Ba tare da ya waiwayo ba ya ce, sallah zan yi tukunna.Kausar ta ce,Abba ina kayi sallar ka dawo kaje damu gidan iya, kada kaje daga can.Ya dubi yaran da murmushi zan zo muje kunji?Suka ce to Abban mu, bari muyi muma sallar.Ko da tayi sallar sake zama tayi gaban madubi tayi sabuwar kwalliya sanan tayi canjin kaya daga jan yadin zuwa leshin ruwan dorawa mara nauyi .Ba kamar ko yaushe da yake kashe waya baina zasu ci abinci wayarshi kunne kuma jifa jifa yana amsa kira.Guri daya taji dadi ya zage ya kwashi abinci kamar yanda yake yi ko yaushe, haka nan haka nan ‘ya’yan shi yana ta surutu da su.Amma ita ya dauke wuta da lamarinta har ta kasa cin abincin ma, so take ta tuno kurun laifin da tayi masa dan kawai ta bashi hakuri.Bata saba da wanan yanayin da suke ciki ba, zuciyarta ta ce ko ya ta kiran wayarki ne ba a ji?Da sauri ta dube shi.Abban kausar nasan kayi ta nema na layi naa kashe ko?Ya dubeta ban nemi layinki ba, ba wuta ne ta ce eh ba wuta.Kutashi muje gidan iya,suka mike cikin murna,Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai masu nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com Kokuma ku kasance taredamu a facebook https://mbasic.facebook.com/HAUSA- Novels-389304544597988/?_e_pi=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
Kausar ta ce,Abba, momi bata dauko hijabinta
ba.Ya ce, bata son zuwa ne, tayi aiki ta
gaji.Wanan ya nuna mata ba a son zuwa da ita
tunda ba a tambayeta ba bare a ce ita ce tace ba
za ta je ba.Sun barta cikin tunani da jimami, ta
gyare gidan musanman gurin da suka ci abinci,
tayi ta jiransu tana zaune a falo tana kalon TV
amma inda zaka tambayeta abinda ake yi a TV
din ba zata fada maka ba.Ita burinta kawai ta
san laifinta, amma ina ta tuna da cewa anjima da
yazo dole zai sauke ko mai dan tasan cewa ba
zasu taba kasancewa gado daya da shi ba ya iya
kauda kai daga gare ta.Itama zata ja aji lokacin
har sai taji dalilinsa, ganin sun kai har sha daya
sai kurum ta cire tayi shirin bacci, kayan baccin
bakake masu matukar daukar hankali, ta dora
hijabi saboda da yara zai shigo.Kausar ce kurun
batayi bacci ba, Al-Amin yana sabe a kafadar
dama, mama a ta hagu, kausar din tana biye
dashi suka shigo.Kai tsaye dakinsu ya nufa da su,
tabi bayan su yana kwantar da su, ya fita ita
kuma ta gyara su, sanan tayi musu adu’a taja
musu kofa.Dai dai lokacin kausar tana cewa
momi sai da safe, sadiya tace, Allah ya kaimu
kausar.Dakinta ta nufa ta sake fesa turare, sanan
tanufi fridge don ta dauki furarshi wadda ta riga
ta dama.Shiru ta tsaya dan ya riga ya dauka, ta
nufi dakin shi.Yana zaune bakin gadonshi sanye
da kayan bacci, laptop ce a gabanshi kan dan
tebirin da ake ajeye mai fura.Kofin yana
hannunshi yana kurbar furar, idonsa sanye cikin
farin gilashi ta ce, tace ashe har ka dauko furar
ka?Ba tare da ya dubeta ba ya ce eh.Ta zauna
kusa da shi wai abban kausar nayi laifi ne da ake
ta share ni?
Ban gane na neke ta share ki ba?Ta ce na gane
yau duk ka canza ko na ce abubuwa sun canza
kamar ba mijina ba maita rairayata?Ya dago ya
dubeta baki min komai ba.Ta dora hannunta a
kan cinyarsa, abba kausar to naganka ne ni yau
irin kamar banyi kyauba din nan.Ya kalleta Dan
Allah ki barni ina yin abu mai muhimmanci ne.Ta
ce, amma dai da aka saurare ni bai fi abin da ka
ke yi muhimmanci ba?Ga mamakinta sai kawai
taji ya daka ma tsawa,kin san me kike fada kuwa
dan Allah tashi ki bani guri a nan,ta zaro ido,
mikewa tayi ta nufi kan gado ta kwanta a ranta
tana cewa ka gama kazo ka same ni ina nan
kwance.Abin ta’ajibi ranar dai haka ya raba dare
yana harkokinshi a internet sabon abu ga Sadiya
mutumin da in yazo satin karshen mako hatta
wayoyin shi kashewa yake suna manne da juna
har sai ya tafi yana cike da kewarsu.Ko da ya
kashe laptop ya kwanta juya mata baya yayi,don
Allah babban kausar me yake faruwa ne?Dan
Allah in wani abu ya faru ne ka sanar dani zan
baka hakuri, ban saba da wanan rayuwar
ba.Cikin zafin rai wanda banta ba ga ni ba ya ce,
nace bakiyi mini komai ba, kina son dole sai nayi
maki karya ne?Dan Allah ki bar ni in huta ki barni
na ce.Ta rike kai to banyi maka laifiba me yasa
ka canza min?Nasanka kai mutun ne mai bukata
a marmatse ka ke zuwa in kayi saty daya, wanan
satyn har saty biyu kayi amma sai naga kazo
bana gabanka.Ya zoro ido to yau ban da bukata
ko dole ne?Ya ja tsaki, tashi dan Allah taf dakinki
bana son jaraba kada ki dameni.Kuka ne ya
subuce mata, ta fita a dakin tunda aka kawota
gidan yau ce rana ta farko da zata kwana a
dakinta ita daya.Dan ko haihuwa tayi basa raba
makwanci, ta fito falo ga mamakinta sai taga
kausar tsaye a falo tayi saurin dai daita fuskarta
tare da share hawayenta ta nufi kausar.Me kika
fito yi?Kausar me kike so?Ta ce, mome naji abba
ne yana fada ne, me kika yi masa?Ta kama
hannun yariyanyar suka nufi dakin yara.Kan
katifarsu ta kwantar da ita ta kuma ta kwanta a
bayanta tare da rungumeta, kausar ta sake
tambayarta momi kinyi laifi ne Abba ya ce ki fita?
kasa magana tayi don al’ajabi ne ke dankare cikin
ranta, ta danne hawayenta ta ce kausar laifi nayi
masa.Kausar ta ce, momi ki bashi hakuri
mana,’to’ Sadiya ta ce zan bashi sai da safe in ya
huce kinji?Kausar tace, eh.Sadiya ta ce ki daina
tashi cikin dare kin ji, tadinga shafa kan yarinyar
tana lallashinta hartayi bacci ita kuma ta koma
duniyar tunani tuno farkonsu.Iya mahaifiyar Aliyu
ya ce ga mahaifiyata, uwarsu daya ubansu
daya,su ‘yan asalin jahar jigawa ne, a karamar
hukumar Hadeja.Mahaifiyarsu ta rasu ta barsu su
hudu mazabiyu mata biyu, kawu Adamu da kawu
Dauda duk iya ce babbar su.Lokacin da
mahaifiyata ta na budurwa, dan haka iya ta
dauketa lokacin suna zaune a Dutse da mai
gidanta da yaranta hudu.Yaya sulaiman
yayazakari, yaya sani, sai cikin yaya Aliyu.Mijinta
ma’aikacine a ma’aikatar gona ta jahar Jigawa,
daga baya yayi ritaya inda ya dawo kaduna da
zama sana din dan uwansa dake noma.A
unguwar mu’azu ya sai gida madaidaici a ciki aka
haifi Aliyu kuma a nan aka aurar da mahaifiyata
inda ta auri mahaifina wanda yakasance
ma’aikacin gidan Raidio kaduna.Amma dan zariya
ne kuma zariyar aka kaita,yana da mata biyu da
yara kusan goma, ko a lokacin.Maimuna
mahaifiyarta ta kasance mai hakuri da juriya, duk
da cewa bai kasance mutum mai cika hakkokin
iyalansa ba.Amma bata taba kawo kararshi gurin
iya ba,don tasan iya tana da fada sam bata da
wasa.Shekarar da yaya sulaiman yayi aure
shekarar ce mujin iya Allah yayi mai rasuwa,sunji
mutuwar ta farat daya yana cikin sallah yayi
sujjada a masallaci har aka idar bai dago ba.An
dago shi sai gawa, ashe mutuwar kenan.Yaya
sulaiman koyarwa yake yi a makarantar yan mata
dake Tudun wadan wada wato Sai yaya zakari
kasuwanci a babbar kasuwar kaduna, duk da
cewa ba wani babban dan kasuwa bane,Sani
kuma da ya gama secondary sai kurum ya shiga
wurin gyaran motoci dan a lokacin babu halin ci
gaba saboda yanda karatu ya zama a kasarmu sai
yayan masu shi.Talaka yana so yake hakura.Ya
Aliyu karamin su kuma suna tallafa mashi don
ganin ya samu karatunshi, kwanci tashi suma duk
suka yiyyi auransu.Lokacin da mahaifiyata tana
dauke da da tsohon cikina don ta jima bata haihu
ba, har lokacin iya bata gane yar uwarta tana
cikin matsala ba, sai bayan ta haife ni.Lokacin da
taga komai babu, abin ci a gidan gashi ya sake
yin aure ya ciko mace ta hudu,iya ta same shi ta
ce, yanzu tsakanika da Allah Abubakar hakan da
kake yi dai dai ne?A ce ka ajiye mata babu
kulawa ba abinci badai baka da shi ba sai don
zalunci?Ya ce ai za a siyo.Tace, gara ma ka siyo
don ba zan dauki zama da yunwa ba, in an ganka
a waje kwas kwas har da mshin din hawa gareka
amma a gidanka da yunwa.A daddafe akayi suna
inda aka rangada min Halimatu Sadiya, iya ta tasa
mahaifiyata ta tafi da ita, tace ba za a bartaba
haihuwar fari ba kulawa ba,Ita kenan gareni dan
wadan can yan uwan namu sai munyi tafiya mai
tsawo kan mu gansu.Sai da mahaifiyata tayi
kusan wata shida lokacin ni da ita munyi bulbul
tamkar kada iya ta bari mutafi, amma yanda
mahaifina ke ta suntirin zuwa yana kuma turo
mutane don baiwa iya hakuri sai ta hakura tace
mu koma.Amma ta ja masa kunne sosai, to dan
saukin yanzun ba kamar da ba, hakan yasa ki
shiyoyin jin haushinta suna ganin ya fifitata shi
ko tsoron karr a dauke ta ne don iya ta tabbatar
masa in tazo taga ba daidai ba to zata tafi
damu.Shakarata biyu ta sake samun wani cikin
tun yana karami take fama da laulayi iya tana
zuwa tare da yayanta akai akai suna duba
mahaifiyata tare da kawo mata abubuwa.Iya taso
ta tafi dani amma lokacin an ce inna da kalafucin
uwa, kulafaci gareni sosai ta hakuraKu ziyarci blog
dinmu domin karanta Littatafai masu
nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?e_pi=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
Gurin haihuwarta kuma taji jiki da kyar ta haifi
yar bubu rai.Sanan itama jini ya balle mata ya
dinga zuba kafin aje Asibiti rai yayi halinsa, ance
iya taji mutuwar nan kaman me.Bayan anyi
bakwai aka raba dan abinda ta bari sanan iya
tace ba zata barni ba dani zata tafi da kyar
mahaifina ya yarda don shima yaji mutuwar yayi
kuka tamkar ranshizai fita , to mafarin zamana a
gun iya kenan.Na taso cikin gata da tarbiya duk
da irin son da iya take yi min, bai sa ta kasa bani
tarbiya ba.Lokacin da aka kawoni gidan yaya Aliyu
yana shekararshi ta karshe a makarantar kwana
ta barewa kwaleji dake zariya.Sam yaya Aliyu
halinsa ba iri daya bane da yayyansa, don su
suna da sakin fuska da fara’a, amma shi kullun
rai a hade ta bakin iya in tana masa tsiya takan
ce na rasa inda ka gado wanan halin naka na
shegen miskilanci, kullun cikin bacin rai sai kace
jakadan yan wuta. Tunda nake gidan bai taba yi
mun wasa ko hira ba, magana in ta hada mu to
bata wuce yazo bai ga iya ba, yace Sadiya ina
iya?Tare da haka ba shi dai raini ko rashin kunya,
sai dai kafi ya ga saurin fushi gami da zafin
zuciya. Yanada matsananciyar tsafta da ibada Iya
na yaba masa a nan, tunda na taso Allah baitaba
nuna mun bacci iya na dare ba, sai dai na rana,
bayan azahar. Duk lokacin da na farka zan ganta
tana yin nafilfilu.
Yaya Aliyu akwai iya saka kaya, bani manta
kawayena in sun biyo mini makaranta suka ganshi
sai kiji suna cewa, sadiya yayan nan naki dan
kwambo ne, ya cika yanga gashi baya
fara’a.Nakan ce kurufa mini asiri kada yaji.Burin
yaya Aliyu aduniya bai wuce ya zama police ba,
kalmar da Iya ta tsana duk lokacinda ya ce mata
shifa in ya gama karatunshi zai shiga makarantar
horar da yansanda.Sai ta ce masa ya daina
wanan tunanin don ita bata son dan sanda, wai a
nata ganin sharri kullun ake koya musu, kullin
suna kan titi suna karbar cin hanci.Wani lokacin
tace, dan sanda da aka ce ko ya mutu gawarsa
tana fita da ban, dan baki take to ban amince
ba.Shi kuma sai yace, iya kiyi min adu’a buri na
kenan zancen zancen ace kaza kaza duk sharri ne
babu ma’aikatan da babu na gari, kuma babu
inda ba battace.Kimin adu’a in zama mai kawo
gyara a cikinsu kuma in na zama dan sanda in
sha Allahu sai kinyi alfahari dani.Takan tabe baki
ta ce, uhm ni rabu dani da wanan zancen, ni dai
insuna yi sauraransu kurun nake yi, don sam in
yaya Aliyu yana fira da iya bana sa baki, domin
tsawa zai daka min ko ya harareni, haka nake
rayawa a raina ba wai dan haka ta taba faruwa
ba.Iya tana yin wainar saidawa a cikin gida,
muna yin ciniki sosai, wani lokacin har da
sha’anin buki suna ko walima duk muna yi da
sana’ar ta take yi mana dawainiyar karatu ni da
yaya Aliyu, sai dan abin da sauran yara suka
kawo mata.Dan suma yanzu ko wanensu yana
nan da dawainiyar iyalansa, karatun ya Aliyu
shine mai cin kudi, dan Alokacin yana karatun
digree sa ne a jami’ar Ahamadu bello dake
zariya.Ku ziyarci blog dinmu domin karanta
Littatafai masu nishadantarwa
Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?e_pi=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
Yana karantar (Engineering) ban san yanda zan
kwatanta muku ra’ayinsa ba, amma shi mutum
ne mai babbancin hali da ra’ayi.Bayan ya
kammala karatun sa ne ya dagewa iya yayyinsa
shifa sai yaje police Acadamy, wato makarantar
horar da manyan yansanda dake wudil jahar
kano, dakyar ya sha kansu.Ko da yake har sai da
kawunsu kannan iya dake Hadeja,Kawu Adamu
ne yaje har gida ya lallashi iya.Bayan ta yarda
tace, to ita fa bata da kudi,yaranta kuma suna
fama da iyalansu, dan haka yaje ya nemi
kudi.Aliyu ya ce, iya ai na fada miki asaida gona
ta, ta gadonmu da aka raba mana.Nan ma da
kyar ta yarda kawu Adamu shineya saida gonar
Aliyu yaje ya amsa, haka yayita zirga zirga
tsakanin kano da kaduna har sai da yayi nasarar
shiga police Acadamy.Ranar farko da yaxo ni
kadaice ina cikin wanke kayan waina bayan mun
tashi, iya bata nan taje kai kudin kayan miyan
wainar gobe, sai kurum naji sallamar sai naga
mutum tsaye kyam da kayan dan sanda riga blue
mai haske wando baki, ga wanan takalmin na su
da hula.Nikuwa dama gani da tsoron Dansanda,
sai naji cikina yana kugi, fuskarshi daure yace,
bakinki yana ciwo ne, bakya iya amsa sallama ko?
Cikin in-ina nace, wa…alai…kassalam.Ya zuba
min harara, yau ne kika fara ganina ne da har
zaki tsareni da idanu ko na can za maki ne?Na
sunkuyar da kai, a’a ya nufi dakin nace bata nan
ta je wurin Isa mai kayan miya, ya ciji ya tsa to
dauko min makullin dakina najena duba inda na
san iya tana ajewa na dauko masa da zan bashi
sai da na dan rusuna.Ya amsa ya nufi dakinshi
nazo na karasa wanke wanken na gyara gurin ya
fito cikin gajera wando da yar T-shirt irin ta
yansanda,Ina cikin kicin zan dora tafashen kashin
waina, yace baki san mutun yazo kiyi mai tayin
abinci ba, kenan ina ganin rowa zakiyi?Nace nayi
zaton ko kana azumi ne, na ga kullun kana yin
azumi,yace, oh, dama kina samun ido ne har kika
san cewa kullum ina Azumi?To yau ban yi.Nace,
duk abincin ya kare sai sauran tuwo kuma baka
cin dumame, sai dai in ko na dafa maka wani
abu.Yace barshi nasha cornfilakes,ya juya ya nufi
dakin sa.Na sauke ajiyar zuciya ban san meyasa
ba yaya Aliyu in yana guri bana so in tsaya a
gurin sai in ga duk ya cika gurin,gashi tsananin
tsoransa nake bai dai taba duka na ba watarana
ne dai da yake iya gadanga take ce masa sai tace
in kira mata shi, ni kuma naje nace iya ta ce kazo
gadanga.Wata tsawa da yayi min kadan ya rage
in saki fitsari, ya dora yatsinsa a dan manuni a
goshi na.In kika sake ce min gadanga sai na
zaneki tas kinji ko?Jikina yana bari nace, kayi
hakuri.Don tsoro lokacin har fitsari nayi a
wando.Lokacin da iya ta dawo tai murna da
ganin autanta, nan suka zauna suna yin fira, cikin
hirar ne naji tana yi masa zancen aure, inda ta ce
gadanga dan Allah ka nemi matar aure kasan
shekarunka nawa yanzu?Yayi dan murmushi ni
kwan nasan shekaruna, muke nan kullum cikin
rubuta date of birth ba dole in rike shekaruna
ba?Talatin da uku ne kacal.
Iya tayi dariya talatin da uku shine kacal?Ai dai
cikin sa’anninka ina tsammanin kai kadai ka rage
ba kai aure ba.Ya ce iya ba ni kadai na rage ba,
kin manta da usman?Ta ce, usman bikin shi kafin
Azumi ba kuyi waya bane?Aliyu ya zaro ido, iya
da gaske?Tace, ko jiya na kira shi na fada masa
yau zan shigo shi ne zai ki sanar dani?Iya ta ce
kila sai kazo din za ka ji zancen.Ya ce, iya kiyi
adu’a kawai amma ayanzu ba mata a ga bana,
kokari na in hada wanan course din nawa.Ta ce,
Allah ya taimaka.Ya ce sauran mu wata shida.Ta
ce, to Allah yasa a gama cikin nasara, ni dai fata
na ka zama mai gaskiya da amana, kayi aiki a
kasarka da kishi.Ya ce in sha Allahu, na gode.Duk
ina jin su har suka gama ya dube ni ita waccen
sunyi jarabawar J S. C.E din?Iya ta ce, tin yau she
har sun amso yan zu kici kicin shiga SS din ta
muke yi, ya ce zo ki bani saka makon na ki in
gani, dan nasan bawata kwanya ce da ke ba.Iya
ta ce, in ji wa?Sadiya boko da islamiya tana da
kokari.Na dauko gaba na yana faduwa na bashi
ya duba sanan ya kalleni babu laifi, amma kina
jin turanci?Na sunkuyar da kai, amma ban iya
bada amsa ba.Ya ce shirmen yaran hausawanmu
kenan, kuna jin tsoro ne kada kuyi ba dai dai ba
ayi muku dariya, to ai gara ayi muku dariyar
sanan a gyara muku.To ni dai daga yau kada ki
kara mun hausa.Har in koma duk kuma zuwan
da zanyi in baturanci zakiyi mun ba bana son jin
maganar ki.Iya ta ce, kuji mun fin karfin hali
gurin gadan ga, wanan ai mugun horo ne.Yare ba
na uwarka ba, ba na ubanka ba kace dole sai tayi
maka magana da si.Ya ce, in ba haka ba yau she
zata iya ga yanda zamanin namu ya zama sai da
karatu, ko da ta gama scondary zaki mata aure?
Iya ta ce, tana samun miji zan sallamata, don
haka kar ka takura mata.Ni dai nayi ciki na barsu
nan suna ta jayayya, yana cewa ilimi ko dan
tarbiyar yara ai ko ni ba zan auri matar da bata
ta shiga jami’a ba.Iya ta ce Allah ya taimaka ni
tawa tana samun miji zan turata can gidan
mijinta shi ne babbar jami’ar ta.Ku dai yan
zamani baku da magana sai dai in kun tashi aure
kun fi son yan boko sabo da tarbiyan yayan ku.To
amma kada ka manta ni banyi boko ba, amma
duk in da kuka shiga yabon ku akeyi ana sha
awarku.Aliyu yayi dariya, to iya in kin lura ai
baban mu yayi boko, kefa kika ce mun lokacin su
yaya sulaiman suna yara sun zo da home work
shi yake musu.Nima lokacin da na taso sune suke
yi mun ba, tace to wanan ce tarbiyar?Ban ce ilimi
baya cikin tarbiyya ba, amma bashi ne
gundarinta ba.Gun darin tarbiya shi ne ka dora
dan ka kan hanyar Allah da monzo (S. A. W) su
rinjayi komai a kan mazaunin shi.Sanan ka cusa
musu Tauhidi su iya rike Amana,Cika
Alkawari,Tausayin na kasa da taimakonshi,
Girmama na sama, in dan ka ya san wanan sai
ka hada masa da ilimin zamani da na adini shi
ne tarbiyya.Kai in dan ka ya san wadancan ya
rike ko bai je boko ba zai yi rayuwa
ingantacciya.Aliyu ya ce, haka ne zancen ki Iya,
Allah ya sa muma muyi tarbiyar yayan mu kamar
yanda kuka yi mana.Ta ce ameen.Ina da ga ciki
ina jin su na ce, in dai Iya ce duk musun ka da
gardama tana yi maka baya ni sai ka
fahimta.Abin da ya bani al’ajabi da mama ki, da
dare na je kai masa abinci dama fakon sa na yi
tayi dan ba zan yar da wata magana ta hada mu
da shi ba, tunda ya ce sai da turanci, niko dan
tsinta tsinta na iya.Dan haka ina ganin shigarsa
ban daki na dauki abincin na nufi dakin sa na
ajiye zan fita sai na hangi wata mujalla can kan
katifar sa, ni kuma da shegen son kalon hotunan
yan film.Na zata irin tasu ce yan fin din India, sai
na koma na dauko na bude jiki na ya dauki
tsuma ganin mata tsirara.Da sauri na rufe wato
dai mujallar ta tsiraici ce, na sake bude wani
shafin da sauri na rufe, ina fitowa yana isowa
kofar dakin.Ya ce cikin harshen turanci me kike
so na cecikin hausa, dama abinci ne na kawo
maka.Ya matso ya damki kunne natamkar zai cire
shi.Ba na ce kada ki kara yi mun hausa ba?Nayi
shiru dan ina tsoron yi masa turanci ya ji ba dai
dai ba ya ci uba na.Ya sake matse kunnan, cikin
turancin da zaniya na ce yayi hakuri.Ya saki kin ci
sa’a daga yanzu ba hausa tsakanina da ke.Duk
cikin turanci yake maganar.Ni dai nayi daki ina
Al’ajabinshi, mutum kamar na Allah ashe dan
iska ne, ya tasa hotunan batsa yana kallo.Shi
kuma da ya shiga dakin sai yaga kamar an jawo
mujarlar daga inda ya ajiyeta, a ranshi yace wato
dai yarinyar nan ta bude mujallar nan kenan,In
ko haka ne ban ji dadi ba, amma sai wata zuciyar
ta ce, kada ka zargeta, domin bata da rawar kai,
tsoranka ma takeji ba zata taba maka komai ba,
sai kurun ya samu natsuwa tare da gaskata
hakan.Kwana biyu yaya Aliyu yayi ya tafi, niko
cikinkwana biyun nan binshi nake da kallon
mamaki.Bayan tafiyar shine na samu ci gaba da
karatu na a makarantarmu ta maimuna
gwarzo.Ku ziyarci blog dinmu domin karanta
Littatafai masu nishadantarwa
Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?e_pi=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
Kwanci tashi su yaya Aliyu an kammala wanan
karatun, buki sosai akayi ko na ce walima dan su
yaya Sulaiman su har can suka je nan gidan mu
kuwa mun aikatu.Anyi wainar shinkafa, da su
zobo da kunun zaki, daga can suka turoshi
kaduna (headquarter) a matsayin A. S. P Aliyu
Tukur.Ranar da ya zo gida na jima a uwar daki
ina tunanin fitowa saboda tsoron maganar da zan
masa da turanci, gashi a fallon iya suna fira.Na
zauna ina bitan abin da zan fada masa da turan
ci, can iya ta kwalo mini kira na amsa, ta ce me
kike yi?Na fito, ya kalleni dama tana ciki, kin wani
kunshe kamar wani munafiki?Na ce, sannu da
zuwa. Cikin turanci na yi maganar, shi sai lokacin
na tuna mai da batun wani turanci.Ya kalli iya
sanan ya kalle ni ya amsa, na ce ina taya ka
murna, ya ce ya gode.Ya tambayi nawa karatun
na ce lfy lau.Da sauri nayi waje ina tsoron kada
ya daukowani zancen da va zan iya amsawa ba, a
rai na na ce, baka sanan wannan ba na fi sati ina
haddar su.Bayan na fita ya cewa iya, to kin ga
dai yarkita soma zama baturiya, iya ta ce, eh, ai
hakan yana da kyau.Tunda ya dawo kullun
zancen shi da iya ba ya wuce kayi aure gadanga,
ka fito da mata sai dai in bai zo gidan ba,
kokuma bai zo mata fira ba.Har ta kare ta ce yaje
gidan hajiya talatu ya nemi diyarta Jamila, yace
iya kiyi hakuri har inga wacce ta yi mun da idona,
bana son cushe cushe.Ta ce, duk fadin unguwar
Mu’azu har yau baka ga wacce kake so ba?Sai ya
ce, ina nan dai ina binkitawa, har dai ta hakura
ta zura mashi ido.Daga baya naji suna hira da
yaya sulaiman wai ta sama mashi magani tana
ganin kamar bashi da lafiya, niko da naji wanan
xancen lokacin cewa nayi a raina, ras yake kila
ma neman matan shi yake yi a waje tunda mai
ya hada mara lafiya da hotunan tsiraici?Kuma
bayan nan ina zaton yana kalon fina finan tsiraici,
don lokuta da yawa in yana kallon in nayi sallama
dakin zai kai abinci ko wani abu sai yayi sauri ya
kashe, sanan ya ce in shigo.In kaset din arziki ne
menene na kashewa?Amma na sa a raina wata
rana sai na kama shi.
Haka kuwa watara na xan kai masa abinci darana
lokacin aikin dare yayi da safe ya dawo,Iya kurun
ya gaisar muna aikin waina ya shige daki ya
kwanta.Sai kusan sha biyu sanan ya farka,
lokacin Iya ta tafi gurin sabo mai shikafar waina,
ta ce in ya farka in kai masa ruwan zafin shida
waina in kuma bredi zaya ci to in kai masa.Ya fito
ya shiga wanka, da sauri na dauki dan flask din
sa na ruwan zafi na nufi dakin, ko mai a kashe
yake amma na san zan kunna in gani tunda
wanka ya shiga saboda shi mutum ne mai
dadewa a wanka.In dai ya shiga tamkar zai canza
fata, don haka ina lokacin sallah ya katato xai
shiga ban daki iya kance bari muyi alwala dan in
ka shiga sai lokacin salla ya fita baka fito ba.Na
jona komai ya kawo na ce oji bulumme can kasa
dan muna funci aikuwa CD yana gama login sai
ga mata da maza tsirara suna aikata masha’a.Da
sauri na kashe na fita naje na ci gaba da aikina
abin da na gani ya girgiza ni kuma naji haushin
kaina da karan bani na.Na fito na dauki waina da
bredi naje nayi sallama ya ce in shigo na shiga na
ajiye xan fita ya ce tsaya, me kika shigo yi nan
dakin?Gaba na ya fadi na ce ni flask na kawo, ya
ce daga nan sai kika yiyi me?Cikin in ina na ce,
banyi komai ba ya Ali.Ya tsareni da idanu, bashi
da tabbacin nayi wani abu amma yana shigowa
yasan an shigo.Ya kalleni, jiki.Na fita sanan na
harari dakin na tafi.A raina na ce dan iska, amma
wani lokaci sai ya kure wa’azi sai kace na Allah.
Kwanci tashi ba wuya, muna cinye kwanakinmu
har mun kammala (SS3) mun zana jarabawa
kuma lokacin ya zo dai dai da saukar karatun mu
na alkur’ani.Munyi komai cikin nasara, kuma nayi
walimata a gidan mu inda iya ta matsawa ya
Aliyu sai ya buga mun memo wanda zan rabawa
kawaye na.Sauran yayyansa ma sun taimako,
baba na kuwa da naje zaria na fada masa dubu
biyarya bani wai inyi hakuri da yake ina zuwa
danhutu can wani sa’in iya tace inyi sabon dinki
da kudi na.Dangi kam sun xo babu laifi, har yan
uwa na na zariya, babanmu ya zo da su komai
na yayi babu laifi.Da yamma ni da kawata Aisha
muna kwashe kujerun da muka zauna akai
mukayi walima a waje da kawaye na.Mun hada
su guri daya sai naga guda biyu wanda ya Aliyu
da wani abokin sa suka zauna su na hira.Ta ce,
kije ki amso wadancan cikin zolaya tayi maganar,
don tasan ina jin tsoron shi.Na ce, ke kije ki
amso.Tayi yar dariya bari inje.Tayi tamkar zata
nufi gurin sai ta fasa.Muyarshi ta katse maganata
da zanyi lokaci daya kuma gaba na ya fadi, Ke!
Na wai waya, zo nan.Naje na rusuna na gaida su
cikin in ina ya ce, ke daga jin maganar ki baki da
gaskiya ko?Na ce, a a.Ya ce, to me nene nayin in
ina din?Nayi shiru, ya kalli abokinsa ga ta.Abokin
ya ce, ina yi muki murna da yin saukar alkur’ani
mai girma, Allah yasa anyi na tsoron Allah.Na ce,
amin.Ya Aliyu ya ce, jeki dama murnar zaiyi
maki.Ina tafiya ya kalli Aliyu ya ce, kanwar nan
taka tayi fa.Ya Ali ya ce, ok, iskancin naka har
agida ma zaka yi?Auwal ya ce bada wani abu na
ce ba, cewa nayi tana da kyau.Kai da ma ka
shiga kayi yar gida tunda duk matan dake sonka
baka kallon su.Ali ya ce don me zan tsaya kallon
yayan mutane, alhalin na san cewa ba auran su
zanyi ba?Auwal ya dan yi masa dukan wasa a
kafada tare da cewa, ko jiya munyi gulmarka da
Sajen Bello, wai ina ma shine mata keyiwa wanan
shishshigin, da sai ya more kuriciyarshi son
ranshi, amma kai kullun cikin Azumin dole, in
kaga mata sai kace kaga Abokanan gaba.Aliyu ya
ce, ban ga anfanin zina ba, koda ba haramun
bace mutum ya gujeta, ya kyamace ta, dan kare
kansa daga cututukan zamani.Ina fada maka ina
da kyama ba zan iya hada jiki da wayan can ba,
kuma dole in naga mata in hada rai tun da ba
halali na bane, kuma ba muharramai na
bane.Kullun dai ina adu’a Allah ya bani mace ta
gari mai kamun kai, kuma da kuke bin matan
Allah ya shiryeku, kai gashi kayi auran ma amma
ba ka daina ba.Kayi hattara duk abin da ka shuka
shi zaka girba, kana kallo wani can zai bata
rayuwar yayan ka yadda ka fada ta yayan
wasu.Ku ziyarci blog dinmu domin karanta
Littatafai masu nishadantarwa
Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?e_pi=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
Auwal ya ce , ka samu cikin adu’a abin ne
dawahalar bari, mata ne nishadin rayuwa, hira
da su ma a kwai dadi ne.Tsaki Aliyu ya ce in kaso
kaji dadin ba?Ni kuwa bana fatan in ji dadin fira
da mace wadda ba tawa ba, ina nufin
halalina.Auwal ya mike, bari ni in tafi kai dama
malami ya kamata ka zama ba dan sanda
ba.Sam Aliyu be mike dan raka shi ba, daga nan
suka yi sallama.Shi kam tunani ya shiga, shima
yana sabo wajen kallon fina finan batsa da
karantar mujallan batsa, duk da cewa bai taba
aikata zina ba ya san wanan laifi ne babba.Kuma
in mutum bai daina ba wata rana zai kai ga
aikata zinar, kuma tunda Allah ya rufamini asiri
tsawon lokaci yana yi ba wanda yataba ganinshi,
ya kamata ya daina.Ya tuna lokacin da ya fara,
wata rana yaje dakin su Auwal da rana lokacin
suna jami’ar Ahmad Bello ta Zaria, ya ga wani
novel a dakin ya dauka ya karanta, ashe na batsa
ne.Daga lokacin sai yaji yana so ya gani, ya ko je
wani shago a kasuwa ya siyo kaset din tare da
mujallar tun daga nan lokaci zuwa lokaci sai ya
siya ya kalla, sanan ya kona su ya sake siyan
wani.Shi da kanshi ya sha fada wa kanshi cewa,
yanda yayi Imani zai tsaya gaban Allah haka yayi
imani za a tambaye shi yanda yayi ya sami kudi
da kuma hanyar da yabi gurin kashe su.Me zai ce
game da wanan kudin da yake sawa yana siyan
batsa?San nan baya karanshi da komai sai karata
da masu hankali?Lallai wanan abune da ya
kamata yayi makansa tun kafin ya mutu.Ya mike
tare da kudircewa daga yau ya tuba,ba zai kara
ba.
Dai dai gwargwado ba xa a ce bani da kyau ba
tunda Allah bai halicci mumuna ba matsawar
mutum yana da kyan hali, balantana a ce mutum
musulmine.Aina ya ga kyau sai dai kuma in ba
tsafta, ni fara ce sol amma bani da dogon
hanci.Wanan baisa fuskata muni ba, haka
idanuwa na matsakaita ne, ni mutum ce mai
tsananin kwalliya ko alwala nayi sai na sake
sabuwar kwalliya.Haka nan iya bata gajiya da
siyan mun kayan kwalliya, sanan bata ganin
bekena duk lokacin da zan bata gurin kwalliya.A
cewarta ya mace doki ce sai da kwalliya, abinda
kawai bata yarda da shi ba shi ne, ayimini dinkin
da zai nuna surata, nan ne zata ce ba zata bada
kwamasho ba gurin yada zina.Ta ce, shigar da
yawancin mata keyi ita ce ke haifar da zinace
zinace sannan zata zuba ko nawa ne ta yankan
mini yadin hijabi amma mayafi dai sai dai inyi
asusu in siya.
Shima din ban isa in siya karami ba sai babba,
kuma mai kauri ban taba jin haushinta ba dan
nasan tana kare nine daga afkawa cikin
shaidan.Dai dai misali ina da farin jinin samari
masu sona, dan ma iya bata bari in fara fita
zance da wuri ba sai da na kai SS2 duk masu
zuwa gurina da aure suke sona.Sai dai ni cikinsu
banga wanda yayi mini ba irin injishi kane kane
cikin raina din nan ba, fada haka iya take cewa
maza ki tsaya ruwan ido daga karshe kowa ya
gudu kizo kina nema.Ai yanxu lokacin ya mace
mai hankali ake dubawa wanda yake da hali mai
kyau sanan ba jahili ba kuma ya kasance yanada
yar sana’ar da zai rikeki, to ki kamashi.Allah
shine mai azurtawa, in da rabo sai kuyi arzikin
tare, ke in ma baku samu anan ba to ya baku na
gobe kiyama.Yawan yi mun wanan nasihar yasa
nake ganin zan iya tsaida Idris kuma zan iya
auransa amman sai mun zauna da kawata
aminiyata Aisha.Mun zauna da ita ita ma tace,
gaskiya duk cikin masu sona babu kamar Idris a
hankali.Mun yanke shawarar in tsaida shi ita
kuma dama akwai makocinsu Bello dake sonta.Ku
ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai masu
nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?e_pi=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
Wata safiya Iya tana kwance ba lafiya dole na
fasa zuwa makaranta tunda mun riga mun hada
kullun waina, sai kuma ciwon cikin dare.Ya Ali ya
shigo da shirin fita, don bai san bata da lafiya ba
sai da ya shigo dakin, ya girgiza da ganinta
kwance cikin bargo dakyar take magana.Arude ya
ce, ya babu lafiya ne?Tace, eh, yace meyasa ba a
tashe ni ba a gida fa na kwana?Ita wacen
sakaryar ba sai ta fada min ba.Iya ta ce ni na
hanata ta ce bari ta taso ka, ya cire hula, bari
muje Asibiti, bari in samo mota, ta ce, a a naji
sauki.Fita yayi sai gashi da likita wani dan nan
unguwar ya duba ta sai gashi hadda ruwa a dora
mata.Ranar dai bai fita bahar rana, bai taba
birgeni ba irin ranar, duk wani abu sai yayi, hatta
bata magani a baki da abinci sai gurin la’asar
sannan ya fita.Su yaya Sulaiman,Zakari da Sani
duk sun zo da matan su, sanan makota na ta
zuwa.Da yaje gurin aiki ya bada uzirin shi sai ya
dawo kusan shabiyun dare, jikinta yayi sauki.Ina
jiyo hirarsu,rokonshi take yayi aure ta ce Aliyu
bani da wani burin da ya wuce inga auranka, kai
na fuskanci kafi son sai na mutu sanan zakayi
aure.Jikinshi yayi sanyi, dan ya kasa tuna ranar
da ta kira shi da Aliyu, cikin tautasar murya da
lallashi ya ce, zan yi iya, in sha Allahu kina
raye.Ta ce, kayya, gadanga kullun haka kake
cewa, ni dai ai tuni na cire rai ka tashi katafi na
yafe maka Allah yayi muku albarka kai dasauran
yan uwanka.Yarinyar nan sadiya dan Allah ko ban
tashi ba kada ku bari ta koma zaria ta zauna
gurin wannan yaron hardai ta sami miji kuyi mata
aure.Ya ce, iya ke ce da kanki zaki aurar da ita
insha Allahu, ta ce shi kenan tashi kaje ka
kwanta.Hankali tashe ya fita bayan ya tai maka
mata ya kawota cikin daki, na tashi idona
naxubar da hawaye, na taimaka mata muka
kwanta.Ina kuka kasa-kasa ta ce,Sadiya lafiya?
Tace iya bana so inji kina cewa zaki mutu ki barni,
ta ce in fada ko kar in fada sadiya ba zan kara
lokaci ba sai dai in ajalina bai zo ba.Da kyar bacci
ya daukeni, lokacin iya tayi nisa da bacci.Shima
Aliyu tun da ya koma dakin shi fa ya kasa ko
zama, lallai dole ne ya nemi mata, sai dai
matsalar shi ta ina zai fara?Bai taba yin budurwa
ba, bai taba soyayya ba, shi kuma yana ganin
kamar raini zai ja masa in yaje kofar gidan su
yarinya.Amma bari gari ya waye yaje wajen
usman amininshi.Kafin ya wuce masallaci sai da
ya fara lekowa dakin mu ni da iya duk muna
sallah, sanan ya wuce,dan Allah ya kawo mata
sauki a cikin daren daga masallaci gidan Usman
ya wuce, ta wya ya kira shi cewa gashi a kofar
gida,Usman ya ce, lafiya?Aliyu ya ce, lafiya ba lau
ba, fito kaji.Da sauri usman ya bude gida ya fito,
sama sama suka gaisa.Usman ya ce, aboki lafiya?
Aliyu ya ce ina fa lfy, jiya tsohuwa ba lafiya, ta
fara bar mun wasiya, sannan tayita jaddada min
burinta kawai nan duniyar shine inyi aure.Usman
yace aboki ba ita kadai ba, ni kaina buri na
kenan, to tunda kaga tsohuwa ta tsananta gara
kayi ko kwa rabu lafiya.Aliyu ya ce, ai baka sani
ba, tunani na yanzu ina zanje nemo mata?Na
rantse maka banda budurwa…

Related Articles

Zaharaddeen Shomar
Whatsapp 08168575100

DARAJAR YAYANA1-02
Posted by ANaM Dorayi on 08:55 PM, 09-Mar-16
Under: DARAJAR ‘YA’YANA
__________________NA ___________HALIMA K/MASHI Usman yayi yar dariya sanan ya ce, ni da zakaji shawarata wanan sadiya ta gidanku?Aliyu yace, ah haba?Usman yace, naga yanda ake yabon hankalin yarinyar, ko a gida tana da matsalane? Aliyu ya ce, sam ko a gida bata da matsala gaskiya, amma ban taba jin koda alamar sonta ba, to wanan yarinyar ma ina ganin ta tsaida wanda take so, in ma ba ta tsayar ba sai inga ta yi mun yarinya.Shekarunta sha bakwai fa yanzu in ban cika ma ba, usman ya ce, dai dai.Nafi son wacce ta shiga makarantar gaba da scondary a kalla ta mallaki hankalinta, ta san yadda zata kula dani sai nine zan koma in kula da ita.Usman ya ce, ba yaran yanzu ba, tunda kaga bata yiba in kaga wata da tayi maka ko a unguwarku ko a kafatanin unguwar mu’azu ka fada min yanxu anjima sai muje, kaga yanxu sai kaje wa iya da kwarin gwiwa.Aliyu yayi shiru yana tunani can ya ce, aboki kasan Allah?Nifa ba wai ina kallon mata bane, na layinmu ma ban sansuba balle na unguwa.Usman ya ce, to aboki ka tsaya a Sadiyar mai hankalice,Sadiya tayi.Aliyu yace inda ta kaicin yake sai kuma in kirata ince ina sonta?Usman ya ce in baka iyawa bi ta sama mana ka samu iya ka fada mata kana son Sadiya, nasan zatayi murna.Aliyu ya ce, aboki daina cewa ina sonta, zadai ayi aure amma ba wai ina sonta ba, Aliyu yace kuma ba zanyi karya ba tunda banji cewa ina sonta ba,har Aliyu yaxo gida tunani yake anya kuwa zai amince cewa yana son auren sadiya? Lokacin da ya shigo dai dai na bare magani na mikawa iya, ta afa tare da kora ruwa, ya tsaya ya rike kugu yana kallon mu, tunaninshi a wanan lokacin lallai babu wanda ya dace ya auri irina, bisa hujjarshi tacewa ba zai sami matsala ba wace take tsakanin iya da matan yayanshi ba.Iya tana kuka cewa cikinsu matar yaya Sulaimance kawai ta san darajarta, kuma tabbas hakane domin sai suyi wata uku basu zo sun gaida ta ba.Ita ba wai tana kwadayin abin hannunsu ba ne, a a ko ba komai taga yan jikokinta yayi, amma Sadiya bata da uwar da ta wuce iya.Dan haka yana nan ko baya nan zata zamo a karkashin kulawarshi, burinshi yaga ya daukewa iya duk wani matsalarta, su kuma yayinshi suji da iyalinsu. Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai masu nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com Kokuma ku kasance taredamu a facebook https://mbasic.facebook.com/HAUSA- Novels-389304544597988/?_e_pi=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
Tunaninsa ya katse lokacin da iya ta ce, gadanga
ka shigo ne?Yayi firgigit, na shigo iya.Na gaida shi
na fita, shima a ranar bai iya yi mata zancen ba,
karshe ma tunani yayi ya samu yaya sulaiman
suyi shawara.Haka kuma bayan sallar isha’i ya
nufi gidan yayan nasa bayan sun gaisa sai ya
sanar dashi abinda ke tafe dashi.Yaya sulaiman
yaji dadin zancen da Aliyu yazo dashi, sanan yace
sai ka samu yarinyar ku daidaita, Aliyu ya ce, ina
ga ba sai na sameta ba, indai iya ta amince shi
kenan.Yaya Sulaiman ya ce, iya ba zata ki ba,
yarinyar ce abinji, in ta ce bata sonka fa?Aliyu ya
ce, ai nima ba wai ina sonta bane, dacewar
auren kurum nake dubawa, shi yasa.Ya Sulaiman
ya ce, shirme kenan, to kai in kaje wajen iyar ce
mata zakayi ba sonta kake ba?Aliyu yayi
murmushi ce mata kurum zanyi ina so na auri
Sadiya, Sulaiman ya ce, Allah yayi mana zabi na
alkairi.Ka bari zanje gurin iyar, duk yanda mukayi
zakaji.Aliyu ya ce to.Yayi godiya yayi masa
sallama ya tafi..Sulaiman ya sami iya cike da
karfin gwiwa, ganinshi babu wanda zaikai iya
murna kai yasan har goron albishir zata
bashi.Amma ga mamakinshi yana gama labarta
mata dalilin xuwansa sai yaga tayi kicin kicinda
fuska ta ce kaine kaga sun dace ka bashishawara
koko shine ya sameka da zancen?Yace, a a dazu
ya zo mun da zancen sai kuma naga dacewar
haka.Ta ce, to ka koma ka fada mashi ban
amince ba, kace mashi ya nemo matarshi can
itama ta nemo nata mijin.Jikin Sulaiman yayi
sanyi ya sake tausasa murya ya ce, iya ban san
dalilinki ba, kokuma akwai abinda kika hango
wanda ba na Alkairi ba?Ta ce, na farko dai kasan
halin gadanga, zuciya ce dashi ga saurin fushi, ga
miskilanci tsiya, ga shegen jin kai.Sanan na sha ji
ko in ce ya sha fada min cewa shi yar jami’a yake
son aura.Niko tawa ko secondary din bata gama
ba.Sulaiman ya ce, iya in kin duba tunda shi din
ya ce ta mashi ai ina ganin ba za a sami wata
matsala ba.Fir iya ta ki zancen, duk ta inda
sulaiman ya bullo sai iya tabi ta wata hanyar,
haka nan yaya sulaiman ya hakura ya fita rai
babu dadi.Aliyu ya sunkuyar da kai yana
sauraron sakonshi a gurin yaya sulaiman, sam bai
zaci jin haka ba, amma sai ya ce, ba komai Allah
yasa haka shine mafi alkairi, na shi ganin ba zai
damu ba, tunda dama ba wai yana sonta
bane.Sai dai kuma yanda ya tsammaci abun yafi
haka, samun kanshi yayi da shiga damuwa, ko ba
ya son yarinyar hakika ya tsananta dason
aurenta.Ya samu iya da kan shi wata safiya yaxo
gaida ta bayan yayi shirin fita cikin dakin sa.Ya
ce, iya me yasa ba zaki bani auren sadiyaba? Ta
lissafo mashi dalilinta kamar yanda ta lissafawa
yaya Sulaiman takuma fada masayaje ya nemo
mata can.Ranshi ya baci amma bai nuna ba, sai
dai cikin sanyin murya ya ce, to shikenan iya na
hakura, amma ba zan taba xuwa ko ina neman
aure ba saboda ina da munmunan halayen da
ban can canta a bani mataba,tace, ni ban ce
ba,ya ce to iya tunda ba a bani a gida ba in naje
nema a wani gida suka bani na cutar dasu tunda
ba su san hali na ba,yana kai aya ya mike tare
da cewa, sai na dawo.Ita kuma lafuzan nashi
suka hanata magana.Ita zahiri ba wai bata son
auren ya Aliyu da sadiya bane, na farko ta san
halinsa, sanan tana tsoron ta tursasa min.Kullun
Aliyu sai yayiwa iya naci amma taki ko ta ga zai
dauko zancen sai ta hade fuska.Wata safiya ina
kwance kangado ina fama da matsananciyar
ciwon mara, dama mun rabu da yin waina tunda
iya tayi rashin lafiya.Ya Aliyu ya ce, a daina yin
wainar duk wata nake wanan ciwon marar.Yaya
Aliyu ne ya shigo gaida iya, bayan sun gaisa ta
ce, har ka shirya fita kenan?Ya ce mata eh, akwai
wani case a hannunsane yana son ya kammala
dashi kafin fitowar(AC) ta ce, to Allah ya taimaka,
a can zaka karya?Ya ce, eh.Sanan yayi shiru ta
ce, da magana ne?Ta sani in har yayi haka to da
magana a bakin sa, ko da yake ta san zancen na
sa daya ne, bai wuce na sadiya ba.Kuma tana
son Sadiyar ta ji ma kunnenta in ta amince
ruwanta don haka ta ce yaya autana?Yace iya dai
maganar Sadiya, Allah iya ba maganar yabon kai
ba, ina da kamalar da za’a bani mata, ya ko ta
gidan waye ‘yar taki ai ba kyau tafini ba,ya fada
cikin sigar wasa, ta ce,duk da haka ba zan baka
ba, kai ita fa tarigata fidda mijinta.Yace dan Allah
iya ki fada mata kinji?Ta ce, au, nice ma zan fada
mata?Lallai ba ma son auran nata kake ba.Ya ce,
ni iya in na fada mata sai naga tamkar zata
rainani ne.Iya ta ce, kun ji girman kan ba?Don
Allah kayi hakuri nifa ka tayar dani,ba zan yarda
ba.Aliyu da ya gaji ya fita.Tun daga lokacin da
naji ya Aliyu ya ambaci sunana na mike zumbur
hankalina atashe,ni Sadiya yaya Aliyu yake nufi
ko wata?Kai in ko nice na more, dan gaskiya yaya
ba irin mijin da zance bana so bane, tab!Wanan
shine tsintar dami akala.A a iya kada kyi min
bakin ciki, ina jin fitarshina fito da sauri ina
kallon iya, ko zata ce wani abu, amma sai ta
shareni, na ta nufintadaga yanda na dauki
al’amarin tunda ta tabbatar naji.Ko daga irin
fitowar da nayi, ganin iya ba zatayi magana ba
sai na ce iya ta dubeni, wai ya Aliyu wa yake so?
Ta tabe baki dan Allah rabu da shi, wai ke, na
dafa kirji da karfi na furta da gaske?Ta ce, zan
maki karya ne?Na ce to iya shine zaki ce mashi
ina da wanda nake so?tace, au.Sharri nayi maki
kenan?Ina ce ke naji kina cewa kin tsaida Idris?
Na ce, ai ban fada mashi ba.Ta ce, meye nufinki
yanzu?Kina so ki ce min kina son Gadanga?Nayi
shiru tare da hade fuska, mamaki ya cikata, ta
ce, Sadiya dama can kina son Gadangan ne?Na
ce, nifa ban ce ina sonshi ba, amma ke meye
dalilin da kika ca baki yarda ba?Iya ta shiga tafa
hannu tana salati.Kin tirke nine lallai sai kinji?To
ba wani dalili bane sai na kare mutuncinki,
gadanga yana da zuciya, gadanga yana da fushi,
sanan ga miskilanci,ina tsoron ki shiga matsala,
gaki karamar yarinya, shi kuma shekaru sun dan
soma ja.Da sauri na ce iya in dai dan wanan ne
na yarda kinji?Ta ce, wai me ya burgekine a dan
sanda duk jikinki ya hau bari?
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai
masu nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?e_pi=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
Na ce, to iya gaskiya ya Aliyu ba irin mutumin da
za a ce ba a so bane .Ta ce, ni dai na ce a a ban
yarda ba.Na mike cikin fushi na fita tsakar gida,
da kallo iya ta bini, matuka ta ji mamaki
musanman ta sanni bani da rawar kai.Ni kuma
kicin na shiga na zauna banyi aune ba sai kurum
naga hawaye suna zuba a ido na, ni kaina har
naji mamakin kaina.To da bai ce yana sona ba
fa?Ranar haka na yini har dare, kusan mutum
uku suka aiko kirana naki fita, iya duk tana lura
dani tana kallona ranar bai dawo gida ba sai sha
biyun dare, sanan tunda a subahi ya fita.Yau
sam na kasa sukuni, iya sai kallona takeyi tana
salla, can bayan ta idar ta ce sadiya!Nayi shiru, ta
ce, nasan kina jina ta shi kawaiki tashi, na tashi
zaune ta ce, sadiya ina ganin baki gane nufina ba
game da zancenkike da gadanga shi yasa har kike
fushi dani.Gadanga bahogon mutum ne, ni na
haifeshi na sanshi tun yana dan karamin shi,
gadanga bashi da dadin lamari, amma in kinji
Allah ya baki sa’a.Sai dai ina so ki sani in da
wanda zaiyi farin cikin aurenki da gadanga to ya
biyo baya na,sai dai duk da haka ba zan kasa
fada maki gaskiya ba.Shawarar da zan baki kuma
ki rage rawar kai in ya fahimci kina doki kimarki
ta zube.A zaton iya zan hakura amma sai taji na
ce, in sha Allahu ba zan sami matsala ba.Ta tsura
mini ido haka kika ce?
Nayi shiru ta ce shi kenan, to da sharadi ba zuwa
kawo kara.Da sauri na ce, to,da kallo tayi ta bina
ni dai na tashi na koma makwancina ina
murna.Na zaci da safe zata neme shi ne ta fada
mashi ayi sai kurum ta share, ko da dai ya fita
da wuri, wasa wasa sam taki zancen inaji lokaci
da yawa da ya dauko zancen zata ce don Allah ya
rabu da ita.Sai dai abinda ke bani mamaki,
kullum yanda yaya Aliyu bai can za min yanda
yakemin ba , amma nakanyi uziri cewa kila sai
iya ta amince sanan za mu soma yin tadi.Cikin
haka ne har aka dauki tsawon lokaci muka shiga
shirin zana jarabawa (SSCE) duk na kori samari na
babu wani mai zuwa tunda na fada musu na
tsaida miji.Shikam ya Aliyu bai san na sani ba,
kullum ya zo gurin iya sai yayi mata nacin shi fa
yana nan yana jira ita kuma takan ce mishi kar
ya dame ta, ba ya ce ya fi son yar jami’a ba?Ya
je ya nema.Ni kuma in ya tafi wani sa’in in ce iya
don Allah ba kince kin hakura ba, tunda na
yarda?Sai ta ce min sakarya, dubi fa ko kallo baki
isheshi ba, amma duk kin tsamgwami kanki don
fitina, ni dan kare mutuncinki nake kin abin nan.
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai
masu nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?e_pi=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
Usman abokinsa yaji shiru batun maganar Aliyu
da sadiya, sai ya zo gurinshi musanman don
zancen , dama ya kirashi a waya yaji cewa yana
nan.Bayan sun gaisa usman ya ce, aboki wai
haryanxu ban sake jin batunka da yarinyar nan
sadiya ba, in mun hadu baka yimin zancen ba, ni
kuma ban tambaye ka ba.Aliyu ya gyara zama
yayi sanan ya lumshe ido don haushi ya ce,
kabari kawai abokina, haushin maganar nake ji,
shiyasa ban taba yi maka zance ba.Ya miko
hannu ya dafa gyiwar usman abokina ban taba
samun abinda ya bani matsala ba kamar
maganar yarinyar, ni abin haushi duk lokacin da
nayi kudirin hakura dazancen sai na kasa.Kullum
adu’a ta Allah ya yaye min ita daga raina, amma
abin ya faskara.Ko son yarinyar ne ya kamani?
Usman yayi murmushi lallai sonta kake yi, Allah
yasa ita ma ta soka hakan.Aliyu yace ina ruwana
da ita?Iyace kurum damuwata, in da ta amince
shi kenan, amma baiwar Allah nan wai zan cuci
yarinyar ita ba zata bani yarinya karama
ba.Ranar harda cewa na tsufa.Usman yace zanje
in sameta aboki, kada kadamu.Aliyu ya ce, ko
kaje matarnan ba zata yarda ba, na dai fada
mata ni na hakura da yin auren.
.Usman yayi ta dariya tare da zolayar Aliyu da
cewa, aboki ka dai shiga da yawa, to da ka ajiye
duk wani girman kai ka dinga kiran yarinya hira
in taga haka zata fi yarda cewa da gaske kake
yi.Aliyu ya ce ka yarda ni ba zan taba iya kiran
yarinyar ba, ko ba Sadiya ba, kuma sanin kanka
ne ban taba ba, so bansan ta ina zan fara ba.Ba
ta ita fa nake ba, in iya ta yarda tayi hakuri ta
aureni dan da cewa auren sai kuma ya ja tsaki
kada ma ta hakura.Tama ji dadin zancen ta samu
miji irina, Usman ya ce, yabon kai?Aliyu yayi
dariya aboki ka fadi gaskiya, ni da ita wa yafi
kyau?Bai jira amsa ba ya ci gaba na farko dai
kaga ita fari ne kurum ya ceceta….. Usman ya
katsishi au, wai dama haryanzu akwai
mummuna?Ni dai yanzu na daina ganin
mummunaai tunda naga alamun kai ya waye, ba
a zama da kazanta, Aliyu ya ce, haka ne, amma
wani wan wani ne a kyau.Usman ya ce, duk da
ka fi ta kyau dai ita zuciyarka ta zaba, zanyi
maka kokari, zanje in samu iya.Aliyu yace tunda
ka dage jeka din, duk yanda kukayi zamuji.
Kamar yanda Usman ya alkawarta yazo ya samu
iya wajen la’asar ina yi mana tuwo, itakuma tana
zaune a kofar dakinta.Na gaida shi sannan na
dauko masa tabarma ya zauna, na kawo masa
ruwa sanan naje na ci gaba da aiki na.Daga inda
nike ina jiyosu suka gaisa sanan ya fara yi mata
zancen da ya kawoshi.Iya dama akan batun
abokina ne da yar uwarsa sadiya, iya dukkan su
naki ne, a ganina wanan abin farinciki ne.Iya ta
tsuke fuska,Usman ina ganin kimarka, zaifi kyau
ka bar zancen nan bana jin cewa zan
amince.Usman yayi shiru yana tunanin yanda zai
bullo mata.Can ya ce, to shi kenan, amma na so
ki amince domin yana cikin wani hali na son
yarinyar nan, nasan halinshi kin san halinshi,baya
daga cikin mutane ma su magana biyu.Yayi mun
rantsuwar ba zai taba aure ba in ba Sadiya ba,
duk duniya ita yake so.Zaman shi haka nasan
yana damunki.Ta ce in duk duniya Sadiya yake so
ita Sadiyar ya tambayeta ta ce tana sonshi? Nifa
ba zanyiwa yata auren dole ba, don in faranta
masa.Daga inda nake a kicin na da ga hannu ko
nace ya tsa tamkar mai bada amsa a cikin
ajinmakaranta, sanan na kwalawa iya kira!!Ta
kalleni tare da yi mun da kuwa, shi dai baisan
dalilin dakuwar ba, tunda ya bani baya, ita kila
ya zaci laifin nayi mata.
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai
masu nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?e_pi=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
Usman ya fahimci nufin iya, shi yasa ya ce mata
Aliyu ya dinga kiran yarinyar suna fira.Ya dubi
iya, to in sha Allahu za mu tuntubi yarinyar, idan
bata amince ba shike nan.Yana fita ya dauko
waya ya kira Aliyu, bugu uku ya dauka. Usman ya
ce, Aboki da farko fara bani goron albishir.Cikin
sauri Aliyu ya ce kada dai ka ce mun
tasaurareka? Usman ya ce, in sha Allahu munyi
nasara Aliyu ya ce shi kenan sai na xo aboki,
gidanka zan sauka kaitsaye daga office yanxu ina
kan wani aiki.Suna cin abinci a falonsu Usman
yana koro mashi bayani duk yanda sukayi a
karshe yace yanzu kaga tana nufin ta yarda sai
dai amma tana so ka kira yarinyar ka nemi
amincewar ta.Aliyu ya tsirawa Usman ido, sanan
ya ce, ai wanan shine mai wahalar, gaskiya a boki
ba zan iya kiranta ba.Usman ya ce, tsoronta kake
jine?Raini ne bana so, yanxu dai kai kaje ka
sameta kuyi magana.Usman ya ce, nima ke nan
zan yi maka yakin neman sonta?Aliyu ya ce, duk
yanda ka ce amma ni in na kira tafa ba ra’ayinta
zanjira ba, umurni xan bata.Usman ya ce, shi
kenan ka bari xanje.Bayan sallar isha’i muna
zaune ni da iya muna cin abinci tare kamar
yanda muka saba, yaya usman yayi sallama shi
da matarshi Anty Abida da yaran shi guda
biyu,tsam na mike daga cin tuwon ina yi musu
sannu da zuwa, suka zauna na kawo musu abinci
da ruwa, sukace yanxu suka tashi daga kan cin
abinci.Na koma tsakar gida bayan na dauki
yarinya wato Ummulkhairi, yarinyar tana da wayo
yar mai kyau taji kitso, na ce Ummulkhairi kina
makaranta? ta ce eh mana, kuma Abban mu yake
kaini har ma da Abulkhairi, nace, iye, to koya
mun karatu.Ta ce, na islamiya ko na boko?Na ce,
a a islamiya dai.Ta gyara zamanta a cinyata ta ce,
in miki sunayen Allah kyawawa?Na ce, eh,ta fara
kenan babanta ya fito, ya kallemu karatu kuke yi?
Na ce, eh, tana koya mun ne.Yayi dan murmushi
ya ce ummu jeki wajen umman ki, ki ce mata ta
jira ni ina zuwa.Ta na shiga daki ya ce, kanwata
zo mana.Na mike na bishi zuwa kofar gida,
nasake gaisheshi nayi , bayan mun tsaya ya
ce,Sadiya nasan ba zakiji mamakin kiran da nayi
maki ba ko?Na ce ba wani mamaki, kila zaka
aikeni ne.
Yyace bahakabane na kiraki ne dan in sanardake
wani abun alkairi, ko da yake ban san yanda zaki
amshi abun ba.Na gane zan cen ya Aliyu, ya
duba duk cikin matan da ke garin nan yaga babu
wadda tayi masa sai ke, tamkar bai san zancen
ba na furta da karfi so!!!Usman ya ce ba wani
abun mamaki bane, dami ne kika tsinta a kala.A
raina na ce lallai ma yaya usman din nan, to bari
in latsa shi.Na ce, ya Usman ka ce masa yayi
hakuri kawai dan na riga na tsaida mijin aure
wanda nike so.Ya Usman ya ce, kin kai shi gida
ne?Na ce, gobe ne iyayan sa zasu shigo gidan
mu.Usman ya ce, in har zan baki shawara ki
yarda zan so ki dakatar da su domin kowa zaki
aura na tabbata bai kai Aliyu ba, samunsa sai an
tona, ko na ce irinsa.In kika sameshi a matsayin
miji tabbas zakiyi alfahari samun muji kamarshi,
mata da yawa suna sonsa, kila sun fahimci
nagartarsa, amma ba matsi in baki sonshi zan
koma in fada masa cewa baki sonshi da aure.Na
kalleshi bance bana sonshi ba, saboda duk
abinda iya ta haifa dole ne in soshi, kai ko wani
ne can ba danta ba in dai ya mutunta ta to zan
soshi bare dan cikinta, na riga na zabi wani
ne.Usman yayi shiru, ya zaci da yayi mun
magana zan amsa da murna, can ya ce, to yanxu
mai zanje in ce masa?
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai
masu nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?e_pi=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
Na ce, ka fada masa zanyi tunani zuwa gobe. Ya
ce, shi kenan, zan kiraki amma kiyi shawara da
kawarki wadda ta sanshi, na san zata fada maki
qualitie din Aliyu. Na ce, ba damuwa. Ya ce, shi
kenan gobe zanzo naji. In kin shiga kicewa Abida
su fito mu tafi daman na sallami iya. Na ce, to.
Bayan tafiyar su iya tashiga yi mun fada wai ai
gashi nan saboda bai daukeni da muhimmanci ba
abokinsa ya turo min, ta san jikina yana bari na
ce na yarda. Na vata fuska tamkar zan saki kuka
na ce, ni fa iya banyi fa rawar jiki ba, ce masa
kawai nayi zanyi shawara zuwa gobe. Ta ce, ato
in kin kimanta kanki yaga darajarki in kuma kinki
ni dai na fada maki babu zuwa a kawo mun kara.
A waya Aliyu yaji duk yanda mukayi, mamaki ya
dinga yi wai wanan yarinyar ce zata ce sai tayi
shawara, dawa zata yi? Kuma ita ce wa? Usman
ya ce ita ce mace. Aliyu ya ce, shi yasa kaga ba
zan iya kai kaina ba ga wata ya in ce ina son ta
ba, bare tayi mun yauki, nidan oya-oya ne.
Usman ya ce ka barni da itakawai na san jan
ajine zamuyi nasara cikin jin haushi Aliyu ya ce,
in taki ka kyaleta kawai, yarinya sai kace wata ta
gold sai ga ruwa nake yi a kanta. Ya ja tsaki nan
ya kashe wayar ba tare da ya sake jin mai
Usman zai ce ba. Kwana Aliyu yayi da zullumin
halin da zai tsinci kanshi, in yarinya taki
amincewa da shi. Da safe ina shara ya fito daga
dakinsa ban san me ke sani faduwar gaba a duk
lokacin da na ganshi ba.Na gaida shi ya amsa
cikin isa, kuma a ta kaice kamar yanda ya saba.
Sanan bai ko kalleni ba sai dai nice na bishi da
kallo. Namiji ne sosai ko tafiyarshi ta shaida
haka, daga ganinshi baka ga rago ba, dama abin
da ya dace dashi kenan jami’in dan sanda. Iya
daga daki ashe tana kallona ta ce, in kin gama
kallonshi sai ki ci gaba da sharar ko? Cikin kunya
da shauki na ci gaba da sharata. Da rana naje
gidansu Aisha kawata nake bata labari duk yanda
muke ciki, tace, tabbas! Sadiya idan zan fada
maki gaskiya ki amince kawai, kada ma ki tsaya
wani jan aji,sau nawa nake fada maki Aliyunku
unique ne?Allah in kika yi sake kin tsaya yauki
kya zo kina na dama, kin san shi da zuciya ya ce
yafasa.Kash!Ina ma nice ya ce yana so?Jin haka
yasa na kagu dare yayi.Har na debe tsammanin
xuwansa dan tara ta kusa, duk na tsure kar dai
ya Aliyu ya hakura da gaske.Can sai na tsinkayi
muryar wani yaro yana sallama ni ina cikin daki a
kwance kan kujera.Iya ce ta amsa salamar don
tana tsakar gidan, ya ce an ce sadiya ta zo inji
wani a waje.Ka fin ya rufe baki na mike, zaraf na
suri mayafi na fita.Iya ta ce, kai jama’a!Kai
jama’a!!Ni wanan yarinya ko dai zaki kai kanki
ne?Na ce ban fa san ko wane ne ba, ma ai
iya.Cikin gatse iya ta ce, ina zaki sani, shiyasa
kike ta sintiri tun daxu kin kosa ko wanene maya
zo?Na ce, sai na dawo.Ta ce, kada ma ki dawo ki
kwana can.Usman yana tseye a gurin da muka
tsaya jiya, na sameshi da sallama, muka gaisa ya
ce to kanwata nazo jin me kika yanke?Na danyi
shiru kamar mai nazari, ya ce, kada ki damu in
har baki sonshi ya ce babu komai.Na ce, ai ba
zan iya cewa bana sonshi ba ko dan iya, don
haka ka ce masa na amince.Usman ya ce,
Alhamdulillah, sai kin ji mu.Ranar nayi farinciki
har nafila nayi don godiya ga Allah, iya ta ce yau
kuma ibadar ce ta motsa har da nafilar dare?Ni
dai ban tanka mata ba, ta ci gaba, Allah ya sa a
dore, ina ta samun gadanga ce akayina san daga
yau shi kenan.
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai
masu nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?e_pi=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
Washe gari yaje ya samu yaya zakari da yaya
Sulaiman yayi musu bayani, su kuma suka sami
dan uwan mahaifinsu dake nan layin kasuwa, a
nan unguwar mu’azu.Nan dai suka sa ranar zuwa
zariya gurin mahaifina don jin zance, Aliyu da
zasu tafi ya bada dubu hamsin ya ce har sadaki
duk yanda ta kaya shi kenan.Mahaifina yayi
murna har yana cewa wannan abu ai da ba sai
anxo ba, ita iya Sadiya tata ce, Aliyu ma nata ne,
da ba shi kenan ba sai dai muzo a yan
gayyata.Kawu ya ce, a a kun wuce haka, kuma
dole abaku hakkinku.Baba yayi ta godiya kafin
daga bisani ya ce bari ya kira dan uwansa.Sun
yanke sadaki dubu talatin sanan aka basu na
gaisuwa goma, sai dai suna dawowa suka fadawa
iya duk yanda akayi.Iya ta ce sam yarta tafi
talatin, su kawo goman nan hamsin ne sadakin
yarta, sanan gadanga ya ciko goma kudin
gaisuwa.Da kyar suka shawo kanta ta amshi
goman, sadaki arba’in kenan.Aliyu dai yana
zaune yana jin su yana kallonsu amma bai ce ko
mai ba.Suka ce an tsaida rana watan tara sha
biyar da shi, lokacin kuma ana watan shida.Aliyu
ya ce yaya Sulaiman lokacin nan bai yi tsawo ba
kuwa?Anawa ra’ayin nafi son wata biyu, iya ta ce,
har ka gama shiri ne zaka ce wata uku yayi maka
kadan?Aliyu ya ce, wane shiri ne mai zafi?Ba lefe
bane ko meye ne kuke cewa ya rage ba?Ta ce,
kana da gurin zama kenan ko nan zaka gyara mu
zauna?Ya ce, a haba dai, zan nemi gurin zama
duk a cikin wanan lokacin.Ta kalli Sulaiman ni fa
in nayi auran nan zataci gaba da karatunta ku
shaida wanan, in ya ce a a za a jimu.Aliyu ya ce,
na sani iya, nima ina son ta ci gaba da
karatun.Ta ce, to batun aure a barshi wata ukun,
sai kaga lokacin ya zama ba ka kammala da wani
abun ba har kake raina lokacin.Ya ce Allah ya
kaimu.Ina zaune cikin ajinmu bayan mun gama
zana paper din mu ta karshe, ina kallon yanda
yaran ajinmu suke ta jin dadi da murna tun da
muka baro hall din.Ta gumi na zabga ina
mamakin irin halin ya Aliyu, yau kusan sati hudu
da sa muna rana amma ko sau daya bai taba
kirana ba, haka nan kuma ko cikin gida ya shigo
ban isheshi kallo ba.Nima fa yanxu na soma
sarewa, anya kuwa mutumin nan yana sona?
Kullum iya sai tayi min gori, yau kam zanje in
nemi ya Usman.Bayan nan na cewa Anty Abida in
yadawo tace ya zo, ina son magana da shi, ta ce
to zata fada masa na ce ina su Ummulkhairi?Ta
ce suna makaranta.Da daddare kuwa sai gashi
ana sallama dani, na mike har ina tum tube.Iya
ta ce, sai karaftu kike sai kace a dakin Ajantina,
na san dai ba wanda kike son gani bane, dan
nasan shi ya fi karfin ya kiraki.
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai
masu nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?e_pi=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
Nace, iya to ai ina so ne na ga ko wanene.Ta ce,
oho ke dai kika sani.Ina fita yaya Usman ne
kamar yanda nayi tsamani bayan mun gaisa ya
ce, Abida ta ce kin zo nema na.Na ce, eh.Na
sunkuyar da kaina ina wasa da yatsuna, na ce
dama nazo ne a kan maganar mu ne da ya Aliyu,
in abin ba zai yuwu ba gara mu hakura tun
yanzu.Ya gyara tsayuwa wani abu ne ya faru?Na
ce to ya Usman a haka ne za mu fahimci juna in
san abinda baya so yasan abinda bana so?Na ci
ga ba, bai taba kirana da sunan muyi zance dashi
ba, ko gida ya shigo ban ko isheshi kallo ba, shi
bashi da wani lokaci ne sai na aikin shi?Usman
yace ba wai zan goyi bayan shi bane amma
ninasan kina ranshi,ki fahimce shi, shi mutum ne
mai kishin kasarsa da aikin sa, shi yasa baya
samun lokacin kansa.Amma da zarar kin zama a
gidansa na san dole ya baki dukan lokacinki.Nayi
shiru kamar maganar ta shigeni, ammada na
tuna ko kallo na bayayi na ce, yaya Usman ka
san Allah ba dan aikin shi bane, ko kallo fa ban
isheshi ba.Usman ya ce, to bari zanyi mashi
magana.Na ce, don Allah kada ka ce nayi maka
magana, kada yayi tsammanin na damu da shi
ne.Usman ya ce, zanyi masa maga na da ma ai,
ba zan ce kece kika sani ba.Kusan sha dayan
dare Usman ya daga wayar Aliyu tare da yin
sallama, bayan sun gaisa Usman ya ce aboki
dazun ina ta kira baka daga ba.Aliyu ya ce, bari
kawai aboki, lokacin ina tsakiyar wani case ne
abin nan yana matukar daga hankalina tare da
bani mamaki.Ka san wani mutum dan kimanin
shekara arba’in aka kama yayi wa yar shekara
hudu fyade.Usman ya zabga salati tare da cewa,
wai aboki wanan wace irin masifa ce?Ko dai wani
tsafi ne?Aliyu ya ce, wa ya sani?Wannan fyaden
na kananan yara yayi yawa.Kullum sai mun sami
wanan case din wlh yanda abin nan ke mun zafi
a raina zan iya kashe irin wadannan mutanen,
don mugaye ne.Idan mata ne su je mana ga
karuwai nan,Usman ya ce, to Allah ya shirye su,
ya tsare mana daukacin musulmi.Aliyu ya ce,
amin aboki to kaji halin da nake ciki, lokacin da
ka kirani lafiya lau dai ko?Lafiya lau dama zance
ne ya kamata mu shirya muje muyi hira da
yarinyar nan ko?Aliyu ya ce, wace yarinya ke
nan?Usman ya ce, sai karinka yi kamar baka san
da zancen ba bayan nasan tana ranka.Aliyu ya
ce, tsakani da Allah sai ka tuna min.Usman ya ce,
ok, tunda yanxu iya ta yarda dole ka manta.Aliyu
ya ce subuhanalla? Dama wai Sadiya kake
magana?To wacce hira kuma zamuyi tun da na
rigaya an gama magana, sai jiran lokaci.Usman ya
ce, ai duk da haka za aje ayi hira ta san abinda
baka so don a samu zaman lafiya.Aliyu yayi yar
dariya.To ni ba haka tsarina ya ke ba, ina zaton
in har zanje gurin budurwa zan jene don ina
tallata kaina in in samu shiga,tonina riga na
samu shiga babu dalilin da zan matsawa
kaina.Usman ya ja tsaki kai dai bahago ne wlh, to
sai ka sai mata waya ko ta waya kunyi
magana.Aliyu ya ce, to yan zu dai kaine sarkin
yakinta ko?Suka sa dariya.Usman ya ce, da gaske
nikeyi, akwai wata waya da ake saidawa mai kyau
nan kusa daoffice din mu (MTN OFFICE) ya ke
aiki.Aliyu ya ce, ka suyo mata in kazo sai na baka
kudin, sanan kai zaka bata don har karshen satin
nan ban san lokacin dawowata, kafin ita ta tashi
na fita.Usman ya ce shi kenan.Washegari da
daddare ya usman yazo ya kawo mun waya wai
iji yaya Aliyu, inyi hakuriza mu rinka waya aikine
yayi masa yawa.Bani da zabi dole na hakura
tunda ga waya har da layin (MTN) ko da na nuwa
wa iya baki ta tabe sanan ta ce Allah ya sa
alheri.Tun da na karbi wayar ko flashing ba a
taba yi mun ba, ga dai lambarshi a ciki ya usman
ya samun duk da cewa har da kudi a layin nawa
nima cewa nayi ba zan kira shi ba.Sai dai in ta
kiran kawaye da yan uwa wadanda nake da
number su.
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai
masu nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?e_pi=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
Wata rana da dadare naji Iya tana yi masa fada
cewa yana zaton haka za ayi auren ba lefe, biki
saura wata daya da kwanaki, amma ba a ga yana
motsi ba.Ya ce, abin ne ya shige masa, amma
gobe zai je ya sami matar ya sulaiman.Ita da
matar Usman Anty Abida sukai ta zaryar zuwa
kasuwa, saura sati biyu lefe ya kammala da dinki
da komai.Iya ta ce ya Aliyu ya bada kudin mota a
kaisu zariya, ni kuma nan kawaye na sun matsa
da batun anko, lokaci yana tafiya gashi ba zan iya
yi mashi magana ba.Aisha ta ce, kiyi wa iya
magana.Na ce, iya kwana biyu bata sana’a , bata
da kudin anko?Tab! Ba zai yuwu ba.Wayata na
dauka inyi kamar zan kira shi in fasa, Aisha ta
amsa na ce kada ki kira shi dan bai taba kira na
ba, ba wani kiranshi da nima zanyi Allah aisha ni
auren nan tuni ya fitan min daga rai.Ace kai kafi
karfin kazo sai dai abokinka?Aisha ta ce, Allah sai
na rubuta masa tex.Ina kallonta ta rubuta
masa.SALAM.INA FATAN KANA LAFIYA?KAYI
HAKURI KILA YANXU KANA CIKIN AIKI NA TSAIDA
KA, DA MA NAYI MAKA WANAN MESSAGE DIN NE
DON NA TAMBAYEKA A KAN MAGANAR ANKO,
DONKAWAYENA SUN DAMU SABODA LOKACI YANA
KAREWA.NA GODE, KA HUTA LAFIYA.Tana gama
rubutawa ta tura masa, maji amsa-maji amsa
shiru, nace kin gani ko?Ke ayi biki haka bani kara
masa batun anko.Aisha ta ce, niko yanda yake
nashi salon birge ni yake, na ce, au!Wulakancin
da yake min din ne yake burgeki?Tayi dariya, ai
ba wulakanci bane rayuwar sa ce haka.
Lokacin yana office din commissiner ya je a kan
nemansa da yayi tsam ya kame kamar yanda
yake al’adar yan sanda, sanan ya soma magana
cikin natsuwa ranka ya dade an ce kana nema
na.Commissioner ya dube shi cikin natsuwa
sanan ya ce da ma na kira ka ne a kan maganar
barawon shanu din nan da aka ce kaki yarda a
bada belinshi.Aliyu ya sunkuyar da kai don
girmamawa, yace ranka ya dade haka ne, naki
bada belinshine saboda bincike ya nuna shi din
ba karamin mai laifi bane.Daji suke shiga da
motoci suna kora shanayen fulani suna kwashewa
su kai kudu su saida, wanan kamawar ita ce ta
goma sha uku amma ba a taba mikashi kotu ba,
azzalumine na gaske,Commisioner yayi dan
murmushi sannan yazo ya dafa kafadar Aliyu ya
bubbuga alamun jinjina, san nan ya ce, Dan
Sanda mai kishi, lallai kasan aikin ka da ka tsaya
binciko wannan files din, ka tattarosu ka miko
min nan, ni nasan yanda zan kawo karshen
lamarinsa.Zan shigo gurinku anjima kaje.Aliyu ya
sara masa, sanan ya fito.Gaskiya in son samu ne
case din nan ya tsaya a hannunsa dan kam zaiyi
gogaiya da zalunci.Shigarshi office din sa kenan
sako ya shigo wayarsa, sai da ya zauna sanan ya
duba.Murmushi yayi bayan ya karanta, a fili
kumaya ce, ko me nene anko?(hahaha,kunjifa
dan rainin hankali inji,shin kuna ganin zai yuwu
ace baisan Ankoba,ai dai kayan yansanama
Ankone,kuma kala biyu, wasu su sa baki
kawai,wasu kuma baki da light blue ko? Cewar
ANaM Dorayi)
Ya kira layin Usman bayan sun gaisa ya tambaye
shi ko menene Anko? Usman yayi murmushi wato
kai dai in kaje ka shige caji ofis dinku shi ke nan
baka tuna meye a cikin garin.Aliyu ya ce, aboki
mu kuwa dake wanan ofishin mu muke da
labarin abunda ke cikin garin, amma ba wanda
ya shafi biki ba.Usman ya ce zaka bata kudi ne
kurum ta shiga kasuwa da kawayenta su zabo,
haka su ke yi.Aliyu ya ce, gashi ni kuma bana son
yawo bare kuma xuwa kasuwa, in dai zani ne in
zan je gidan zan tsaya nan wani super market in
sayan masu, guda nawa ake siya?Usman ya ce,
da ka basu kudin.Aliyu ya ce, ba zata kasuwa ba,
wanan shine ra’ayi na, zan siyo musu zani.Usman
ya ce shi kenan, sai ka suyo musu mai kyau.Aliyu
ya ce ina ruwa na da zabe, ni dai kawai in dau
zani.Don haushi Usman ko sallama babu ya
kashe wayar.Aliyu ko da wuri ya bar office din ya
bi ta kasuwa ya sai zaunnuwa kala uku ko
wanneguda bibbiyu ya nufi gida.Iya tana zaune
tana yankan kubewa ni kuma ina daga kicin ina
kwashe tuwo ina mulmulawa a leda ina sakawa a
kula ya Aliyu ya shigo da sallama.
Kusan kwana hudu ban sashi a ido na ba , da ya
zauna yana gaisheta.Ta amsa ya ce, ga zaunnuwa
anko ne suka ce ko menene ma?Ta dauki ledar
tana cirowa ta re da fadin kaine ka siyo ankon
gadanda da kanka?Ya ce, to duk ba zani bane,
shi nan sai su zaba.Ina kallo daga ciki kuma ina
jin su, tun kafin in fito zaunuwan suka tafi
dani.Ya ce, naki ne da nata.Iya ta ce, to mun
gode, da ma ina so inyi maka zancen gidan ne, a
ina kasamu?Ya ce, to ni dai nafi so a can kasan
layinku, gefen makabarta din nan, to ba a samu
ba sai na dawo neman na siyarwa, kudina
dakekasa yanxu za su iya semin gida, amma
albashin wanan watan da na wancan watan hada
mana za ayi.To ganin kurewar lokacin sai kurum
na barshi yanxun anjima zamuje mu ga wani gida
da yaya Sani da Usman wai ciki da falo sai kichin
da ban daki dubu dari da hamsin.Iya tayi shiru
tana nazari, can ta ce ina nufin kasan gidan su
babba ne?Ya ce ciki uku ne da kicin da ban daki
sanan ga filin da mutum zai iya fakin din mota
har biyu.Iya ta ce kuma nawa?Da sauri ya ce wai
miliyan daya da dari takwas.Ta ce, ina ganin zaifi
ka siya gidan in yaso sai a daga bikin.Ya dubi iya,
ai saboda bana son dagawar shiyasa na hakura
da siyan gidan.Iya ta ce siyan xai fi maka sauki
ka huta da biyan haya, auran kurum za a daga
ba.Ya ce ba dagawa za’ayi ba, abinda ya sa in an
daga za ayi asara da yawa.Abokaina sun kashe
kudi gurin kati mai tsada tare da wasu abubuwan
abokan aikina suma sun kashe kudi gurin shirya
bukin.Iya ta ce to, kana ji ko, yanda za ayi kawai
a daura auren da buki, sai ta zauna gida kafin a
gama gyara tunda dai nan a gida ne ba a dawa
ba, bana so ka rasa gidan nan ne muhalli a bariki
ba karamin rufin asari bane
Aliyu ya ce, shi ke nan sai ayi haka din bari zan
kira yaya Sani sai muje dake ki ga gidan sai a
biya.Lumshe ido nayi cikin jin dadin an fasa daga
bikin, kai naso in tare a gida na ranar amma baji,
buri na dai a daura auren, amma da iya ta so
kwafsawa wai a daga.Ya mike ya juya da nufin
fita ida nunsa sukasauka a kichin a inda nake, da
sauri na ce ina yini?Sai da ya dauke kai sanan ya
ce, lafiya.Har ya fita ina kallonshi.Iya ta katse ni
da cewa, wata rana sai kin gaji da kallon shi.Na
sunkuyar da kai kunya ta rufe ni, ban santana
kallona ba sa karya, in dai gadanga ne gaki ga shi
nan.
Pink din muka zaba ni da Aisha, sai dai muna
zuwa kasuwa aka ce dubu uku ce gashi kudin
aisha bai kai ba.Sai muka dawo gida da kyar
mamanta ta cika mata muka koma muka
siyo.Muka roki mai shagon ya ajiye mana da mu
siya da yawa.Yamma tai mana a kasuwa gashi
ana wahalar mota.Muna tsaye a kan titin kano
Road, na ce bana son magariba tayi mana tun
daya muka fito gashi iya ba ta san mun koma
unguwar mu’azu mun dawo kasuwa ba.Aisha ta
ce, sai dai muje mushiga dambancen ko za mu
samu, na ce zamuje.Ta kan legas street wani
lokacin ba a wahalar mota.Muna tafe wai wani
mai mota ya tsaya, ‘yan mata kuzo mana.Na ja
tsaki tare da kara sauri, Aisha ta ce, lafiya?Ya ce
rage muku hanya zanyi.Na ce Aisha, kema kika
tsaya tambayarshi.Haka mutumin nan ya ci gaba
da bin mu yana magiya, duhun magariba ya
shigo na ce Aisha ko dai mu tsayar da mutumin
nan ya kai mu gida?Don ina tsoron fadan iya.
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai
masu nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?e_pi=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
Tace, nima hakan zan ce,dai dai lokacin ya sake
cewa ku kuwa tunda na ce Allah ya kamata ku
saurare ni, dan kun san mugu dai ba zai yi muku
sallama ba.Aisha ta ce unguwar Mu’axu muke.Ya
ce, ai hanya ta ce ni kuma Nasarawa zanje.Cikin
far gaba muka shiga motar ya ce mun a’a ke
dawo gaba dai ki nuna mun hanya , na koma ga
ba.Ya tam bayi sunayen mu, ina shirin xollo masa
karya sai naji Aisha daga bayana ta ce, ita Sadiya
ni kuma Aisha .Ya ce, masha Allah , sunaye masu
ma’ana.Ya dube ni, Sadiya dan ke fa nake ta
wanan bibikon sai aka ci sa’a kina da sunan
matata, ni sunana Auwal.Hakika jin sunanki ya
kara samun sonki Halimatu duk wace ta amsa
wanan sunan takan zama mai hakuri da hange,
bata rani bata daukar raini, macen rufin asiri zan
so na sake samun ki.Na ce matar taka ta hada
duk wanan halin shine zaka yi mata kishiya?Ya ce
jin dadin halinta yasa zan kara.Aisha ta ce bakai
mata adalci ba, au, ke fa sunan uwata ne ke da
zaki tayani yakin neman shiga?Aisha ta ce, nan da
sati biyu ita ma tana dakin angonta.Da sauri ya
ce, da gaske?Ta rantse mashi tare da fada mashi
ashobe muka zo siya.Daga nan nayi shiru bai
sake magana ba harya shigar damu layin kasuwa,
na ce sauke mu a nan ma mun gode.Sai mu
karasa.Ya tsaya muka fito, ya ce marya ba
godiya?Na dawo dai dai saitin shi na ce, mun
gode, na ce kayi hakuri muna sauri ne dare
yayi.Ya ce shi kenan, Allah ya baki zaman
lafiya.Juyawar da zanyi in tafi tare da cewa amin,
sai maganar ta tsaya, sa kamakon ya Aliyu da
nagani tsaye yana kallon mu.
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai
masu nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?e_pi=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347

Zaharaddeen Shomar
Whatsapp 08168575100

Darajar Yayana 1-03
Posted by ANaM Dorayi on 10:51 PM, 14-Mar-16
Under: DARAJAR ‘YA’YANA
_________________NA ___________HALIMA K/MASHI Duk da kasan cewar duhun magariba ba zai sa in kasa gane bacin ran sa ba.Gaba na ya fadi, irin wanda ban taba yi ba.A fili na furta na shiga uku!Aisha ta ce, me nene?Bakinta yayi shiru sakamakon ganindatayiwa abin da nagani.Kusan minti biyu yana kallo na, ko da banga fuskarshi sosai ba na san a daure take .Sai yaja tsaki sanan yayi babban titi abin shi.Muka kwashi sauri ni da Aisha inayi ina waiwaya shi, a zuciyata ina cewa yau na kade, Aisha ta ce muyi wa ni kin ga da sauki tunda mama ta san mun xo mun koma ne.Munyi sallama iya tana tsaye tsakar gida tana cewa, kai ni wadan nan yara ko ina suka shige ne?Kai Sadiya bata da hankali, ki fita tunda hantsi har magariba, to ko kasuwar kwari ta kano suka je?Ko jiran mu gama sallamar bata yi ba bare ta amsa ta hau fada, Aisha ta shiga jero mata dalilan mu, ta ce ku refa mun baki, ko kasuwar kano kuka je ya ci a ce kun dawo tadubi Aisha ta ce uwaki ta ganki hankalinta ya kwanta, masu shegen rawar kai.Ta bini ke kuma, sai ki jira xuwan gadanga don tun yamma yake shige da fice bai ganki ba, har dai ya kare ya ce ita wanan yarinyar ina tayi ne?Ina son ta hada mun abin shan ruwa ina azumi, na dafa kirji na ce, to me kika ce masa?Ta harare ni karya zan masa?Ce masa nayi kinje kasuwa sayan anko, yayita fada me yasa na barki don baya son xuwanki kasuwar ne yasa shi siyo ankon dakansa.Na ce, na kade.Na dauki buta dan yin auwala, a xuciyata inatuno yanda ya ganmu muna fitowa a motar, da nayi salla nayi addu’a Allah ya yayyafawa abin ruwan sanyi.Da a zamar sa ya shigo da sallama ga ba naya fadi da sauri, don haka ma ban iya amsa sallamar ba, dakinsa ya shiga bayan wasu mintina ya fito tsaf tsaf cikin shirin fita.Ban taba ganin dansanda da kaki yake masa kyau matuka ba irin ya Aliyu, kan cinya ta na dora fiskata ganin ya nufo dakin Iya.Ga zato na da ya karaso zai zabga min mari,ina jiyoshi yana cewa iya ya tafi sai da safe, ta ce, can zaka kwana?Ya ce eh, ta ce, Allah ya tsare mun kai, ya kuma bada sa’a ka yawaita adu’a.Ya ce to ina yi iya, zan kara kulawa.Ya sake wuce ni ya nufi fita, da kallo na bishia raina na ce, zaki na maza sarkin jin kai.Nan ya tafi ya barni da kamshin sa sai dai da dukkan alamu yana fushi dani.Da dare ina cikin daki kwance kan gado, juyi kawai nake zuciyata tana mun nazari a kan kallon da ya Aliyu zai mun, ganin da yayi mun a motar wani kamar in kira shi in bashi hakuri, sai na fasa.Na rubuta sako kamar haka:YA ALI DON ALLAH KAYI HAKURI IN NA BATA MAKA RAI. Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai masu nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com Kokuma ku kasance taredamu a facebook https://mbasic.facebook.com/HAUSA- Novels-389304544597988/?_e_pi=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
Ban jira amsa ba don nasan ba samu zanyi ba,
amma ga mamaki na sai naji sautin shigar
sako.Da sauri na bude na soma karantawa.KUL!
BANA DAYA DAGA CIKIN MUTANEN DA SUKE
DAUKAR LOKACIN AIKINSU, SUNA HADA SU CIKIN
LAMURANSU NA DABAM.SAI KI RIKE WANAN DAN
GABA.Na lumshe ido ina son yin nazari a kan
kalaman nasa, na san dai kul! Dan gargadi ne ya
yi mun kenan ba ya bukatar a shigar masa
lokacin aikin sa.Nayi juyi ina mai yiwa kaina jajen
auran ya Aliyu, yanxu auren ya fi ban tsoro fiye
da birgeni.Washegari sukuku na tashi,Iya ta ce
jiya kuna can kuna gararin yawon ku mahaifinki
ya zo yayi ta jiranki har ya tafi.,na ce kash!Ko da
yake na san dole ya dawo kafin bikin.Ta ce ba
dole ne ba , kudi ne ya kawo sadakin ki da akayi,
sai gudumawar su dubu hamsin.Na ce hamsin
iya?Yaushe hamsin zatayi mun kayan daki?Ta ce,
ina laifi, mahaifinki fa yanxu ba aiki yake yi ba,
tunda yayi ritaya sai dai dan noma.Shi ko noma a
kasarnan yanxu dai ba a dauki maiyinsa da
mutunci ba, shine koma baya a gurin gwamna
ti.Su ba ga taki ba ba ga tallafi ba, dan
gurarenda suke nomawan ma kwanaki
yakecemun gwamnati ta ce zata amshi wurin.Na
ce iya gurin da ma ba nasu bane?Ta ce, Sadiya
kenan, dama talaka yana da guri ne a a wanan
karnin?Sai wanda Allah ya taimaka ya kuma tsaga
da rabonsa.Gurinka da takardu da komai za a
amshe maka,dubu hamsin ai yayi kokari.Na ce
haka ne Allah ya rufa asiri, duk abindaza ayi dai
dai karfinmu za muyi.Iya ta ce, in sha Allahu sai
kin zaba yata.Jugun nayi ina kallon Iya, baiwar
Allah nan tana sona fiye da yayan da ta haifa,
abin da take min ko ita ce ta haifeni sai
haka.Kusan duk dare sai bacci na ya katse, in yi
kiri kiri ni kadai cikin xullumi irin zaman da zanyi
gidan ya Aliyu.Na gama duk hashashen da zanyi
ban hango jin dadi ko kulawa a cikin auren ba, sai
yanxu na gane nufin iya ta guje mun wahala ne,
gashi lokaci ya kure mun bani da damar in ce
bana so.Kusan karfe uku na rana ina zaune ina
yankan farce na tare da gyarawa, sautin shigowar
sako naji, sharewa nayi amma naki dubawa don
nasn MTN ne.Sai kuma wata zuciyar ta ce mun in
duba, gaba na ya fadi ganin sunan ya Ali, na
duba cewa yayi.KI SAMENI A DAKI NA
YANXUN.Duk da cewa ina fargaba sai da na dan
sakemurza hoda tare da man lebe, sanan na
fesaturare.Iya ta kalle ni tana zaune gefe tana
gyaran goron ta da yayi tsutsa
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai
masu nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?e_pi=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
Ta ce, to mai aljanun kwaliya don a sarar turare
ana zaune kin hau feshe feshe.Na ce, iya yaya
Aliyu ne yake kira na, ta ce ya shigo ne?Na ce ina
zato, amma ta waya ya turo min.Na suri hijabi na
na nufi dakin gabana na matukar faduwa.Nayi
sallama ya amsa, na shiga kallo daya nayi mashi
yana sanye da gajeren wando da(t-shirt) fara sol
na sunkuyar da kai sanan na tsugunna tare da
cewa gani yaya.Sam bai ko kalleni ba, hasalima
danna wayarsa yake abinsa, nayi kusan minti uku
sanan ya ce (ba tare da ya kalli inda nake ba).Ya
sunan saurayinki da na ganku jiya ya sauke ku a
mota?Ban san lokacin da na zauna ba don tsabar
tsoro.Sanan na ce, ba saurayi na bane.Lokacin ne
ya dubeni cikin wata irin harara da murya ta isa
ya ce, ba karamin zunibi ba ne wajen dan sanda
mai laifi yaki amsa laifinsa.Kar ki raina hankalina
kokaryata ni, sunansa kurum na tambaya.Murya
ta ta soma rawa alamun kuka zai kubuce min, ya
dora yatsansa dan manuni akan leben shi ta re
da cewa, shhhhhi!Kul!Kika min kuka, ko rawar
muryar nan bani son ji.Ya ci ga ba duk da
dadewarku da shi baki san sunan shi ba?Nayi
kokari na kalaci miyau na hadiye shi tare da
kukan da ke son kwace min.Na ce, yau ne na
soma ganin shi, yana ta binmu yana rokon mu
wai mu tsaya muka ki, toda muka ga duhun dare
muka yarda ya kawo mu, don ana wahalar mota
kuma kudin mu ba zai ishe mu mu hau achaba
ba.Ya maida kanshi ya kwanta rigingine, ya kuma
ci gaba da danna wayarshi.Kusan minti biyu
sanan ya ce, wa yake so cikin ku da yake ta
binku?Da dama yana ta binku ne kawai ya rage
muku hanya duk da dimbin jama’ar da ke jiran
mota a gurin?Tsoro ne da faduwar gaba suka
karu gareni, cikin in-ina na ce, am.. Em.. Haka ya
ce wai ni yake so.Da sau ri ya tashi zaune, cikin
daga murya ya ce, menene?Da sadakin nawa a
gurinki?Da sauri na ce, ai Aisha ta ce mashi aure
za ai min.Ya zuro kafafunsa kasa, oh, da ke baki
fada mashi ba?Na ce, ta rigani yin mga na ne
shine dalilin da ya tsareni da idanunsa.To me
yace da ta fada masa?Haka ya ce Allah ya sa
alkairi.Ya sake komawa ya kwanta.Jeki zan
bincika, in na samu zantukanki ba gaskiya sai kin
sani.Zaraf!Na mikexan fita sai ya sake cewa, me
ya fada miki lokacin da zaki tafi ya kiraki?Na ce,
ya ce ne ba godiya?Shine na ce mun
gode.Tamkar ba shi na bawa amsa ba, don bai
komotsa ba bare ya dubeni.Ina ta tsaye har
lokacin da ya kula dan kansa, sanan ya ce, kina
da wata maganar ne?Na ce, a a.Ya ce, to kin
tsaya min a kai.Na tabe baki a raina na ce,
masiffafen ikon ka zan dauke shi kuwa?Tsuntsun
dayaja ruwa……ANaM)Na fice, duk da ba lokacin
zafi bane jikina sharkaf da zufa, kan kujera na
zauna ina maida numfashi.Iya ta ce, me ya ce
miki ne?Ko abinci zai ci?Na ce a’a mun dai yi hira
ne.Ta ce, shine kika yi wujiga wujiga sai ka ce
kunyi dambe?Sakon da ya kara shigowa wayata
shi ne ya hana ni baiwa iya amsa, ko da yake
dama bani da amsar.Sunan shi na kara gani na
bude sakon, cewayayi.NA MANTA BAN
GARGADEKI BA, DOMIN KE TAWA CE TUN KAFIN
NA BADA SADAKI, BARE NA BIYA KUDINKI.Naaje
wayar a gefena, na zari buta zuwa ban daki ba
don zanyi wani abu ba sai dan inkaucewa tam
bayoyin iya.Sauran sati daya biki iya ta zauna da
duk yayanta, sun shirya yanda za su gabatar da
komai cikin tsari.Ina tsakar gida ina jiyo su, iya ta
kwala min kira sadiya!Na amsa, zo kije gidan
Hajiya Umma Rimaye matar Likita Hassan ki ce
mata tayi wa maiyin alkaki magana?In sunyi
maganar nawa ne kudin?Na ce to.Na shiga dakin,
kaina sunkuye dan harda ya Aliyu a gurin, ta ce
maza-maza ki dawo, dukkwanakin nan na kula
baki son aike.Ina shiga uwar daki na tura mashi
sakon cewa iya ta aikeni, ya bude ya gani amma
sai ya ajiye wayarsa, sanan bai ce mun kala
ba.Neko sai nayi zamana gefen gado, jin shiru
ban fito na ta fi ba iya ta ce, kin tsaya kwalliyarki
ta jaraba ko?Na ce, a a.Ya san shi nake jira, sai
ya ce ba aikenki akayi ba kina jiran menene?Na
fito na tafi.,ya Usman ne ya kawo mun katinan
bukin a ranar da dare.Lallai su na kula biki zasuyi
na sosai.Farko zasuyi walima bayan daurin aure,
sai kuma dinner, sanan akwai police day, shi
kuma washe garin daurin aure zasuyi shi,
damisalin karfe uku.Ni da Aisha da Fatiman ya
Sulaiman muka shiga rabon kati.Ana saura kwana
hudu biki, Anty Abida matar Usman ta kirani ta
waya naje, bayan mun gaisa ta ce, kina dan
gyaran jikinki ko?Na ce da me?Ta ce dan shirye
shiryen mu na mata.Na ce, a a ni bani da kudi
anty.Anty ta ce, baki tambayi ango ba?Na ce
anty, ni ba zan iya tambayarshi ba.Nan take ta
kira wayarshi ta sa handsfree, ya daga tare da
amsa sallamarta, ya ce madam ya akayi ne?Ta ce
ango, ango ka sha kamshi.Ya ce bansha ba
tukunna.Suka yi yar dariya, ta ce dama maganar
gyaran jikin amarya ne, ka san anayi.Ya ce ban
sani ba gaskiya wane irin gyara kenan?Ta ce
dogon bayani ne yanzu dai kudi muke bukata.Ya
ce nawa ne?Ta ce talatin ne kacal ba yawa.Ya ce
madan kuna so sai kun tsotse ni tas! Ya fadi? Ta
ce tashi muje gidan Hajiya Umma Rimaye.Na ce,
a a, ita ce mai gyaran jikin?Ta ce, eh.Nace na ga
iya gurinta ta aikeni in kai kudin alkaki.Ta ce, eh,
ai kawarta ke yin kayan buki, ita dai ke gyaran
jiki.Na ce gaskiya tana da kirki.An hada kayan
dilka masu kyau an lailaye ni da su, duk da
kasantuwata fara ba karamin kyau nayi ba,
kwana uku zanyi ina zuwa.Kuma ran na uku za
ayi mun lalle.Iya da kanta tayi ta yabon kyan da
nayi, haka naita zuwa ranar da na cika kwana
uku ta kira mai zanen lalle inda aka zuba min
fulawa.Abinka da fara, kowa sai tanka ni yake ta
ce,tunda gidan su yana da girma kawaye na suzo
nan a yi masu na su lallan na ce, to na
gode.Abida ce ta amso kudin ta bada, Usman
shine ya bamu kudin walimar mu.Wani abun da
ban gane ba duk dare sai iya ta dama mun wata
fura wace ita ta hada kayan hadin da kanta,
sanan ta va inno yar sokoto ta daka mata.Furar
tana da danko, furar sai kace magani gashi duk
yawanta in ta dama sai ta tsare nina
shanye.Sanan da safe ta xuba gero a turmi ta
surfe shi, wai zata tara na dama kunun safe
saboda yan buki, amma tana gamawa zata wanke
shi ruwan farko ta tsareni sai na shanye ina kuka
ina komai.Tun ana jibi daurin aure wasu suka
soma sintirin taya aiki, makota dangi duk sun cika
gidan, yan gefen su iya da na baba na.
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai
masu nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?e_pi=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
An yi mini kamu inda aka feshe mu da turareni
da kawaye na kamar yanda muke yi a nan
Kaduna.(Ina yan kadunan,yakukeyi kubamu
Labari,ANaM) Gidan matar yaya sani mukakwana.
Zariya za a daura aure amma an ce ni ba saina je
can ba, tunda ba tarewa zan yi ba.Na nufo gida
dan kwasan kayan da zanyi anfani da su in nayi
wanka.Su ya Aliyu na ta shirin tafiya gurin daurin
aure, an kawo motoci.Ya Aliyu ba ya gurin sai
abokanan sa sun taru a kofar gidan mu, kunya ta
kamani, na ja gefen hijabina na rufe fuskata.Ina
jin wani cikin su amaryarmu ki bude idonki kada
ki fadi mana.Sai naji muryar Usman yana cewa,
sarkin kunya kenan.Zan shiga soro (zaure) naji
mun zabga karo da wani, da sauri na bude
fuskata, gaba na ya fadi.Ya Alyu ne har wayarsa
da ya na magana tafadi.Da saurina tsugunna dan
dauke, tare muka hada hannu zamu dauki wayar.
Hannunshi ya taba nawa.Ba ni kadai ba, na kula
harshi yaji abin da naji, tamkar wutar lantarki ta
jamu.Shi ne ya janye hannunsa, na dauki wayar
na mika masa tare da furta kayi hakuri.Kala bai
ce ba, sai amsar wayar da yayi ya tafi, na bishi
da kallo yayi matukar kyau cikintsaleliyar shadda
mai ruwan suminti, tana tamaiko.Kamshinsa ya
cika zauren, a fila na ce na more muji, na juya na
nufi ciki.Sai tsiya ake min Amarya-amarya.
Munyi walimama inda nai ta canjin kaya, kusan
karfe hudu Aisha ta miko min wayata, sa ko ya
shigo na bude kamar yanda na zata ya Aliyu ne,
in da ya ce, “Alhamdulilla” na kalli Aisha dubi
abin da ya ce, ta karanta da murmushi ta dube
ni, kin zama tashi dole yayi hamdala ga
Allah.Nace, Allah ya sa haka yake nufi, wanan
danjin kan?Sakon shi ya sake shigowa musalin
karfe bakwai na safe, na idar da sallah ke nan,
ya ce kije gidan Usman da ga can za a dauke mu
ni da ke dan zuwa dinner, kawayenki kuma su
xama cikin shiri su tsaya a kofar gidan mu,
please, banda marasa hankali, bayan sallar isha’i
za a tafi.Na ce, Aisha kinji mutuminki ko?Ta da
fani, me ya ce?Na mika mata wayar ta karanta ta
dube ni.Ki dauki kayanki da zaki sa ki tafi can ki
shirya, ni kuma zan kula da sauran kawayenmu a
nan dan mu shirya cikin tsari.Kinsan su ya Aliyu
masu aji ne ba irin tarkacen nan suke so ba.A
gidan Abida nayi salar isha’i sanan na shirya da
taimakon abida da yake ita ma in dai kwalliya ne,
matirial ne na saka riga da siket ruwan madara
da ratsin kore.Sai nesa kore takalmi da jaka duk
koraye, sarka kuma ja sai muka yi anfani da ja a
kwalliyar fiska ta gashi ya sha gyara, da ta shiga
fesa mun turare sai da na soma atishawa, kaloli
ta samun masu kamshi.Da na kalli kaina a
madubi sai na ce Alhamdulillah ni ce haka?Ita ma
sai yaba ni take yi, ta shirya, sun zo daukarmu
Usman ya ja motar suna gaba shida Abida ni
kuma a ka bude mun baya ashe ya Aliyu na cikin
motar.Sanye yake cikin lallausan yadi ruwan
madara, kalar kayana ke nan hular kube ce kai
yayi kyau matuka, sam bai kalleni ba.Waya ma
yake yi motar tana tashi wutar motar motar ta
dauke dai dai lokacin kuma ya gama wayar.A
hankali motar ke tafiya motar shiru sai sanyin
(AC) da wani dan sauti dake tashi a raidiyon
motar mai sanyaya rai, ban san ko wacce zabiya
bace mai wakar ba, tunda ba sauraran wakar
turanci nake ba.Sai dai wakar tamasoya ce,
kalamar zabiyarsun haddasa min shiga wani irin
yanayi, na lumshe ido tare da jingina baya na a
kujerar motar.Kamar daga sama naji saukar tafin
hannunsa a saman nawa, da sauri na ware
idona, a zatona bayanan zabiyar ne suka sani
dan karamin mafarki.hhhhh,kujita da shiririta..
Amma sai naji yatsunsa suna ratsa tsakiyar nawa,
lokaci guda kuma ya matsatse su tsam.Na dube
shi da sauri sam ba zaka ce shi bane.Don har
yanxu yana fuskantar inda dama yake fuskanta,
na kalli hannuwa na ma duk da cewa a kwai
karancin haske bai hana ni ganin sarkakun
hanuwan namu ba.Na sake mai da baya na jikin
kujerar tare dasauke yar karamar ajiyar
zuciya.Lumashe ido nayi ina tuno karon da
mukayi dashi da zun, goshi na da hanci na suka
dakikirjinsa.Na tuna hanuna da nasa suka hadu
wajen daukar wayar.Hannuwa na farare sun sha
lalle, na lura da yanda ya tsurawa hannuna ido
na yan sakwanni a lokacin. A raina ina ta mamaki
da tam bayar kaina, shi wanan ya canza daga jin
kan ne?Koko isa ce tasa shi yin haka?Wata zuciya
ta ce koma me nene mijinki ne a yanzu.Tsayuwar
motar ne yasa ni bude ida nuna.A zatona in zai
fita dole ya sakar min hannu,amma har muka fito
hannuwan mu sarke, a haka yayi ta daga waya
na kalli gurin da muka zo, an rubuta Cristal
Garden da wani rubutu mai yi kala kala na
wuta.Usman ya shiga ciki ya fito sanan muka
shiga tare.Dam gurin ya cika da mutane an
wadata ko ina da kayan ciye ciye da na shaye
shaye, naga muta ne manyan mutane da banyi
tsammani ba.
Anci ansha kuma anyi wasa da kudi, sai dai duk
yanda abokan ya Aliyu suka so muyirawa yaki ko
mikewa tsaye.Dan haka duk wanda ya matsu da
ya yi mana liki sai dai ya ishe mu a kan kujerar
mu, abokan shi da kawaye na sun sha rawa.Sai
kusan sha daya a ka tashi, mu kam sai sha biyu
sanan muka tafi don sai da aka kwashe kowa.A
kofar gidan mu motar ta tsaya, na yunkura zan
fita, sai naji ya dafa hannuna, wato ya dora
hannunshi a kan nawa.Na kalleshi shima ya kalle
ni, dai dai lokacin Usman ya fita, da ma mun
sauke Abida a gida.Aliyu ya ciro wayarshi ya
haska fiska ta, ya cire hannunshi da ke kan
nawa, ya dora a kan kuma tuna ya shafa har
zuwa dokin wuya na.Sannan ya juya bayan
hannunshi ya shafi haba ta, dole na lumshe
idanuna abin sai kace a mafarki.Ya tsansa dan
manuni ya saka ya gewaye lebuna na, na bude
ido ina kallonshi, murya kasa kasa ya ce, ki bar
wayarki a kunne zan kira ki.A jiyar zuciya na
sauke, sanan na amsa a kasalance to.Tsakar
gidan mu cike da mutane duk sunyi shinfida sun
kwanta, kasancewar lokacin damina ne amma
anyi kwana biyu ba ayi ruwa ba.Don haka gari
duk ya dauki zafi.Na nufi uwar daka, nanma duk
jama’a ne kwance, gado na dai ba kowa.Na cire
kayan jikina nai daurin kirji sanan na fada kan
gado.Iya can na varo ta a falo tana yin sallar
nafila, a rai na na ce iya koda biki ba a daga
kafa.Filo na dauka na rumgume ina tuno
abubuwan da suka faru yau, tamkar almara ji
nake yau na zama mace sosai.Karar ringing din
waya ta shi ne ya dawo dani cikin hankali na, na
dauka cikin faduwargaba na ce salamu a
laikum.Muryarshi can kasa kasa ya amsa sanan
yace ke da waye ne a nan?Na runtse ido dan
yanda muyarshi take ratsa dodon kunnena, na ce
ni da mutane amman sunyi bacci sunyi shinfida
ne a kasani a gado nike, ya ce ok, kin san me
yasa na kira ki?Na ce a a ya ce, saboda mu
fahimci juna…
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai
masu nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?e_pi=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347.
A raina na ce abin da ya kamata a ce shine a
farko ya koma karshe.Tamkar ya shiga raina.Ya
ce kila kiga abun babu tsari ko?Kafin na bashi
amsa ya ci gaba.Ni irin nawa tsarin kenan, kina
jina?Na ce eh.Yace to yanxu sai ki fada mun
dokokinki kafin kiji nawa.Da sauri na ce ya Aliyu
ai bani da wata doka sama da ta Allah da
manzonsa, wada suka tsara ita ce abin bina doka
ta ni kadai in bika.Gud to me kike so me bakya
so?Zan so in soma jin naka yaya, tunda kaine
babba.Ya ce, to da farko dai bana son kazanta,
duk inda zan shiga a gidan bana so in shaki wani
wari.Kuma bana so in ganki babu tsafta ko in
shaki wani wari daga jikinki, sannan ina son
komai a kan lokaci.Na san kin fi kowa sanin ni
dan oya oya ne, komai cikin hanzari bani son
kasala, bana son musu ko gaddama.Abu na kusa
da karshe bana son duk wani abu da zai shiga
lokacin aiki na, ina fata kin fahimta?Na ce eh.Ya
ce yan zu sai inji naki.Na ce, ni dai bai wuce uku
ba, duka da zagi ne bana so.Sai nayi shiru.Ya ce,
ina jinki, saura daya.Na ce imm…. Bashi kawai
ma.Ya ce a a, ki fada in nayi maki cikin rashin
sani fa?Bana son mu munafunci juna,fadamin
duk abinda ke ranki da xuciya daya.nace
amm…dama kishiya ce bana so dai,kuma bamuyi
sabo daxan fada maka ba.shi kanshi shiru
yayi,nasan yana mamaki ne don bai zaci jin haka
ba,a zuciyarshi shi kamshiru yayi saidai bai ji
wani mamaki ba saboda yasha samun case din
mata akan kishiya.ganin kishiya ce abu na karshe
da mata suka tsana.nima shiru nayi gabana yana
ta faduwa,tsai din dana ji araina na raya cewa
magana xai dankaramin mara dadi,can yace ba
xan yi miki alkawari ba in na duba cewa komai
na rayuwata rubutaccene tun fil’axal kamar
yanda yake ga kowa.kifahimta,baxan taba yi miki
karya ba,don kawai kiji dadi.sai dai shawara daya
xan baki,kiyi kokarin tsare duk hakkokina,ta yiwu
in kinyi hakan bazaki rage gurbin wata ba
Kuma kila baxan ji sha’awar karawa ba.(Lallai
yaya kazama abokona,muna da ra’ayi daya
dakai, dan haka me sona nima namiki nasiha
makamanciyar ta Yaya Aliyyu,kiyi kokarin
kyautatawa,tayanda zaki rufe idanuna daga ganin
dukkanin wata mace da matsayi irin na soyayya
bayan ke. ANaM Dorayi)
Nayishiru tabbas nasan gsky yafada,amma kishi
ne daninasan wanan tundaga ranar da kunnena
yaji ya Aliyu ya furta yana son aurena.can kasan
xuciyata tunani ne kada wata rana yace xai so
wata har ma ya aureta.duk sauran samarina da
duk wanda yaxo da niyyar aurena nakan fada
mishi koda na aure ka banason kishiya fa.Toh shi
xakin nawa ina naha fuskar fada masa,shine sai
yanxun…ya katse tunanina da cewa,nasan baki
fahimce ni ba akan batun kishiya,don haka a aje
zancan gefe muyi mai amfani.nima naji abinda
bakiso zan kuma kiyaye insha Allahu.kiyi baccinki
sai dasafe kar ki manta gobe akwai ranar yan
sanda.bikin da suka shirya mana,ina fatan zakiyi
shiri?muryata sarke nace Allah yakaimu goben.
shine ya katse wayar sannan nakashe tawa na
kwanta,kalamansa ne ke yawo cikin kaina na
damu da bai min alkawari cewa baxai min
kishaya ba har bacci yayi gaba dani.(kabwata duk
lokacin da saurayi yace bazaimiki kishiyaba to
kisani hakan mafificiyar karyace a hasashena,pls
kabwata karkisa saurayin yayimiki wannan
alkawari kawai dan gudun bacin ranki,ANaM)
Ya aliyu ya iya magana cikin natsuwa,kai inason
gayen sosai.
Dasafe kin fitowa nayi ina yin sallah asuba dama
komawa nayi nacigaba da bacci. da Iya ta tashe
ni sai na langabe nace mata kaina ciwo yake yi
nan ko banason tashine in ta aiki ga mutane. sai
kusan sha biyu sannan na tashi nayi wanka na
karya.Aisha taxo muka sha hira anan ma muka
xabi kawayanmu da zamu je bikin anjima
dasu.yau kam shigar Green da Golding nayi
nawani leshi mai kyan gaske,abinka da farar
mace kayan sun dauke ni duk da cewa wai farin
ne yacece injiwasu
Duk yau ban sa shi a idona ba sai yanzun da za
mu tafi., yau kam gadanga kusar yaki kakinsa
yasha na yansanda, ya iya aje hularsa a kai
tamkar sai da ya yi course din sata,wani dan
sanda ne ya jamu zuwa wajen, guri yayi
guri,Usman shi ya taho da sauran kawayena,
Police band sai tashi take ga wasu yan sanda
suna ta bin kida fareti. gurin zamanmu na
musamman muka nufa înda masu kidan suka
dafo bazanmu da kida. ya Ali da abokansa da
fareti suka yi tafiyar har zuwa gurin zaman har
wani yana cewa yakamata matar dan dan sanda
ta îya fareti itama . sun yi wasa kala kala har
wani wasan su wai lokacin suna makaranta suna
cin garin kwaki,anci ansha anyi rabon
abubuwa.sai bayan magriba muka dawo
gida.karfe sha biyun dare dai dai wayata ta soma
ruri da sauri natashi nadaga yace xo mana
natashi xaune na kalli shashin da Iya take, tadan
rumtsa kafin lokacin sallarta ya karato,Na tashi
sadaf-sadaf tamakar munafuka nafita, a kofar
daki nayi sallama, ya amsa na shiga.Kwance
rigingine na same shi yana danna wayarshi,
jikinsa sanye da farar singileti tareda gajeran
wandonta.Nayi saurin dauke kaina don kunnyar
ganinshi a haka.Na rusuna kaina a kasa ga ni
yaya ba tare da ya dube ni ba ya ce, tun cake
din da kika bani a baki dazu gurin party nan ne a
ciki na,yun wa nake ji.Na dube shi me zaka ci?
Shima sai lokacin ya dube ni, me kika ga ya dace
in ci?Na ce, ko za ka fara shan ruwan zafi tun da
ka jima baka ci abinci ba, saboda cikin ka
yawarware?Ya ce to yaya za ayi, na samu ruwan
zafin?Na ce sai na dafa maka, na mike tare da
ajiye wayata a gefe na nufi kicin, ina kunna risho
naji takun tafiya, sai ga iya tsaye a kaina ta ce,
na farka ban ganki ba lfy kika kunna risho?Na ce,
yaya ne ya kirani a waya wai yana jin yunwa shi
ne zan dafa mashi ruwan zafi , ta ce, hum!Ki dai
kiyayi kanki, kuma ri rage wanan barin jikin,
sanan kiyi maza ki dawo daki na ce, to.Ina
komawa dakin dauke da dan flaks dinsa na
ruwan zafin na same shi yana danne danne cikin
waya ta, na juyo na jawo kofi zan zuba masa ya
dube ni baki da numbata a she?Na ce ina da ita
mana.Ya ce in gani.Ya ciro number ya miko min
wayar, na amsa na danno sunansa inda na sa ya
Ali, ya ce ok, bani ruwan zafin, na zuba a kofi na
hada masa sanan na mika masa.Sai da ya amsa
ya kurba sanan ya ce, amma na zaci cewa na
wuce wanan matsayin na yaya.Na kalle shi eh
haka ne.Ya dauko wayarshi ya danna ya nunu
min numbata a wayarshi.Yayi saving dinta da
suna my choice, a fili nafurta my choice, ya ce
nima sai a canja min suna ko?Muka kalli juna
cikin ido sannan na soma danna wayata, ya ce
zauna sosai mana, sai kace ba dakin mijinki ba?
Na zauna sannan na soma rubutawa na sa
honey, sai na goge na sa darling, shima na goge
sai kuma na rubuta sweet Aly.Zan goge yayi zaraf
ya amshe wayar ta re da cewa in gani me kike
rubutawa kina gogewa?A fili ya ce sweet Aly.Yayi
dadi ki barshi haka.Ni kuma tuni na sunne kaina
cikin cinya ta don kunya.
Ya ce ai babu wani sauran kunya tsakanin mu,
kinyi alkawarin za ki rinka kirana sweet dinki har
gaban kowa?Na dubeshi cikin kunya sanan na
sunkuyar da kai ina wasa da gefen hijabina na ce
ba dai ga ban muta ne ba, yace to ni gaban kowa
zan ce maki my choice, sunan ya da ce?Na saka
yatsa a bakina ina dan wasa da shi,na ce me
yasa ka zabi ka sanya min zabin ka?Ya dan kara
matsowa, dan duk duniya ke kurum zuciyata ta
zaba har mamakin ki tai lokacin da muka taya
wai saida kikaimana yanga kafin ki amsa.Na
yunkura bari inje in kwanta, ya ajeye kofi bakya
jin dadin firar tamu ko?Ya ci gaba, kiyi hakuri
dani ban taba fira da mace ba shi yasa, na dube
shi tare da dan zare ido ya ce baki yarda ba ko?
Nace naga kana dan sanda ka ce baka taba fira
da mace ba?Amma ba wai ban yarda bane yayi
dariya gaskiya bana yi, tsakanina da mace sai dai
in matsalar da ta shafi aikina ne ta hada ko har
yanzu baki yarda ba?Na ce na yarda na mike
tsaye ya ce, firata ba dadi ko?Na ce, da dadi
mana.Ya ce to shi yasa kike so ki gudu? Iya ta ce
kar na dade,yace ta manta ni mijinki ne ya ce ok
sai da safe?Na ce tam, har na kai bakin kofa
yace, gaki dai baki son kishiya sai ina ganin ba
zaki iya kula dani ba.Ina tsoron kada hakan ya ja
maki kiashiya. Cak!Na tsaya cikin wata murya
wacce ban san ina da ita ba na ce, sweet Aly,
Allah zan iya kula da kai fa ka ji?Kasa amsa ni
yayi don jin irin muryar da nayi anfani da ita.Na
ruga da gudu cikin kunya shi kam shiru yayi yana
mama kin mata.Lallai mata abokan nishadi ne,
dubi yar hirar nan da yayi da yarinyar nan ya
shagaltar dashi ya koma kamar sakarai, yayi
murmushi sanan ya kwanta.Nima kwanciya nayi
ina tuno abin da ya faru tsakaninmu duk da
kallon da Iya ta bini da shi, da na shigo sai dai yi
nayi kamar ban lura ta ji haushin dadewar da
nayi a wurin yayan ba.Washegari ban tashi da
wuri ba sai wajen tara lokacin baki suna ta shirin
tafiya gida jen su.Sha biyu kowa ya kama gaban
shi, sai mu munata aikin gyaran gida ni da
iya.Kusan karfe uku na yamma ya kirani wai a
kwai fura ko?Don anzowa iya da fura da nono
lokacin biki, na ce masa nono yayi tsami, sai dai
in ya siyo yogot ya shigo da shi ya ce to.
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai
masu nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?e_pi=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
Tunda na idar da la’asar na zauna zaman zabar
kayan da zan saka iya dai tana kallo na na sauke
akwatuna na zabo atamfa cikin kayan aure na.Da
na idar da sallar isha’i kuwa na shiga zabga
kwalliya ina ta feshe jikina da turaruka.Iya ta
shigo ta zauna bakin gado ta tsareni da idanunta
ko da bata fada ba nasan abinda kallon nata
yake nufi.,don haka nakoma nima bakin gado na
zauna tare da ajiye dan kwalin da na dauko zan
daura.Ta ce sadiya ni ba wai ina hanaki ki lura
da mijinki bane ko ki shige masa a ana fi so ki
bari sai kin tare, shi fa namiji babu ruwan sa da
zancen kunya, in baki ji nauyi na a matsayin
mahaifiyar Aliyu ba ai kyaji kunya na a matsayina
na uwarki.Saboda iya shege ko watsewa yan biki
basu tafi ba kin tafi dakin miji kin raba dare
saboda rashin kunya?Na sunkuyar da kaina rai
bace a zuciya ta na ce, har ga Allah shi yasa na
so in tare a daki na, ta ce daina bata rai, daraja
nike nemamaki da kima in kin tsare kanki har sai
kin tare kifi kima a idonsa, ga dai misali a gidan
ku.Kiji tsoron abinda ya faru da yar uwarki ta
zariya Harira ya faru dake, kan ta tare tayi ciki a
gidan mijin nata ya shiga yi mata wulakanci.Kin
manta banda ubanku tsayaye ne ai cewa zaiyi
cikin ba nasa bane, shi yasa in andaura aure ba
a tare ba mace ta mika kanta ba karamin so
mijin keyi mata ba za ya daraja ta.Wani dama
sha’awa ce ta kawosa gurin mace da ya biya zaiji
baya sonta, amma in tana gidansa fa?Ai yasan da
kunya ya ce yayi aure sati daya ya kori
matar.Jikina yayi sanyi, tabbas babu ja a batun
iya,kuma haka ne batun Harira, tayi goyon ciki a
gida ta haihu a gida ba ta tare ba.Kuma ya
saketa da kyar ya amshi cikin amma har yanzu
dan yana hannun uwarta agidan mu ita kuma
tayi aure a Hunkuyi.Na saka kaya a sanyaye na
zauna ina kara nazarin abubuwa.Har dakin iya ya
shigo suka gaisa ya ce, ina yarinyar nan?Ta ce,
tana ciki.Kamar daga sama sai naji ya ce, my
choice.Na fito da sauri tare da amsawa, duk da
nasan iya bata san me yake nufi ba.Amma tana
da saurin dago abu, zata san cewa suna ne na
musanman ya sa min, na amsa sannu tare da
gaishe shi.Ya miko min yoghot din in kin gama ki
kawo min.Na ce to,ya dubi iya bari nayi wanka.
.Na shiga da sallama, yana zaune kan sallaya da
alama salla ya idar, na ce baka sami jam’i bane?
Yace, shafa’i da wutiri nayi.Zan tsugunna ya ce
zauna a bakin katifa mana.Kina yi ya ce, sai kace
ba dakin mijinki ba.Ya gyara zama kan sallayar,
sanan ya dauko wata laide dake gefe ya bude ya
ciro kunshin takarda ya warware yana fadin.Kin
ganni da son kilishi shi yasa na saimuku
Balango.Ya dauki daya ya saka a bakin shi, zo in
baki a baki. Nace na koshi ni na ci abinci tun
dazu.Yace wanda kika ci da ban nawa nama ne,
matso kiji.Na dan sunkuyo ban sauka daga kan
katifarba, shima ya matso ya miko nannu ya sa
min abaki, na amsa tare da rufe fuskata cikin
tafukan hannaye na.Ya ce fada min gaskiyarki, ni
dake yanzu ba wani batun jin kunya. Kin kosa ko?
Na daga kai alamun eh, yayi yar dariya kinyi kyau
da wanan kwalliyar ta wace?Nasake makale kaina
cikin cinyoyi na, na ce eh.
Ya matso sai kurum naji ya kama ka fada ta, ya
saka dan yatsansa yana bin zanen fulawar, jikina
ya dauki bari don ji nake tamkar susa yake
min.Shima nasan yaji abin da naji don naji
muryarshi ta dan sarke.Ya ce wata gwana ce ta
zana maki wanan fulawar?Na ce wata yarinya
ce.Ya ce, yayi kyau.Ina son farar mace na dan
ware ido ina duban shi.Me yasa?Ya saki kafada ta
Ra’ayi nane kawai ba dan komai ba, ke fa?Na
sun kuyar da ka, kalar ka nafi so a cikin
maza.Yayi yar dariya, wace iri ce kala ta?Na ce,
wankan tar wada baka cikin farare kuma fara
cikin bakake.Ya tashi daga mazaunin shi ya dawo
kusa dani kan katifar.Kina nufin duk mun dace da
zabin mu?Ban iya amsawa ba saboda yanda ya
kusance ni, jiki na da na shi har suna haduwa.Ya
saka hannun shi a kafada ta ya manno nijikin sa,
fada mini gaskiya can dama kina sona?Duk da
halin da nake ciki na faduwar ga ba sabo da irin
yanda ya makale ni, bai hana ni tunanin wanan
mutimin ya cika tam baya.Ko yana zaton nima
mai laifin ce?Ya dago fuska ta, kalli cikin ido na ki
fada mun. Zan gane in kinyi karya kwa yar idonki
xata nuna mun.Naji mamakina lokacin da nake
furta can dama ina son ka kai fa kana sona?Cikin
wata ma yaudariyar murya nayi maganar.Kurum
sai na fuskanci le bunan shi a kan nawa yana yi
mun sumba, lamarin ya zo min sabo, ko na ce
bako.Ya dinga yi mun wasu abubuwa masu
firgitani har na zama bani da karfi.Tsoro na daya
kada ya gota daga haka, saboda ina tsoron
Iya…..zandakata Anan,muhadu a lokaci nagaba
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai
masu nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?e_pi=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347

Zaharaddeen Shomar
Whatsapp 08168575100

Darajar Yayana1-04
Posted by ANaM Dorayi on 10:48 PM, 16-Mar-16
Under: DARAJAR ‘YA’YANA
______________NA _____HALIMA K MASHI Nayi karfin halin zame jiki na daga na shi, yakwanta rigingine na mike sai da safe.Ya miko hannu ya riko nawa hannun, cikin wata rikitaciyar murya ya ce, ki zo nan mu kwana.Da sau ri na ce, tab Iya ba zata yarda ba.Ya ce, ina ruwanta, ni ba mijinki bane?Na ce to ai ban tare ba.Ya saki hannu na.Da sauri na fice.Na tabbata in na shiga daki haka iya zata fahimci wani abu, don duk kwalliyar fiskata ya goge min.Don haka sai na bige da sabar buta na nufi bandaki, na zo nayi alawala.Ina shiga uwar daki ta bini da kallo tana kwance kan gadonta.Na cire kayan jiki na dauko rigar sallata nayi shafa’i da wutiri.Ta tabe baki bata dai ce min komai ba ko takula duk na tsargune?Oho.Da kyar na samu bacci ya soma dauka ta sabo da tunanin abubuwan da suka faru tsakani na da shi.Shigowar sakonshi dan sautin ya farkar dani, na bude na duba cewa yayi, kin hanani bacci my choice kixo ki taima ka min please.A raina na ce mai zanyi maka sweey Aly, ka dan bani lokaci mu tare, kiranshi ne ya katse tunanina,sa sauri na farka dan ina tsoron kada ringing din ya farkar da iya, duk da cewa na san tana jina don bata da nauyin bacci.Can kasan makoshi na nayi sallama ya amsa muryarsa a raunane, har mamakinsa nake ina girman kan? Ina isa da jin kan?A she dai mace dai ita ce namiji.In ba mace rayuwar namiji ragaggiya ce.Ya katse mamaki na da cewa, kizo kinji?Ba zan iya bacci ba ki taimake ni.Nace iya fa tana jinmu ka bari sai tayi bacci.Ya ce dagaske zakixo in jira ki? Na ce eh.Sai ya yanke niko gaba daya ma sai na kashewayar, na amsa masa cewa zan xo ne kurum amma ba dan zan je din ba, sai don ya barni.Kuma ko ba dan iya ba ina tsoro, tunda ban san yanda abubuwan suke ba.Na makele fulo ina tunanin ko a wane hali yake ciki yanzun, na jima kafin bacci ya tafi dani.Nayi mafarki kala kala masu dadi wai muna ta shawagi a cikin wata duniya ni da ya Ali.Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai masu nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com Kokuma ku kasance taredamu a facebook https://mbasic.facebook.com/HAUSA- Novels-389304544597988/?_e_pi=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
Da safe kuwa fuskarshi a murtike, don ko amsa
gaisuwata baiyi ba, lokacin da yazo gaida Iya ina
gai da shi,hakan bai yi min dadi ba, na kunna
waya ta na tura masa sakon ban hakuri tare da
ce masa jiya naso inzo Iya ce bata bari na fito
ba.Ko ya gani ko bai gani ba oho, bai dai bani
amsa ba, na dafa ruwan tea na kai mai na same
shi ya gama shirin fita yana daura ta kalmi.Na
shiga da sallama ciki ciki ya amsa, ina shiga ya
dubeni fuska daure ya ce, lfy?Cikin wata murya
irin ta a salin jarumin maza.Jiki na ya dauki bari
na ce, dama….dama tea ne.Ya ce fitan min da
shi ina azumi, fargaba na ya karu, iya ce jiya ta
fash….Ke!Ya katse ni, fita a nan dan Allah.Na fita
da sauri, zugun na zauna ina tunanin yanda ya
Ali yake canza launi tamkar hawainiya…
Kimanin kwanaki uku kenan yayi mun dif, inna
gaida shi baya amsawa, haka nan in abinci na kai
mai ko yaushe sai ya ce yana azumi.In iya tayi
mashi magana ke nan, in nice ma na kai mishi ni
abu sai ya koro ni, ina girki a kicin iya ta fita
lokacin sai ga Aisha kawata.Naji dadin zuwanta ta
tayani,muna fira na bata lbr duk halin da nike
ciki na kara da cewa, ya Aliyu gaba yake dani, iya
ta sa ido sosai dan ganin ban bada kai ga miji na
ba, ba tare da mun tare ba.Don Allah Aisha ki
bani shawara, ta ce, ni dainawa ganin in har zan
fada maki gaskiya kibi mijinki, daga lokacin da
aka daura muku aure da shi dukkannin hakkokin
shi sun hau kanki.Nayi ajiyar zuciya tace, nasan
kin san komai ma kina yi ne kamar baki sani ba
nace Aisha nasani,Iya fa idonta yana kanmu.Ko
daki na shiga sai kiga tana kai kawo, in na fito
kuma tayi ta yi mun kallon tuhuma, to ki bashi
shawarar ku fita wani wurin mana.Nace tap nice
ma zan bashi shawarar?To an ce maki iya za ta
barni in fita ne?Aisha ta ce, yanda kika gani,
amma in nice zan bi miji nane.Rayuwar nan ta
yanxu mata suna bin maza har inda suke,
balantana mijinki dan kwas irin wanda basu da
yawa a cikin jama’a?Ku ziyarci blog dinmu domin
karanta Littatafai masu nishadantarwa
Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?e_pi=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
Na ce nima ina tuna haka, shiyasa wlh ban so ba
da ban tare ba, kamar yarda ko wace Amarya
take tarewa a dakinta. Ki tayani da adu’a don sun
sani a tsakiya ita tana kallo na a mai rawar kai
na shige masa,shi yana kallo na mara
biyayya.Aisha ta ce, abu ne fa mai sauki ke ce
kika dauke shi da zafi, in kin bi mijinki kinga dole
ta barku.Na dubi Aisha ta ce, fa ba zai dubi
mutuncina ba, Aisha ta ce, in bai sameki a
mutuncenba ba?Kin bi maza ne?Na kai mata
duka, kinji ki da wani zance, in na bi tare muka
bi kenan.Ta ce ke ce da wani shirme, in kin ga
namiji yaga rashin mutuncinki ya sameki kin bi
wasu….(Biri fa kuma yayi kama da
mutum,watakila irin haka tafaru da yar uwarki da
Zaria,shiyasa mijin yayi inkarin kasancewarvcinkin
a matsayin nasa,hartakai ga saki ANaM Dorayi)
Kalu bale ga masu saida mutuncinsu a banxa.
Aliyu tukur ya tsaya a gaban shugaban shashin su
na binciken manyan laifuka, mataimakin
Commissioner.Ya ce ASP Aliyu zanfi so idan kana
tsayawa a kan aikinka, ina nufin ka rinka
dakatawa a madakatarka.Sanan ka rage kishin ka,
domin kasar mu a yau in kace haka zakayi lallai
ba zaka kai ko ina ba.Ina yi maka magana ne a
kan barawon shanu din nan, mutumin mai girma
commissioner ne, na tabbata da yana gari baza
ka kamashi ba bare tsarewa.Inma kayi nasara ka
kama shi, ba zaiyi minti talatin a tsare ba kai ba
a taba kama shi ba, yaranshi kurum ake
kamawa.Da sunyi waya da commissioner zaisa a
sake su, nayi mamakin ma da commissioner bai
tsawatar maka ba, ya ce kawai ka bar case din a
hannunsa.Ran Aliyu ya baci, shi da ya shiga aikin
dan sanda kishin kasarshi da kawo gyara, sai
kuma su rinka ganin barna suna kauda kai?Ya ce,
yallabai ina rantsuwar da mukayi da alkur’ni
cewa zamuyi aiki tukuru bisa amana da gaskiya,
idan dannanda bai zama mai kishi da gaskiya me
za a kirashi?Idan dan sanda zai rinka amsar cin
hanci yana hulda da manyan azzalumai yana
daurewa barayi gindi suna zalunci, za a kirashi
mai tsaron lafiya al’umma.AC ya dagawa aliyu
hannu, dakata ASP, wannan tambayoyin zasu fi
dacewa kayiwa CP su, ni shawara na baka.Da
akwai mutane irinka da yawa wadanda suka
nuna kishi, wasu anyi musu canjin gurin aiki zuwa
wasu garuruwan da ba zasu sami irin wanan
barnar ba bare suyi gyara.Wasu anyi musu sharri
an koresu, kai wasu sun mutu yayin da wasu da
yawa suka ajiye hularsu.Ban hanaka yin kishi da
gaskiya tare da kin karbar cin hanci ba, sai dai
ina mai baka shawara ka dinga tsayawa ga
kananan masu laifi, jeka abinka.
Aliyu yana zaune a office din shi, kansa ya dauki
zafi yana tuno sa’insa da sukayi da Barawon
shanun, inda barawon yace, kai yaro wanan ba
wani bakon abu bane satar shanun da muke
yi.Haka nan mu nan Headquarter gidan mu ne
kaine mutum na farko da na taba bawa cin hanci
ya maido mini.Nafi tunanin kana daga cikin
mutanen da basu da rabo, amma kai bako ne
ko?Aliyu ya ce, ba jin tarihi ko maganar cin hanci
na xo ba, nazo nan ne dan in kama ka,a
matsayinka na mai laifi, ni kuma na hukuma.Duk
wadan nan baya nan zasu biyo baya in munje
office, yaranka muka kama kuma suka ja
sunanka.Barawon ya zaro ido tare da daga murya
ya ce, kai bako ne shiyasa baka sanni ba amma
muje.Aliyu ya ce nasan ko ban sanka ba, bako ne
ni bako ne wannan ba damuwata ba ce.Ku ziyarci
blog dinmu domin karanta Littatafai masu
nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?e_pi=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
Sun san Aliyu bai san wanene wanan barawon
ba, shi kanshi barawon cewa yayi zakayi da
nasanin kamani.Aliyu bai ce kala ba, ya nufi
Office din sa zuciyarshi cike da son nunawa
wanan baron cewa hukuma bai bar
kowaba.Amma me? daidai lokacin da yake bada
ummarnin ashigar da kara ne shugaban shashin
su AC ya ce, kajira tukunna sai an sami ummurni
daga commissioner.Dafawar da akayi mashi itace
ta dawo dashi daga dogon tunaninsa.Ya dago
kai.Insperctor kamal kaita ne ya ce Sir, ka daina
damuwa da irin wadan nan matsalolin, sanan ka
ci gaba da yanda kake, Allah zai kawo maka
dauki dan yana tare da irinku.Sai dai dama baku
cika farin jini ba a cikin yan sanda, saboda kowa
yana ganin cewa zaku toshe masa kafar
samu.Shawarata ka bar batun Barawon nan ko
ba komai kayi namiji tunda ka kamo shi, ka kuma
tsare shi.Sanan Allah ya doraka a kan CP bai
dauki zafi a kanka ba.Aliyu ya mike tsaye, na
shigo aikin dansanda cike da kishi da buri, gami
da kwazo.Manufata insamu waddanda zasu
fahimci niyyata don mu kawo gyara cikin
hukumar yan sanda.Na tabbata ko cikin
headquarter din nan akwai masu kishi da yawa
wadanda suke jin irin abinda nake ji yanxu a
zuciyata. Inspector ya ce, hada dani, sai dai ina
mai bakin cikin sanar da kai cewa ba zamu kai
labari ba, tunda daga sama a ake tadiye mana
kafa.Aliyu yace inko haka ne zaya ci gaba da
faruwa, watarana zan iya ajiye hulana.Inspector
ya ce, ranka ya dade kada kasaka haka a ranka
tun yanxun, kaji a cikin xuciyarka cewa burinka ya
cika, Allah yana tare da mai gaskiya.Ranka ya
dade ka duba tashin farko bin diddiginka yasa
sashinmu na bincike suke shakkarka, ina son
mutum irinka.Aliyu ya lumshe ido tare da cewa
zantukanka sunyi mun allura inspector, zan kara
kaimi.Da wanan ya cigaba da aikin sa.Daf da zai
tashine aka shigo da wani da ake zargi, ya kalle
gobjejen mutumin sanan ya dubi yan sandan.Me
yayi shi kuma wanan? Sajan Ado ya ce, ranka ya
dade, kato kamar wanan aka kama yayiwa yar
shekara takwas fyde,ran Aliyu ya tunxura, ya
runtse ido cikin takaici, ya ware ido ya kalli
mutumin cikin tsana ya ce, wai wane irin
zaluncine wanan kuke yiwa jikokinku?Cikin rawar
murya mutumin ya ce ranka ya dade na rantse
maka ba ni bane, sharri sukayi min, na rantse
maka.Aliyu ya harareshi, ba kowa bane yake
amsa laifinsa da sauri.Ya kalli yan sandan suwaye
suka kama shi?Sajan ya ce ranka ya dade ga
mutanen da suka kawoshi can, sune suka
kamashi da yarinyar a shagon shi tana ihu.Yace
ina yarinyar yanxu?Sukace an tafi kaita Asibiti.Ya
kalli mutumin yaja tsaki ya ce, ya ce ku rufe shi,
yanxu ba wani sausauci ga irin mutanen nan
masu cutar da kananan yara ta ta hanyar fyade
Ya koma office din sa cikin ta kaicin fyadan nan,
kullum sai sun samu irin wanan case din da yar
da jarirai yafi yawa, amma yanzun yanaga zasu
xo daidai.Ya kira sajan ya ce, ya kawo masa
takardar tuhumar (statement) da ya duba tsaki
yaja, ya dubi sajan.Kullum dai abin iri daya ne.Ya
tabe baki, sanan ya dubi a gogonsa, yau shida
zan bar nan, duk wanda ya nemeni
saidasafe.Sajan ya sake kamewa tare da fadin
yes sir!Sai kuma wanan mutumin yaya za ayi da
shi?Aliyu ya ce, ba maganar beli ko wani ya zo
zuwa gobe za a hada bincike a turashi kotu.Sajan
ya sara masa sanan ya fito.Da dunbin wanan
damuwar ya iso gida, daga ganinshi kasan akwai
abin da yake damun shi, kan katifarshi ya zube
rigingine bata re da ya cire koda ta kalmi
ba.Lokacin da ya shigo ina zaune a kan kujera a
kofar daki ina karatun wani littafi (SIRRIN BOYE)
na Anty Bilkisu.Ga al’adarshi in ya shigo dakin Iya
yake fara shiga kafin ya dawo dakinsa, ya cire
kaya in sun gaisa.Ya shiga wanka.Amma yanxu
tunda ya shigo shiru, iya ta fitodaga bayi (ban
daki) na dubeta na ce, yaya fa?Ya dawo yanayin
shi kamar na mara lafiya, ko baya jin dadi ne?Ta
ce, ba wani ke dai kina sonzuwa gurin mijinki ne,
kuma ba zan hanaki ba.Na hade fuska, Allah iya
nifa ba wai zanje bane fa.Ta ce, kije ki duba ko
lfy,naki tashi, dan dama ina tsoron inje yayi mun
wulakancin shi, ya ce nafita shiyasa naki
zuwa.Ganin da iya tayi tabbas ba zan shiga ba
kuma tabbas bai fito ba sai ta shiga dakin. Yan
da ta ganshi warwas a katifa batare da ya cire ko
takalmi ba, sai abin ya bata tsoro.Cikin saurin
muyar ta ce, Gadanga!Ya dago kai da kyar ya
dubeta, wani matsanancin ciwon kai ke damun
sa.Ya ce na’am Iya sannu.Ya tashi zaune,
ciwonkai ne ya hanani shigowa ciki.Ta ce,
matarka nema ni take ce mun ka shigo cikin wani
yanayi, bari a kawo maka magani ka sha.Yace
zanje Asibiti in anjima bayan magariba.Duk
kwanakin nan da haka nake ta yawo da ciwon
kan nan.
Ta ce, to kasha maganin yan xu sai kayi sallar da
dan karfin jikinka, kaje asibitin da dan kwari.Ya
ce, to.Ta kwala min kira Sadiya.Na amsa ta ce,
dauko min magani panadol kizo da ruwa.Naje har
gabanshi na ajiye da ruwan ina yi mashi sannu
yaya, ya jikin?Ko kallo na baiyi ba bare ya amsa,
mamakin yanda naga iya tan gutsi gutsi da
maganin, ta dubeni dauko mun cokali.Na dauko
ta jika ta bashi a baki tare da fadin, shiyasa nake
fargaban ciwonka gadanga.Duk da dai ba yawan
ciwon kake ba, amma kin maganinka shi ke
wahalar da kai a ciwo dai dai yake da na yaron
goye.Shi yasa duk lokacin da katashi ciwo bama
jita dadi.Ya sha ya koma ya kwanta, dai dai
lokacin aka kwada kiran magariba.Ta dube ni,
bari inje inyi sallah, nima na biyo bayanta.Ta
dakatar dani da cewa, jira tukunna muga yanda
jikin zaiyi.A raina na raya cewa dan ta ga ina
fashin sallah, shi kuma bashi da lfy.Shi kam yana
kwance, na isa gurinsa gabana yana ta faduwa,
duk da ina zaton zai daka min tsawa ban fasa yin
abin da nayi niyya ba.Gabansa na tsugunna ina
kwance masa takalmi, na cire su na aje gyafe,
sanan na kwashi kafafunsa na zubasu a kan
katifar.Har lokacin idanunsa biyu amma suna
lumshe, haka nan hannunsa yana dafe da
kai.Kusan minti shabyar ina zaune can gefe, ya
tashi zaune yana kici kicin cire rigarsa, na taso na
balle masa boturan, sanan na sabule rigar sai
farar singiletin, ita ma ya kama ya cire.Na kalli
kirjinshi gashi ne kwance na kauda kai don sai da
naji wani iri.Ya sabule wandonshi, sai gajere na
ciki, shima na kwashe su na zaba su a cikin
kwandon da yake zubawa.Naga yana kokarin
tashi nace mai zaka dauko in dauko maka?Ka
zauna kawai.Ya ce, bani jallabiyata.Na bashi fara
kal mai dogon hannu, ya mike zai fita, na ce ina
zaka je?Ya ce masallaci.Yana fita na shiga gyaran
dakin, ban taba yi masa gyaran daki ba sai
yau.Ko yaushe da kansa yake yin gyaran dakinsa,
nayi zaton zanga mujallun da na taba gani da, sai
kuma ban gani ba, har na gama.Iya ta idar da
sallah, ta sake lekowa ko ya tashi, na ce ya je yin
sallah, shiru shiru ashe daga can ya tafi
asibiti.Har kusan tara gashi bai fita da waya
ba.Iya da kanta ta fita har masallaci layin mu,
wanda suke sallah tana nemanshi.Duk wanda ta
tambaya sai su ce mata tare dai suka idar da
sallar isha’i.Da ta dawo sai na ce mata ko dai
yatafi Asibintin da ya ambata ne?Ta ce zata iya
yuwuwa ya tafin, tun da ya ambata.Nan dai
muka zauna zaman jiran tsammani,mun kasa ko
cin abinci.Sai sha dayan dare da yan mintuna
dan acaba ya sauke shi, ni da iya har rige rigen
fita muka yi, shi ne muka yi masa sannu ya
amsa, iya ta ce, muna ta neman ka.Ya ce, natafi
Asibiti ne shi yasa ciwon kai ya matsa min da
yawa.Amma na sami allura da magunguna, kuma
na kwanta canne kamar yanda likitan ya ce in
dan huta, Alhamdulillahi kai yayi sauki.Ta ce to
me zakaci yanzun?Ya ce, nasha tea a can kafin
ayi min allura, muka shiga dakin shi ya zauna
bakin gado.Iya ta fita nima na mike zan fita, sai
ta ce ki dan tsaya ke saboda dare ko?Na koma
na zauna ya kwanta tare da lumshe ido.
Wayarshi tayi ringign, ya daga ya kalla sannan
yaja tsaki, bari na kashe wayar nan ina so in dan
huta.Har zai kashe sai ga ma bari yayi anfani da
wanan damar ya nunawa sadiya anafa ribibin shi
har da take masa yan ga.Don haka sai ya daga ni
dai naji yana fadin yaya mati na me ya faru ne?
Ban zaci jin muryarta ba, ashe ya saka
hanfree.Sai kurum naji ta ce, lafiya lau sir, ban
gankaba ne an ce ka tashi tun six, ya ce akwai
wata matsala ne matina?Ta ce babu, naso in
ganka kawai, kayi hakuri kasan ganinka kawai
yana cire min damuwa dayawa, dayawa, amma
sir sai kanayi kamar baka san haka ba.Yace
matina yanzu bani da lafiya ne, ban dade da
dawowa daga Asibiti ba in nafito da safe zamuyi
maganar.Ta ce to Sir, nagode Allah ya kawo
sauki.Raina yayi mugun baci, a gabana yake
magana da wata arniya har take ce masa ganin
shi yana sata sukunni da kwanciyar hankali?Yana
ajiye wayar ya kalleni, na hada rai matuka na
mike ya ce, ina zaki?Nace zanje in ci abinci ne, da
kyar nake magana.Ya ce, au dama baki ci abinci
ba?Kamar in kai masa duka don ta kaici.Mutumin
da yayi nasa guri bai fada muna ba muka yi tsuru
tsuru cikin damuwa.Shine zai ce dama ban ci
abinci, ya mai maita tambayar nace um, ya ce
kina ciwon baki ne?Nayi shiru yace in kin ci ki
dawo, tunda Allah yasa yau naji da kunnena ba
iya ce take hanaki zuwa wurina ba, karya kike yi
mata.Ban tanka shi ba na wuce, a raina na ce ba
zan dawo baCan kusan daya saura ina ta tubka
da warwara na kasa bacci, ni nasan kaina ina da
mugun kishi, sai ga sako ya shigo cikin wayata
cewa ba zaki dawo bane?Na tura masa amsa da
cewa eh, ka kira Matina.Yana ganin haka yayi ta
dariya, sakonshi ya kai ke nan, don haka shima
kurum sai ya kashe wayarsa ya kwnta.Da Asubahi
iya taje dubashi ta sake shiga dan duba shi, sai
ta samu jiki yayi sauki, har ma ya tafi
masallaci.Don ya Aliyu ba rago bane namiji ne, ga
juriya da izza, matsalarsa daya in yana ciwo kin
magani,yayi tawa iya shagwaba sai kace karamin
yaro, shi a dole auta.Nikam har gari yayi haske
ban tashi daga makwanci na ba, tunda ina fashin
Sallah ba wai ina bacci bane kurum takaici ne ya
hanani tashi.Jiya ko baccin kirki banyi ba, saboda
takaicin ya Aliyu.Iya ta shigo, ke ba zaki tashi kije
ki gano mijinki ba?Ko da nafito kin xuwa nayi na
debi ruwa na shiga wanka.Ina fitowa nayi zaman
shafa mai duk ina jan lokaci ne don yayi abinda
zaiyi ya kama gabanshi.Bana ma ko son ganinshi,
lokacin da na shirya na nufi kicin a tsammanina
ya fita.Ina tsakiyar kunna risho sai naga mutum a
kofar kicin tsaye.Na rasa dalili in zan ga ya Aliyu
sai gabana ya fadi.Na kalli fuskarshi, gaskiya har
ya dan rame na ce ina yini?Ya ce ban yini ba, ni
yanxu zafiya ce, sanan ba zan amsa ba tunda
baki san hanyar daki na da bazakije ki gaida ni
ba.A raina na ce ina matina?Ita batazo ta duba
ka ba?Ya katse tunanin da cewa,ruwan zafi nake
so zanyi wanka.Na kalleshi, ban taba ganin yayi
wanka da ruwan zafi ba, nace to bari in dora
yanzun, bai ce, kala ba ya koma daki.Da yayi zafi
na sirka na kai masa ban daki, sai naje na ce
masa ga ruwa can.Lokacin yana waya, da hannu
yayi min alamar cewa in je yaji.Na tsargu da wa
yake waya, don haka da nasaki labule sai na
tsaya.Ji nayi yana cewa, kada ki damu, yanzu
zanfito.Jikina yayi sauki, ai da tunaninki na kwana
araina.Na girgiza kai tare da yin kwafa.Tabbas da
matina yake yin waya, nayi kicin ina yin magana
ni kadai, na ce to ita wanan shegiyar matinar me
ke tsakaninsu?Nemanta yake yi ko me?Wata
zuciyar ta katseni da cewa, ba kina gudunsa ba?
Ai ga Matina zata maye gurbinki. Jikina ya sake
mutuwa, na shiga tambayar kaina mafita.Wunin
ranar sukuku nayi shi, na kasa tuna yanda zan
bullowa abin.Duk jin su iya nake ko da can da
suke cewa ba ruwanshi da mata, ni nasan da
ruwanshi tunda ni naga mujallun batsa a dakin
shi.Wanda baruwanshi da da mata me ya
ruwanshi da irin kallon tsiraici?Dole ke nan inyi
yakin rabashi da matan banza.Wata zuciyar tace
haka ba zata yuwu ba, sai in zakiyi aikinki a
matsayin matarsa, lallai saikin mika kanki a fili na
ce ya na iya?Ku ziyarci blog dinmu domin karanta
Littatafai masu nishadantarwa
Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?e_pi=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
Muna zaune a falo da iya washe gari da safe,
yazo yiwa iya sallama zai fita, nima na bude
baki da nufin ce masa sai ka dawo.Amma da
yake matina ce a raina sai kurum naji na ce
masa ka gaishe mun da matina.Har ya juya sai
naga ya tsaya cak, sanan ya waiwayo fiskarsa
dauke da murmushi ya furta cewa zataji in sha
Allahu.Ya juya ya tafi, ni kam kamewa nayi
tamkar gunki, a zuciyata tambayar kaina nake
dama mutun na iya kuskuren magana ya furta
abinda ke son zuciyarshi ya bar na saman leben
shi?Kash!Ban so nayi zarar bunun nan ba, abin
takaici harda murmushi na ambaci sunan
masoyiyarshi.
Kwana uku suka shude ina cikin damuwa,na san
Iya ta lura banza kawai tayi mun,narasa abinda
ke yi min dadi, ni ba fita nake ko ina ba, ba TV
Garemu ba bare nayi kallo, ta lalace ni kuma ba
ma abociyar radiyo ba.Wani kayan haushi ko
littafi na dauka da sunan karantawa sai in kasa
fahimtar komai.Na san kaina ina da shegen kishi
na ban mamaki, ko saurayina naga suna yawan
gaisawa da wata budurwa hankalina kan tashi,
bare a ce miji na.Tabbas da Ya Aliyu ya skar min
fuska da tuni na same shi munyi ta, amma ya
Aliyu ya wuce haka.Ku ziyarci blog dinmu domin
karanta Littatafai masu nishadantarwa
Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?e_pi=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
Cikin sauri sauri ya Aliyu ya shiga shashin su, ya
kalli sajan Ado ina barawon?Suka kaishi ya
shiga.Ya tsura mutumin ido, aransshi ya ya ce
kai wanan mutumin baiyi kama da barawo
ba.Ya kalli Sajan, kawo abin zama, sai da ya
zauna sanan ya kalli mutumin.Kaine barawon fili
ko?Hawaye suka soma kwarara daga idanun
tsohon, don bakin cikin sunan da aka kirashi.Ya
ce cikin rawar murya, ranka ya dade ni ba
barawo bane, ban taba sata ba.Aliyu ya juya
kulkin dake hannunshi ya dan jefashi, sanan ya
cafke.To baba ya akayi har ka mallaki filin da
kake gini?Ya ce, ran ka ya dade filin nan na
gajeshi ne a gurin mahaifiyata, don mahaifinta
manomine.To ina zaune a gidan haya ga iyali,
ina da mace daya ga yaya takwas.Yan samarin
yara na a makota na roka sunakwana, ganin
kullum nauyi na karuwa, sai nayake shawarar
gina fili na ko da daki biyu ne rak.Na soma gini
ni da yaya na, dan sana’ar mu ke nan ta
leburanci da yaran.Mun soma ginin kawai sai
ganin yan sanda nayi sun xo kamani, ban san
abinda nayi ba.Aliyu ya ce, to baba naga
takardar bayanin laifinka, naga cewa ana
zarginka da laifin yingini a filin da ba naka ba,
filin tsohon jami’in dan sanda ne.Tsoho ya ce,
dana wlh wanan filin nawa ne, kowa ya sani a
unguwar mu ina da takarduna ina da
sheduna.Kuma ni da aka kawoni nan ba a
tambayeni ankawoni nan aka jehoni ne
kawai.Babu wanda yaji ta bakina.Aliyu ya ce ka
tabbata kana da takardu da shedu?Tsoho ya ce
ina dasu ranka ya dade.Aliyu yace zamu mikaka
kotu kuma in sha Allah zan tsaya maka sai kayi
nasara.Cikin izza ya nufi wajensu Sajan Ado,
yace sajan, yace Sir, bayan ya kame.Aliyu yace
waye ya kawo wanan mutumin?Sajan ya ce,
barawon fili?Aliyu ya ce, eh shi.Sajan ya ce CP
ne yasa a kamo shi.CP da kanshi?Ya tambaya
cikin mamaki.Yace shi, amma AC ne ya tura.Kan
Aliyu ya daure, ina takardar bayanan da kuka
bani dazu?Sajan ya sake daukota, Aliyu ya kalla
ya sake karantawa, wanan rubutun kofur bala
ne ai, sajan ya ce, eh, Aliyu ya ce kira min
shi.Ya juyya ya koma office din shi.Ya tsare
kofur da idanun shi waddanda basadaukar raini,
kainne ka rubuta wanan takardar ko?Ya kame,
eh, nine Sir, ya juyya mishi baya, amma ai baka
tambaye shi ba ka rubuta da yawun shi.Ko
menene dalilinka?Kofur cikin daburcewa ya
ce,Sir ai nima AC ne ya ce na rubuta haka, sabo
da raini mutumin yake so ya kawo wa tsohon
mataimakin IG.Aliyu ya daga hannu da nufin
dakatar dashi, tsaya min kowa ya cuta sai a ari
bakinsa a ci mai albasa?Ya ninke takardar ya
zura cikin aljuhunsa, yace dauko wata kazo muje
ka sake rubuta ainihin bayanin da yake daga
bakinsa, mu masu kare Al’umma ne da
rayukansu ba masu danne masu hakkin ba ne
da kuma kashe su.Kofur dake biye dashi ya ce,
sir, wanan tsohon mataimakin IG yana yawan
kawo mana matsalolinshi a nan, kullum
maganarshi bata wuce an cuceshi.Ku ziyarci blog
dinmu domin karanta Littatafai masu
nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?e_pi=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
Aliyu ya ce dan ya taba zama jami’in dan sanda
bazaiyi anfani da wanan damar ba, sanan yayi
anfani da mu.Alkawari na daukarwa kaina ba
zan bar zalunci ba, matsawar naganshi zanyi
yaki dashi.Aliyu ya tsananta bincike kuma cikin
kwanaki kadan yagano cutar tsoho wanan
jami’in ke son yi, don hakka ya tattara dukkan
bayanai ya turasu zuwa kotu.Gobe da safe ya
tabbata in anje can tsohon zai sami hakkinsa,
saboda bayanai da hujjojin da Aliyu ya
hada.Yana tsaye a bakin titi zai hau a caba zuwa
gida Inspector Kamal ya sameshi a gurin, ya ce
ranka ya dade zuwa yanzu yakamata a ce ka
mallaki abin hawa ko da mashin, amma in san
samu ne a ce kana da mota.Aliyu yayi
murmushi, kada kadamu, ko mai lokaci ne, ya
ce in dauko maka na aiki mana ba sai ka sha
mai ba?Aliyu ya ce, a a na aiki anyi shi ne dan
aiki kawai.Ispector ya ce, kana birgeni Sir, komai
kana barinsa a muhallinsa.Lokacin da aka raba
mana mashina baka zoba.Aliyu ya ce, ko ina
nan ba zan amsa ba, don bana son bashi.Ya
karasa zancen tare da tare dan acaba.Wayyarshi
ta dauki tsiwa, ya cirota cikin hanzari ya daga
saboda ganin sunan AC, hakuri ya baiwa dan
acaban, sanan ya komaciki kamar yanda AC ya
bukata a cikin officeya same shi, kai kawo yake
ransa a bace ya dubi Aliyu.Me yasa ba bada
damar a kai barawon filin nan kotu?Aliyu ya ce,
angama bincike ne sir, sanan doka ta hana a
tsare mutum tsawan lokaci ba tare da an kaishi
kotu ba.AC ya ce, na san dai na rigaka sa kaki
ko?Bai jira amsa ba ya ci gaba da cewa, don
haka kasan na rigaka sanin doka.Ya koma
kujerarshi ya zauna.Wanene ya hada binciken?
Kai kasan ma da wa yake rigimar?Kasan filin
wayake son kwacewa?Aliyu ya ce, nine da kaina
nayi binciken sanan nasan rigimarsu shi da
tsohon IG ne, kuma CP ne ya sa a kawoshi.AC
ya ce, gud, to zan sake mai maita maka, in an
kawo mai laifi da umurnin CP dan Allah ba
ruwanka da shi, in zaya shekara.Ran Aliyu ya
baci, ya ce, Sir, amma ba akan haka mukayi
rantsuwa ba.AC ya daga masa hannu ban ce
maka inason tunatarwa ba, sai dai ina son
kasani ka kusan kai CP bango, dan kana son
shiga cikin lamarinsa.Sanan kayi hanzarin cire
kanka daga cikin lamarin tsohon, ka barsa yayi
nashi binciken.Shiru Aliyu yayi, amma ji yake
tamkar ya kama da wuta don zuciya.AC ya ce,
ka iya tafiya.Aliyu ya fice da kunan rai.Matina ta
hangoshi cikin sauri ta bishi, yana tsayawa a
bakin titi tana tsayawa, ta ce barka da warhaka
yallabai.Ya furzar da wani huci mai zafi, sanan
ya ce barka dai.Tace ina tuni yallabai ya runtse
ido don yanason saita zafin da zuciyarshi ke
yi.Baya so ta fahimci yana cikin damuwa, sanan
ya budesu sun kada sunyi ja, sanan ya ce
matina zanfiso mu zauna a matsayin abokai, na
fada maki bani da sha’awar auran mata
biyu.Ina yi maki adu’ar samun mijin da ya
fini.Ta ce, samun kamarka ne yallabai sai an
tona, kunyi karanci a cikin al’umma.Ba duka
namiji mace kamata zata bashi kanta ya kauda
kai, har yanxu ina tuna ranar, ranar da na fada
maka ni da kai muyi soyayya koda bamuyi aure
ba.Ku ziyarci blog dinmu domin karanta
Littatafai masu nishadantarwa
Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?e_pi=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
Na fada maka cewa wata gara basa da zan
maka shi ne, zaka iya yin duk yadda kake
sodani na mallaka maka kaina, amma sai kayi
mun nasiha ka kuma nuna min cewa addininka
ya yi hani da hakan.Na sami kaina da sonka
tare da son addininka, sanan cikin aikinka kowa
yasan kana kwatanta gaskiya da amana.Ina
tsoron in auri wani cikin masu addininku ya sake
ni, dan ku hausawa ance kuna da sakin aure
amma kai nasan ba zakayi haka ba.Aliyu ya
kasa kallonta dan ta daureshi da jijiyoyin
jikinsa.Ya ce, Matina ki amshi addinina da zuciya
daya, sanan kisa a ranki zaki sami mijin da ya
fini, nima zan tayaki da adu’a.Ta gyara tsayuwa
kada ka damu, ni zan ci gaba da zaman samun
irinka, alfarma daya nake roko in zaiyuwu, in na
kiraka ka daga wayata.Sanan in kazo nan muke
rinka gaisawa.Ya ce dan mun hadu mun gaisa
ba damuwa,abin da zaiyi dan wuya ki rinka
kirana ina da mata, nasan bazata so hakan
ba.Ta rausayar da kai gefe, cikin raunaniyar
murya ta ce, na gode,ka fadiwa matarka cewa
ta rikeka da kyau, dan tana cikin matan da
sukayi sa’ar zuwa duniya.Murmushi yayi duk
lokacin da kuka hadu saiki fada mata da kanki,
na barki lfy.Yana kan mashin yana tunani ko me
yasa yake samun irin wanan matsalar?Mata suyi
ta sonshi suna binshi, amma shi bai damu da
su ba.Matina yana kulata ne saboda musulantar
da take sha’awar yi, ya san in yazama sanadiyya
zai sami ladan hakan.Daga nan tunanin sa ya
koma kan matsalarshi ta office, in dai da irinsu
AC da PC anya kasar nan zata gyaru?Lallai
kasarsa Nageria tana cikin wani hali, kullum
burin nasama ya danne na kasa, sam ba a son
gaskiya.In ka tsayawa halas dinka sai mutane su
rinka yi maka kallon dan kauye.Ya girgiza kai
sakamakon tuno tsohon nan da yayi, shi da
gaskiyarshi da filin sa da komai ba a tausaya
masa ba, kasancewarshi mai rauni ana neman a
zalunce shi.Mai dama yana anfani da damarsa
gurin cutar mai rauni, yasan in ba wani ikon
Allah ba tsohon nan ya rasa filinsa kenan, in
yasamu ya fita da ransa kenan.Duk lokacin da
irin wanan ta faru sai yaji tamkar ya bar aikin
dansanda, amma da ya tuna kudirinshi na kawo
canji da gyara, sai ya hakura, da wanan sake
saken ya isa gida.
Niko tun lokacin da na furta masa cewa ka
gaishe da matina cikin kuskure, ban sake yarda
mun hadu dashi ba.Kusan kwana uku wasan
buya muke yi har iya ta fahimci cewa na guje
masa, amma bata nemi jin ba’asi ba, yi tayi ma
kamar bata san me ni ke yi ba.Sam ban zaci
dawowarshi a wanan lokacin ba, domin cikin
kwanakin nan sai dare yake dawowa.Ni kadaice
a gidan,Iya tun bayan la’asar sun tafi Asibitin
dutse duba wata makociyarmu da bata da
lafiya.Sun tafine da ma da sauran
makotanmu.Na wanke hijabaina da na Iya ina
shanyawa,daga ni sai best, zanina kuma iyarshi
kugu.Ina shanya ina mitar cewa iya sunje sunyi
zamansu, nasansu da son tafiyar kafa, yanzu
haka ma da kafa suka tako.Banji sallamarshi ba
sai dai naji ya ce ina suka tafi?Na waywaya na
kalle shi, da gudu na shige daki dan kirji na duk
a waje yake.Dan murmushi yayi sanan ya shige
dakinsa.Ina zaune bakin gado ina kallon jikina
sai ganin shi nayi tsaye a gaba na har uwar
daki.Ku ziyarci blog dinmu domin karanta
Littatafai masu nishadantarwa
Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?e_pi=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
Naja hijabina, ya ce ina tambayar iya kina gudu?
Ya hade fuska tamkar bai taba dariya ba.Tsoro
ya darsu a raina, cikin in ina na ce,Asibiti suka
tafi.Ya ce, dan kada ki bani amsa shine kika
kwasa da gudu?Nayi shiru, ya ce kin min
banza.Nace yi hakuri dama zan dauko dan kwali
nein daura.Ya ce, ok, ni zaki boye min gashin
kanki?To ajiye hijabin in ga gashin tunda halas
dina ne.Gabana ya soma faduwa, na zame
Hijabina ya ce ashe ma ba wani gashi kike dashi
ba, cire hijabin daga jikinki in gani.Na kalleshi da
sauri ya kauda fuska yana yatsina baki, sai kace
zai ga abin kyama.Na cire hijabin na ajiye cikin
sauri kuma na sa hannuna na rufe kirjina.Ya ce
cire hannunki.Na cire tare da runtse idanuna.Sai
kurum naji yasa hannu ya turani baya, na fadi
rigingine na bude idanuna da sauri ina tsoro,
yasa hannu ya janyo best din sai ta yage, kirjina
ya bayyana.Tsayawa yayi yana kare mun kallo,
ya tabe baki, dama best din taki rubabiya ce?
Sallamar iya ta tsakar gida ce ta sani tashi
zumbur, na dauki hijabi saka.Cikin tsoro mai
tsanani na ce ga iya nan.Shi kam ko a jikinshi.Ya
tabe baki tare da daga gira sai me?A zato na bai
fahimci nufina ba, don haka sai nayi nufin
fahimtar da shi katafi da sauri kada ta ganka a
nan tayi zaton ko wani abu ne.Sai naga kurum
ya zauna bakin gado, na zaro ido dai dai lokacin
da ta shigo falo tana cewa Sadiya ina kika shige
ne?Kin ganmu sai ynzu?Da sauri na fito cikin in
ina na ce gani nan, kun…kun dawo?Eh, lafiya
na ganki a hargitse?Ta ce ba ko mai.Na yi
waje.Ita kuma ta nufi uwar daki, gabana yana
faduwa.Tana shiga ta ganshi zaune bakin gado
yanawaya, ta ce au, ka dawo?Ya ce, eh, na
dawo tun dazu, waye babu lafiya kika tafi
asibiti?Tace matar mai besfa ce a asibiti mukaje
duba ta.Ya ce, Allah ya bata lafiya.Ya mike bari
in karasa masallaci.Sai tin kunne na naji
maganar shi, a hankali yace sarkin tsoro.
Sam ya kasa bacci abin da ya kalla daga
yarinyar kurum yake tunanowa, juyi yayi har
gari ya waye sai ya dauki waya da nufin kiranta
dan yana togon cewa ita din halas dinsa ce.Sai
kuma ya tuna cewa yarinyar ba zatazoba, sanan
ga iya, kai!Shi fa ba zai iya jira sai sun tare
ba.Da safe naje kai masa abin kari, lokacin ya
gama shirin fita kawai zaiyi, ya amshi kofin daga
hannuna ya kurba.Sanan ya kalleni kin kawo a
latti, kin san da wuri nake fita. Na ce, a
shanarmu ce ta jike shi yasa, sai da masu shago
suka bude iya ta fita ta siyo.Ya ce my choice.Na
kalleshi zan sunkuyar da kai, ya ce a a kada ki
sunkuyar da kai, kalli cikin idona, bana son
wanan sunkuyar taki tana cutar dani.Na kalli
idon shi, ya ce yau ina bukatarki, na gaji ina da
mata kullum nine cikin azumi.Nayi kwalkwal zan
soma kuka, ya tsareni da idonshi, ya kuma
hanani sukuyar da kai.Cikin raunaniyar murya
na ce, kasan dai iya ba zata bari ba.Ya ce daina
karya da iya, na gano ma ba ita take hana ki ba
tun da ranar nan in an ji ta ce ki zauna da ni,
lokacin bani da lafiya.Ya mika min kofin tare da
cewa, zan fada mata, jeki abinki.Na tafi ina
mamakin shi, musanman da naji ya ce zai
fadawa iya zanso inji ko me zai ce mata na kasa
karyawa don zullumi, ina ta juya biredin dake
gaba na, kamshin turarenshi ne yasa gabana
faduwa.
Ya ce, iya na tafi.Ta ce to auta na, Allah ya
tsare.Ya ce, amin.Yana wucewa na sauke a jiyar
zuciya.Cikin jin dadi na gutsire biredi, na dago
kofin shayi na kurba sai naji takun sawunsa ya
dawo, take naji shayin ya sane.Ya ce au, na
manta iya.Ta ce, na’am iya za a zo a dauketa
taje ta gaida matar oga, ko bani ba wani zaizo
daukarta. Na kalli iya, shi dama vai jira amsaba
ya tafi, ganin kallon da take min sai na tsargu,
na taihashashen baki muka hada.Don haka na
ce, iya ke ce masa ba zanje ba,Allah ni bana son
xuwa.Ta harareni, bakya son zuwa ne kika bari
ya tafi baki ce ba zaki ba, sai nice zance karki
je? Bayan kun kitsa abinku?Ta taba baki haba
yayan nan, na fa rigaku zuwa duniyar har da
kuke son maidani wata sakara. Na ce iyya Allah
ba haka bane, ba mu kitsa komai ba, ni bansan
ko mai akai ba, ban san da wata magana ba sai
da yayi yanxun. Ta ce kwaji da shi, nifa bance
kada kije ba, ke da mijinki zan hana ki?Ta fada
cikin gatse sanan tayi tsakar gida tabarni zaune
cikin damuwa.Da naga har la’asar babu wanda
yazo nemana, kuma shi bai dawo ba, sai naji
dadi kuma na dan saki jikina. Cikin haka wayata
ta fara ruri, na daga a raina ina adu’ar Allah
yasa ya ce an fasa.Sai naji ya ce ki shirya
Usman zaizo ku taho.Sai da na daga murya
yanda iya zata jiyo, sanan na ce, yaya, Allah iya
ta ce bazanje ba. Iya daga inda take ta ce, a a
ba ruwa na ni Sa’adatu, ban hanaki ba ni ko
baku hada baki ba ni yar bada shawara ce.Yace
to najiyo abinda iya ta fada, don haka na baki
minti talatin ki shirya.Sai ya kashe wayarshi.Na
ce na bani yanxu yaya zanyi?Don Allah ku bani
shawara, inbi mijina ko in nunawa iya
harshashenta ba haka bane?
Taku Halima K/Mashi kemuku godiya. Awanna
gabarma Kanwarku Sadiya tana neman shawarar
ku, Saimun hadu a cikin littafi na biyu.Ku ziyarci
blog dinmu domin karanta Littatafai masu
nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?e_pi=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347

Zaharaddeen Shomar
Whatsapp 08168575100

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button