D U N I Y A – page 4

            BY


                MissDmk ✍🏻
EOW✊🏻

Page 4

Mahyfiyar Ali bataso ba, amma ya ta iya? Aikin gama ya gama, Kawu Garba ne ya dube Abby da Ammy yace sai ku sanar dashi cewa an tsaida ranan bikin su a ranan bikin nadin sabon Sarki…
Su Khadijat murna har baka, cikin kunya ta rugume Gimbiya Hajara wato kakarta tana murmushi,aka rufe taron da adu’a…

Ammy tana Komawa daki ta kira Ali a waya,bugu daya ya amsa bata tare da bata lokaci ba ta bukace ganin sa b4 8pm, amsawa yayi da toh kafin ta yanke Kiran…
8pm yayi mai a Part din Abby, kowa yagansa yasan yana cikin damuwa, cikin girmamawa da biyaya ya gaishe da iyayensa kafin ya zauna kusa da kanwarsa Maryam, Maryam tace blood azubo ma abinci? Girgiza kai yayi alamar A’ah,

Abby yayi gyaran voice kafin yace son ALLAH da yayi mu yafi mu sonsa shiyasa ya amshe ransa. kuka,tunanin bashine Mai Martaba yake bukata ba,adu’a shine abinda yake bukata.Yanzu ba wannan ba nasan kana da labarin Khadijat..

Cike da mamaki ya dago, yana kallon Abby, kafin yace Abby Wacce Khadijat?

Abby yace Khadijat nawa ka sani? Idan kuma akwai wata Khadijat daka sani apart from Khadijat Abbanka Hamza sai ka gayamin..

Ali yace Abby me ya same ta? Ya fada out of curiosity..

Kamar yadda Mai Martaba ya fada Haka zai kasance, kashirya aurenka nan da wata Biyu, Abby na fadi haka ya mike yabar parlor…

Ali is outta words and finding it hard to believe, Ammy tazo ta dafa shi tace son, ka kwantar da hankalin ka, ka cika wasiyar kakan ka, please accept this as your faith kayi biyaya..

Ammy ban shirya yin aure Yanzu ba, besides banda niyyar yin aure Don ALLAH kice Abby ya janye wanna batun.. Please Ammy abeg of you, yafada maganar kamar zai yi kuka..

Haba Ali? Me acikin aure da baka so eh? Besides yarinya she’s young, beautiful and amazing lady..bata da makusa koh kadan, make some time with her and get to know her Son..

Ammy a halin da nake ciki yanzu bazan iya yin aure ba, inama ace Inada daman fada maki cewa aure zai iya zama babba barazana agareni?duk wannan maganar da Zuciyar sa yakeyi, kafin yace Ammy Don ALLAH ku janye maganar auren nan…

Haba Aliyu? Yanzu sakayar da zakayi wa kakar naka kenan? Ina kaunar da kk nuna mai? Haba Aliyu kayi hakuri ka aureta kacika Final wish Papa.. Jeka ALLAH yay ma albarka ta fada tana shafa fuskarsa kafin ta mike tabar parlor, daman maryam tuni tabar masu parlor sai bayan sun Gama ta fito ta same shi absentminded sabida ta kirashi yafi sau uku amma be amsa ba, sai can ya dago fuskarsa nan tasa kamar besan wanni abu dariya ba.. Mikewa yayi without saying anything yabar palace din gabadaya..

Farin Hijab roba roba ne ajikinta wanda yake nuna kome na jikinta zaune take gaban Murhu awaranta, ga mutane cike a bench suna jiran a sallamae su..

Wanni ne ya zo gun tare da wata sunyi zunbi students tana ganin su, taja hijab gaban goshin ta, tace you welcome how do you want your wara? With sauce or pepper?

Da mamaki suke kallonta jin tayi turanci, saurayin yace give me 300 wara with pepper, budurwa tace mine with sauce but I’m so surprised like are you in school?

Tasleem ta girgiza kai ba tace kome ba don batason dogon bayani daze sa su bukace Ganin fuskarta, fara sallamar wanda suke kan benchi tayi,sukam students zama sukayi suna labarin new iPhone da ya shigo,
Budurwa tace now you’ll see Temi with this latest iPhone, that girl ehn she’s something else.. See Colins I don’t think she came from a wealthy family…

Wanda aka Kira da Colins ya kwashe da dariya yace Jay you’re jealous of her.. Kema from her dressing and everything zaki gane cewa iyayenta nada kudi, ke koh shoes inta kade ya isa yasa ki gane suna da kudi..

Karya ne colins, Temi na runs girl, dafa a hostel take yanzu fa cemin akayi ta kama gidan that’s worth 400k..zai magana kenan Tasleem ta miko masu package din awara daman haka takeyi Inda yan makaranta ne sai tasa masu a roban takeaway inda yan unguwa ne sai tasa masu a Leda, 1k suka bata sannan suka bar mata change din.
Bayan sun tafi ne ta buga Uban salati, tabbas zama bai gani ba, “harta ma takalmi ma sai Ansa ma ido? Ah gaskiya dole na nema kudi bare mu da zamu faculty of Life science inda akace yan gayu da masu kudi sunfi yawa zuwa bikin suhailat ya kamani kam dole nayi anko wata kila na hadu da wasu hot guys” Kiran sunan ta da Mal Nazeef yay ya dawo da ita daga duniyar tunanin ta,

Barka da zuwa Mam Nazeef tayi magana cikin shagwaba..
Barka dai hoorun enn, ya fada yana murmushi..

Haba dai Mam Nazeef? Wane ni da wannan suna? Ta fadi magana tana dan cokaro dan bakin ta…

Hmmm Talatu kenan, bakisan irin baiwar da ALLAH yay miki bane shiyasa kk fadin haka, nide burina na malleke ki a matsayin mata..

Murmushi tayi kafin tace ALLAH koh? Yace Eh Sosai ma hoorun enn, Yanzu dai ba wannan ba Mam Nazeef, tayi magana tana dan sunkuyar dakai kasa,

Toh menene fada inji hoorun enn, cikin shagwaba tace dama maganar walimar saukana kasan dai bamu da karfin siyan rago da biyan kudin sauka..

Kekam bana gayamik cewa na biya miki ba? Sannan kuma nace zan aiko da kaji biyar na makaranta

Cikin shagwaba tace Mam Nazeef baze issa ba fa, abokanai na yan areas zasu zo kuma yakamata na karamasu, ka hadamin da dubu goma man.. “

Gaskiya Talatu banda kudi Shima wannan dubu ashirin adashe na shiga sabida ke, kinga inda na biya kudin sauka 10k Saura 10k shine na kajin.. Zatayi magana kenan wata bakar mota tayi horn, cikin kwarkwasa da kisisina ta mike tafara takawa wanni yaga yanda take tafiya zaka rantse kace tafi karfin shekarun ta,
Sauke glass din motar Alhji yayi ta sunkuyar dakai tace ina wuni Alhajee, na nawa za akawo ma? Tande baki yayi kamar wani tsohon Maye yace Talatu koh? Murmushi tayi tace eh to, Talatu ce…

Talatu Inajin dadin waranki, Gaskiya koh naci bai isana shine nace why not gobe by 10am kizo guests house ina kiyimin na kamar dubu goma,

Zaro da Manya idanuwa ta waje tayi tace Alhajee dubu 20 fa kace? Kaikam mai za kayi da wara na dubu 20?

Talatu kenan, bawai ina numfi waran dubu 20 zakiyi min ba, A’ah kawai kudin aikin waran ne dubu 20,Inda kin rena ne sai na kara maki..

Murmushi tayi tace toh Yanzu ya kk so ayi? Amma kamata yayi ka bayar da kudin in yaso sai nazo maka dashi can na soya…

ciro da bundles 200 guda daya,ga kuma complimentary card na sai ki kirani dashi, saida ta waiga taga Mam Nazeef baya kallonta tayi saurin amshewa ta cusa a hijab kafin tace Alhajee Nagode saide banda waya,

Ya salam yarinya wayeyya kamar ki ace baki da waya? Toh inda kinzo zamuyi magana wayar, amma Yanzu ki nema Waya sai ki kirani,
Toh Alhaji bara azubo ma waran tana fadin haka ta juya tana tafiya, Alhajee kam suma zaune yayi yana mamakin yadda yarinya nan take da cikar hallita,kuma daga Ganin ta danya ce shakaf, gobe zansha romo harda luguda don yarinya zata kawo wuta.. Kyalkyalce da dariya yayi yace zanta shanawa da ita harna kwashe gara.

Talatu kam kwashe sauran waran tayi ta packaging mai, Mam Nazeef yace dukka ya siye?
Murmushi tayi tace walhy kuwa kulum in yazo na dubu yake siya tana fadin haka ta kai mai motar da yazo amsa sai ya hada da hanun ta yana lashe baki kamar he’s craving for something.. Saurin Janye hanunta tayi tace sai nazo Alhajee..

Murmushi yayi yace toh Talatu, sai kinzo koh yay magana yana kashe mata ido yana Jan motar ta saki baki tace…..

09074267236
MissDmk✍🏻
Thanks

Be the first to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published.


*