Hausa Novels

Darajar ya yana part two 2

Darajar Yayana2-01
Posted by ANaM Dorayi on 09:52 AM, 20-Mar-16
Under: DARAJAR ‘YA’YANA
__________________NA ___________HALIMA K/MASHI Assalamu’alaikum, barkanmu da warhaka fatan kuna lafiya,nasan kunjini shiru a cikin wannan littafin,lallai kam kusan incemuku babu wani kwakwkwaran dalili face rashin kulawa daga gareku,saidai dayake ni nayi niyya dole incigaba,da wannan nake bawa masu yawan bibiyata hakuri,In Allah ya yarda da sannu zamu kai har karshen littafin, Na tashi na shiga wanka ina yan kun kunai,ko kallona Iya bata yi ba, sosai nayi gayu atanfa fara da sirkin purple ne. Haka takalmana da mayafina duk purple ne, na fesa turaruka sosai.Iya ta kalleni ta ce, da ma na san kun hada bakine shi ne za a gwada min bariki, in dai namijine kuje Allah ya taimaka. Ni dai nayi sororo raina babu dadi, sannan bani da mifita.Har cikin gida Usman ya shigo suka gaisa da Iya, sanan yace zamuje ne ta gaida Ogansu Aliyu.Iya ta ce, menene na shirya karya Usman ku da matarku.Nina haifeku fa har da kukega zaku yi mun wayo, a gaida Gyambo karshen girma kenanko? Usman ya sunkuyar da kai yana dan murmushi cikin jin kunya, ni dai na ce sai na dawo.Da mota yazo na shiga, gidansa muka fara zuwa ya ce inga Abida matarsa minti biyu. Ina yin sallama ta amsa, sanan ta ce kai Amarya kin tsula kyau sosai, taja hannuna zuwa bedroom din ta. Zo muyi yar shawara,Bakin gado muka zauna.Ta kalleni a da banyi zaton zaki zama mai taurin kai ba.Na zaro ido ina kallonta, ta ce, ranar juma’a da daddare mijiki nan ya ci abinci tare da mijina, ina daga ciki ina juyo su mijinki yana fadawa mijina halin da yake ciki na takura.Gashi kinki ki bashi hadinkai, har yana cewa wani dare da kika ki sauraranshi har ya dagawaya ya kira wata yar sanda dake nacin sonshi ta kuma sadaukar da kanta gareshi.Har ta daga sai kuma tsoron Allah ya shige shi, Allah ya taimaka ya tashi ya shiga yin nafila, daba dan haka ta faru ba, me kike tsammani?Na ce, wai Allah, daga nan sai zina.Tace kina da kwamasho ko baki da shi?Na ce, ina dashi.Madallah.Ta dafani yanxu abinda nakeso dake, kinga ke yar zamani ce, ki rike mijinki, in ba haka ba sai wasu su rike maki shi.Na ce, anty iya ce, Allah ba dan Iya ba zanyi duk abin da yake so.Ta ce, to baga shi yau zaku fita ba, in kin dawo Iya ganewa zatayi?In ba ke kika fada mata ba.Nayi shiru ta ce, to kisani kina cikin tsinuwar ubangiji, in yanxu kika mutu mijinki yana cikin wanan halin sai kin hadu da fushin Allah, ma tsawar ba shi ya yafe maki ba.Gabana ya shiga faduwa, na ce, Allah anty nitsoro nake ji ban san yaya abubuwan suke ba, nima bansan yana fushi dani.Tayi murmushi ba wani wahala.Ta girgiza kafadarta, ki amince da mijinki a duk lokacin da ya bukaci haka na rokeki.Na raunana muryata, in na sa muku aure ba?Na ce eh.Ta ce ki ceci kanki daga halaka fa, kin san komai ke ba jahila bace….Muryar Usman ta katsemu da cewa wai me kike kitsa mata ne?Zo mutafi kinji.Ta ce, jeki kada yajimu basusan naji firarsu ba, dan Allah ki kama mijinki hannu bibbiyu ko bakya son shi?Na sunkuyar da kai ina sonshi mana, bari dai in gani ko zan iya ina tsoro.Na fita muka tafi.,ban san ina muke tafiya ba, don kaina yana sunkuye ne ina wasa da yatsuna.Har zuwa lokacin da motar ta tsaya.Ina daga kaina COMMAND GUEST na gani.Ya ce jirani kadan ina zuwa.Gaba na ya shiga faduwa, koda ban san ko inane nan ba na tabbata Hotel ne tunda naga an rubuta guest.Bayan wasu lokuta ya dawo yana waya, danhaka da hannu ya yafito ni, na fito a baya nabishi yana ci gaba da tafiya tare da tin waya.Kuma na fahimci kamar da ya Aliyu suke magana, dan naji yana fada mai ga mu nan yanxu zamu shiga cikin hotel din.Kuma ni zan wuce ne dan Allah kayi hanzari muka ratsa falon muka nufi jerin dakuna yasa makulli yana bude wani daki.Dai dai lokacin sako ya shigo cikin daki wayata, na ciro na duba.Cewa yayi kishiga kijirani kadan my choice.Na kalli Usman yayi murmushi ba da jimawaba zai zo, yanzu zaki ganshi.Na shiga cikin dakin ina dari dari, tare da yankalle kale, ya tako ya shigo dakin.Kada ki damu ya dauki remote ya kunna TV, kiyi kallo ga tashar India nan abin sonku mata.Ya nuna mata wata takarda.In kina da muradin wani abu ga wanan takardan ga numbe waya ki kira ki zabi dayadaga nau’in abincin da kike so ko na sha, za a kawo miki.Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai masu nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com Kokuma ku kasance taredamu a facebook https://mbasic.facebook.com/HAUSA- Novels-389304544597988/?_e_pi=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
Har ya kai bakin kofa sai kuma ya dawo, ya ciro
wallet dinsa ya bude ya ciro katin MTN ya miko
min.Gashi ki loda a wayarki.Ya sake juyawa ya
tafi, tare da cewa ki kulle kofar in yazo zai
kwankwasa sai ki bude, na barki lafiya.A sanyaye
na ce, na gode.Tunda ya fita ta gumi na hada,
tunani da zullumin abu biyu ne na farko in ya zo
mai zai faru?Sanan yaya zan kare da fada iya in
na komagida?Ban ma san takaimaimain lokacin
da zamu bar nan ba.Fim din da ake yine ya dan
shagaltar dani, don haka ban lura da lokaci ba,
sai da na kalli a gogo na rude, shida dai dai na
yamma.A raina na ce tafiya zanyi…..kwankwasa
kofar ya dakatar dani, na bude cike da faduwar
gaba, a zatona shine ashe ma aikacin gurin ne
yake tambayata ko zanci wani abu?Na ce a a yace
kada ki damu Oga ya na nan zuwa, ban tanka shi
ba na maida kofar na rufe.A raina nace wato har
sunsanshi tunda gashi suna cewa yana zuwa.Na
ce wa yasani ma ko yana zuwa da mata…..na
katse zancen da cewa a’u’zubillah, ba kyau
munmunan zato.mikewa nayi ina ta kai komo a
tsakar dakin, tunanina wa zan kira wanda
zaikaiwa iya waya in mata bayanin cewa yaya
nake jira mu dawo.Can na tuno da Bello, na kira
wayarsa dan akwi number shi a wayata, kuma
yana kiran Aisha itama tana kiranshi da layi
na.Muka gaisa, na ce dan Allah Bello in kana
kusa ina son magana da Aisha ne, tayaya zaka
taimaka min?Ya ce bani minti hudu zuwa biyar a
kai mata. Na ce nagode. Sai da na bari kusan
minti shida sanan na kira cikin sa’a kuwa ta
daga.Na ce,Aisha taimako nake nema a wajenki,
don Allah.Ta ce na me?Na ce, kin sani ne?Mun
fita har yanzu bamu dawo ba, shine nakeso kije
kicewa iya don Allah kada taji shiru mun nan
dawowa.Ta ce, keda wa kuka fita?Na turo baki
tamkar ina gabanta, nace da wanan ya Aliyun
mana.Da sauri ta ce, au, ke da mijinki kika fita?
Bata jira amsa ba ta ci gaba da cewa, to ba zan
fada mata ba, na zata ma ke da wata ce, to in
shekara ma zakuyi ina ruwanta?Ta ja tsaki.Dan
Allah malama in zakiba mijinki kulawa ki bashi
kulawa kawai, sai an jima ta kashe batare da
nasake jinta bakina ba, nayi sororo ina kallon
wayar.Shi kuwa ya Aliyu daidai wanan lokacin ya
isa gidansu iya.Tana girki yayi mata sannu da
gida, ta ce yauwa ina yar tawa?Ya ce, yace yanxu
zanje in sameta in nayi wanka daga gidan oga
xuwa gidan sauran Abokai na.Murmushi iya tayi
ta ci gaba da cewa, wai ni za’a yiwa wayo, nifa
na haifesu, ni fa duk abinku kar nake kallonku.
Shiri yayi ango sosai, sai zuba kamshi yake yi, ya
nufi masauki na comman bayan yayi tsarabar kaji
da lemuka da kalolin madara masu tsafta. Ya
gaisa da masu tarbar bakin inda wani daya yake
tabbatar masa da cewa a jiyarsa na nan a ciki,
sun lura da ita yanda ya kamata.Kwankwasa
kofar ta re da muryarsa naji, inda yake cewa
Dear my choice.Jikina ya dauki bari, naje na bude
kofar tare da yi masa sannu da zuwa.Na amshi
ledojin hannunsa, kallo yake tayi tunda ya shigo
har ya maida kofar ya rufe, na ajiye ledar na
zauna kan kujerar dake kusa da gadon.Kai tsaye
yazo ya zauna kan hannun kujerar.Dear my
choice kinjini shiru ko?Yayi maganar cikin wata
laulausar murya
Na kalli a gogo gabana ya ci gaba da faduwa,
nace gashi har magariba ta karato, yanzu iya
tana can aiki yayi mata yawa, tana kuma jira
na.Ya kama hannuna me zakiyi mata da zata
jiraki?Na ce abincin dare mana.Ya hada tafin
hannuna da nashi ya sarke.Sanan ya dan matsa,
in kin tare a gidanki wane zai dinga yi mata aiki?
Cikin raunaniyar murya na ce, zan ke aika mata
duk abin da naci.Idanu na suka kawo ruwa don
tunanin rabuwa da iya.Ya dago fiska menene na
kuka?Na ce, ina tunanin rabuwa da iya ta ne.Ya
kwantoni jikinsa.Yi hakuri kanwata, ai ba wani
nisane tsakanin mu da iya ba, kullum nasan
zatazo ta duba ki, in bata zoba kuma mu
zamuje.Na kalli cikin idanunshi, da gaske zamuje?
Ka min alkawari fa.Ya ce, in sha Allahu.Ya ciro
fari kar din hankici mai kamshi daga aljihunsa ya
soma share min hawaye.Tashi kiyi alwala muyi
sallah sai muci abinci.Gurin da na idar da sallar
ya sameni, ya bajekomai gani da shegen kwadayi,
amma fargaba ya hana ni ci.Duk hankalina tashe
yake, ya lura da haka, sai ya soma lallashi
na.Haba Sadiya my coice, me nene naga duk kin
damu?Nifa mijinkine na sunna.Nace, to ai iya ta
ce kada wani abu ya faru tsakanin mu, har sai
mun tare.Ya ce to zata sani ne, ko ke zaki fada
mata?Na soma kuka, ina kallon fuskarshi.Wlh
yaya zata gane.Zumbur ya mike daga kusa dani
ranshi a bacce, ya soma yin magana cikin daga
murya.Kina fakewa da Iya ne kurum dan kawai ki
cucheni, ba fa haramun zan aikata ba.Kinsan ina
kyalekine ina lallabaki, in nace zan gwada maki
isa ba zaki iya kwatar kankiba ko?Jikina ya soma
bari, yaya don Allah kayi hakuri…..Yi mun
shiru.Ya katsane, sai wahala kike bani kina wani
inyi hakuri, ba zan hakura ba, haka nan ba zan
matsa maki ba, amma ki sani baki ba komawa
gida ko da zamu shekara a nan harsai kin yardar
min a bin da ya halasta min.Na fara kuka wiwi
shi kuma ya fice ya zare makulli ya kulle ni ta
baya.Na fada kan gado ina kuka, wata zuciya ta
ce mun gara fa kiyarda dan sai kin dibi kunyar da
bakiso a hannunki, don dan shi namiji babu
ruwansa.Ku ziyarci blog dinmu domin karanta
Littatafai masu nishadantarwa
Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?e_pi=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
Dasauri na dauki wayata na soma kiran layin
sa.Tayi ringing kusan sau biyar sanan ya daga,
cikin kuka na ce, yaya dan Allah kazo na
yarda….Da zafin rai ya ce, bana so, ke har kin isa
mzacen da zaki ja raina?Bari kiji wani abu, baki
son ki dade kada iya ta zargeki ko?To ina mai
shaida maki cewa nan zaki kwana, in yaso in kin
koma gida sai inga maizai faru.Ya kashe wayar,
ransa ya baci dani sosai.Daya wayarsa ta soma
ruri da sauri ya cirota don in yaji ringingi din ta
daga office ne, duk da ba ganinsa yake ba sai da
ya nutsu da ya daga ya ji muryar.Cikin sauri
sauri yake magana.ASP kana ina ne?Aliyu ya ce,
ina nan kan titin waff Road.Ya ce, yauwa kana
kusa ma, yi hanzari ka iso nan (headquarter) ka
kwashi yara ku nufiunguwar rimi layin dan marina
gida mai lamba tara, yan fashi sun shiga gidan
sunyi fashi.Sanan sunyi gaba da babban yaron
mai gidan.Ga ni nan zuwa ranka ya dade.Aliyu ya
amsa cikin izza, a duk lokacin da aiki ya taso
Aliyu yakan mance da duk lamarin dake gaban sa
matsawar ba salla ba ce.Sun isa gidan da yan
fashin suka shiga, Aliyu tare da inspector Adamu
da sajan Musa, sai kofur Bala.Cikin natsuwa Aliyu
ke kallon ko ina, kafin ya soma magana.Hajiya
sannunku da juyayi.Ta ce, yauwa.Cikin kuka da
rawar murya ta amsa, ya ce ina mai gidanki?Ta
ce, baya nan, kuma dama sunce shi sukazo
nema.Ya kalli kofur wanda tuni ya soma rubuta
komai, ya sake maida kanshi ga Hajiyar.Ta ina
suka shigo?Ta ja majina, sanan ta ce ta kofa.Ta ci
gaba, sun ga Yusuf ya shigo a cikin motar baban
su to sunyi tsammanin shine tunda gilashin mai
duhu ne.Don haka sai suka biyo shi.Aliyu ya ce,
shi Yusuf din daga ina yake?Ta ce, daga masalaci
ya ke, babansu yayi masa waya, cewa yaje ya
dauko motarsa.Don ni ya soma kira wai in kira
masa Yusuf ya dauki motar, sai na ce ya kira
layin sa ya fita masallaci.Kuma ba lallai bane
daga can ya dawo gida ba, Aliyu ya gyada kai
alamun gamsuwa sanan ya ce, motar ta samu
matsala ne?Ta ce, a a.Sau biyu ana biyo shi ana
kai masa hari a motar da dare shi ne dalilin da
yasa sam bayason karfe tara tayi masa a motar
na dare.Yau ma mitin ne zasuyi da ya taso musu
da gaggawa kuma bai san lokacin da zasu tashi
ba.Aliyu yayi taku zuwa tagar ya daga labulen
windon yana kallon harabar gidan haskenta
kamar duhun magariba baiyi ba.Ya waiwayo ya
dubeta wace mota ce daga cikin wayan nan
motocin guda uku?Ta karaso ta daga dayan
labulen windon wanacan (hondar ce) baka CRV.Ya
saki labulen yanzu mai gidan ya sani?Ta ce, a a
yana kashe duk wayoyin shi ne in zasuyi
mitin.Ina ne gurin aikin nashi?Aliyu ya bukata
cikin rawar murya ta ce, shine manaja a first
bank.
Aliyu yayi shiru kamar mai wani nazari, can ya ce
zaki iya fada mun kamannin yan fashin?Ta ce,
eh, zan iya.Babban su baki ne dogo kuma kamar
yanada yare, don hausarshi bata goge ba.Sai dai
kila muslmi ne, sauran kuma biyu fararene ina
zaton fulanine, biyun dake waje ne ban tantance
su ba.Aliyu ya jefeta da wata tambayar, yaya kika
yi tsammanin musulmine? Ku ziyarci blog dinmu
domin karanta Littatafai masu nishadantarwa
Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?e_pi=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
Ta ce, haka kawai naga kamar musulmine.Aliyu
yayi guntun murmushi.Bari mu barki haka, yanxu
bari muje mu dora bincike.Ta sake fashewa da
kuka.Ran ka ya dade ka taimake ni yanzu yaya
za’ayi mijina ya samu labari dan kada ya fito
sukama shi?Aliyu ya ce, kada ki damu, zamu
bashi kulawa da tsaro, sanan ki saurara sosai
nasan zasu kiraki ina zaton garkuwa zasuyi
dashi.Kiyi mana saving din number, in kuma ba
number ki kiramu ki sanar da mu.Ta ce, to
yallabai na gode.Ya ce ba komai kiyi adu’a.Suna
fita ya kira AC ya koro masa komai, AC ya ce, to
yanxu ku fara ji da maigidan nata, sanan kunsan
yanda zakuyi ko?Aliyu ya ce, yes Sir!Sai dai ina
kake ganin za a bashi mafaka tunda ba dama mu
barshi ya koma gidansa?AC ya ce kuxo nan dashi
daga nan sai a kaishi inda ya dace.Aliyu ya kara
cewa yes sir.Ya dubi yaran kumaje first bank.Sha
biyu da minti ashirin, Alhaji auwal ya fitoa rikice
daga cikin banki, gama mitin dinsu ke da wuya
police commissioner ya kira shi bayan ya kunna
wayarshi.Ya fada mashi cewa ga yarana nan zasu
taho dashi dan kare lafiyarsa.Alhaji auwal ya ce
saboda me ranka ya dade?Commissioner ya ce,
masu bibiyara ne suka shiga gidanka, amma ka
kwantar da hankalinka za a kama su.Suna tafe
cikin mota Alhji sai adu’a yake yi yana tunanin
me ya tarewa wadan nan bayin Allah?Kofur ya
ce, Alh kaji cewa sun tafi da yaronka?Aliyu yayi
mashi tsawa da cewa kofur?Da sauri kofur yace
yes sorry sir.Alhaji Auwal ya ce ranka ya dade
wane dan nawa dauka Yusuf? Aliyu ya ce kada ka
damu, in mun isa can zakaji komai a bakin
yallabai, kuma duk abubuwan zasuxo da sauki.
Alh. Auwal ya ci gaba da adu’a.
Ofishin commissioner yayi tsit tamkar babu
mutane sai karan (ac) da na fanka.CP ya kalli
Aliyu dake kame, ya ce nasan kana da kwazo
Alhamdulillahi,yanzu sashin binciken mu na
takama da kai.Domin aikinka kanayinsa da
karsashi gami da izza.Ya kalli Alh. Auwal kada ka
damu Alh, babu abin da zai samu yaronka.Zamu
baka kula shi kuma zamuyi dauki badadi da
su.Alh, ya ce, kana ganin ba zasu kashe shi ba?
CP ya ce, ai kudi zasu nema munsan irinsu, sai
dai yanda tayi kwatancen shi ina zaton bako ne
kila kuma ya jima yana yi bamu taba arba dasu
ba ne.Amma wanan karon in sha Allah za mu
hadu.Ya kali Aliyu ASP aje ayi shiri yanda ya
kamata.Ina bukatar barayin nan tako wane hali
sai dai banda kisa zan saurari wayarka a ko wane
lokaci kwa iya tafiya
Sai da Aliyu ya tunkari gida sanan ya tuno da
wata Sadiya, amma duk da haka bai wani damu
ba dan yasan zata sami kulawa yan da ya
kamata.Ya sake ciro waya ya kira, jim kadan aka
daga, ya ce Ibrahim dan Allah ajiyata na nan?Aiki
ya rike ni da safe zan turo aboki na ya tafi da
ita.Ibrahim ya ce ba ko mai yalla bai.Sun saba da
Ibrahim ne sakamakon wata matsala da ta taba
tasowa a Hotel din su Aliyu suka bincika case
din.Ibrahim shine me kula da dakunan kwana na
cikin Hotel din.Motar yansanda tayi faking a kofar
gidansu Aliyu ya shiga gidan da hanzari.Sai da ya
gama shirinsa sosai sanan ya nufi dakin iya.Tana
kokarin fitowa suka ci karo, yace iya na kama
hanya zantafi wajenta aiki ya taso.Usman zai tafi
ya daukota ko da gobe ne.Kar ki damu canma
gida ne gidan Oga ne.Haushi ya hanata magana,
Aliyu ya dafa kafarta, ki min adu’a iya da yan
fashi zamuyi arta bu, kin san aikin mu bakin rai
muke yin shi.Ta ce Allah ya baku sa’a.Gudu gudu
ya fito.Da kallo ta bishi har ga Allah bana son
aikin dan sanda amma bata so ta bata rai a kan
haka, dan kada ta tauye shi.Ta tabbata adu’ar ta
ita ce daukakarshi, fushinta zai iya tauye shi a fili
ta furta, Allah ka yi wa yaran nan Albarka
dukansu, ka dorasu a kan hanya ma daidaiciya
amin.Nikam a a lokacin ina can tsoro, fargaba da
bakin ciki sun isheni.Kai har da nadama.Naji
haushin kaina da naki bin umurnin mijina, gashi
yanzu ya tafi yana fushi dani.Nasan mala’iku ma
ba zasu raga min ba, kuma iyar da nake cewa
zata yi mun fada in taga na dade, to sai dai ta
kashe ni.Dan ina ganin tabbas nan zan kwana.Da
na bi umurninsa kila da yanxu mun tafi gida cikin
jin dadi.Kila ma yayi ta shi min albarka, mala’ku
suna amsawa.Naja tsaki tare da cewa, kash!
Nima ban yi ba wlh.Haka nayi kwanan zaune,
danma na rage daren da yin nafilfili, sai da nayi
sallar asubahi sanan na kwanta.Bacci ya tafi dani,
ban farka ba sai kusan sha daya.Kwankwasa kofa
ne ya tasheni, nazo na ce wanene?Ya ce, Ibrahim
ne.Na ce, ai ya rufe dakin ya tafi da makullin.Ya
ce, ba ko mai ga wani makullin, me kike bukata?
Nace ba ko mai, akwai abinci a nan dakin dayazo
dashi jiya.Ibrahim ya ce, to shi kenan.Ina jin
takun tafiyar sa, na zauna a gurin dantsabar
takaici, bani da ma ranar tafiya gida ke nan.Shi
kam dai dai wanan lokacin yana gidan Alhaji
Auwal cikin falonsu inda yake sauraron bayani
daga bakin Hajiya.Yanda sukayi da yan fashin da
suka kirata.Ta ce, kamar yanda kayi zaton zasu
kira sunkira ni yau ya da safe.Aliyu ya ce, karfe
nawa?Ta ce takwas da rabi dai dai suka ce kudi
suke so naira miliyan uku da rabi.Sun ce in har
ba a sami kudin ba zuwa jibi zasu kashe shi,
kuma sun ce basa son jami’an tsaro su shigo ciki,
kuma basa so a nemi ragi.Me kika ce musu?Ta
ce, ni kuma duk abin da suka ce da to nake ta
amsa musu. Ya gyara zama ya ce, ina suka ce a
kai musu kudin?Wai filin golf.Ina number da suka
kiraki?Ta dauko wayar ta fito da namber ga ta
nan.
Ya amsa ya dauki number sanan ya fita harabar
gidan yana sanar da CP halin da ake ciki.CP ya
ce, ka tafi da layin kamfanin su, wane layi ne?
Aliyu ya ce (MTN) ne.CP ya ce, maza ka tafi dashi
ka tambatar kayi abin da ya dace da wuri, dan
kila cire layin zasuyi ko kuma anjima su kira da
wani layin da ban.Aliyu ya ce, an gama sir.Sai da
yaje office din Usman sanan ya tuna da
Sadiya.Bayan sun gama magana akan abin da ya
kai shi, dama usman MTN yake aiki, sanan ya ce,
wanan yarinyar mai shegen tsoron tsiya, kuka
tayi ta min na barta na tafi abina.Idan ka tashi
dan Allah katafi ka taho da ita don ni ko ganinta
bana son yi.Usman yayi murmushi, sanan ya ce,
kayi mata uzuri, kasan yarinya ce sai a
hankali.Usman ba da bata lokaci ba ya sanar da
manajan su, nan take aka soma gudanar da
bincike a kan lambar.Sun gano layin a yanzu baya
kan waya, amma sun hada komai yadda da an
dora shikan waya zasu gano inda mai layin
yake.Nan take kuma ya kira CP yayi masa
bayani.CP ya ce, good! Kara zage damtse in kuma
kana bukatar yara duk sanar dani.Yes sir!Inji
Aliyu.Ku ziyarci blog dinmu domin karanta
Littatafai masu nishadantarwa
Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?e_pi=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
Na idar da sallah azahar ke nan sai naji alamun
ana bude kofa, fatana Allah yasa yaya Aliyu ne,
in sha Allahu yanzu nan zan bashi mamaki
Sai dai kashi!Ya na budewa sai naga yaya Usman,
ya ce tattaro kayanki muje gida.Na dauki jakata
da mayafi, sanan na gaishe shi, ya amsa tare da
cewa ki kwaso lemukanmana.Na ce, na kishi da
su. Ya ce, ai kya kai wa iya tsara ba ko kina nufin
gidan Oga ba a baki ko mai ba duk da cewa kin
kwana?
Yayi tambayar cikin zolaya, na dawo na dauka,
har ya taya ni sai lokacin naga Ibrahim din da
suke nagana, gajere ne baki.Sai da muka tsaya
Marhaba Store ya kara min tsaraba wai harda
turmin zani matar Oga ta ce a ba Iya.Da zan fita
nace masa nagode, ya gai da anty Abida, ya ce
zata ji.Sanan ya ce, ki saki jikinki don kada ta
gane ba can kika je ba.Ina yin sallama iya tana
zaune, cikin faduwar gaba na isa gurinta ina yi
mata sannu, ta amsa fiska daure.Jikina yayi
sanyi, nayi karfin halin cewa.Iya kin ganni sai
yanzun?Tun da yaya ya kaini ya Aliyu bai zo ba
har sai da na kwana, wai suna aikin wani case ne
a hannun sa.Iya ta ce, kai ma dallah da jin haka
sai nayi shiru, don na san zance na bai shiga Iya
ba, na mika mata leda.Gashi inji matar ogan yaya
din wai in baki tana gaida ke.Sai naga iya tayi
murmushi ta girgiza kai, sanan ta ce an gode.Tun
lokacin ban sami bakin magana ba sai daki da na
shige na kwanta.Har yanzu haushin kaina nake ji,
da na sani nabi umirnin miji na, gashi wanda
naki don ita bata yarda ba, kuma nayi imani ko
da mezan ran tse ba zata yarda da ni ba.Aliyu
yayi nasarar kama dan fashin nan tare da
taimakon masu layikan wato network na
waya.Don yan fashin sunyi anfani da layika
dabandaban, ya kama oga tare da wani yaronsa
guda daya, jim kadan bayan an basu kudi sun
saki yaron.Sun dauki hanyar kawo da a lamun
zasu bar Kaduna ne, ya harbi tayarsu sanan ya
harbi ogan a kafa.Sauran sun gudu shi kuma
dayan tsayawar da yayi zai dauki kudin daga but
din motar shi ya kawo Aliyu yayi nasarar kama
shi.Wanan gaggarumar nasarar ta sa an karawa
Aliyu girma daga ASP zuwa DSP, inda aka tara yan
jaridu suka watsawa duniya.
Duk kwanakin nan da aka dauka sam Aliyu baya
shiga harka ta, in na gaida shi zai amsa amma ko
kallo ban isheshi ba.Haka nan har daki na same
shi don inyi masa murna kan karin girman da ya
samu, amma sai ya ce dan Allah in fitar masa
daga daki.Har Iya ta na ce mun Allah ya kara,
tun da na ba da kaina ba loka cin da ya da ce ba
ai yazama dole in jure wulakanci, bani da hujjar
yin musu dole in yi shiru.Gadan gadan ya tada
aikin gidan sa, da alamu ya sami kudi, ranar
wata a Abar bai fita da wuri ba.Sai da suka shirya
sanan sun fita hanya sanan ta soma yi masa fada
me yasa yake yiwa marainiyar haka?Ya ce, bata
jin magana ne, gara ma ki mata fada tun yanxun
don ba zan dauki gaddama ba.Sunje iya nata
santin gidan, ta ce gobe kawo kayanta ko?Aliyu
ya ce, amma na dakin anjima zan kwasosu har
da TV da su Radiyo, kema na sai miki TV.Ta rinka
godiya.Washegari makota da yan uwa tare da
matan yayan mu sukazo suka yi mun jere, da
dddare kuma aka yi mun rakiya.Iya tayi mun
fada sosai, kuma ta kara nanata mun cewa tunda
ni na dage da son ya Aliyu lallai in lallaba
halayanshi.Don bata so in kawo mata wani kara’i
sananta sa mana Albarka tare da yi mana adu’a
tagari.Kowa ya tafi sai ni daya, nayi sallar isha’i
da shafa’i da wutiri, sanan nayi wanka, kwalliya
sosai nayi duk da cewa ina cike da fargaba zai
kalleni ko ba zai kalle ni ba.In ma ya kalleni ni
me zai faru?Goma da wani abu naji ana
kwankwasa kofar gidanmu.Da sauri naje na bude,
shi daya ne kuma sanye da kakinsa na dan
sanda, ke nan shi Abokanai ba zasu rakosa ba
kamar kowane ango.Na amshi kayan hannunsa,
jakace da leda tare da yi masa sannu da zuwa,
ban zaci zai amsa ba, amma ga mamakina najini
a jikinshi ya rumgumeni tsam.Sanan ya amsa da
yauwa sannu.Ina makale a kafadar shi ya kulle
gidan mu.Ina mamakin halin yayan mu sosai,
tamkar bashine yake gaba dni ba.Abaki yayi ta
bani kazar da ya shigo da ita tare da madarar
holandia.Duk fargaba ya cika ni, amma haka
naita sha har sai da yaga kamar zanyi amai, ya
ce, kin koshi?Na ce eh.Munyi Sallah inda ya dafa
kaina yayi mun addu’a.Bai bata lokaci ba gurin
ibadar aure, wasanninsa sunyi mun nauyi.Don
haka na soma rokonsa yayi hakuri, mai makon
haka sai yaji kamar wata sarewa nake busa
mashi.Nasha wahala a wanan daren nawa na
farko, domin duk wani haushinsa sai da ya huce
shi, sanan ya dawo yana tausaya min.Don shi da
kanshi bai sai saita kanshi ba.Shi ya taima ka min
na gyara kaina.Ku ziyarci blog dinmu domin
karanta Littatafai masu nishadantarwa
Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?e_pi=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
Ba mu jima da kwanciya ba aka kira sallah, ya
tafi masallaci nima nayi tawa sallar.Naso
kwanciya amma sanin cewa zai fita da wuri yasa
ni shiga kincin don hada abin kari.Lokacin da ya
dawo zatonsa zai sameni a kwance, sai ya ganni
kicin.Ji kawai nayi an rumgumeni ta baya.Na
gaida shi ya amsa ya ce, naje nayi bacci don
yasan ina jin bacci, na ce ba komai inya fita zan
kwanta.Tare muka karya, sanan ya ce, inzo in
cuda masa bayan sa tun ina jin kunya har na
gyare don kuma yariga ya tsomani cikin
ruwan.Tundaga ranar komai tare muke yi, wata
masifafiyar soyaya yake nuna min har na dinga
mamaki, sai dai ina gyaruwa wajen kwanciya.Don
ya Aliyu mabukaci ne fiye da zatona, rana, safe,
dare office ma sai ya dawo, haka nayi ta jurewa,
saboda yana ririta ni kamar ya hadiye ni.Satin
mu biyu nayi fari fiye da da, fatata ta goge,
amma na rame.Dan Almajirin da ya so min shine
ke min aike, kullun sai na saka mai abinda muka
ci ya kai ma iya.Ranar da nacika sati biyu ranar
iya tazo, dukinda nayi iya tana da ido, bayan na
bata ruwa da abin tabawa sai na zauna kusa da
ita ina cewa iya nayi kewarki sosai ke fa?Ta ce,
Sadiya kewa ai ba a magana.Amman kuna zaune
lafiya?Na ce lafiya lau, Iya.Yaya na ji dani, baki
gani ba.Tace Sadiya ni sai naga kin rame, kina cin
abinci kuwa?Na ce, ina ci mana.Aka kwankwasa
gidan, na ce gashi nan ma.Da sauri naje na
bude, ya manneni a jikin sa na ce iya tazo.Ya ce
tana nan?Na ce eh.A zatona zai sake ni amma
har fallon mu saida ya zauna sanan na zame na
barsu suna gaisawa da Iya.Na kawo masa ruwa
da abinci, yace my choice ba zan ci abinci ba,
dama nazo ne in dubaki kawai don na kira
wayarki a kashe.Nace yanzu aka kawo wuta, ka
kuma san batir din baya rike chaji.Ya ce, haka
ne.Zan chanja maki wayar ma, Iya ma in sai
mata.Tace ni yanzu gadanga in ka hada ni da
waya ban san yaya zanyi da ita ba.Na ce, zaki iya
mana, mun gode yaya.Yayi murmushi tunkafin a
siyo?Ta ce, ai nasan tunda ka furta zaka
aikata.Iya ta ce, gadanga kai naga kayi bul ka
kara kiba ita ko yar tawa duk ta rame.Ya kalleni,
ashe bani kadai nake ganin wanan ramar ba, to
ko Asibiti zamuje?Na ce, yaya babu inda yake
min ciwo sai muje Asibiti?Yace rama ciwo ne My
choice, zasu baki magani.Iya ta ce, ni da na zaci
ko rigima kuke.Ya ce, haba dai, ai yar taki tana
da biyayya.Iya tayi murmushi sanan ta ce, haka
nike so,Allah yayi muku albarka, ya baku yaya na
gari.Yaya ne, ya amsa da amin.Tare da dago
haba ta.Iya ta ce bari na tafi.Naje daki na dauko
dubu daya na ce, iya gashi, ta ce ina kika sami
kudi?Na ce, in abokan yaya suka zo suka bani, ko
na bashi sai ya ce in ajiye abina.Kuma ni ko katin
waya shi ke loda min.Ta amsa tare da ce min
Allah ya anfana.Na ce, Iya da kin dan bari sai
anjima.Yaya ya harareni ke zakiyi mata aikinta a
gida?Na ce, (cikin shagwaba) ba ina kai mata
kullum ba, ia yana isarki ko?Ta ce har ma in rage
in ba wani.Sai dai duk da haka ina yin girkin
saboda almajirai ko yan ciranin nan na
mokatanmu.Na ce, har yanzu iya kina ci dasu?Iya
ta ce, wanda ka bada shine naka.Nace to ki tsaya
zanyi da yawa sai in sa miki.Aliyu ya kawo hannu
ya dan mintsineni gefen ciki na, tare da cewa
sauran aikin ke zakiyi mata?Iya ta nufi hanyar
fita tana fadin Sadiyayyena kina in zauna shiko
gadanga korata ma yake.Da sauri kuma cikin
dariya ya ce, lah, iya bankoreki ba, nima yanxu
zanfita nazo duba ta ne kawai, kuyi zamanku ni
bari na tafi. Duk muka sa dariya, Iya ta ce a a
yayan nan ni dai naji dadin yanda na sameku
haka, fatana Allah ya kauda shedan tsakanin
ku.Ta bude kofar gidan ta fita, ya bita nikuma
nayi mata alkawarin xuwa inyini in an
kwanabiyu.Ku ziyarci blog dinmu domin karanta
Littatafai masu nishadantarwa
Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?e_pi=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
Bayan ya dawo daga yi mata rakiya ya sameni
ina gyara gurin, ya makaloni jikinsa ya dago
fiskata.Sarai kinsan abinda ya kawoni, shine kike
rokon iya ta zauna ko?Gaba na ya fadi, amma sai
nayi yake tare dafadin ba haka bane.Muka nufi
dakinsa.Na rasa duk lokacin da yaya zai zo mun
da wanan batun gabana ya dinga faduwa
kenan.Na kasa sabawa.Ko shi ke sani rama?
Oho.Kawaye na duk wace tazo sai tayi zancen
ramata, haka Aisha, ta damu da son jin dalili
Na dage kan cewa ba ko mai, tunda bai kyautu in
fada mata yanayin mijina ba.Munje Asibiti likita
shima ya sha mamakin jin banda matsala kuma
ba inda yake min ciwo, amma na rame.Sai dai ya
ruvuta mana magunguna masu sa cin abinci,
amma duk da haka sai a hankali.Wani dare anty
Abida ita da Usman sun kawo mana ziyara
munata hira, sai Aliyu ya kawo batun ramata, aka
danyi zancen har Usman yana tsokanata da cewa
ina tsoron kishiya ne ki daina tunani, aboki na
naki ne ke daya.Nayi dariya sanan na ce, nasan
haka shima yasan haka.Yaya Aliyu yayi dariya.My
choice ban maki alkawari ba fa.Na ce, yaya kaima
kasan ko bakai min alkawari ba kai nawa ne ni
daya.Abida taja ni bed Room dina muka zauna
bakin gado, ta kalleni wai me yake damunki? Na
ce, ba ko mai wlh.Ta ce, ki fada mun ban sani ba
ko zan iya taimakonki.Nayi shiru ina nazari, can
nace anty ba ko mai, Allah sai dai ina zaton ko
dan yaya yana da yawan buka ta ne?Kin san
Allah anty na yaya bashi da hakuri hatta kai da
na ganshi ya dawo gaba na ya dinga faduwa ke
nan.Ta kada kai zancen ke nan, amma wanan ba
abin damuwa bane, da farko ki daina tsorata har
gabanki ya dinga faduwa.Kisa haka aikin da ya
zaman maki dole, aure bauta ne, in zakiyi sallah
gabanki na faduwa?Na ce, a a.Ta ce aikin gida fa?
Na ce, a a.Ta ce, wanan ma kisashi cikin dolenki,
tunda zama ne ba na kare ba.Gashi baki son
kishiya.Tayi dariya sai dai zan fada maki wasu
abubuwa da zasu taimakeki, dauko biro da
takarda.Na ce, to.Na tashi na dauko memo, ta
soma bayani kamar haka:
ki samo Dabino,Zuma,Aya, da Cukui zaki maidasu
gari ne, sanan ki dinga zuba madara peak da
zuma kina sha kullum safe da yamma.Kinji daya?
Na ce eh, na rubuta.Ta ci gaba, ki samu,kankana
ki dinga yawan shanta har kwallon,na ce gashi
kankana bata dame ni ba, ta zaro ido to kuwa ta
dame ki, kuma kya iya yanyankata ki zuba mata
madara peak ki dinga sha shima har
kwallo.Sanan a kai na kan Akuya, ki dafa shi da
romo, sai dai bazaki zuba mashi mai ba,
maimakon mai ridi zaki zuba da yawa ki cinye ke
daya.Haka kuma zaki sami garin dabino ki fasa
kwai da madara peak ki juya ki shanye.Nace wai
zan iya duk wanan?Ta ce, ki gwada tun gobe zaki
sanya ya nemo maki amma karki fada masa
dalilinki na son kayan, kawai kice zakiyi anfani da
su ne.
Kan batun ramarki kuwa, ki canza abin kari, da
me kike karyawa?Na ce,Tea ne sai Bread da Kwai,
watarana inyi kunu da kosai, ko indomie da
kwai.Ta ce ki koma cin dankalin turawa da
agada,ko doya da kuma kwai, in da hali harda
farfesu.Shayinki kuma ya zama yaji sugar da
bota, milo da madara.Ki zuba sosai yayi kauri
kisha.Sanan kirinka baccin rana shima baccin
yana sa kiba, sanan da daddare kici abinci
sosai.Na ce, to anty na gode.Ta ce, ba komai, ke
dai kada kiyi wasa, in kinyi su da kyau na tabbata
sai kin dawo neman wasu.Ko da yake ban fada
maki na tafin hannu ba,kin san hannu yana daya
daga cikin mai aikawa da sakonni.In mijinki mai
yawan kama maki hannu ne, ki samu zautun ki
kwaba da suga ta narke, kullun in zaki kwanta ki
rinka shafe hannunki.Sanan ki rinka shafawa a
lebunanki, nace to na gode anty sosai.Sallamar
yaya ce ta katse mu, ya ce, me ta baki kike ta
godiya?Nace abubuwan karin kiba ne wanda zan
rinka karin kumallo da su.Ya kalli Abida dama
zaki iya wanan taimakon amma kika share mu?
Muka sa dariya harda shi.Ya ce, mun gode.Ta ce,
ba wani abu bane wanan har da za ayi mun
godiya.Kai dai ka dage da siyo wa.Ya ce, in sha
Allahu ko su ke nan kudin za a siya, me nene da
me nene za a siya?Na ce, na rubuta zan nuna
maka.Yayi murmushi, to da kyau, yace kizo, abiki
yace zaku biya ta gidan yar uwarki ko?Ta ce, eh,
tare da mikewa na shiga dube duben me zan
bata, turare na bata mai kyaunace ta kaiwa
Ummulkhairi.Ka fin ya dawo da ga rakasu, har na
gama rubuta abinda ta ce na rinka karyawa da
shi,ya ce agada da dankali sai da safe, nayi
godiya da cewa Allah ya kaimu.Cikin satyn na
hada duk wani abu da anty Abida ta fada mun,
na shiga anfani da su.Kafin wata daya naga canji
sosai, yanzu bana wahala da duk dawainiyar da
miji na yazo mun da ita.Sanan nasoma cika ina
cika kayana gwanin sha’awa.Shi kanshi yaya wani
sabon ji dani ya sake ko mai tare muke yi in har
yana gida ni dashi mun zama abu daya.Ko tari
nayi sai ya tabbatar ba na cutarwa bane, haka
nima ina binshi sau da kafa, da ya nuna ra’ayin
abu zan masa balle ya ce my choice ina son
kaza.Ai in na soma sai ya gundire shi, duk abinda
bai so na kiyayeshi har abada.Shinfidar da muka
yiwa rayuwar mu ba zan iya bada labarinta ba,
kowa yana mamakin mu tamkar mun shafe
shekaru goma muna soyayya kafin muyi
aure.Muna cikin wata na uku iya ta matsa masa
wai sai ya maidani makaranta, form din (N.C.E)
ya sai min bada bata lokaci ba na zama daliba a
makarantar horas da malamai dake riga
cikun.Aliyu ya ce, ya zama dole in nemi avin
hawa ko don ke.Na ce Allah ya bada iko.Ba da
jimawa ba kuwa ya ,mallaki motarsa dai dai ta
talaka.Ku ziyarci blog dinmu domin karanta
Littatafai masu nishadantarwa
Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?e_pi=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
Don haka bani da matsala sai dai yanayin aikin sa
ya ce in ya sami lokaci zai rinka koya mun, na ce
to.Ban jima ba na iya mota, sau da yawa ni ke
kaishi gurin aiki in dawo, sanan in tafi
makaranta.Kai yaya ya nuna mun dukkan gata, a
lokacin jini ke babu matar da ta kaini sa’ar zuwa
duniya a zamaninnmu. Wata safiya na farka da
zazzabi, mura, ciwon kai da sauran su, gashi
ranar yaya ba gida ya kwana ba, saboda wani
case da ke hannunsa.Bana kiranshi in dai yana
wurin aiki, amma shi in ya sami lokaci yana kira
na.Ina kudindine a kan gado naji ringing waya ta,
da kyar na lallaba na dauko, na daga.Ya ce, my
choice kin wuni lafiya?Cikin wata murya na ce,
lafiya lau.Ya ce, me ya same ki naji ki haka?Wani
dan kukan shagwaba ya subuce mun na ce,
zazzabi.Nanfa ya rikice sai gashi a gida bayan
minti ashirin.Banyi ko wanka ba ya sani a mota
sai asibiti, gwajin farko ciki ya bayyana, murnar
da ya Aliyu ya dinga yi ta rinka bani mamaki.Kula
da tarairaya ina ganinsu gurin sweet Aly na da
iya, cikin ya sa ni yin kyau, duk da na sha wahala
kafin yayi kwari.Sanan na bude nayi kiba gwanin
sha’Awa.Lokacin da cikin ya tsufa sai kuma na
kumbura abin da yayi matukar daga hankalin
yaya.Duk da cewa likitan ya ce babu
matsala.Cikin haka aka chanja yaya zuwa kogi,
ranarda ya zo mun da maganar na sha kuka.Duk
da ya zaci dama zanyi rigima bai tsammaci har
haka ba.Yayi ta lallashina da cewa, sadiya my
choice,ki kwantar da hankalinki.Ai duk matar mai
kaki San sanda ko Soja da sauransu, dole ta
kwana da sanin akwai yawon zaga duniya.Banzaci
zan dade haka ba tare da an canzani wani gari
ba.Na shafa cikina yanzu baka nan zan haihu?In
katafi yanzu sai yaushe zan sake ganinka?Ya ce
da na sami sarari zanzo, na kwanta a jikinshi.Ni
dai zanbika sweey Ali kaji yaya na?Ganin yanda
na rikice sai ya ce, to shi ke nanmu tafi tare ko?
Na ce, to sanan nayi shiru.Ana gobe zai tafi yaje
suka hada baki da iya,na zage ina ta hada kaya
har yana taya ni, sai ga iya tayi sallama.Na ce,
sweet yaya na dubi iya tazo kamar tasan zamuje
sallama.Iya ta shigo har cikin daki na, ta kalli
kayan da akwatinan ta ce, wanan fa, kwalima ce?
Na ce iya kin manta gobe ne fa zamu tafi can
jihar kogi inda aka tura yaya.Iya ta ce, zakutafi ko
zai tafi?Ina zaki tafi da wanan katon cikin ga
kumburi?Na kalli yaya na wanda ke ta aikin jera
min kaya na a cikin a kwati.Ni ina kwasowa daga
cikin sif.Kin kallona yayi, sai da na ce yaya!Ya
kalleni na ce, kaji kuma wai ba tare zamuba, inji
iya?Ya ce, eh, a a ai kinji ta ce saboda cikinki na
ce, tabdi jan!Ni kam ba zan zauna ba.Iya ta ce,
lallai Sadiya ba inda zakije yar dadi muji, ni yanzu
ma zuwa nayi in tafi dake.Na saka kuka, iya
sororo tayi tana kallona, shi kuma sai ya tashi
tsam ya dawo kusa dani.Iya kije gida zan kawo
ta.Iya ta mike ai ba wani lallashi ba in zata zo
dan ma kada ka sake yi mata karya.Ke ko yanxu
ance ki bishi kya je?Na ci gaba da kuka na iya dai
ta tafi tana cewa sai kiyi ta yi.Tana fita ya
rungumeni, haba my choice ni na lura iya tafimu
gaskiya.Ki bari in kin haihu sai muje, ina zo zan
tafi dake.Yanzu kinga dole inje in ga yanayin
garin.Na ce, yaya dama na san cewa baka damu
dani ba, can na san baka sona.Ya manneni a
jikinsa, inji wa yace bani sonki?A zaman da
mukayi baki fahimci matsanancin son da nake
maki ba?Na ce, to me yasa zaka tafi ka barni?Ya
ce, ina canne amma na rantse maki zuciyata tana
tare dake.Yanxu ni dake bamu san haihuwa ba,
gashi yanayin aikina ba na za,ma bane bugu da
kari ba mu san kowa ba in haihuwa ta zo maki
bana kusa yaya ke nan?Nayi shiru a raina na
tabbata haka ne, amma damuwa ta daya, yaya
na nasan ba zaka jure zama ba mace ba, don
nasan yanayin ka.Ina tsoron matan zamani.Ya ce,
au, dama dan wanan ne?Nayi maki alkawarin ba
zan kalli wata ya mace da sunan so ko wani abu
ba, baki tunabaya ba?Na tsare kaina kuma Allah
ya tsareni, ba wanan a raina, nace to ya ya
zakayi?Ya ce, azumi mana, ko can shi na tayi ta
irin na annabi dauda.Inyi yau gobe in huta, kada
ki damu ki kyautata min zato, bani da sha’awar
aikata kazamin laifi irin su zina da
makamantansu. Na kalleshi na yarda da kai
mijina, kuma ni da kai mutuwa ce zata raba
mu.Zan jira dawowarka, amma za ka dinga
yawan kirana?Yace, kema na yarda ki kirani duk
lokacin dakike so, nace to amma dai mu kwana
abinmu a nan da safe in katafi sai na tafi nima.Ya
ce, sammako zanyi, na ce, eh, duk da haka, ya
ce shi kenan, sai muje da daddare mu kai
kayanki ko?Na ce, eh.
Hakika yaya na sweet Ali ya tafi ya barni da
tsananin kewarsa. Kafin ya kai munyi waya yafi
sau goma.Haka nan na hakura na saba da kwana
ni daya, daran wata lahadi na farka da wani
matsanancin ciwon ciki da baya.Kafin in tashi iya
yaya na soma kira, ya daga a rude na ce yaya
zan mutu ka yafe mun, nayarda wayar saboda
ciwon mara da ya murdo min.Kalamaina suka
farkar da iya, tazo tana cewa haihuwar ce Sadiya?
Yaya ya kashe ya sake kira a rude, iya ta daga ya
ce Iya don Allah…………Kuyimin hakuri indakata
anan zuwa lokaci nagaba sai mudira daga inda
muka tsaya,fatan zanga comment dinku
rututu,kafin nan nake cewa zaku iya ziyartar blog
dinmu domin karanta Littatafai masu
nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?e_pi=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347

Related Articles

Zaharaddeen Shomar
Whatsapp 08168575100

Darajar Yayana2-02
Posted by ANaM Dorayi on 09:51 PM, 02-Apr-16
Under: DARAJAR ‘YA’YANA
________________NA ___________HALIMA K/MASHI Irin tarbar da kikayimin ta mutunci shi yasana boye kalatata,boye kishinki zaifi alheri, sama da bayyanashi don yanda na yi mani bakikaini son mijinki ba, haka na yi imani na fi ki kishin sa,in kina musu lokaci zai tabbatar miki dahaka. Kije kiyi aikinki sannan ki kunna min T.V Na harareta tare da jan tsaki na nufi dakin yaran. Sun gama cire kayan, Kausar tana linkewa, Al’ameen ya ce,’Mama wace ce wannan??? ….. Na ce ‘Bakuwa ce, Na kunna musu T.V dinsu, na ce kar su fito sai an kira sallah. Nima na shige dakina na fada kan gado. Maganganun yarinyar sun ratsa ni, har na rasa tunanin dayakamata inyi. Ina buqatar shawara, domin na lura da ‘yar iskar matar nan batazo dawasa ba. Wa zan kira don neman shawara? Aisha ko Abida? Aisha ba ta san d wannan zancen ba, bari kawai in kira Anty Abida tunda ta san da matsalar. Ringing na uku ta dauka na ce, ‘Anty Abida ya gida da yara. ‘Ta ce, Lafiya lau. Na kwashe komai na fada mata, ta cika da mamaki, sannan ta ce, ‘Shawarar da zan ba kikar ki bari ta gane lagon ki kar ki nuna fushinki, kuma kar ki kulata kuyi tashin hankali, ballantana ta yi furucin da yaranki za su gane,ki jira zuwan shi muji hukuncin da zai yanke. Na ce, ‘To shi kenan Allah yayi mana jagora.’Ameen, Ta ce. Na kashe wayar ina nazarin maganganunta. Ita ko ‘Yar Gwari, Mujidat tuni ta ciro wayarta ta soma chatting da abokanta. Murfat ke tambayarta wai yanzuntana ina? Mujidat ta ce tana Kaduna. Murfat tace, ‘Ashe muna kusa ni ina Abuja jiya muka zo tare d Alhaji Karimu zai yi meetina na kwana biyu.. Mujidt tace lallai kina cikin kudi, murfat tace sosai ma, abokinshi Alh muslimu ya tambayeki .Mujidat tace yakiranima bandaga wayar ba, kinsan ina ina yanxu? Murfat tace ba kin ce kaduna b? Mujidat tace ina gidan officer Aliyu,Murfat tace kina hauka ne? Zaki je gidansa? sai matar sa ta kasheki a banxa? Mujidat tace ai matar tashi wawiya ce, har ruwa ta bani nasha, bayan na gaya mata cewa mijinta ciki ya min, tace ina baki shawara ki cire cikin nan kixo gurin masu sanki, officer ba sanki yake ba. Mujidat tace , ni inasonshi, zan tsaya nai fada a kanshi, saboda ko nadawo zanta tunanin shine, bazaki fahimta bane saboda bakitaba shiga tarkon So ba, ni kuma na shiga tarkon So mai tsanani.Murfat tace to yaya akayi kika gane gidan?ina kwance Hotel ba lafiya , sai ga wayar direban shi wai Ogafa an canxa shi zuwa Abuja, yanxun haka ya tafi in gaya miki duk sai na rude, take na miqe ina roqon Adewale ya taimakeni , yace sai nabashi kudi, bani da kudi sai dana roki samarina , suma shegu ban samuba sai dana musu alqawarin basu kaina, ina bashi kudin yace naje kaduna zai turo wani dan sanda daga can Headqurter su, yayi Tanbaya kan Aliyu Tukur aka fada masa sunan unguwar su, sannan na nufo Kaduna, nasha wahala kafin na iso, sabida motar dana shiga me arhace, inazuwanan na samu wani dan sanda da Adewale ya hadamu , shima akwai kudin da akayi alqawarin xan bashi, sai daya dafe shi,sannan yayi min jagora zuwa unguwar su Aliyu, nan ya bar ni wai in nemi gidan, wai in mun shig unguwar tare, asirinsa zai tonu, na Adewale ma haka,nadade ina yawo, sannan na samu gidan mamanshi, na shiga bata nan, sai nace a kai ni gidan matarshi, Murfat tace ke yar neman bala’i ce, bari tasa miki guba a abinci kici ki mutu, mujidat tace shi yasa bazan taba cin abincita ba,Murfat tace kidai yi ahankali, garinsu kikazo, tace a garinnasu sai in karbe mijin kuma na zauna lafiya.haka suka yita chat har xwa wani lokaci, Niko munyi sallar magariba har na zubawa yara abinci, 9 da yan mintina yya Aliyu ya iso gida,da ita ya soma cin karo a falo, ckin zafin rai yace me zakiyi agidana?itam cikin daga murya tace goyon cikin dakayi min, abinda naji kenan, na miqe ina kallon yarana,Kausar ce kawai idanta biyu tana yin homework dinta, na miqe na fito da sauri, dai-dai lokacin yana cewa, zan nuna miki kurenki na biyoni gidana yar iska karuwa.nakamashi ina fadin yaya yara fa? itama tace yan iska dai, namijin karuwa. na dafa kaina dan takaici, yar bariki tana zagin mijina da nake girmamawa a gabana, najashi zuwa dakinsa, nace, haba yaya, kamanta cewa kana da yara a gidan nan?dubi yanda yar bariki tazo har cikin gidanka tana zaginka?sabida mutuncinka daka sai da,ai dama haka ne, dukwanda yabar maganar ubangijinsa dole ya fadawa dana sani, da wace rana zaka iya hada yau a gurinka dan bakin ciki? ni dai a gurina babu, ya dago kai ya dubeni, Sadiya nayi nadama sosai wallahi, ba sai ta kanjamau kadai Allah yake kama mazinaciba, in Iya taji batunnan na shiga uku, nasan bazan kara yin daraja ba, kila ma ta cireni daga yayanta, ga wannan matsiyaciyar da alamu fallasa tazi min,nace to yanzu dai nema mata masaukin da zata kwana, in yaso da safe sai mu zauna da ita mu kafa mata sharuda,ya kama hannuna, wadanne irin sharuda za’a kafa mata?kara min haske, sai musa mata sharudan cewa ka yarda zaka amshi dan,amma za’a rufa asirin cewa ba’a son kowa ya ji, dan haka za’a ce mijinta ne ya rasu, iyaynta suka koreta saboda ta musulunta,na tabbata duk wanda yaji haka zai tausaya,to inta haihu sai ta bamu yaron ta tafi abinta,yace wazai rike yaron?nace ni mana, Yya ko ban aure ka ba ai xan rike maka da, bare kuma ina matarka na kasa rike jininka? yadan yi shiru yana nazarin batuna , can yayi dariyar yake yace,Sadiya baki tunanin me mutane zasu ce?in sun gammu da jariri?me zamu fadawa yaran mu? idan sun tambayemu nan gaba? nace ai zamu fada musu dan mu ne, amma bani na haifeshi ba, tunda dama a musulunci bai da gadonka,kaga ba zamu sami matsala ba, ya sake yin shiru, can yace ina ganin fadin gaskiya kawai shine mafita, saboda duk rintsi karya bata kaiwa ko ina baki tunanin cewa nan gaba zata zo nemn danta?kuma asiri zai tonu? nace Allah zai rufa asiri, kai dai da safe mu sameta da batun muji yanda za’ayi.yace shikenan, Allah ya rufa asiri,to yanzu ina zata kwan?ka kaita dakinka,yace a’a, sai dai yara su dawo dakinki, ta kwanta acan , amma bazata kwanar min a daki ba, araina nace yanxun ba, amma da ai tare kuke kwana ma. yace kota kwana a falo? a’a ,bari in kaita dakin yaran.haka kuwa akayi,muka kaita can.Da safe dana kai mata abin kari sai tace a’a, tanada maltina da kuma biredinta, bata cin abincin kowane guri, da kanta takeyi, nace good, sannan na fita.mudai sama-sama mukayi bacci, kuma sama-sama muka karya, duk sai tunani muke, yaya kuwa sai nadama yake, dan dadin da yabi na watanni yaja masa zubewar mutunci na kila tsawon shekaru.misalin sha dayan rana yace in kirata ,muka zauna yara suna makaranta lokacin, ta fito sanye da riga da siket na jeans, kanta babu dankwali, cikinta kuwa har ya turo, ta zauna tana taunar cingam, yaya yace Mujidat dama mun kira kine don mu tattauna dake, shawara ta farko zanbaki dubu dari biyu ki zubar da cikin nan,ta daga masa hannu, ban amince ba ,koda zaka bani duniya da kayan cikinta, inbaka mantaba nafada maka, badan kudi nake tare da kai ba, sonka da kauna ce kawai, kuma cikinnan, (tasa hannunta ta shafa cikin)ribar soyayya ce, taya zan zubar dashi?kawo wata shawarar dai muji,kalamanta sun konan raina tamkar in tashi a gurin,amma sai na shanye.yace to naji, zaki zauna damu ki haihu, amma da sharadin baxaki fadawa kowa komai ba,duk abin dana fadawa mutane zaki tsaya akan haka ne?ta dan yi tsai tana tunani can tace ,zan yarda, amma idan na haihu meye makomata? zan tafi da danne?ko kuwa zan barshi anan?sai lokacin nasa baki , zaki tafi ne kibar yaron a wurina, sai ki tafi abinki,wata ran,xaki iya xuwaki ganshi duk bayn wani lokaci, tayi min wani kallo, tare da yin kwai da cingam dinta kato, sannan ta fasa shi taci gaba da tauna duk muna kallonta, tayi yar dariya, in naki fa? cikin zafin rai Aliyu yace , sai ki tafi da cikinki, danma kin samu zan amsa? nasan uban dayayi miki? tace , ka manta dararen daka yi ta kwana dani?cikin bacin rai yace in baki yarda ba malam kizo ki fice min daga gida kije kiyi duk abunda zaki yi. tace zan fi son haka , dan zama gidan mamanka ze fimin wal-wala, dan haka zan je na fada mata ina dauke da jikanta, ta bani masauki, ni dashi muka kalli juna, yace kije man , zanfi san haka.nace , a’a ,kedai barshi a wancan tsarin,tace in dai har za’a barshi cikin sirri, tonima zan kawo nawa sharadin?Aliyu kam takaici ne ya hana shi daga kai, ban taba ganin shi cikin wannan yanayinba, na takaicida bakin ciki.nace fadi sharadinki muji?tace sharadina sai dai in na haihu zai AURE NI…. kalamanta na karshe suka tafi da numfashina, tsawon kiftawar ido, huhu, nayi nasarar janyo nimfashi na,idanuwana suka futo sukayi jajir, zufa ta ketomin, ta tuntsureda dariya har Aliyu ya dubeta, nima lokacin na dubeta, tace ,ya kika yi saurin firgita?naga keda mijin naki kamar tagwaye, shawarar ku daya, kun burge ni, kuma nasan yana sonki, kuma nima ina san shi dan nasan qualities dinshi, na baku zuwa gobe kuyi shawara. (Uhm!Allah yakayuta,ANaM Dorayi) Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai masu nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com Kokuma ku kasance taredamu a facebook https://mbasic.facebook.com/HAUSA- Novels-389304544597988/?_e_pi=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
Aliyu ya harareta, Allah ya kiyaye ni Aliyu na
aureki,ai ko zan yiwa matata kishiya na nemo
mata yar mutunci bake ba karuwar titi,tir Allah
ya tsareni, ya miqe, na baki awa daya kibar
gidana, ko kuma yan sanda su zo su fita dake, da
kyar na miqe kafafuna sunyi sanyi, dakina na
nufa don ko ganin gabana banayi,zuciyata tamkar
ta faso ta fto,rigijif na fadakan gado, inasan yin
kuka amma na kasa, lallai kuka ma rahama ne,
tunda idan kayi shi zaka samu sauki,
Hannuwanshi naji a gadon bayana, ji nake tamkar
ya doramin wuta,zuwa,yanxu nasoma tsanar
yaya Aliyu,gaskiya hakurina yana son ya kare,
danzan iya danne komi, amma banda batun
kishiya ,zan iya hakura ya aureta, amma kuma
zan juri zama da ita?(Mata kenan,da kishiyar
gida!..Allah ka karemu daga bin soye-soyen
zukatanmu…..Ameen.ANaM Dorayi) Birkitonin da
yayi shine ya katse min tunanina yace, haba My
choice, kada wannan ya dameki, zanyi waya
yanxun xa’a turo min yara su tafi da ita, xuwa
ynxun ban damu duk duniya tasan cewa na mata
ciki ba, ai nima dan Adam ne kamar kowa, ban
wuce kuskure ba, nace aika riga ka tafka
kuskure,dole ne ka aureta, kuka ya subucemun,
naci gaba da magana cikin kuka wane hali Iya
xata shiga in taji wannan labarin?ita da ba
cikakkiyar lafiya ba, me zaka cewa y’ay’anka ?
wadanda tun jiya suka damu dasan sanin wacece
wannan bakuwar? y’an ‘uwanka, wane idan kake
dashi da zaka kallesu?su da sukeyimaka kallon
mutunci da kima? ga abokai da sauran mutan
gari?kada ka manta, shi fa mutunci madara ne,
in ya zube sai dai a kwashi kasa,ka riga kayi
abinnan da hausaw ke cewa TSALLE DAYA ME
JEFA MUTUM RIJIYA….ya rike kanshi, sadiya na
yarda duk wanda ya bar layin da aka ja masa a
matsayinsa na musulmi dole yayi nadama mara
amfani,danasan abubuwa zasu zama haka da
banbi san zuciyata ba ,dam malamai suna gaya
mana zuciya wata tsoka ce ajikin dan adam me
hadari in kabi sonta sai ka halaka, ya dube ni,
yanxu kin yarda? kinaga ba wata mafita sai ta
auren ta? nace to inban yadda ba ya xanyi ,nasa
masa kuka ina fadin na amince ka aureta,
,kallona ya dinga yi tamkar na zame masa wata
sabuwa a sanyaye yace”nasan kin hakura ne
saboda ni, amma nasan bakya san kishiya,amma
kina ganin cewa nan gaba bazaki damu ba?na
runtse ido, zuciyata tana wata irin tafasa nace,
batun zan damu ko bazan damu ba a ynzun ba
shine mafita ba,na bude jajayen idanuwana ina
kallonshi, sai dai ina fatan daga baya ba zka
canzamin ba? ya rungume ni, Sadiya kada kiyi
tinanin haka kada kiyi fatan haka, ki tayani
addu’a Allah ya bani ikon yi miki irin halaccin
dakikayi mini,banda kamar ki har abada,kuma ke
kadai nake so ke daya kwal. Haka ya yi ta fada
mini maganganu masu dadi da kwantar da rai,
har zuciyata ta dan sauka. Yaya ya fito ya fita,ni
kuma na kira Anty Abida na fada mata, ta ce
hakan ya yi in ta haihu ya aure tan zai fi sauki a
bakacin ta haihu ta ba ku yaron. Na ce, To ya zan
yi tunda shi ya janyo. Nan dai muka yi sallama
nafito na kuma dora abinci,sai dai ina gamawa
ita ma ta soma dora nata,ban damu ba tunda
neman sulhu muke. Misalin hudu yara suna
Islamiyya suka shigo shi da Usman falo suka
zauna, na kawo ruwa da abinci.Usman ne ya sha
ruwan shi kam gogana har wata ‘yar rama ya yi,
ya kalle ni ya ce, Kira yarinyar nan. Na ce to. Na
daga labulen dakin yara tare da yin sallama, ba
ta amsa ba sai dai ta dago ta dube ni,rufdaciki ta
kwanta kan katifar su Kausar tana chatting, na
ce, Ki zo in ji Mijina. Ta yi min kallon kishi zan ce
ko na tsana, sannan ta ja tsaki. Ni dai na juya na
ce musu tana zuwa. Zan tafi Yaya ya ce in zauna,
na samu guri na zauna. tafi minti shida sannan
ta fito,munyi jugum-jugum kamar masu zaman
makoki, ta tsaya kerere , gani. Ya harareta
.Kizauna mana kin ce wani gaki? Ta zauna tare da
fadin .yau kuma da wacce aka zo? Duk muka yi
shiru, irin zaman nan da ake cewa mutuwa ta
ratsa. Can Aliyu ya ce”Usman wannan ita ce
Mujidat,kuma na maka bayanin komai,dan haka
sai ka dan ce wani abu”.Usman yace”bani da ta
cewa,sai dai ke.ya nuna Mujidat,karkisake kice
zakici zarafin wannan baiwar Allah ko nan gaba
“yakalli Aliyu”ya kamata wannan ya xama cikin
sharudan da zaka gindaya” Aliyu ya kalli
Mujidat”na yarda in kin haihu zan aureki, amma
ki sani so daya tak inayiwa matata ne,dole ki
bata girma da daraja,musamman data soma
bazaman aure ba, sannan zaman haihuwarki ina
gani can wani waje zan nemamiki haya” cikin
sauri na ce ban yar da ba, ai ta zauna anan,
kada a dinga zagayawa “Usman yace “haka ne
kuma,amma kina ga batakura? Na ce “bakomai”
Mujidat dadi ya rufeta ,kuma nan take ta nuna
murnarta, ta kuma sake bayyana tsantsar san
data ce tanawa mijina,dan haka dole tazauna
dani, ban bari ta kai karsheba natashi nayi kicin
abina.tsayawa nayi tsakiyar kicin shuru,anya
kuwa ban yi wautaba?ban zalunci kaina ba?ban
debo rvmuwan dafa kaina ba?amma sai wata
zuciyar tace kedai kada kiyi wannan tnanin, tunda
kin sadaukar da kimai ne dan asirin mjinki y
rufu,Allah ya sani Zuciyarki daya da ita,kuma
Allah zai shige miki gaba. Nasauke ajiyar xuciya
nace Allah gani gareka,sai da suka fito ne naji
muryar Usman na cewa”Madam na tafi”nace “ka
gaida min su Ummulkhairh dasu walida”yace
xasu ji.
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai
masu nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?e_pi=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
A ranar Aliyu ya koma Abuja,sabida an dameshi
da kira,gida ya koma sai ni da ita saikuma
yarana,a daren nan naje na fadawa Iya yanda
muka tsara zancen,tayi ta tausaya mata,tare da
shiwa yaya albarka tace ai gara daya taho da
ita,tace in an barta sai ta koma ruwa, tabar
musulinci, nace “ai shine” Iya tace Allah sarki,
naxo in yi mata ta’axiyya,banda abinku, daba
nan kuka kawota ba? Tunda ni kadai ce?nace”Iya
ki barta can kawai,sabida bata jin Hausa sosai”
tace”to shkenan ,kema Allah ya biya ki” na ce
amin.
Daren ranar mun kusa rabashi a waya yaya yana
shimin albarka tare da yi min alkawuruka kala-
kala na riqe ni amana,tare da kyautatamin daji
dani duk wani dadin zaman aure,har sai da aka
kira shi, yace minxai fta gurin aiki1 nce Allah ya
tsare.
Haka muka zauna da Mujidat,bata min
magana,sai dai ni in mata.innayi kamar in
shareta,sai na tuna da haramcin gaba,dan haka
in lokacin sallah yayi tana falo sai in ce
mata”lokacin sallah yayi” wataran
tace”to”wataran tayi min banxa ,sai dai ko ta
amsa ba dole ne ta tashi tayi sallar ba.abinci
kuwa,da kanta take yi,takanyiwa yara
magana,amma ba wai wasaba, sai dai in tana
san abu tace kai bani kaza, ko ke bni kaza. Sun
dameni wai yaushe wannan bakuwar zata tafi?
bata da kirki su suna san ta tafi,nce musu bazata
tafib,Antyn su ce baban su ya kawota ,kuma tana
da kirki,dan dai yanxun bata da lfy ne
shiyasa.suka yi shiru badan sun fahimce ni
ba,intaji fita tana san zaga gari sai dai kawai inga
ta fice bako mayafi. Sai dai nayi masa waya nce
ka fada mata in zata fita ta dinga saka hijabi ko
mayafi, saboda an ce ta musulunta, in tana fta
haka asiri zai tonu.ya ko kirata yace ta
kiyayeshi.kar ta bari tayi abinda zai toxartata,tace
ita bata da hijabi.yayi min waya wai in bata
hijabai guda 2, sannan yace ya hanata fta,kuma
ta sani ya zuba masu sa mata ido a unguwar,
dan kar tai xaton cewa xata fita wani gantalinta
ta dawo masa gida,ko kuma zata yo wani mugun
abun.tace karya damu,dama ita burinta aurenshi,
kuma tunda ta samu bata da matsala da wani
namijin can waje, tana zuwa matsa jikine.
Duk wani zaman kunci na dauka a zaman
Mujidat, sai dai ban damu sosai ba.ganin Aliyu
baya sakar mata fuska sosai.komai tace masa
tana so sai yace ta tambaye ni,bai cika zuwa
gidan bama, sai daiyazo ya debemu da yara mu
tafi can Abujan, akwai lokacin da sai da muka yi
sati uku saboda yara sun samu hutu. Ranar da
muka dawo har da shi ,mun samu ta tana kuka
wiwi, wai bata da lafita,nce masa muje Asibiti,
amota fadi yake Allah yasa ckinnan ya fta, na ce
dan Allah kabari, ka mata addu’ar alkhairi, bayan
dogon bincike likita ya gano tana shan maganin
tari na yara,wanda mata da maza kan sha sabida
su yi maye. Likitan ya ja kunnanta da cewa in ta
ci gaba d sha za ta kashe danta. Muna hanyar
dawowa gidan na ce, Ki daina kada ki je ki yi
sanadin rayuwar danki. Na dube shi. Kayi mata
magana ta daina shan pakalin. Ya ce, ‘Ina
ruwana, ta yi ta sha indazata mutu ma kina
ganin ba zan fi son haka ba? Ta ce, ‘Eh, na san
dama haka za ka ce, kuma sai na haihu lafiya. Na
ce, ‘Inma banda ke mene ne abin sha cikin
maganin mura? Ya ce, ‘Ai ba za ta daina rayuwar
bariki ba. Ta yi shiru tana nazarin dalilinta na
sha,tsabar son shi ne da take yi. Shi kuma ya
kwashe Iyalan shi suka bar mata gidan shi yasa
take sha sabida rage damuwarsa, ga shi ashe za
ta janyo makanta ne, ‘Yar shigarda ta samu a
watse, don ta san in cikin nan ya zube shi kenan
korarta zai yi batada sauran garkuwa za ta jure
ta ci darajar dan da za ta haifa. Ta shiga wata
bakwai lokacind ta cewa Yaya a waya wai tana
son ta fara zuwa awon ciki, ya ce ta fadan in ta
matsu.kin fada min ta yi sai shi ne ya tambaye
ni. ‘Mujidat ta yi miki batun awo? Na ce, ‘A’a,ya
fada min yanda suka yi na ce ‘Ka bari sai ka zo
sai mu yi zancen gani gata, in ya so sai a je
Asibitin a kuma sayi duk wani abu d ake buqata.
Bai amsa min ba ya canza zancen da cewa,
‘Akwai wani bincike dazai kawo ni Kaduna me zan
samu? Na ce, ‘Duk abin da ka ke so. Ya ce,
‘Yanzun ina takura sosai a gidana in na zo zan
dauke ki mu fita a wani masaukin bakin mu dan’
huta. Na ce, ‘Yara fa? Ya ce, ‘Ga gidan Iya. Na
ce, ‘To ma tafi mu bar mai ciki, kar a yi na
wancan karon. ‘A yi ta yi mana, ina ruwana,
daman na san haka za ki ce. Ya ja tsaki tare d
kashe wayar shi. Na sani tabbas rayuwarmu ta
canza yanzun, amma wayaja? Shi ne. Allah yasa
mu dace, ameen. Wata Asabar Aliyu ya nufo gida,
yana karya kwanar unguwar su sai ya ga jama’a
cirko cirko tsaitsaye gungu gungu, wadansu kuma
suna ta maida yanda aka yi,yayin d kunnan shi
ke dauko masa sautin wasu muryoyi suna ihun
neman dauki. Kasancewar shi jami’in dan’ sanda
dole ne ya bincika, don aikin shi ne kare rayukan
al’umma da dukiyoyinsu, ko da ba a unguwarsu
ya ga hakaba, dole ya tsaya.
Don haka ya gangara gefen titi yayi Parking din
Motarsa,yana fitowane wasu matasa sin tsaya
suna dan tattauna batun,Aliyu ya usa gurinsu
fare da yi musu salllama,suka amsa,ya
fambayesu abindake faruwa,daya matshin
yagane Aliyu dan haka yace “yallabai wallahi ‘yan
sara sukane” Aliyi yace ‘yan sara suka kuma?
Yace eh! Wasu matasane ance daga hayi suke
suka fada layinnan suma sara da sukan duk
wansda suka ganiyanunamasa inda
cincirindonbjama’a ke tsaye yace ‘can
meshayinnena Buba suka soka,sannan suka sari
me lemun kysa dashi”
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai
masu nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?e_pi=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
Aliyu ya isa gurin daidai ana kokarin sashi amota
yace “bakuyiwa yansada wayaba” ?wabi yace “tin
dazu muka sanar dasu” Aliy yadagawaya yana
sake miran yansanda yana shedamusu cewa a
turomasa mota sabida ‘yan sara suka sun sgigo
ungywarshi ,shine yavasu damar kai masu jikin
Asibiti sannan shikuna yacigaba da gudanar da
bincike jafin isowar yansanda.
Tanbaya yaitayiwa mutaben gari kan yansara
sukan;kasancewar mutanwnmu akwai tsoro da
rashin cikakken wayewa ga wasu sai zuka mi
bashi cikakaken hadinakai.sannanda yanufi
motaesa dan karasa gida,sai yaji wasu matasa
biyu suna magana,dayan yanacewa, “kasan Allah
Aminu su Dawa Adone suka jamana wannan
bala’indashi da Bangis Kauri” Aliyu yace “Kanina
kananyfin Dawa Ado din tsokanarsu yayi?
Duk suja waiwayo suka kalli Aliyu,ganinshu da
nayan Yansanda sai sukace a’a bamusaniba,suka
juya da nufi.n tafiya Aliyu yace tsaya kuji absan
cewa kunsan wani abu,dan Allah kubani
hadinkai.Dayan da akakira Aminu yace,’mufa
zabcenmu daban, ‘yansanda basu da
amana,dazarar kafadi wata magana sai reshe
yajuye da mujiya a kama mutum a tsare”
Aliyu yace ba gaskiya bane,shaci fadine da shrri
irin na wasu mutane suke jifan jami’an tsaro
dashj,mu masu kare rayukan Al’ummane da
dukiyoyinsu bawai masu sharrib,kudinga bamu
hadin kai,tahakane zamu iya gano bara gurbin
al’umma.”
Dayan wanda kebada labarin yace, yallabai
yallabai tsorona kada a kirani shaida,suganeni
insun fito suzo su sassareni”.
Aliyu yace “sam sunanka bazai fitoba, vabu
wanda yasan munyi haka dakai.” Yadafashi.
“Kagama zo nan mushiga daga mota dan kar
wasu sugane kaine kafadamin,kayarda ba
cutardakai zanyiba,taimako zanyi,kaga in ba’a
dauki matakiba zasu iya dawowa.Zaka iya sanin
ko kanwa tsautsayi zai fada?nasan kanada
dangi,da mahaifanka, sannan ga kanka ko
kanada yakinin cewa bazasu dira kankaba?
Saurayin yace “hakane yallabai”
Syka shiga Mota harda saurayin da dayan yace
Aminu.
Aliyu ya kalleshi yace ‘kanina kai ya sunanka?
Nasandai abokinja shine naji ka kira da Aminu”
Yaron yace “Buhari’
Aliyu yace ‘Buhari wane Dawa Ado?’
Buhari yace “Dan dabane,sunada yawa a
ungywarnan,saidai su da bangid sune sukai kauri
suna a ungywarnan”
Aminu yace, “wasuma sunce gudansu Dawa Ado
ana siyar da wiwi,wasu yarsu dake zaman kanata
agubta yake ajiyewa”.
Aliyu yace “to mene labarin wannan fadan?”
Buhari gace,”to nidai mundawo Masallaci jiya da
Magriba dayake layinmu daya da Dawa Ado,sai
naganshi zaune tare da wasu yandaban,
,yaranema wadanda basufi shekara sha shida sha
biyarba,yana fada musu cewa zamu fadawa ‘yan
hayi har naji ya anvaci sunan wani dan daban
hayin yanacewa lallai yanaso ayimasa yankan da
bazai tashiba,ko yatashi kada ya moru.Nidai na
wuce nabarsu,saidai ina zaton kan wiwi ne sjke
fadan, dan naji yanacewa “ankawo mishi kaya
kafin yazo shi wancan ya siye”
Aliyu ya girgiza kai alamun gamsuwa yace, to
yanzu kuyimin kwantabcen gudansi Dawan
dakuma Bangis din, ‘ sukace to.
Nan sukayimasa kwatance yacuro kati mai dauke
da lanbarsa a jiki ya basu,.
“Gashi kusa lanbobina a cikin wayoyinku,sai ku
kirani ko kumin flashing inkira dan insamu taku
lanbara,kunsan dalili?
Sukace a’a. Yace dan kucigaba da bada gudun
mowa cikin hnguwar nan,duk lokacin da kukaga
wabi abu mo kukaji makamancin wannan sai kuyi
maza kukira daya daga cikin wadannana
lanbobin. Ya sanya hannu ta baya yaciru yan
dubu dubu guda biyu ya mika musu tare da
cewa,”Ba cin ganci vane kyauta
nabaku,aikinmuma dazakuyimin ba na kudibane
taimakon kaidakai zakuyi.”
Da murna suka karba, sunyj masa godiya,take
nan suka bashi lanbobinsu,sannan suka gangara
inda suja nunamasa gidansu Dawa Ado da
Bangus Kauri.sanna ya gan ga ra ya ajiyesu ya
wuce hidansa.
Likacin d na ji kwankwasa kofar ina kicin ina
kokarin dafawa yara Indomie, don ni a koshe
nake Iya ta aiko min da dambu, nacishi sosai
bayn La’asar shi yasa. Na nufi kofar cikin raina
ina tunanin ko waye? Ina bude kofa na yi sororo
don bai fada min zai zo ba. Na ce, ‘Oho! Abin
‘Yar haka ne? Ya shigo, sannan ya rufe kofa, ya
kamo ni ya rungume, na karbi jakarsa muka nufi
ciki. Mujidat tana zaune a falo ta ce, Sannu. Ya
ce, ‘Yauwa. ‘Ba tare d ya kalletaba. Muka nufi
dakinsa ina fadin. Kausar, Al’amin ga fa babanku.
Da gudu suka fito dga dakina, muka dunguma
dakinsa mu duka. Na ce daka fada min kana
zuwa Allah d tuni na yi maka abnci na
musamman. Ya ce, ‘Ai rikici na tarar a unguwar
shi yasa da tuni na iso. Na ce, ‘To yanzun me za
ka ci? Ya ce, Me ki ka dafa? Na ce, Ban dafa kmai
ba, yanzu daizan yi wa yara indomie,sai dai
muna da miya a fridge sai na dafa maka farar
shinkafa. Ya ce, ‘A’a ku tashi muje gidan cin
abinci. Na ce, ‘To ka canza kaya mana, ko kuma
ka yi wanka. Ya ce, ‘Duk yanda ki ka ce. Na dubi
Kausar ‘Mu je in ciro muku kaya ki sa musu sai
ke ma ki sa.’Na dube shi. ‘Bari in ba su kaya.
Gira ya daga min na fita. Na dawo na taimaka
masa ya yi wanka. Ya shirya, nima na canza
kaya, duk Mujidat tana zaune a falo tana
kallonmu, sai na ji tausayinta ya tsirga a raina,
na ce, ‘Ki tashi muje cin abinci. Saida ta yi min
wani kallo, sannan ta ce, ‘To. Mun fito sai ya
Aliyu ya ganta, ya ce, ‘Ke fa? Da sauri na ce,
‘Tare za mu je mana. Tsaki ya ja,sannan ya ce,
‘Ni yanzun ba nida damar sakewa kenan? Ban
tanka masa ba, a raina na ce wa yaja? Lokacin
dakuke shanawar ku ai ba ka ce an hana ka
sakewa ba. Da farko yaso mu ci a can,amma
yanzun sai ya ce kawai mu yi take away sabida
bai so zuwanmubada Mujidat. Daga nan sai ya
nausa da mu can gurin kasuwar Bacci, wani katon
shagon saida kayan wuta, na ce me za mu yi
anan? Bai kula ni ba don na lura ya ji zafin
zuwan Mujidat. T.V ya sai mana ta bango
(Plasma),mai kyau sai tsada,sannan ya sayi
resiba,ban san inda zai sa ba. Sannan muka je
wani babban store ya kwasarwa yara kaya har da
keke ya saiwa Al’amin. Yara sunata murna muka
isa gida. Ita dai mujidat duk inda muka je da Ido
take binmu, tare da yatsina fuska,jifa jifa tana
tabe baki tare da tsaki. Ni dai muka yi ciki ta
zauna a falo.
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai
masu nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?e_pi=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
Dakina ya kai T.V, na ce ba na ka ba ne? Ya ce,
‘A’a naku ne,don na lura ke da gidanki,amma kin
bar wa wata falon ki. Na tsura masa ido, ‘Yaya
na gode. Ya harare ni, Lokacin fa dakika samin
suna kin yi alkawarin kirana Sweety Alinki,amma
yanzu sam kin daina na manta rabon da ki kira ni
dawannan sunan. Na ce, Yi hakuri Sweet dina. Sai
na ji su Kausar da Al’amin sun sa dariya.Kausar
ta ce, Momy Abba ne Sweet? Muka kalli juna cikin
dariya na ce, ‘O.K, waton kun tsaya jin mu ne?
Al’amin ya katse zancen da cewa, Abba wai ita
Anty bakuwa sai yaushe za ta tafi? Kausar ta
zabga masa harara, ‘Ina ruwanmuda wata can
Anty Bakuwa. Muka sake kallon juna cikin
mamaki. Na lura fa Kausar ta tsani matar nan.
Nace, Kausar ai ba tafiya za ta yi ba ita ma ta
zama ‘yar nan gidan. Kausar ta zaro ido, ‘Ta
zama ‘yar gidan mu kumma? Ta tura baki,ni dai
Abba ta koma gidansu, kullum sai ta dinga
hararata, ko kuma tayi ta hana mu kallon T.V. Na
ce to ba ga shi Abbanku ya siyo mana wata ba?
Ta yi shiru. Na ce, ‘Kar ki sake yin haka. Ranta a
hade ta ce, to Momy. Mun ci mun sha muna ta
hira har yara suka yi bacci, sannan muka gyara
masu kwanciya, sannan muka nufi dakinshi.Yayo
alwala tare d cewa. Je ki yo alwala muyi Isha’i.
Na yi murmushi , sannan na ce, Wanka zan yi
don ina fashin sallah. Ya runtse ido tare d fadin,
kash! Ga shi gobe zan tafi. Na ce, Kar ka damu
zan yi maka irindabarun da muka sabayi da.
Dariya ya yi, sannan ya ce, shi kenan. Da safe ni
mkadai ce na fito na hada abin kari, sannan yara
suka ci suka fito. Babansu yana kwance na ce
‘Bari in kai su makaranta. Ya mike. ‘Yau ba
Lahadi ba? Na ce, ‘Hadda suke zuwa Asabar da
Lahadi. Ya ce, ‘To ki yi sauri ki zo ki kara yin wata
dabarar. Na yi masa hararar wasa. ‘Bashi yasa na
ce amAuran Mujidat zai taimaka maka ba ya
hade rai, sannan ya koma ya kwanta. Na dauki
makullin motarsa. Bari in ari motar ka. ‘Nan ma
bai tanka ba. Lokacin da muka tafi Mujidat tana
soya kwai a kicin, na cewa Kausar su je su gaida
ta. Kullum dama sai na sa su sun gaishe ta,
kamar kullum sai d ta yatsina fuska sannan ta ce,
Lafiya. ‘Na fita abina. Mujidat tana ganin fitar
Sadiya da yara sai ta maida kofar ta rufe,sannan
ta nufi dakin Aliyu yana kwance sai ya ga mata
tsaye a kanshi tana girgiza. Zumbur ya mike tare
d fito falo, don gudun kar ta kara janyo masa
wani laifin a kan na da. Ita ma ta biyo shi tana yi
masa kallon banza kana tsoro kada matar ka ta
dawo,shiyasa ka fito kar ta same mu tare.ta yi
‘yar dariya. ‘Ai ka gama kuskure tunda har kayi
ajiya a jikina na zo in yi maka gargadi ka rage
nuna tsana da kyama gare ni, in ba haka ba na
rantse maka zan je gidan mahaifiyarka in tona
komai. Aliyu ya ce,’Ai har abada ba zan so ki ba,
kin ci darajar matata data dage sai kin zauna da
mu, banda haka ke din banza. Ta tuntsire da
dariya, ‘Ai ba ka san wani abu ba, ai ita kan ta
matar taka sa’a ta ci d ta kasance mai son
kwatanta adalci, banda haka wallahi da sai ta
raina kanta a wannan zaman da nake yi a gidan
nan, don sai dai inmu dinga kwana da kai gado
daya.ya harare ta, Ni kuma da yake zan tsaya ne
ina kallon ki har ki shigo mini daki,kuma ki sani ni
Allah ya shirye ni. Ta ce, ‘Oho! Yanzun kana
tsammanin cewa kai wani shegen mai imani ne?
Ta yi murmushi mai sauti,sannan ta girgiza kai.
‘Abu daya zan fada maka shi ne ka gode min da
na kawo shawarar auren ka,sannan ka godewa
matarka da ta yarda da in aure ka,ta samawa
kan ta lafiya don wallahi da sai dai ta sallamawa
kan ta domin matsawar ina numfashi duk inda ka
ke sai na bi ka,kuma sai ka yi duk yanda naso. Ya
gyara zaman shi sannan ya ce, ‘Kin yi kadan
shaidaniya. Sannan ya kautar da kai.sam bai
tsammaci zuwan ta ba,sai dai ya ji ta a jikin shi
‘yar barikin ta san lagon shi,wanda baya iya
bijiremata, zuciya muguwar nama har za ta
amince,amma sai Aliyu ya yi ta maza ya hankade
ta duk d tana da ciki, sannan ya ajemata mari a
fuska,ta shafa kumattun tana kallon shi bayan ya
mike yana mata kallon banza,ta yi ‘yar dariya.
‘Dubi yanda idanunka suka canza launi, ban da
cikin jikina da sai na tabbatar maka cewa in ina
nan dole ka rayu da ni,Kasa ba ta amsa ya yi kai
tsaye ya nufi dakinsa ya shiga ya kullo
kofa,sannan ya zauna bakin gado tare da rike
kan shi ya ma rasa wane irin tunani zai yi.Can
kasan makogwaron shi ‘Hasbunallahu Wani’imal
Wakil yake fadi can a hankali ya ji kmai yana
warewa, ya kwanta rigingine ya tabbatar cewa
Mujidat shaidaniya ce, za kuma ta yi duk abin
data fada, auranta kam shine mafita, inbahaka
ba zata jashi zuwa wuta,tunda in tana raye bazai
fasa zinaba.Yadauko wayar shi ya soma kiran
layin matar shi.
Ina daf da gida naji wayata tasoma ruri, nayi
kwana,sannan na daga. ‘Yaya dai Sweety Aly? Ya
ce, ‘Ina kikene? Kin san dai daga ni sai wannan
shaidaniyar a gida. Gabana ya fadi, sam ban tuna
haka ba,nace ‘ga ni nan yaya ina daf da gida. Ita
ce ta bude min gida lokacin da na buga,sai dai
tana bude min ta juya a raina na ce, ‘Hakan ma
nagode. Na aje mota,sannan na nufi ciki. Zaune
na same ta tana sanye da dogon wando na jeans,
sai ‘yar best yanayin shigarta na bata min rai,
musamman in yaya yana gari. Na murda kofar
na ji ta a kulle, na kwankwasa ya bude na bi shi
da kallo, don son in fahimci wani abu, amma ban
gane ba, don haka nace. ‘Lafiya? Ya dube ni, ‘Me
ki ka gani? na ce, ‘a’a bakomai.naga kakirane na
dadene? Ya ce, ‘a’a, kin san ina jiranki ne a sake
yi min irin dabarar jiya.nayi dariya, ‘ai bana
batun dabara barima inyi wanka don ina zaton
anjima zan yi sallah. Damurna yace, ‘Haba? Na
ce, ‘Allah. Ya ce to shiga ina jiran ki. Saidai kuma
ina fitowa na same shi zanzare cikin kakinsa yana
daure takalmi, sororo na tsaya cikin mamaki kafin
nayi magana sai wayarsa ta soma ruri,ya dauka
da sauri. ‘Buhari inajinka. Daga inda nake na jiyo
wanda ya kira da Buhari yana cewa,Yallabai
muna zaune ya wuce kamar yanda nasoma
fadamaka dazun, shi Dawo Ado, malun malun
yasa yana riqe da Adda sannan malun malun din
ta jike sharkaf da jini. Aliyu ya ce, ‘Dan uwanka
Aminu ya kira ni ya fada min wai ‘yan sara sukan
nan sun ce za su sake shigowa anjima, zan fito
yanzu. Yana ‘aje wayar ya dauki dayar ya kira
headquater ya buqaci a turo masa ‘yan sanda
mota biyu. Ina mamakin yanda Yaya keda izza
cikin aikinsa, yanzun nan ya rikide daga soyayya
ya kma zakin maza,ya kama kofa zai bude nace
“Sweet aliy ka manta daniko?” ya waiwayo da
sauri, sannan ya dawo ya rungumeni jikinsa ya
sumbaci kumatuna”ya za’ayi na manta dake?
Ashe zan iya mantawa da kaina kenan?ya dago
fuskata”sai na dawo”na saki murmushi”Allah ya
tsare min kai mai sona”ya sakeni ya fta da sauri.
Sun kama Dawa Ado,Bangis Kauri, sannan suka
dinga fadin sunan yan daban suna kama
su.kazalika sun dire hayi,inda can ma suka
kamasu da yawa,ya mikasu yakuma basu
shawara cewa suyi bincike kan yaran
sosai.sannan su tabbata sun mikasu kotu.
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai
masu nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?e_pi=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
Hakanan da dare ina Sallah a dakina,misalin
takwas wanda yanzun yazama na yara,Kausar da
Al’ameen suna kwance ruf da ciki suna
Homework ,Aliyu ya shigo da Sallama,suka amsa
tare dayi masa sannu da zuwa,ya kalli Mama
dake bacci can gefe yace”wai shin mamana tayi
nata Homework din ne? Kausar tace”eh Abba
sunyi tare da mumy”dai-dai lokacin na kammala
addu’a ya tayani shafawa, na kalleshi”sannu da
zuwa” cikin murmushi nayi maganar
yace”yawwa,sannu matata”muka sa dariya, ya
rusuna saitin kunnena yace “kisa yarannan suyi
bacci da wuri” kafin in bshi amsa wayar shi
tasoma ruri.ya daga da sauri,nji yana fadin “Yes
Sir” nace Allah yasa ma zaiyi kwanan gdan yau.
Ilai kuwa, yana gama wayar ya kalleni”
yanzunnan zanwuce Abuja” na zaro ido”Abuja
kuma da daren nan?” yayi dan yake”aikinmu
kenan, ahaka muka yi rantsuwa babu dare ko
rana,duk lokacin da aikin yataso zamu fuskance
shi”na lumshe Ido ahankali nace”yanayin aikinku
yana shafar rayuwarku”ya mike zumbur”muje ki
hada min kayana” Kausar ta tashi zaune”Abba
bari muxo mu rakaka motarka”nace “a’a , ci gaba
da Homework dinki in yashirya zaizo har nan sai
ku raka shi,” tace to. Tara dai-dai ya kammala
komai,dan ban amince ya tafi bai samu nutsuwa
ba, sabida tsoron kada shaidan ya sake ribatarsa
ya kuma kyallo wata,lokacin da muka zo gurin su
Kausar tini duk sunyi bacci. Ya tsuguna duk ya
sumbaci kumatunsu, sannan ya dauki hanya,na
raka shi mota,sai daya tashi sannan na koma
,ban tsaya wani tunani ba na kwanta don Inda
sabo na saba da tafiyar Yaya cikin dare, sai dai
Adduar Allah ya kare min shi.
Kusan sha biyun daramen wata litinin na jiyo ihu
cikin baccina, na tashi da sauri ashe nakuda ce
takama Mujidat. Da gudu na fada cikin dakin tana
zaune dirshan tana juyi da ihu, na ce ta kwanta,
bari na gani ko mota ta da mai. Kafin na dawo
har kan da ya fito sai ihu take har su Kausar sun
tashi nace mota ta ba mai bari in kira Iya. Na
kira ta na fada mata, tacebari ta taho tind dare
bai yi Sosai ba. Kai Mujidat akwai raki, har
nadaina Jin tausayinta, sai dai haushi.Kafin Iya ta
shigo dan ma Ya fito, masha Allah jariri
sambalele, sai dai abin ya yi ta fadar da gaba na
yadda naga yaron tamkar Yaya. Iya ce ta yanke
cibi sannan muka gyara ta tsaf da danta. Kusan 3
dare suka samu bacci, Ni da Iya muka koma
dakina. Ta dubeni. “Sadiya!” na kaleta da
faduwar gaba. Tace, “jaririn nan baki fahimci
komai ba?” Na girgiza kai “A’a iya ban fahimta
ba. Bashi da Lfy ne?” Tace, a’a kama naga yana
yi da mijinki sak, tamkar an tsaga kara, ko
‘ya’yanki basu yi kama da shi ba kamar wannan
yaron, tsorona daya Kar dai ace Gadanga ciki
yayowa wannan yarinyar. “Nayi saurin cewa,
“a’uzu billahi! Iya ba kyau ayiwa mutum
mummunan zato, kin San wannan ba halin Yaya
bane”. Ta ce ‘eh, to haka ne, amman fa mutum
yakan canja daga halinshi da aka San shi dashi.”
na ce, a’a fa iya ita fa wannan da mijinta, kafin
ya mutu mun sha gaisawa da shi. Kuma shi
kamanni hakayake sai kiga baku hada komai ba
amman Kuna kama.” ba don Iya ta gamsu ba
tace to Allah yasa hakanne. Na ce ameen. Nan
mukayi alwala muka kama nafila, addua ta Allah
ya rufawa mijina asiri Kar duniya ta gane wannan
matsalar.
Da safe lokacin da na shiga dakin tana zaune da
danta a hannunta ta tsura masa ido tamkar ba
ita bace tayi ta kurma ihu ba. Na ce ‘kin tashi?”
ta ce, ‘eh mun tashi, kin ga yarona sai kace
Babanshi, naji dadin haka,Dan bazai sake min
musu cewa ba cikinsa bane.” da sauri na ce,
‘kibar maganar nan mana, yanzu bari kuyi wanka
in na kai yara makaranta sai nazo na kai ku
Asibiti.” ta yatsine baki “kin sanar da mjnki?”
nace, a’a kin San Iya tana nan ba dama in masa
zancen ki.’ ta dauko wayarta tana cewa, “ina
ruwana da Mamansa taji. Layinsama a kashe
yake.’ tayi tsaki ta jefar da Wayar, Ni dai na fice
na kama aiki na raina bace, ban cika ganin
laifinta ba Dan shine musabbabin komai.
Da zamu Asibiti na sauke Iya a gida na wuce
dasu. An duba su ance duk suna lfy, muka tsaya
kasuwa na siya abubuwan da basu da shi,sannan
muka nufo gida.
Tsakiyar gado na zauna sannan na soma Kiran
layin mijina, bugu biyu ya daga, nayi Sallama ya
amsa tare da cewa. “Yaya na jiki cool da yawa?”
Na ce, ‘Yaya budurwarka ta haihu.” budurwata
kuma? Ya fada cikin sauri. Na ce, eh Mujidat
danta yana nan namiji……zandakata a anan zuwa
wani lokacin kuma,fatan zaku kara hakuri dani
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai
masu nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?e_pi=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347

Zaharaddeen Shomar
Whatsapp 08168575100

Darajar Yayana2-03
Posted by ANaM Dorayi on 04:31 PM, 23-Mar-16
Under: DARAJAR ‘YA’YANA
________________NA ___________HALIMA K/MASHI Ta soma kwalla a kwai su, amma sun zo sun kasa kamo barawon.Ya ce, to daga sun zo ne zasu kamo barawo kamar suna da Allahn musuru?Ina ganin ki hakura kawai in ba a kwai wanda kike zargi ba.Ta ce, cikin jaka ta yake a dakin na, ni na tafigidan kawata, mama ta tana shigowa sai kanena sun ce kuma basu ga wanda ya shigo cikin dakin ba.Aliyu ya tabe baki.Shirme kenan, sai ki hakura kawai.Ta mike tana share hawaye, shi ke nan nagode.Sanan ta tafi.,har ya gama shirin sa tsaf zai tafi sai ga wayar commissioner yana neman sa yana isa aka dan ka wani aiki a hannunsa.Dole ya fasa tafiya ba don ranshi ya so ba.Washe gari ranar goma dai dai dawowar shi ke nan daga wurin motsa jikin da yaso xuwajiya hakan bata samu ba sai yau. Waya ta buga daga bakin gate ne, mai gadi ya ce, yallabai bukur jiya ce ta dawo.Cikin damuwa take oga.Dan sanda ya kara da haka ne don don tunanin cewa in ta fito yau ma zai sami kwaleliyar dubu daya tamkar jiya.Aliyu ya ce ka ce mata zan fita ne ta dawo da yamma, bata jin dadin haka ba amma me nema yana tare da samu, don haka sai ta hakura ta tafi.A ranar ta saka hotonta da ainihin sunanta aaccount din da ta bude kuma Aliyu ya amshia botar ta.Da yammancin ranar bata zo ba domin ta dana sabon shairi, sha biyu zuwa karfe dayan dare ta san lokacin da take ganin shi a online ne, don haka sai ta hau.Cikin sa’a yana nan ta soma da tura masa hotonta a inbox, yana ganin hoton ya gane ta.Ya ce, oh, daman ke ce kika yi mun basaja don in karbeki?Ta ce, naga in ba haka nayi ba ba za ka kulani ba.Kuma ina da matsala kai ne nake ganin zaka magance mun.Aliyu ya ce matsalar me?Ta ce, kafin in fada maka matsalar tawa, ka fara kallon hotunan nan.Aliyu ya ce, to.Duk a tunanin sa matsalar ta ta shafi aikin sa ne.Matsalar farko sassan kirjinta ne, haka ta turo gabobi duk tsiraicinta ba inda ta babu inda ta rage.Ya ce me nene ma’anar hakan?Ta ce, ka duba hotunan da kyau?Ya ce, eh.Dama ina so ne ka gani da kyau don in nayi maka saimatsalar tazo da sauki, domin tun ranar da na ganka na haukace da sonka.Ka taimake ni.Aliyu ya rasa me zaice don ta kaici da bakin ciki, sai kawai yayi blocking din ta amma mehotunan da ta turo sun hau cikin hotunanshi.Ya dinga bin su da dai dai yana sharewa, amma da yazo kan na farkon na kirinta sai ya tsaya yana ci gaba da kallon hoton har ma ya kasa goge shi.Cikin daren tunaninsa ya soma gurbacewa, da safe karfe shida wayar bakin gate ta shigo, bai dauka ba don lokacin bacci yana kanshi.Don baiyi wani bacci ba can kuma a bakin gate din shi kanshi mai gadin yana son wanan bakuwar ta samu shiga sabo da ya san in ta fito zai samu wani abu.Ya ce, madan me yasa jiya da yace ki dawo baki dawo ba?Ta lallaba jakarta ta ciro yan dubu guda biyu, gashi kasa kati.Da sauri ya amsa ya tura a aljihu kamar yana tsoron kada wani ya amshe masa, ko kuma ita ta ce ta fasa.Ya shiga zuba mata godiya, ta ce, tunda jiyaya ce na dawo ban dawo ba me zai hana in shiga kawa yanzu?Dan sandan ya zaro ido oga yana da ka’da sai dai in yayi fada zaki fiar da ni?Tayi masa fari da idanunta, kada ka damu inyayi fadan zan wanke ka.Tun da shiga falon ta ke ta kalle kalle, falon nashi ya birgeta duk da cewa ba wani kayanalatu ya zuba ba.Ta zauna kan kujera ta bude jakarta ta dauko hoda da turare ta sake gyarawa.Sanan ta cire rigar sanyin dake jikinta saura singilrti, ta ajiye mayafinta ta gyara gashin dokin dake kanta.Sanan ta dauki wayarta ta soma kiran wayar ne ya tasheshi, wata isaka yaji tana kadawa tamkar za ayi ruwa.Windo ya nufa ya daga labule kamar yanda ya zata, hadari ne, yaji dadin haka ko don yakara mikewa.Wayar ta sake kacamewa da ruri, yana dubawa yaga number yarinyar, tsaki ya ja tare da yin jifa da wayar kan katifar sa.Ya bude kofar nifinsa yaje kicin ya samu abin tabawa, cak ya tsaya sabo da ganin yarinyar gaban shi ya soma faduwa, lokacin da zuciyar shi ke tuno mashi hoton.Yayi karfin halin daure fuska, sanan ya ce, da izinin wa kika shigo min gida?Ta mike ta nufosahi, da izininka masoyi na, ka manta ka ce in dawo jiya? Ban sami dama ba shine na dawo yau.Ya ce, to fita a gidan nan fita, ya nuna mata hanyar waje.Ta zauna a hannun kujerar dake kusa da ita,da ma ka bari mun fahinci juna.Ya juya ya shiga dakinsa a fusace, durowa yaje ya dauko bindiga nufinsa yayi mata barazana.Ya fito da ita ya saita ta, kwashi kayanki ki fita.Hakika gabanta ya fadi don bindiga ko makerinta yana shakarta.Amma duk da haka sai ta jajirce, ta runtse ido hawaye suka soma zuba,zanfi so ka kasheni feye da ka barni a raye amma baka amshi soyayyata ba.Zanyi alfahari in ka kashe ni da kanka, kuma kacewa jami’an tsaro ni na yafe maka ko sun tsinci gawata a gidanka.Aliyu ya ce, muje ki fita ni bana son jin komai daga bakinki.Sun isa bakin falo Ruwa ya tsuge mai karfi wanda hakan ya sa ya kyale ta.Ya shiga daki ya adana bindigar, sanan ya hau katifar sa ya kwanta. Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai masu nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com Kokuma ku kasance taredamu a facebook https://mbasic.facebook.com/HAUSA- Novels-389304544597988/?_e_pi=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
Gurbataciyar zuciyar sa ta shiga kitsa masa wasu
abubuwa, dauko wayar sa yayi yana kallon
hoton da yarinyar ta turo masa.Cikin jikinsa
sanyi yake ratsawa na ruwan dake
sauka.Mujidat turo kofar dakin ta shigo, kasa
magana yayi lokacin da ya waiwayo yaga ta raba
jikinta da tufafi.Yayi ta maza ya daka mata
tsawa, mai makon ta fita sai ta nufo gurinsa da
gudu ta fada masa.Shedaniyar shu’uma ce
yarinyar, don haka bata samu matsala sosai ba
gurin amincewa da gayyatar da tayi masa, zuwa
ga fadawa tafkin zunubin shedan ya sake
kawata abin ga zuciyar Aliyu.
Har yake ganin haram ta shigeshi fiye da
halalinsa.Mujidat ta amince Aliyu ne irin mijin
da take so ta samu.Duk runtsi ba zata barshi
ba, sai da kanwa takar tsami kwannafi ya
kwanta.Aliyu ya shiga jin cewa bai kyau ta ba.Na
dama ta shigeshi, ya mike cikin bakin rai ya nufi
ban daki zuciyar shi yar bakin ciki tana tunanin
shi cewa, wanan wankan da zaiyi anya zai fidda
mai da dattin zunubin daya kwasa?Ya fito ya
same ta kwance, haushinta ya kamashi sosai.Ya
dauki makulli ya bude durowarshi ya ciro kudi
batare da ya irga ba yan dubu dubu sabbi ya
mika mata.Gashi an gama ruwa ki tashi ki tafi
na rokekikar ki sake dawowa gidan nan.Ta
kalleshi cikin damuwa an ce maka neman kudi
nake yi?Ta mike ta soma saka tufafinta, so da
kauna kurun nake nema a gurinka baka da
kudin da zaka iya bani.Ta fice ta dauki jakarta
yana tsaye a tsakiyar falo yana kallonta ta fita
tare da cewa sai ka sake jina.
Ranar Aliyu yajima bai fita ba, na shi ganin
mutane zasu gane abin da ya aikata, kuma sam
baya son ya tuna.Sai istigifari yake yi, in dai
haka mazinata suke ji lallai zina bala’ice, ya
gargadi masu gadinsa lallai kada su sake barinta
ta shiganmasa gida.
Mahaifiyar mujidat yar asalin wani kauye ne a
Ilorin can jahar kwara, an ce dai asalinsu fulani
ne, amma yarbanci suke yi kuma yarbawa suke
kiran kansu.Musulmine su amma musulincin
nasu sai a hankali.
Mahaifiyar Mujidat mai suna Bukolatayi aure da
Mahaifin Mujidad hakimu bayansun haifi yayan
Mujidat dan suna fari kenan, mai suna
Latif.Wanan al’adar yarbawa ce mace taje aure
amma sai ta haihu za a daura, tasu hikimar wai
a gani in mai haihuwa ce.Bayan Latifa sun sami
Sikirat sanan Mujidat, mahaifin su mujidat
direban taxi ne, mahaifiyar su kuma tana da
shago a bakin kasuwa.Tun tasowar Mujidat bata
ji sam yar karya ce da son bobo, tunda ta lura
tana da kyau ai sai ta mai da kyawun nata
tamkar abin kasuwanci. Tun tana shekara tara
ta soma amsar kudi tana fansar da mutuncin ta,
haka ita mahaifiyart fitina gareta ko yau she
tana biye da mata wanan ya sa ko karatun kirki
bata yi ba, tana secondary idanunta sun gama
budewa, manyan mutane suke daukanta.Da
farko iyayanta sunda mu don mahaifiyarta ta
sha yi mata duka sanan tayimata tsarki da
ruwan barkono, amma da ga baya da ta soma
harka da manyan mutane tana kawo musu kudi
sai suka shiga shi mata albarka.Haka nan basu
damu tayi wata bata zo ba in dai zata yi musu
aike.A zuciyar su tafi yan uwanta Latifa da Sikira
wadda take aure a garin Ilorin.Kuma dalilin
ziyarar da ta kawowa anty sikira ta hadu da
Aliyu.Kuma har ta koma gida so da kaunar Aliyu
yasa ta ta dawo Ilorin don samun muradin ta.Jin
kai da jan aji irin na Aliyu shi ne ya sake burge
ta, amma sai gashi tashin farko ta same shi
cikin sauki.Tabbas in ta nace ba da dadewa ba
zai zo hannunta.Karfe tara na dare ta kira
numbar wayan mai gadin gidan Aliyu wanda ta
amsa dan bukatar kanta.Bayan ya daga ta
tambaye shi ka ganeni?Ya ce, a a ban gane ki
ba.Ta ce, sanana Mujidat daga nan cikin gari ni
ce wace na amshi numbar ka jiya bayan na fito
gurin Oga ya ce, ok madam ce ko?Sorry madam
na gane ki, ta ce oganka ya shigo?Ya ce, eh, tun
bakwai yana gida kuma naga alamar ba zai fito
ba, sai dai yayi mun kashedin cewa ko kinzo
kada in barki.Mujidat tayi shiru tana mamaki,
me zai sa ya tsaneta haka?Duk da ta mika masa
kanta kyauta, amma sai tayi wani
murmushi.Indai kissa tana magani to zatayi
mun, ta ceda me gadi in na baka dubu biyar
yaya zan samu in shiga?Yayi shiru yana
nazari.Lallai yana bukatar kudi don yasha kan
matsalarshi da maman Bilikis, amma dubu biyar
yayi masa kadan.Yace madan zan iya dabara in
kin ban dubu goma, zan fadawa Oga cewa
mamana ba lafiya nasan zai barni in tafi.Don
haka ta ba faruwa amma nasan kafin inbar
wurin sai an kawo wasu lokacin ke zaki samu
shiga dan su basu sanki ba.Kuma kafin in tafi
zan lalata wayar cikin gidan, ta ce hakan yayi
zan sameka da kudin in ka kamla komai ka
kirani.Yana kashe wayar yaga Aliyu tsaye a
bayan shi
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai
masu nishadantarwa
Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?e_pi=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
Dfarko ya rude sai kuma ya tuna cewa duk sun
yi maganar ne cikin yarensu na yaroba.Aliyu ya
ce, ina ta kiran waya baka daga ba?Ya ce, oga
jikin mama ne ya tashi shine dan uwa na ya
kirani.Aliyu ya ce, jikin ta ya sake tashi?Wani
ciwo ne ke damun ta?Ya ce hawan jini ne, Aliyu
ya sa hannu ya lalubo dubu biyu ya mika mashi
tare da cewa, Allah ya kara sauki. Ya kara da
cewa kaje ba sai ka jira wasu ba, bari nayi waya
su zo.Da murna mai gadi ya fita ya kira mujidat
yace, tayi sauri kafin wasu masu gadin su
zo.Cikin sa;a ta tura kofa ta shiga, haka nan
cikin sa’a ta riske shi a cikin falo zaune da yar
shirt fara irin mai kama jikin nan.Sai gajeren
wando, kalkon labarun kasa yake yi NTA, turo
kofar ne yasa shi waiwayawa, zunbur ya mike
yana nuna mata waje.Fita la’ananiya, ta saki
jakarta ta nufeshi, haba masoyina, ina sonka
sosai tsaya kaji.Ta kai hannu zata taba shi ya ja
baya.Ki fita kawai, ta zauna kan kujera, ba zan
sake barin gidan nan ba ko zaka kashe ni.Ya
biyota ta zagaya ta fada bedroom dinsa.Ya rasa
me zai yi mata, sai kurum ya kira yaransu daga
headquarter, jin haka dama tariga ta tanaji
dabararta.Taciro wayarta ta danna wani hoto ita
da shine suna tsaka da aikata masha’a ta
dauko.Kalli hoton nan ka gani, ina da irinsu da
yawa har na kati na wanke.Aliyu ya fizgi wayar
ya kalla, duk da ya girgiza amma bai nuna mata
ba ya ce, yace amshi wayarki ba kati ba in kin
gadama in kin tashi ki sa shi a kan profile din ki
na fcbk,ko a jikina.Ke ce mace mutuncinki sai
yafi nawa zubewa.Tayi shiru ta rasa me zata ce,
ya ce fita.Ta daga hannuwa biyu, naji naji zan
fita, ta matso gunsa amma ya kamata a ce
kanayiwa mesonka kallon mutunci da kima.Ta
soma kuka, ka tuna ba nice na dorawa kaina
sonka ba, ya kamata ko baka sona saika fada
min magana mai sanyi.Ya runtsa idanu, burinsa
ta fita domin zuciyarshi ta soma
tausayinta.Sanan ga shi dan can gefe yana rada
masa wani abu.Ya bude ida nunshi, shi ke nan
naji ban kyauta ba amma dai yanzu ki fita
kawai, domin ni da ke ba hurumai bane.Ki tuna
da abin da ya faru ni dake she karanjiya laifi ne
babba, kin sani.Ta matso ta kama hannuwansa
ka min afuwa sonka ne ya sani haka.Yanzu ina
jin yunwa ko zaka tai maka min da wani abu in
ci sai in tafi?Ya ce, duba kicin sai dai in bread za
ki ci.A kicin tayi ta zagayawa tana tunanin me
zatayi ne don ta samu ta kwana a gidan.Ta
dauki wuka ta dauko bread wai za ta yanka,
amma sai ta kulle ido ta sharbi yatsanta da
gangan, sanan ta saki kara.Cikin hanzari ya nufi
kicin da ganin yanda jinike zuba ya sa shi shiga
da sauri ya rike ya tsan nata.Kasancewar yana
da yar akwatinshi ta taimakon sai ya gyara mata
ya rufe shi sanan ya ce, muje a maki Allura sai
ki wuce inda kike.Ta soma rawan sanyi wai ba
zata iya tashi ba, barinta da yayi ta dan
warware shi ne ya kawo kwananta a
gidan.Domin tuni shedan ya ribace shi, duk da
yana zargin ta yanka kanta ne dama don kada
ta tafi, tun daga ranar ta zama gidan tamkar
matarsa, wanan ne yasa ko da ya koma gida
sadiya taga canji.
Wata hudu kenan da soma shiga matsalar mu
da ya Aliyu, amma tamkar na shekara biyu, duk
na rame na lalace har bana so inyi baki don
kada suce lafiya?Cikin wata hudu ya zo so hudu
duk karshen wata ke nan kwana dai dai yake yi
ya tafi sam baya kulani in yazo magana fiska a
daure yake min.Ya manta da wani hakki nawa
da yake kanshi, domin nima mutun ce ba ice
ba, ina shan wahala da kewarsa.Darare da yawa
ina zubar da hawaye don kunci da kewa, gashi
yayi mun sabo da yanayin sa na rashin
hakuri.Usman da Anty Abida sune kawai suka
san halin da nake ciki, ko iya da amininiyata
Aisha sunyi juyin duniya amma ban shaidar
musu da ko mai ba.Usman ya ce, duk lokacin
da nake bukatar wani abu bai min ba in
tambaye shi, ni gaskiya ina da jin nauyi.Yau in
na ce gashi gobe in ce gashi ba zai yuwu ba,
abin da kawai na tsana shi ne inga arana babu
makaranta, amma don abin anfani kamar su
abinci ina maneji.Tunanin kama sana’a ya
shigeni, na ce lallai ina bukatar in kama sana’a
don in samu in kare DARAJAR YAYA NA,
wadanda a yanzu sunfahimci tsakanina da
baban su a kwai matsala.Ba kausar ba hatta
Al’amin ya san cewa mahaifinsu ya canza, don
watarana da ya shigo daki ya same ni ina kuka,
sam banji shigowarsa ba sai naji an dafa ni.Nayi
ta maza na share hawaye na na kalle shi da
murmushi, ranshi a dagule ya ce, momy waye
ya saki kuka?Na ce Idona ke ciwo.Ya ce, mama
Abban mu ne ko?Na ce, a a Abbanku bayanan?
Yace, shi ne mana, ya ce ki barshi in na girma
zan maki duk abin da kike so, in kaiki maka, in
sai maki komai.Na rungume shi tare da cewa, to
yarona naji dadi na gode kaji.Ya ce momy ki
daina kuka kin ji?
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai
masu nishadantarwa
Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?e_pi=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
Bayan fitar Al’amin ne na shiga sabon tunani,
lallai matsala tsakanin miji da mata tana kawo
rabuwar kan yaya, tana tauye yara.Domin zuwa
da nayi open day din su a makaranta nan
malamarsu take yi mun korafin cewa yarinyata
Kausar sam yanzu bata da hazaka kamar
da.Bata da kuzari sam, ta ce kowa ya san
Kausar Aliyu Tutur a makarantar nan ya san ta
da kokari ga surutu, ga wayo.Haka nan duk
wanda ya yi mata bata kyalewa, amma daga
wancen term zuwa wanan tazama tamkar
doluwa ba karatu.Bata iya rama fada, karamin
yaro sai ya doke ta ta tsaya kuka, sanan tsaftar
su ta ragu, a da yaran suke zuwa na daya a
tsafta wanan karon sun koma na biyu.Don haka
kiyi kokari ki canja kila matsalar daga wajenki
ne.Afili na ce, lallai daga gurin mu ne,
matsalarmu zata maida yaranmu baya, dole in
kawo canji duk yanda zanyi gidan mu ya koma
gidan farin ciki kamar da da taimakon
Allah,Wayata na dauko na soma ruga sako
kamarhaka.KALMOMI SUN YI KARANCI
TSAKAKKEN YANAYI, FADIN YI HAKURI KADAI BA
ZAI GAMSAR BA.AMMA DUK DA HAKA INA ME
BAKA HAKURI, BA DAN NAYI LAIFI BA, SAI DAI
INA DARAJA DANGATARMU FIYE DA
SHEKARUNA.DA WANAN SAKO NAKE SAKE BAKA
HAKURI TARE DA AIKO MAKA DA ZUCIYATA KA
AMINCE DASHI DON SAKE DAWO MIN DA
FARINCIKI NA.INA FATAN ZA MU KOMA FIYE DA
DA, ZUMA TA ALY NAYI KEWARKA, INA TSNANIN
SONKA.
Na tura mashi ina tsammanin ganin sako kokira
amma shiru, duk wani tunani ko dabara nayi
amma babu nasara.Wata laraba da yamma su
kausar an koro su kudin islamiya, gashi dama
abincinmu ya kare, nafita hannuna da Nera Dari
na siyo garin rogo da suga.Nufina su sha da
dare, duk da ina tunanin yaya zan sha kansu su
sha gari da dare, sai lokacin da nake dawo wa
yana ba yana a mota direbanshi yana janye da
shi.
na shigo gidan zan Rufe sai naga mutum kamar
daga sama ya nufo gida, gaba na yayi muguwar
faduwa.Sam yanzu bana son ganin shi, don
tsananin tsoron sa nike ji, ko sallama baiyi ba ya
fara da ce mun, daga ina kike?Cikin in ina na ce
sha….shago baje can gurin hadi.Yin me?Na ce,
gari na suwo da suga.Gari?Ya tam baya tare da
zaro ida nu.Na sa dan yatsa na akan le buna na
tare da fadin yi hakuri yara suna ciki.Sai me? Ya
katse ni, na ce sai me in yara suna ciki, wato
sabon salon zubar da mutunci wanan kika samo
ko?Kamar ni a ce matata tana zuwa shago siyan
gari?Na nufi ciki raina a dagule, in ya bamu
abinda zamuci ishashshe ai ba zan fita siyan gari
ba, na raya hakan cikin raina.Kai tsaye daki na
shige na ajiye garin na fada ban daki don gudun
kada yara suji, da gudu suka rungumeshi suna
mashi oyoyo, al’amin da shi da mama, Kausar
tsayawa tayi tana kallon su.Ya dube ta ke
Kausar ba zakiyi min oyoyo ba? Ta ce sannu da
zuwa Abba.Ta juya ta nufi dakin su.Da kallo ya
bita cikin mamaki, me hakan yake nufi?Ta soma
yiwa yaran sa fanfo ne?Ya mike ya nufi dakin ni
kuma jin shiru sai na fito ina shigowa falo najiyo
muryar sa.Kausar ina tambayarki kin yi mun
shiru na ce me nene kike fushi?Sai na jiyo
muryarta tana cewa, Abba ni bana so ka dawo,
sabo da in kana nan kullum cikin fada da momy,
ni bana son tana kuka.Itama ta soma kuka, na
zaro ido cikin mamaki yarinyar,na saurara inji
me zai ce, fatana Allah yasa zancen Kausar
yazama sanadin fahimtar shi.Muryarshi ne ta
katse ni, ok wato uwarku tana kitsa muku
magana a kaina ko? Mamanku ta shirya muku in
nazo ina cutarku ko?Ya sake tambayarta cikin
daga murya, ban san lokacin da na fada dakin
ba ina fadin haba yaya.Yanzu me ya kawo
wanan tunanin?Tayaya za kayi mun wanan
zaton?Na kalli kausar fita.Ta fita na maida kofar
na rufe yana tsaye rai bace yana kallo na.Nayi
kasa da murya tare da tausasa ta, yaya wanan
sauyin da kakawo mana cikin gidan nan wlh ba
sai na kintsawa Kausar ko mai ba.Tana ji tana
gani, duk kokarin da nayi dan cewa basu
fahimta ba amma hakan bai samu ba.Saboda ka
kasa gyarawa, har takai ko a makaranta yaran
sun koma baya.Hawaye suka soma zubo min
masu zafi, na taka na isa inda yake tsaye nafada
jikinshi na kan kame shi.Yaya ka taimaka kayi
hakuri ka zubar da makamanka ka dawo mana
da farincikin mu.Ya ban bareni tare da hankade
ni har sai da na fadi, ya soma magana cikin
ihu.Tayaya kike so in yarda dake cewa bake
bace kike bata ni a wrin yarana ba?Yar wanan
yarinyar da bata gama sanin kanta ba shine har
zata san matsalar wani? To ni dake dasu munsa
hannu tunda kin zabi haka.Shiyasa sam bana
son zuwa garin nan, saboda takaicinki, kin zama
saikace sanda don Rama.
Kullun mahaifiyata tana tuhumata cewa bana
kula da ku, yanzu dan zubar da mutunci wai
kinje shago siyan gari.Na fashe da kuka yaya
yaushe rabon ka ajiye mana abinci?Tun zuwan
da ka tawo da wanan matsalar.Ya daga hannu
rufe min baki, yanzu ina yi maki magana ne a
kan shiga tsakanina da yarana.In zandau komai
ba zan dau wanan ba, ya kamata ki sani.Ya juya
ya fita bayan ya bude kofa.Kuka sosai nayi na
tsawon minti daya, sanan zumbur na mike na
fita.Mama tana kwance a tsakar falo tana ta
tsotsan yatsanta, ita bata san me ke
faruwaba.Ahmad yana zaune kan kujera ya
takure, Kausar na shiga raba ido in gani, can na
hangota gefen kujera ta makure tare da toshe
kunnuwanta, tana nufin bata son jin abinda ake
yi, ga kuka tana yi.Tayi sharkaf da majina,
dakinsa ya shige shikam naje na rumgumo
Kausar nazo na hadasu da Al’amin ina
lallashinsu.Duk da cewa nima hawaye ke
kwaranya a idanuwa na, Al’amin yazo yayi mun
rada a kunne, ki hada shi da Iya kinji Momy ta
rama maki(don duk zatonsu ni iya ta haifa ba
baban su ba) Najasu muka koma dakinsu, na
ce, Kausar Al’amin kuyi hakuri ni da Babanku za
mu koma kamar da, ba da jimawa ba kunji ko?
Kausar ta dago kai, yaushe momy?Na runtsi ido
hawaye na kwaranya na ce, bada jimawa ba
Kausar kinji?Duk suka makaleni, Al’amin yasake
cewa kin hada shi da Iya ne, da sauri na ce a a
ko ku kada ku fada mata, ba na ce muku bata
da lafiya ba?Kuna so in taji da muwa ciwonta ya
tashi?Duk sukayi shiru, nace kuna so ta mutu?
Da sauri suka ce, a’a,na ce to in kun fada mata
zata mutu.Kausar ta ce, bazamu fada ba.Na
share hawayena sanan na kallesu.Muna ciki har
aka kira magariba, na taso su mukayi salla.Tinda
na fito banga Mama ba, nasan tana gurinshi,
suna ciki ko sunfita oho.Na jika musu gari suka
zauna, Allah ya taimakeni suka kama sha.
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai
masu nishadantarwa
Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?e_pi=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
Kausar tana cewa,Momy in nazama babba zan
dinga siyo mana kayan abinci.Al’amin ya ce,
momy ba na rigata ba.Yaya kausar nine
zandinga siyan ma Momy ko mai, na ce to tun
yanzu nagode, Allah ya raya ku, ku girma cikin
aminci da Albarka, suka ce amin.Raina yayi
sanyi yar firar nan da muka yi da ya rana sai
gashi sunyi sallama shi da mama tsam ya tsaya,
ganin suna cin gari.Na lumshe ido na hadiye
takaici na, sannan na ce sannu da zuwa.Bai
amsa ba yayi ciki, kamar in zauna sai kuma na
bishi.Ya aje mama ya zauna bakin gado tare da
dafe kai, na ce, ina maka sannu.Ya dubeni
idanu jajur.Yaya na ke cin gari da dare?Na ce,
to yaya bamu da komai ne.Na dubi mama,
zomuje ki ci gari.Ya daka min tsawa, ki daina
kira min sunan garin nan, ba zataciba.Ko
Inyamuri ya sha gari da daddare? Wanan shine
na karshe in ba haka ba rai zai baci, ban ce kala
ba na juya, cirko cirko nagasu Kausar a
falo.Kausar ta toshe kunne, Al’amin na tsaye
cikin damuwa,nakamasu muka koma na ce su ci
garin amma sai suka ce sun koshi.Kausar ta
kwanto kan cinyata, Al’amin ya kwanta kan
kujera na kwantar da kaina nima a hannun
kujera.Wai ta wace hanya zanbi gidana ya dawo
kamar da?Wa zai ban shawara dan ni ina ganin
tawa basirar ta kare kan haka.Allah ka bani
mafita.Muna nan har aka kira isha’i, na tashi
naje nayi sallah suma sukayi sai ga mama ta
shigo da nama da Holandia, na ce, suci.Al’amin
dai ya ci amma Kausar kin ci tayi waita ta koshi,
na rungumo ta, Kausar kina fishida Abbanki ne?
Tayi shiru, na ce ki fada min.Ta ce, eh momy
shima yanzu ya daina sonmu nace, a a yana
sonmu fushi yake yi in ya huce zai dawo kamar
da.Sai kurum naji ta ce, wane ne yayi masa
laifimomy?Na ce, ni ce, ta ce, bakiyi mashi ko
mai ba, ba ma kullun kina bashi hakuri ba
tunda yaki yayi hakuri ya daina sonmu.Bani da
bakin magana sai shiru ina mamakin Kausar,
yar wanan yarinyar har tana fahimtar abubuwa
kai abin da mamaki sosai.Haka na lallaba su har
sukayi bacci na kulle mana kofa sanan nima na
kwanta na fada kogin tunani.
Wa she gari da wuri na tashi nayi salla da
wanka, sanan nayi musu shirin makaranta, duk
a dakinsu.Nace suje su gaida baban su.Kausar
ta noke tare da daure fuska za ta soma kuka,
na ce, haba Kausar, kuje ku gaida Babanku
mana.Kina so ne ya j haushi irin jiya?Jiya ma kin
ki sakar mashi fuska ne shi yasayayi fada.Ta ce,
to momy yanzu tsoronshi nake ji.Na ce, daina jin
tsoro kinji Kausar, yana sonku.Daga nan ki bashi
hakuri.Ta ce, to.Amma sam fuskarta ba wani
annuri, ina biyeda su har kofar, Al’amin ya
kwankwasa daga ciki yaya ya ce, wanene?Mama
da jin muryarshi sai ta ce, Abba.Ya ce mama.Na
bude kofar suka shiga, yana kwance kan gado
da waya a hannunsa, da Alamu cht ya ke
yi.Kausar ta dan tsaya nesa dasu kanta a
kasa.Al’amin ya zauna bakin gado,Mama ta
hayekan gado, ya rungume mama da Al’amin
sanan ya tashi zaune.Al’amin ya gaida shi,
Mama ma cikin hausarta mara dadi ta gaida
shi.Ya kalli kausar daga inda take.Zo nan.Ta tafi,
ya janyota zuwa jikinshi, ta ce ina kwana?Ya ce,
ba zan amsa ba Kausar har sai kin fada mun
me mamanku ta ce maku nayi, kuke jin haushi
na?Kausar ta ce ba ko mai Abba, Al’amin ya ce
ta ce ne fa muzo mu gaida kai.Ya kalli Kausar,
yanzu kunfi son mamanku fiye dani ko?Al’amin
ya ce, muma ka daina son mu Abba.Ya ce, ok,
haka mamanku ta fada muku?Kausar tayi saurin
cewa momy bata fada mana haka ba, ta ce ne
kawai muje mu gaida ka.Ya dungurewa Kausar
kai yar karama da ke kin iya munafunci, ba zan
kara yi maki tsaraba ba.Ya kalli Al’amin, in ba
ka daukar maganar mamanku zan sai maka
keke kana so?Al’amin ya kama murna ina so
Abba.Ya kalli mama, mama na ke kuma in se
maki motar ki ta wasa ko?Na juya kicin ina kuka,
mutumin nan zai raba mun kan yara, zai kafa
min jam’iya yan partyn shi da nawa.Jin takun
Kausar yasani share hawaye, cikin sheshekar
kuka ta ce, momy kinji Abba zai sayawa su
Al’amin da mama tsaraba ban dani.Na tsugunna
na rungumota jikina ina shafa mata kai, yi
hakuri Abbanku wasa yake yi miki zai siyo miki
kinji?Ta ce, Allah momy da gaske yake yi ba ya
cein fitar masa daga daki ba?Na ce, yi shiru zai
sai maki.Da kyar tayi shiru.Na bata jug na ce,
kije wajen Iya ki ce mata in ta dama koko ta
baku, karfa ki ce mata wani abu ya faru kinji?Ta
ce to.Ta tafi nikuma na zauna a kicin cikin ta
gumi.Kausar ta sami Iya kwance ta gaida ta, ta
ce kausar menene?Ta ce, wai in kin dama koko
ki bamu, iya ta ce shine aka turoki ba Abbanku
ya dawo jiyaba?Me yasa bai rakoki ba?Tayi shiru
Iya ta ce to muje in se maki koko gidan ladi me
koko dan kulluna jiya ya kare, kice mata na ce a
jika maku gero tunda jifa jifa kuna shan kokon,
ban cika son abin siya ba.Sam iya bata fahimci
bamu da komai a gidan bane, tunda lokaci zuwa
lokaci sukanje su amshi kokon.Ta samu masu
kosai sanan ta rakata har kusa da gida.Tanaji
tana fadan turota ita kadai a wanan safiyar, ta
ce da uwarku tana tattalinku amma yanzu duk
ta canza,na rasa me ke damunta.Suna shan
koko da kosai kausar tana fada min sakon Iya,
na jika gero na ce to za a jika,suka gama na
dauki Mama na nufi kaisu makaranta, kusan
wata guda a kafa nake kaisu makaranta, don
mota tuni nayi fakin dinta gefe na rufe ta don
ba mai ba na da kuma kudin siya.Ina dawowa
na tarar da shi da Usman zaune yana
karantowa Usman laifuka na.Na gaida Usman na
shige daki, na hau gado na kwantawa,bawai don
bacci ba ko don hutu, sai don tsabar ta kaici.Can
na jiyo muryarshi yana kira na, ya kalle ni.Kin
san na fada maki ba zan dauka ba ki rabani da
yara na ba.Jiya na shigo gidan nan wai Kausar
tana yin fushi dani yar karamar yarinyar
nan.Al’amin yana fada mun na daina son su,
tayaya zan yarda wanan tunaninsu ne?Usman
ya daga mishi hannu saurara aboki na, ka barni
in gama magana ta don kada kakatse ni.Usman
ya kalleni,Sadiya me yake faruwa ne?Na runtse
ido don ta kaici, yaya Usman duk abin da ya
faru Abban kausar shine sila.Na koro mishi
komai tun daga farkon rigimar har zuwa
yau.Sanan na ce yaya Usman tsakani da Allah
kullun yaran nan suna kallon muna fada, ko
ince daga yazo sai shiga tashin hankali zasutashi
da tarbiya me kyau?Ya ce, a a.Na fada musu
yanda mukayi da malamansu. Ga rashin abinci
wane laifi na masa, ni dai yanxu tunda gani
gashi kurun ya fada min laifi na, wlh zan bashi
hakuri mu koma kamar da yaran mu suma su
sami natsuwa.Usman ya kalli Aliyu, aboki kaji,
sai ka fada mata laifinta don matsalar tazo
karshe.Aliyu yayi mun wani kallo ke dai kawai
baki son zaman lafiya ne, duk ki dauki damuwa
da bakin ciki kisawa kanki.Sau nawa zan fada
maki baki yi mun komai ba?Usman ya ce, to na
rokeka aboki ko mai ya wuce.Ya runtse ido tare
da fadin shi ke nan.Na dube shi nima in sha
Allahu ko mai ya wuce.Usman ya ce,
Alhamdulilla, yanzu sai ka tashi mushiga kasuwa
don nima abincin gida na ya kare.Nan dai suka
fita.A cikin mota Usman ya kalli Aliyu.Aboki ka
canza fa,Aliyu ya kalleshi wacce irin canzawa
nayi?Usman yayi murmushi sanan ya maida
hankalinshi titi.Kayi kiba sanan dabi’un ka sun
canza.Aliyu ya kure Usman da ido, zaiyi magana
kenan wayarsa ta soma ruri, ya ciro ya kurawa
Screen din ido,sha wara yake ya dauka ko ya
yanke,Usman ya kalle shi, daga mana abokina,
Aliyu ya katse kiran sanan ya kalli Usman,daga
jin kira sai kace in daga ba tare da kasan me
kiran ba?Usman ya ce, jami’in tsaro zai ji
shakkar daga kiran koma wanene…….Kiran
yasake shigowa, sai kurun Aliyu ya dagadan
kada Usman ya dago abinda ke faruwa.Ya ce,
yaya?Mujidat ta ce, muryarka nake sonji, nayi
kewarka da yawa, don Allah ka dawo yau.Tana
magana kamar zata yi kuka, salon dake narkar
masa da zuciya,take ya manta da wa yake tare
har ya furta cewa.Kada ki damu gobe kamar
yanzu muna tare,ta ce, to Zaki na sai mun hadu
a internet.Sai da ya salameta sanan ya tuna
yayi baram barama.Ya dubi Usman wanda bai
ce kala ba, ya soma nade tabarmar kunya.Wata
abokiyar aikina ce, muna gabatar da wani
aikine.Usman yayi murmushi sanan ya ce, sau
da dama in mutun ya shiga aikata rashin
gaskiya sai kaga ya zama makaryaci.Ita ko karya
illar ta da kayi so daya kafin ka fitar da kanka
sai kayi kusan sau goma.Aliyu ya kalle shi, me
ya kawo wanan zancen?Usman yayi dariya, ka
tsargu ne?Aliyu ya kalli gefe, intsargu da me
kuma?Usman ya hade rai, tsayar da halayenka
haka nan Aliyu.Ya gangara gefe titi yayi fakin
dazu nake ce maka dabi’unka sun canza ko?
Aliyu ya kalli titi muje zuwa da maganarka, in
wani zai fada mun aboki ba zan yarda ba,
amma gani ina zar ginka cewa kana hulda da
matan?Aliyu ya kalleshi da sauri, haba aboki,
nasancewa zaka iya bada shaida cewa ban
kasance mai shiga lamarin da mata suke ciki ba,
bare har inyi hulda dasu.Usman ya ce to amsa
min wadan nan tambayoyin.Aliyu ya cire hankici,
ya share zufar fuskarsa sanan ya ce, ina
jinka.Usman ya ce, na kira layinka sau uku wata
macece take dagawa.Na farko da dare ne gurin
karfe dayan dare, don in fada maka rasuwar
kanwata, sai kawai wata mace ta daga wai ka
shiga wanka.Na biyu da safe wata jumma’a don
mu gaisa ta ce ka fita gurin masu gadi, na uku
gargadi tayi mun in san lokacin da zan
dingakiranka yanzu kana cikin halin da bazaka
iya daga waya ba.Sai na soma lissafi giya kake
sha da har ba zaka iya daga waya ba, koko
menene?Sanan ita wanan matar yakuke da ita
har zata kasance a inda kake ciki tsakar daren
nan .In zuciyata ta zargeka sai wata ta shaideka
da cewa ba aikin ka bane, abin da bakayi ba
kana yaro ba na zaton cewa zakayi shi da
girmanka.Amma yau da matarka take fadin
yanda ka kaurace mata, sai na amince kana
neman mata, don kai ba me hakurin zama baka
tare da mata bane.Aliyu ya hade rai tare da
duban Usman, me cece shaidar ka ta zahiri?Duk
abin da kafada bai zama shaidar da zaka
amince ina bin mata ba.Ba zan iya zama ba
mace ba, shekaru nawana dauka can baya babu
auren?Usman ya ce kila lokacin baka san
amfanin matan ba,amma ni shawara daya zan
baka, inma zakayi harkar bariki to bai kamata ka
wulakanta matarka ta sunna ba.Aliyu ya ce, dan
Allah mu rufe wanan firar.Usman ya ce kafin
mu rufe sai nayi maka nasiha duk da cewa bani
da tabbas akan zargin da nake yi maka.Na san
mutun yana canzawa kamar yanda wahainiya
take canzawa zuwa duk kalan dataso.Nasihata
gareka in ka canza daga fari zuwa baki don
Allah ka saki wanan layin ka koma dai dai ko
don gudun zunubi, ko don tsoron azabar
Allah.Ko don kare mutuncin yayan mu, ko don
kare lafiyar ka daga cututukan zamani.Sanan
maganar zubewar daraja da kimarka a idon
wayanda suka san kanayi. Aliyu ya runtse ido
cikin in ina yace, muje aboki don Allah.Suna tafe
yana share zufa, lallai zancen Usman ya shige
shi.
Ko mai na abinci zuwa kayan tea sun hada
muna, lokacin da suka dawo ina kwance
kangado ina karanta littafin gidan zahra.Sau da
yawa in ina karanta littatafan Hausa sukan debe
min kewa halin da nake ciki, har na sha cin karo
da irin matsala ta.Sun ajiye min kayan abinci
suka sake ficewa, na fada kichin na shiga girki,
yarama da suka dawo makaranta sai murna
suke sun sami lafiyayen abinci.Yaushe rabon
muyi girki da kifi ko nama, yau gashi har
farfesun kan rago mukayi.Da daddare na fada
ban daki na sake wankana sheka kwalliya duk
tunanina yau za a shalabari.Sai dai muka
kwanciya ya juyya min baya, na gaji hakurina ya
kare don haka na ajiye kunyata na fada masa
cewa, yau ni ina son a faranta min.Ya ce, shi
gaskiya baya jin zai iya wani abu yanzu don duk
a gajiye yake.Nace, haba yaya, nima fa mutunce
kamar kowa, sama da wata hudu ka juya min
baya.Baka tsoron sharrin shaidan?Ya tashi
zaune a fusace, kina nufin zaki bi maza? Iye?
Fadamin zaki bi maza? Nasauka daga kan gadon,
ban ce zanyi zinaba yay, amma zuciya bata da
kashi, in na kasa jurewa fa?Na durkusa kan
gwiwowina, yaya ka taimake ni ka fiddani wanan
yanayin, ka tuna ni ban taba gudunka ba.Ya
mike ya dauki filo.Sai da ya kai bakin kofa
sanan ya ce, ina ganin kina cikin fitunananun
mata bari naje falo in kwana. Rufda ciki na
kwanta a kan gado ina kuka, wani mai kunci
daga bisani na dangana na fada ban daki na
sakarwa kaina ruwan sanyi yayi ta zuba tundaga
tsakiyar kaina.Ban fito ba sai da naji sanyi yana
ratsani, na fita naje kan gado na dukunkune sai
zazzabi da ciwon kai.Haka na kwana har safe da
kyar nayi Sallah na sha magani, sanan na fita
kicin.Shi kam a ranar ya koma kusan karfe biyu
ina kwance ya tsaya kaina wai ni fa zan tafi.Ba
tare da na dago ba, na ce Allah ya tsare, ya
ajiye kudi a gefe na tare da fadin, motarki an
gyara na ce uhm.
Duk da cewa Aliyu yana kirana a waya mu gaisa
yanzu duk abinda muke bukata yana
kamantawa, sai dai ya barni cikin kewa.Haka
nan ko a waya da mun gaisa shi ke nan sai ya
ce in bashi yaranshi suyi magana,ba wata hirar
soyaya ko ta rayuwa bare in sa rai zamu koma
kamar da.Duk da cewa yanzu yaran nan sun
dan saki jikinsu sai dai duk da haka da sun
ganni cikin takura ko damuwa yanzu zakaga
sunyi mun narai narai tamkar zasuyi kuka.Ni dai
a bisa halin da nake ciki gara ace bukatun ya
dai na yi mun ya bani kulawa da soyayya sunfi
mun duk wani abin duniya da zai sai min.Na
hakura ne saboda DARAJAR YAYA NA, sam bana
so in zube su inyi gaba.In ban rike suba naje
can inyi wahalar yayan wasu.
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai
masu nishadantarwa
Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?e_pi=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
Wata rana naje kitso inda nake zuwa a can layin
zage-zagi wani gida, gidan haya ne maidauke da
matan aure da dama.A kulun naje gidan ina
karantar abubuwa na rayuwa da dama a gurin
matan gidan.Farko matar dake yi mun kitso, sau
da yawa mijinta in yadawo bata iya sakin kitson
taje gurinsa.Haka zai gaji da zama ya fito ya
dauki bokiti ya ja ruwa yaje yayi wanka.In kuma
da abinci ya ci ya fito in ya ciro kudin cefane ya
bata sai ta amsa a raine, yauma da nazo kitson
hakan ne ta kasance.Ya bata dari biyu ta juyata
sanan ta maida masa tana fadin gaskiya malam
bazata isa ba.Ya ce ba da garin tuwo ba, kuma
naga manja?Ta ce yau kwana uku muna tuwo,
ta kalli yaranta dake gefe suna wasa.Habu kunji
babanku wai yau ma tuwo sai suka rugo da
kansu gaskiya baba yau bazamuci tuwo ba.Ya ce
to me ni dai kudin nan ke nan.Ta ce, ko tuwon
ne ma kudin nan ba isar muzaiyiba, ya ce haba
Tasallah, ba kifi ba nama kice dari biyu baza tayi
miya ba?Ya shura takalminsa yayi gaba.Ta daga
murya sai dai ayi maka ciko kuma kana zuwa
zaka bani kudi na.Yaran suka hau mita, shi
baban nan kullun tuwo.Na kalleta cikin mamaki
sanan na ce, na kusan daina zuwa kitso gurinki,
ta ce zaku tashi ne?Na ce a a na ce nagaji da
yanda kike daukar mijinki ba a bakin ko mai
ba.Dubi yanda kike sa yaranki suna yi ma
mahaifinsu rashin da’a da raini, wanan tarbiya
ke nan?Tayi yar dariya hajiya kenan, Allah hajiya
ba haka bane, ace mutun kullun ba ci gaba, ba
ya neman wata sana’a a caba yake.Na ce, na
lura baki da godiyar Allah ta salla. Ranan fa ina
kallonki da yaranki kuka ce masa kun gaji da
shinkafa, san nan baki sanin mijinki ya dawo ki
bishi daki ba…..
Allah sarki Rayuwar Aure,kowadai da tasa
matsalar,damadai haka Rayuwar take,tanada
manyan matsaloli guda hudu wadanda duka
daya takan haddasa rashin jin dadi daga
bangare daya,Immadai -:
Mijin baya jin dadin zama da matar,misalin
Tasalla me kitso da Mijinta,kokuma…
2:Matar ake zalunta ,Misalin Aliyu da
Sadiya,Kokuma …
3:Suna zaune lafiya a junansu, Amma dangin
matar ba kaunar mijin,shima Wannan Babbar
matsalace a auratayya,Wacce ke Haifar da Babar
Matsal..kokuma…
4 angin mijine basu son Matar, wanda nasan
da yawanku kunfi sanin wanna matsalar,..
Lallai dukanin gidan auren da suka samu kubuta
daga dukkanin matsalolinnan nazama wajibi Su
godewa Allah,akarshe Dukkani gidan Auren dake
da matsalar makamanciyar wadannan Ya Allah
ka kawo musu agaji,mukuma Ya Allah
kahadamu da abokan zama nagari
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai
masu nishadantarwa
Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?e_pi=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347

Zaharaddeen shomar
Whatsapp 08168575100

Darajar Yayana2-04
Posted by ANaM Dorayi on 06:34 PM, 29-Mar-16
Under: DARAJAR ‘YA’YANA
__________________NA ___________HALIMA K/MASHI Assalamu’alaikum, fatan kuna cikin koshin lafiya… Sagir Ali, Shamsusdden Usman,Fatima Ahsan,Maman Ummi,Shamsiyya,Ummi Amal,Aisha and Aisha Kaka Zanna nagode da kulawarku,sannna inna jin dadin yanda kuke kulawa da shige da ficena,shirun da kukaji yafarune sakamakon ayyuka da sukaimin yawa,fatan zakucikaba da bibiya dakuma hakuri dani. nagode zamu Dora yanzu….. Ruwan wanka sai dai ya diba yaje yayi, wanan rashin dabi’ar har ina?tasake yin dariya, to ni in nashiga dakin in ya dawo me zan masa?Na ce, auran kiyayya aka maki?Ta ce, a a ni na kaishi gidan mu, ta ci gaba kin sani ni gaskiya ko ya dawo bana shiga, shi yanzunnan zaice zai rungume ni, niko na tsani haka,ka debo rana ka wani ce zaka rungume ni, salon su Habu su fado dakin?na ce menene dan yaranku sun ganku rungume da juna?Kai ke dai baki da dabi’a,irinku ne ake kwacewa miji cikin sauki,daga baya kizo kina ya ci amanar ki,ni dai in baki canza haliba zan daina zuwa,ta ce;to Hajiya za’a sake, ai ku hajiya cikin daula kuke baku da matsala.Nayi murmushi Tasalla kenan.Shiyasa na ce, kina da hange, ki kalli kasanki mana,Misali waccan Maman Rashidan kuke ce mata ko wa?Tunda nake zuwa gidan nan bai fi so nawa naga ta daura tukunya ba.Kullun in kazo zakaga yaranta suna cin dumame, ko garin rogo amma ban taba ganin mijinta ya dawo ta barshi ya dibi ruwan wanka da kanshi ba, ko ta shareshi taki shiga daki.Sanan sau biyu na taba ganin mijinta nasan yayi sa’ar mata, duk cikinku ‘yan nan sasan da na taba ganin shigowar mazajenku da fitarku ita kadai ke yi wa mijinta sannu da zuwa da yi mashi addu’a in zai fita.Tasalla tayi yar dariya, hajiya kenan, ita waccen ai bata san kimarta ta ya mace ba, in banda haka yaushe zan zauna babu abincin kirki.Amma kina like da mutun kullum sai tayi wankan asuba don jaraba.Na ce, tafi ku godiyar Allah ne da biyayya.Sanan zakuga cigabanta kuna nan, sanan yaranta sunfi naku tarbiya da tsafta.Tasalla ta bata rai,Hajiya mu bar maganar nan, amma ko su maman Auwal zaki tambaya matarnan tana shiryawa yaranta kinaya ne don in mutane sunzo su rinka gaidasu don a ce suna da halin kirki.Na ce, ba wani bayan aike ma ina kallon naku yaran amma baku aikensu don kunsan cewa bazasuba, sai dai ku kira nata.Daga nan Tasalla tayi kus, niko na ce in sha Allahu duk randa zan kuma zuwa sai nayi wa yaranta kwalima tunda naga yaranta basu fi girman su Kausar ba, a raina na raya hakan.Ina Mota na kusa isa gida da motar dama naje gidan kitson da mota ne, sai ga kiran Aisha aminiyata, cikin hanzari na daga ina fadin.Kin haihu kenan? Tayi dariya yau andace kullun na kiraki zancenki daya ne kin haihu?To ga yarki nan a gado.Na ce, Alhamdulillahi ga ni nan.Na kira layin Abban kausar kamar yanda na zata har ta tsinke bai dauka ba, na sake kira.Muryar mace naji cikin harshen turanci tace wakike nema?Sai da sitiyarin ya kusa kufce min, na samu na tsaya tunda cikin unguwa ne, na sake yin sallama cikin rawar murya.Ta ce kina bukatar taimako ne?Na katse layin zufa ta soma tsatstsafo min.Na rude matuka, na kifa kaina a kan sitiyarin ina fadin Allah yasa mafarki nake yi.Na kuma kallon wayar ina shawaran in sake kira ne ko in barshi, sai ga kiranshi ya shigo da sauri na daga amman na kasa magana, Muryarshi ne yanzu ya ce hello!! Dazun bakiyi magana ba sai wata irin muryanake ji.A sanyaye na ce dazun ba kai bane wata ce ta daga.Da sauri ya ce wata wa?A wayata?A’a sai dai in network ne yasa ki kika ji haka.Ya saki zancen da cewa, lfy dai?Na ce eh dama ina dawowa daga gidan kitso ne sai Aisha ta kirani ta haihu.Ya ce wace Aishan?Na ce, ta mamana.Ya ce, Allah ya raya, kin cika son yawo.Na ce to yaya in banje yanzun ba dole in sake fitowa don inyi gabadaya.Ya ce to shi kenan ina yaran?Na ce sunje yiwa iya wuni, ya ce ban son fa kina tafiya ke daya fa.Ko mama bakya iya yawo da ita sai ke daya tsura?Na ce, to yaya sun kwana biyu ne basu je sunyi mata yini ba.Ya ce, to shi kenan kardai kiyi dare don na sanku in kuka sami surutu na ce to. Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai masu nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com Kokuma ku kasance taredamu a facebook https://mbasic.facebook.com/HAUSA- Novels-389304544597988/?_e_pi=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
Bayan ya kashe wayar ya nufi gurin Mujidat da
ke zaune kan kujera tana dafe da kumatu, inda
Aliyu ya watsa mata mari sakamakon shigowa da
yayi ya ganta ta daga masa waya.Ya kalleta in
kika kara yi min gangancin daga min waya sai na
mugu saba maki, don zaki koma inda kika fito.Ta
mike tsaye kana jin tsoron matarka ne don kar
tasan muna tare ta ce ta fasa aurenka?Cikin
gatse Aliyu ya ce haka ne.Don haka kada ki kara
daga min waya.Ya juya ya shiga dakinsa rai a
bace.Mujidat ta mike tsaye tana kai kawo, wai
mutumin nan yana nufin duk son da nake masa
yafi son matarshi a kaina?In ma yana boye mata
ne sai nayi sanadin da zata sani, in sha Allahu.Sai
dai ta mutu ko ta bar mun shi, don na yi imani
na fita son shi, zanyi komai don naga na rabasu
da makircina kawai,ta hada yatsanta babba da
na tsakiya taja suka yi kara, wanan wata Alama
ce da take yi duk lokacin da ta ma kanta
Alkawarin aikata wani abu cikin izza.Ni kam
kwana nai da motata zuwa gidan Aisha, amma
zuciyata cike take da wasi wasin abin da kunne
na yaji wai netwok ne.Anya kuwa ba binne ni
yaya yayi da rai na ba?Nayi murna da ganin
Aisha cikin koshin lafiya tare da jaririnta.Na dauki
yarainyar ina juyyata, mashaAllahu,Bello ya fiki
karfin jini daga ita har Najib shi suka biyo.Na ce
haka dai su mama suka ce, na ce, ina angon
karnin?Ta ce ya fita na kwantar da yar na kalleta
a Asibiti?A gida kafin ya samo mota har kai ya
fito.Innarsu da mamanmu da ma suka zo sai
kurum suka amshi haihuwar, na ce shi kenan
Allah ya kawo shi cikin sauki.Na nufi wata kula
dake gefe, na ce me suka barararaka miki?Na
bude kular, ta ce tuwo ne, miyar kuka, kinsan
tsaffin nan sai suce wai maijego sai da
tuwo.Muka sa dariya, na ce a ni na horu da tuwo
gurin Iya, haihuwar kausar har wani baki nayi
nayi muni dan uban nan.Muka sa dariya.tace, ai
daga baya Anty Abida ta hada maki sabulu, na ce
ai ta min kokari yanzu ba abin da bana hadawa
da kaina.Ta ce zaki hada min sabulunma nace to,
haka mukai ta fira har shida, sanan mukayi
sallama naje gidan Iya na kwashi yayana muka
tafi gida.
Na kasa bacci cikin dare sai juyyi nake kaso
hamsin da daya na zuciyata, yaya Aley yayi
min.Tabbas zan zama wawiya in ban amince yaya
yana neman mata ba.Yaushe rabon da ya dora
yatsansa kan nawa?Kullun dare ina kwana da
kewa, hawaye na suna kwaranya.Na tashi zaune
in ko haka ne wane mataki zan dauka.Zuciyata ta
dauki zafi ina fidda wani huci, lallai in ya kasance
haka zamuyi rigima ba karama ba, don ba zan
dauki wulakanci a kan matar banza ba.
Washe gari da safe ina ta tunanin yanda zansake
cewa yaya zan sake komawa gidan Aisha, saboda
in na haihu kulun tana hanyar har ayi
suna.Amma ni ko haihuwar Najib dinta banyi
mata wani sintiri ba, yaya hanawa yayi.Kuma
bana son fita batare da izininshi ba.Don nayi
imani shi baya kallona Allah da ya halicceni yana
kallona.Text na tura mashi cewa zanje gidan
Aisha lokacin suna tare da Mujidat suna
karyawa.Ya dauka ya karanta, sai ko ya hade rai
ya soma kiran layi na na daga.Tunkafin in karasa
sallama na ji ya ce, ban amince ba kullum fita,
saboda ki dinga kallon maza ko? Na zaro ido na
mike da sauri na nufi daki dan su Kausar suna
nan gida don anyi musuhutu.Kuma bana so suna
jin matsalar mu.Ya ci gaba da fadan shi, na ce
wacce irin magana kake yi yaya?Don in dinga
kallon mazaje fa ka ce?Kana nufin in na fita haka
nake yi?Ya ce, oho miki, amma ban yafe ba in
kika leko waje, nace naji ai tunda ka hana ba zan
fita ba, amma cewar da kayi wai ina kallon mza
nike son inji hujjar ka.Kana ga don ka shuka
fulawa ta fito kaki kayi mata ban ruwa sai ta
mutu?Na ci gaba, haka ne zata mutu amma
kasani ni nasan DARAJAR YAYA NA.Ko don su zan
kare mutuncina kai shaidane budurwa gar ka
bare ni a leda, ka san haka kuma kullun ina
Adu’a Allah ya kare ni daga sharrin zamani.Ban
jira amsarshi ba na kashe, sanan na fada kan
gado ina kuka.Sai kurum naji hannun kausar a
baya na tana fadin.Momy kiyi hakuri ki kyale
shi.Da sauri na share hawaye na taso kausar
bana ce in ina waya a daki ba ku daina biyo ni?Ta
ce momy ki daina daga wayar Abbanmu, ko ya
kiraki ni bana so yana saki kuka.Na ce naji muje
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai
masu nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?e_pi=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
Kwana uku da yin sunan yar gidan Aisha ya ta ci
sunan Fateema, sai ga yaya da rana tsaka ina
mamakin yanda yanzu yake son yimin dirar
mikiya.Ko yana zargin ina fita ne?Oho.Nayi masa
sannu da zuwa ya amsa na ce, baka fada ba
gashi banyi abincin rana ba.Jiya sun bar
shinkafar da na dafa da dare, sai kawai nasa a
firiza yau na duma ma, amma bari in maka ko
macroni ce.Ya ce barshi bani da yunwa, in na fita
zan siyo fura.Sai da yayi bacci sanan ya tashi yayi
wanka ya fita.Duk ina dakina ina karanta littatafi
,tinda nalura bai bukatar ganina kusadashi, nima
hakan yafi min sauki don in yana gari nafi jincewa
nima macece in kwana cikin kewa.Washegari ya
fita zuwa gidan su Iya na dauko jakarshi, don
kwashe kayan wanki wanda ya dawo dasu kamar
yanda na saba.Ina daga suit din shi zan rataye
wata takarda ta fado, na dauka har zan maida
masa cikin Aljihun rigar sai wata zuciyar ta ce
bude mana ki gani, na bude.Yar wasika ce aka
rubuta da harshen turanci, ga abin da yake
rubuce.ZUMA NA KA TAFI DA TUNANINA, HAR
KAJE KADAWO KASANI ZA KA BARNI CIKIN KEWAR
LALLAUSAR FATAR JIKINKA.BA ZAN GUSHE BA HAR
SAI KA DAWO KA SAME NI CIKIN KEWAR LEBUNAN
KA MASU SANTSI TARE DA (YAWUN) KA ME
ZAKI.ALLAH YA DAWO MUN DA KAI
LAFIYA…..Kafin na kai karshe tuni na jike da
zufa, ina gamawa na ga gari yana juya min, ban
an kara ba sai dai naji ni a kasa ribin jikina a
gado rabi a kasa.Kusan minti biyar sanan na tashi
zaune sa sake karanta takardar ina kuka wiwi har
da majina tabbas yaya mata yake bi,domin
takardar ta nuna haka, mata ce kawai ya dace
tayiwa mijinta irin rubutun nan, wata zuciyar ta
tambaye ni ko dai ya sake aure ne?Duk da uban
kishi na sai nasami kaina da cewa inda ma auran
yayi zanfi son haka, da bin matan banza.Na soma
kaikawo cikin gidan ina tunanin matakin da zan
dauka.Shawarar wa zan nema?Na shiga dakina
na fada kan gado na dauki wayata na shiga
kiranshi, amma sai wani tunani ya fado min.Bari
kawai in kira Hajiya Baida’u, marubuciyar littafan
da nake karantawa danneman shawara.Dan ita
bata sanni ba balantana inyi zaton zancen zai iya
yaduwa, sanan tana da basira nasan zata sani a
hanya.Ringing na biyu ta daga, ta daga muka
gaisadama na saba kiranta, na ce Anty ina
nemanshawara ne.Leta na gani a jakar me gida
na wanda ke Alamta cewa yana tarraiya da wata
mace.Ta danyi shiru na dan lokaci.sanan ba yan
wanan letar kina da wata shaidar?Sanan can
dama halinsa ne?Na ce, a to a da can ba na
zarginsa, sai da ga baya na soma zarginsa domin
Anty kwata kwata ya kaura ce min kusan wata
shida zuwa bakwai yanzun,kuma Anty shi mutum
ne mai zurfin sha’awa, ba zai iya daukar ko
kwanaki ba ba tare da mace ba bare watanni.
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai
masu nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?e_pi=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
Ta ce kuma ba gudan sa kike ba har hakan ta
faru?Na ce wlh Anty Allah ya sani ban ta ba juya
masa baya ba, har matsalar nan ta shigo.Ta ce,
kuma kina gyara jikinki ba ji yayi kin zama wata
iri ba?Na soma lissafo mata abubuwan da nake
hadawa, ta ce, lallai kina kula da kanki.Na ce,
anty yanzu in yazo in fada mashi takardar don
yasan na sani?Ta ce, a a tunda kinga zarginsa
kike yi kenan baki da tabbas, ki boye takardar
kuma ko a idonki kada yaga damuwa.Ki bishi a
hankali, ki boye sirrin nan tunda uban yayanki
ne.In shaAllahu sai kiga Allah ya dawo maki dashi
kan hanya, na ce,Anty zanyi yadda kika ce, amma
zan ci gaba da bincike.Ta ce, za ki iya amma ki
sani tsananta bincike shima matsala ne, don zaki
iya ganin abinda zai saki hawan jini, na ce anty in
na tabbatar da gaskiyar zan tunkareshi ne in
nuna masa nasani.In ma zai aureta ne gara ya
aureta da zaman banzan nan, ta ce haka ne,
amma kada ki manta da adu’a, na ce insha
Allahu, ina magana cikin kuka.Ta kwantar mun da
hankali da cewa, ki daina kuka, na ce anty me
nene maganin bakin ciki?Ta ce karatun Alkur’ani
zuciyarki zata wanke sarai.Na ce, to anty na
gode.Muka yi sallama na kwanta nayi kuka sama
da minty biyar sanan na tashi na boye takardar
na ci gaba da aikina ina kuma ci gaba da
kuka.Wanan wane bala’ine Abban kausar ke son
jefa ni, ni da ‘YA’YA NA?Ya manta cewa duk abin
da kayi da Dan wani kaima sai anyi da naka?Da
na koma daki sai naji komai nasa kyama yake
bani, shi kansa yanzu kyamarsa nake ji, na
karasa kwashe kayan nasa ina yi musu kallon su
kansu suna dauke da zunubin zinar da yake
yi.Tunda su Kausar suka shigo naga sun tsura
min ido ita da Al’amin shine ya soma
magana.Momy me yasameki a ido?Na ce, ba
komai, ciwo yake min.Sai naga sun kalli juna.Na
tsugunna tsakaninsu menene?Na tambaye su
tare da yin dan guntun murmushi da na kirkiro
ko nace yake.Al’amin ya ce, yaya kausar ce tace
bata so Abba yazo in yazo yayi ta saki kuka, kuma
fa ko an tambayeki sai kice ba komai shi ne nace
ai yanzu ya daina.Amma muna zuwa sai muka
sameki kinyi kuka, ku,ma muka tambayeki sai
kice ba komai.Kausar ta ce, na canka ko Al’amin?
Abban nan ni bana sonshi yanxu.Al’amin ya bata
fuska, nima bana sonshi, bakin ciki ya turnike ni,
bana son kallon da yara suke yiwa
mahaifinsu.Nace kausar ku daina cewa bakwa son
mahaifinku,bana fada muku in kunyi Sallah ku
rinka adu’a Allah ya kawo sauki cikin lamarinba?
Allah yana amsar adu’ar kananan yara, sukace
munayi sosai Momy kullum.
Ko da ya shigo kasa kallonsa nayi, ganinake zan
iya cin kwalarsa, don haka na sa kaina a daki na
rufe tare da sa sabon kuka.Ya kalli su Kausar, ina
mamanku?Al’amin ne ya ce, tana dakinta, yazo
ya buga kofar kamar kada in bude amma sai
nafasa na bude
Ya tsura min ido lafiya?Na kalleshi, me ka gani?
Ya ce, fuskarki na gani a kumbure, na taba baki
sanan na shafa fuskata.Kila baccin da nayi dazun,
ya ce wanan kumburin baiyi kama da bacci ba,
ya fi kamada wanda yayi kuka.Na mai wani irin
kallo.Don yanzu bani wani ganin girman shi, na
ce ai ban san tsawon lokacin da kuka na zai
dauka ba kafin ya tsaya.Ya ce to Allah ya kyauta,
ya juya tare da fadin to a zo a bani abinci.Sai da
na dan bata lokaci sanan naje na shirya komai na
dawo abina.Ku ziyarci blog dinmu domin karanta
Littatafai masu nishadantarwa
Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?e_pi=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
Washe gari ya fita, sai dai duk Aliyu a dame ya
bar garin ya rasa gane kukan da Sadiya take
zabgawa, nashi ganin bai san yayi mata wani abu
ba tun zuwan shi.Rashin kulata ai ba yanzune
farko ba, to kukan na menene?Dole Akwai wani
abu, abin da yasake birkita masa lissafi yanda ko
wayarta yakira sam bata iya dagawa.Rana ta
hudu da komawarshi, ya gaji ya kira kayin Usman
ya fada masa halin da ya bar Sadiya, da kuma
rashin daga wayarsa da take yi.Yamma likis
inayiwa kausar kalaba na wanke mata kai ina
cewa sai gobe zan kaita kitso, sai ga Usman.Muka
gaisa sannan na ce, shigo falo, kausar kuma nace
suyi wasa a nan tsakar gida.Usman ya kalleni,
mijinki ya ce baki daukar wayarshi, kuma ya tafi
ya barki cikin kuka.namike naje na dauko mashi
takardar da na gani cikin kayansa.Shi kanshi
Usman kasa dago kai yayi ya dube ni, can ya ce,
lallai abin da nake zargi ya tabbata, amma don
Allah ki kara hakuri kuma in sha Allahu ko mai zai
wuce. Yanzu bari inje da takardar nan saboda
bincike, na ce yaya kayi hakuri kabar takardar
nan a hannuna saboda ta zama shaida a duk
lokacin da na masa zancen ya musa.Usman ya ce
nima da ma don hakan naso na aje ta guri na,
amma ajeta gunki, na amsa sannan mukayi
sallama.Ya kira Usman dan jin yaya?Usman ya ce
ta ce mun ba komai tana bukatar hutu ne da
dago waya, Aliyu yayi shiru, mamaki yake ji,
kuma yana ganin kamar da wani abu sun hada
bakine ita da usman.Aliyu ya ce, amma bakayi
mata fada ba, in ita ta manta cewa mijinta nake
ya kamata kai ka tuna mata. Usman ya ce, aboki
yanzu kaga aikinike, kasake kirana wani
lokacin.Ya katse wayar ba tare da ya jira amsar
Aliyu ba.Afili ya furta cewa, tabbas akwai wani
abu.
Tabayanshi Mujidat ta rungume shi.Dear wai me
ke faruwa ne?Tunda ka dawo na kasa gane
kanka.Ya kalleta cikin zargi kin sake daga wayar
matata ko?Tayi rau rau, wlh Honey ban daga ba,
ta somayi masa wadan su wassan ni tana rada
mishi a kunci me yasa ba zai mata irin son da
take yi masa ba?Ita fa zata iya mutuwa a kansa,
amma shi yafi son matarsa da ita.Ya hankadeta
tare da fadin dan Allah barni ta yaya ma zaki
hada kanki da matata?Matar sunna wacce ke
zaune don ni kadai, ta soma kuka tunda na hadu
da kai na daina hulda da kowa, nima ina zaune
nan ne dan kai daya.Aliyu ya ce, ban tabbatar da
hakan ba, tunda dana fita zaki iya fita, ta sake
dawowa ta rungume shi, na rantse bana bin
kowa kai daya nake so da kauna.Kuma bazan
daina sonka ba har na mutu.Aliyu ya zauna kan
kujera tare da rike kai, itakuma ta kwanto a
kafadar shi.Tunani take yi a zuciyarta yanda zata
ban bare ma’auratan.
Ina zaune ina danne dannen wayata, nima ina
son bude shafin nan na fcbk don ganin me
duniya take ciki?Aisha kawata da Anty Abida duk
suna ciki har Aisha tana bani labari wai da akwai
malamai sosai.In shiga nan in shiga nan dayake
ina da karanbani sai gani na bude fcbk, banyi
anfani da sunana ba ko adareshi na.Bayan kwana
biyu sai ga Aisha ta zo mun yawon Arba’n, na
nuna mata ta ce, ai na gani kin turo min sako, na
ce yau she?Ta ce duk wadan da kike da numbar
su za su gani, in kin bude, na zaro ido, har da
Abban kausar?Ta ce sosai ma, amma ba lallai ya
lura ba tunda bakiyi anfani da komai naki ba.Ta
nuna min yanda zan dinga komai, bayan tafiyarta
da dare ina kwance, na shiga fcbk nan na shiga
frnds, dinsa, mace daya na gani Mujidat.Na shiga
profile dinta hotunan da tasa nata yana daga
cikin wadan da sukayi like wani gurin ma har
yana cewa kin yi, sanan ga hotunan shi kala kala
cikin photos din ta wasu ta rubuta one an only,
wasu ta rubuta my Husband.(Tofa)
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai
masu nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?e_pi=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
Na tashi xaune wai ya aure ta ne? take kaina ya
sara, duk da ina cewa gara ace auranta yayi fiye
da ya neme ta sai na samu kaina cikin wani
tashin hankali mai tsanani.Na soma kiran layin Ya
Usman ba tare da na damu cewa dare ya dan
soma ba,cikin kuka nike cewa ya Usman ina ganin
fa auranta yayi bai fada mana ba. Yace,Habadai
wacece? Na karanto masa komai yace, kiyi hakuri
ki kwanta zan bincika,kada ki kara hawa fcbk
din,kurum ce masa nayi to amma muna yin
sallama dashina tura mata frnd request, cikin
sa’a ta amshe ni, da yake ita ma na ganta online.
Nace ban ga tasa marriage ba amma naga hoton
mijinta, ta ce eh za dai suyi auren ne, nace ni yar
kano ce ita fa? tace Lagos, amma yanzun tana
Illorin a gidan wanda zata aura.Kuka wiwi na
dinga yi yanzun menene abun yi? na tambayi
kaina, ta tambayeni ina da miji? sai nace mata
bama tare, tace ayya, yakamata mu daidaita.Ita
in sunyi aure bazata taba yarda su rabu da
mijinta ba don tanaji ko uwà r da tahaifeshi bata
kaita sonshi ba,ai ina gama krt na sauka daga nrt
na soma rero kuka tare da yin danasanin wannan
bin diddigin.Alwashi na sha duk randa yazo za’a
yi mai yuwuwa. Ba zan zauna ina wulankanta ba
haka kawai a debo ciwon zamani a kawo min
yarana su zama abun tausayi,na sake zama cool
ko yaushe cikin krt alkurani yana wanke min
zuciya, don haka yanzu bana daga wayarsa sai
dai in yaransa na kusa ya kira na mika ma
Kausar nace ta dauka.Ranar Kausar har tambaya
na take Mommy meyesa ba ka daga wayar Baban
ko yana mki fada ne? Nace a’ah munyi maganar
cewa yake in Kundawo zai kira ku ne,a haka
muka kwashe wata, ranar kwatsam sai gashi,
mamaki da naji banda Mama ko Al’amin bai je ya
masa oyoyo ba?nima batare da na Kalle shi ba
nace sannu da zuwa, yace Yauwa ya dubi yaran
yace Al’amin baku ganin bane, nukamun ganka
Abba sannu da zuwa.Yayi cik ba tare da ya amsa
ba ransa ya baci sosai da wannan ko in kula din
iyalanshi suka mishi,don haka ya dauri aniyar
Cima Sadiya zarafi yau dinnan, nasan dole zai yi
wannan tunanin dan haka na hada ma yara kaya
na kwana daya nace suje gidan Iya su kwana
tunda sati ne gobe, suna fita na kulle gidan na
shiga fall na kulle kaina na cire key din na nufi
daki,ya cire kaya sai gajeren wando zai shiga
wanka,nace toh Abba kausar yau fa zamuyita ta
kare a gidan nan ko ni ko kai?ya juya yana min
kallon mamaki sannan yace ke ina zaton kin soma
shan fakalin ko?nace ‘eh wai don ma ba Zina
nakeyi amma ka bani kunya, ba tsoron Allah ba
kunyarshi baka tunanin darajar yayana ka aje
karuwa a gidanka Kuna fasikanci,saukar Mari naji
tau,sannan yace in ji wane makaryancin, na rike
kuncina ka mareni Akan wata ‘yar iska, toh bazan
iya zama da fasiki ba ka dinga azabtar dani a kan
karuwa na warware gefen zani na ciro yar
takarda na mika mishi, ga aikenta zuwa gareni,
sannan na dauko wayata na same shi yana krt
takarda duk jikinshi yayai sanyi, nayi maza na fito
da pics dinsu da nayi saving, wannan ma karyace
ba hoton ku bane?na soma kuka ka cuce ni ka
cuci yarana haka kake nufin ayi ma Kausar?ya
daka min tsawa kina hauka ne kike ambato sunan
yata cikin wannan maganar?nace ba dadi kake
ma yar wasu?Na sake fashews da sabon kuka ka
bani takarda ta, bazan iyazama da kai ba!kina
haukane zaki ce na sake ki,toh bazan iya ba me
Zancewa Iya?nace in itace matsalar ka bazan fada
mata komai ba in baka sake ni ma zanje yanzu in
fada mata! hanklainshi yatashi ya dauki jallabiya
ya sa nikam ficewa nayi naje dakina na sure hijab
na bude Kofan falon ya rike ni kina hauka ne zaki
je ma Iya da wannan zancen?nace me zai
hana,ya kamoni na kwace nayi waje na bude
kofar gida kafin na bude ya daukoni cak,dakina
ya jefa ni kan Gado yace kina hauka ne?yace nayi
laifi kiyi hkr ki nutsu Muyi magana, nace kai ni fa
na daina Sonka kuma girmanka ya zube a gurina,
ganin zanga-zangar tayi yawa sai ya kulle ni ta
baya ya daga waya ya kira Usman yace don Allah
yana son ganinshi yanzu a gida,ina jinsu a falo
yana fada ma Usman shi bai San ina ji ba wai
duk na daga hankalinta har wai ina kwacewa ni
dole sai naje na fada ma iya.Usman yace aboki
tambaya daya zan maka kayarda kana aikata
laifin nan?yayi shiru ,Usman yace in har ka iya
amsarwa shine zai kawo karshen matsalar, yace
toh ai na fada mata cewa naji na kuma amsa
laifina don haka ta tsaya Muyi magana
taki,Usaman yace a’uzubillah, Aboki me yarude
ka ka fada wannan harka?wlh aboki kurum na
tsinci kaina a wannan halin, ka San zuciyata bata
da Kashi ga kuma sharrin shaidan, Usman yayita
masa nasiha sannan yace a jira ni na fito fuskata
suntum nace Nifa Usman na gaji ba zan zauna
ba,Usman yace yi hakuri nasan kinyi hakuri kuma
inshaAllah bazai kara ba,na kalleshi nasan zai
chigaba kawai ni gara ya aureta in son aure
suke,inkuma matan da yake bi da yawa toh ni
bazan iya zama ba.Usman ya Kalle shi gaskiya ne
Aliyu yace ita kadai ce muke tare wlh kuma itama
tsautsayi ne, Usman yace ko kayi nadama sanin
zaka koma can ku sake haduwa shi yasa ta kawo
shawara cewa taje tayi istibrai in ya so sai Kuyi
aure.Aliyu yace ina bazan auretaba ni nakuma yi
miki alkawarin cewa mun rabu da ita inshaAllah,
a gaban mu yayi waya ya kira maigadinsa yace a
fitar da Mujidat daga gidan kafin ya dawo, itama
ya kirata yace mata ya gode da wasikar da ta sa
mishi a cikin kaya don ta raba shi da matarshi
don haka maza ta bar mishi gidanshi,bai jira
takare kanta ba ya kashe dukkan phones dinsa.
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai
masu nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?e_pi=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
Ni Sam bai wani Burgeniba,suna cikin gidansuna
ta bani baki har magrib,suna fitowa nayi wanka
na sha magani nayi sallah ina zaune kan
dadduma har sai da nayi sallar Isha dama banyi
girki ba,na hau gado abuna na chigaba da kuka,
na soma barci naji ana shafa ni a wuya abunda
na jima ina kewa amma sai naji tamkar ana
shafa min kaya.Na ture hannunsa a kunne ya
rada mincewa’My choice zan zame miki sweet Aly
dini har abawa ba zan sake chanzawa ba,natashi
zaune muna kallon juna cikin ido nace yaya Sam
yanzu in ka fadi magana bana yarda matsalar
mutum ya kama karya kenan har a gane shi,na
sauka daga kan Gado naje na jingina da bango
ina kallosnshi shima ni yake kallo nace yaya ni fa
nadarmarka bata shige ni ba don nasan dole sai
Kun sake haduwa da yarinyar aurenta kawai shi
ya fi dacewa da kai,ya nufoni amma ina ce an
gama maganar nan,bazan iya auaran ta ba har
ta Haifa min yara na gari Domin ba uwa ta gari
bace,itace tayi ta bibiyata har sai da komai ya
faru kinga kuwa in na aure ta ta kuma ganin wani
shima xata iya cewa tana sonshi,ya kama
hannuna ki yafe min mukoma kamar da, Abban
Kausar na hkr amma sai Kamin rantsuwa cewa
bazaka kara aikata wannan halin ba?
Cikin sauri yace’na rantse ba zan sake ba nayi
alkawarin, nace toh shi kenan na zame hanuna
naje na kwanta sannan nace yawuce, ya Tako ya
zo ya hau gado ya kawo nizuwa jikinshi na tashi
zaune yaya kayi hakuri bazan sake iya hada
shinfida da kai ba har sai kaje kayi gwajin cutar
kanjamau!!!!! Zumbur ya mike tsaya tare da rike
kanshi Sam baiyi tunanin wani HIV ba tunda yake
tarayyada yarinyar, ya fara sintiri a tsabar
dakin,nace da baka yi tunanin haka ba ko?ya
sauke ajiyar zuciya ‘ban yi wannan tunanin ba
wlh Sadiya amma bana zaton tana da shi,tunda
tsawon zamnmu ban taba ganin tayi wani ciwo
ba,nace ba a nan take na, Ance mace tana yin
shekara goma ciwon bai nuna ba,kawai kaje kayi
gwaji in ma tanashan magani a boye wa zai sani?
zufa ta rufeshi sai lumshe ido lallai kamar yana
ganin ta tana shan wasu kwayoyi har ya taba
tamabayar tace na family planning ne,fita yayi da
sauri na tashi na biyo shi ina cewa ina zaka
Abban kausa’r yace’koma asibit zanje yanzu
nan……..
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai
masu nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?e_pi=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
toh fa sai ku biyo ni cikin Kashi na uku don Jin ya
xata kaya shin Aliyu yana da ciwo?taku Halima K/
Mashi

Zaharaddeen shomar
Whatsapp 08168575100

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button