BOƊƊI complete Hausa Novels

🌀🌀🌀BOƊƊI
the beautiful 🌀🌀🌀🌀
Story and writing
(Z. B. M.)
09066017177
marubuciyar:
ZAINAB abu’ƙaya
BANI BA AUREN SOJA
NIMA DANAWA LAIFI
AUTAN MOMY
And now
BOƊƊI
IN THE NAME OF ALLAH THE BENEFICIENT THE MOST MERCIFUL,
ALL PRISE BELONG TO YOU ALLAH LORD OF THE WORLD
🥰
“` ~NASA DAUKAR DA WANNAN BOOK ZUWAGA MAHAIFIYA can’t luv you lees mom 🥰 heart ♥ 🍀 much luv for you 🌷 😍 ammah~
I don talk any more🤫🤥
🆓And 🆕
Page
0️⃣1️⃣……… Adamawa jihar yola ƙauyene dake cikin garin mayobelwa mai suna. Genle Sanyi da albarka ta sauka a wannan safiya mai sanyaya zuciya dake cike da kunci kara haskaka annuri mai murmushi kowane ruhi, a wannan safiya ne mutanen garin Genle suka shaida aure tsakanin ameenatu da kuma angonta Abubakar, A°mmun yasama wannan aure albarka, cikin gida kowa sai farin ciki yake yi masu bakin ciki ko na gefe,
Furera aguje ta shige gida tana rusa kuka kamar wacce aka mata mutuwa cikin tashin hankali innah tace lafiya Furera cikin kuka tace innah kamar bakijin meke faruwa a gari ba, tace to Naji amma ya muka iya da ƙaddarar Allah dolene ameenatu matar Abubakar ce, cigaba da kuka Furera tayi innah sai rarrashi take yi amma abu yaci tura can naga ta mata radi a kunne tace Allah innata dariya suka yi suka tafa, hmmmm nidai banji mesukaceba nace Intayi tsami zamuji…
Dare duk aka gama wata al’ada aka kai amarya izuwa gidanta su goggo sunyi kokarin wajen mata nasiha duk Ameenatu batada hayaniya kowa sai son barka, fatan mu Allah yakawo xuriya dayyiba,
Wata yarinya fara mai zubin Larabawa dake sakkowa daga sama fara’a sosai a face ɗinta tana ummu na shirya umatanen dake zaune afalo naga duk sun Mike matar da’aka kira da ummu tace kai bintu, Aida mun tafi kema rigima gareki wani dake gefen ummu yace aike kike biye ta dama tun dazu ashe zaman giranki muke, baki ta tura alamun shagwaɓa, kowa dariya yayi sukayi hanyar fita, alama dai dukan su yaran ummu ne don suna matukar kama,
Airport na gihar Kano suka nufa ummu sai duba time take 10 minutes ya rage girji yaka raso aikuwa sunje cikin sa’a suna isa jirji yasauka,
Shine fitowar farko daga girjin wani fari zubin Larabawa shima sak yan uwansa wato maleek Ibrahim wanda ake kira da Sayyid………………..
More comments more typing
Share pls 🙏
Follow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/ISJTXVOAvK5AlxunOo3OHZ
BOƊƊI the beautiful.
🥰
group one 1⃣
wannan group na masu comments ne inkinsan ba zakiyi comments ba zakijiki awaje 🙅🏻♀️
Share pls
🌀🌀🌀🌀BOƊƊI the beautiful
🌀🌀 🌀
Story and writing
(Z. B. M.)
WOMEN WRITERS ASSOCIATION📚
(Domin Marubuta Mata)
✨(W.W.A)✨
https://www.facebook.com/106752595253176/posts/107924965135939/
marubuciyar:
ZAINAB abu’ƙaya
BANI BA AUREN SOJA
NIMA DANAWA LAIFI
AUTAR MOMY
And now
BOƊƊI the beautiful
IN THE NAME OF ALLAH THE BENEFICIENT THE MOST MERCIFUL,
ALL PRISE BELONG TO YOU ALLAH LORD OF THE WORLD
🥰
“` ~NASA DAUKAR DA WANNAN BOOK ZUWAGA MAHAIFIYA can’t luv you lees mom 🥰 heart ♥ 🍀 much luv for you 🌷 😍 ammah~
Happy birthday mommy ii°di milaadi sa’iid 🎂🤝💃🏼💃🏼💃🏼💃🏼💃🏼Allah yara miki lfy da nisan kwana uwata Aishatu.
0️⃣2️⃣………bintu ce tafara hango Sayyid aguje ta isa gareshi tana “marhaban ya Sayyid tasharraftu bi ma’arifatika” murmushi Sayyid yayi wanda yake bayyana tsagwaran kyawunsa, yace da bintu kaifa anti ta mayar mishi da lastun bikhairi, lokacin sun ƙaraso ummu tace bintu Allah ya shiryeki, welcome my son hugging ɗin juna suka fara yi cikin farin ciki da ganin juna gida suka wuce domin Sayyid ya huta gajiya…
****rayuwa ta cigaba da tafiya dadi babu dadi ameenatu na zaune tareda mijinta sun kula da juna furera kuwa na nan kan bakarta narashi son ameenatu,
Tushen labari………
Mlm sunusu shine mahaifin Abubakar yanada mata biyu ta farko wato uwar gida kulu, itace mmn Abubakar sun daɗe kafin Allah ya basu haihuwa a lokacin ne Mlm sunusi ya karo aure ya auri innah mmn furera lokacin ma a riga an haifi furera taxo da ita gidan saboda baban furera Allah ya mishi rasuwa.
haka kulu ta zauna da innah cikin kunci domin bata jin dadin zama da ita sai abunda innah tace ake yi agidan, lokacin da Abubakar ya isa aure sai furera tace duniya shi take so kulu batason wannan hadin auren saboda haka tastaya itama sosai domin kare danta Mlm sunusi labari ya iskeshi yakira Abubakar ya tambaye shi yace idan yanada wacce yakeso to yakawo shi kuma lokacin sun fara soyayya da ameenatu ƴar A°mmun dajin labari Mlm sunusi yayi farin ciki inda yasamu kanin sa tasi’u suka je suka samu A°mmun da maganan kowa yayi farin ciki domin haɗa zuriya da mutanen kirki, ba ɓata lokaci aka tsaida magana,
Labari ya iske furera da innah tashin hankali matuka suka tsinci kansu sunyi iya shige da ficensu amma suna gani aka yi aure,
Bayan wata biyu dayin aure ameenatu tasamu juna biyu Abubakar yayi murna kulu ma tayi farin ciki sosai haka ta cigaba da renon ciki har lokacin haihuwa,
Daren Alhamis ameenatu ta kwana tana naku da duk yanda takaiga dauriya abun yaci karfin ta Abubakar yafara fita hayyaci sa yaje ya kwakwa sawa innah Ladi wacce dama mafi yawa ita ke karban haihuwa agarin, Sanyin asuba yafara ratsowa gari yacika da ni’ma Ameenatu tana cikin wani hali inna Ladi sai fama take dukan su sun hada zuwa har shi Abubakar dake kai komo awaje innah Ladi tace kuyi nishi ameenatu kai yafara fitowa ai kuwa data yunkura ɗaya biyu kawai saiga sun buleliya fara tas yarinya tafaɗo tana callara ihu masha Allah. Alhamdulillah abunda Abubakar ke faɗi lokacin da yaji kukan jaritiyarsa, zai shigo suka yi kicibus da inna Ladi tace Abubakar jira mana barina shirya su.
Cikin farin ciki yayi alwala ya nufi masallaci koda gari ya waye kowa yasamu labarin haihuwa Abubakar yafara tozali ya kyakkyawar ɗiyarsa bakin sa ba abunda yafara kira sai BOƊƊI am ya kalli ameenatu cikin harshen fula tanci yace nagode dawannan kauta da kika ban kunya baisa ameenatu ta dagoba, mutane kowa yaxo sai son barka bakin ciki kuwa kunsan masu ji bazai wuce furera da uwar ta innah ba.
Domin ko kowa yaxo amma bandasu.
Ran suna yarinya taci sunanta hauwa kulu BOƊƊI
Wato sunan mmn Abubakar kulu, amma ana ce da yarinyar BOƊƊI, haka ameenatu ta cigaba da renon yarinyar ta cikin so da kauna Abubakar yafara tafiya galingo domin kasuwanci idan yatafi yakan daɗe kafin yadawo duk abunda ke faruwa furera bawai ta hakura bane tanan tana neman hanyar da zata samu dama kuma har lokacin taki auren kowa tace ita sai abubae, duk lokacin da tayi tozali da BOƊƊI sai ta jefeta da mummunan kalma domin ana kawo ta wajen ta kwarar ta, BOƊƊI kamar yar Larabawa kyau kam ba’a magana ga kwantattacen gashi akanta farace tass Zara zaran gashin ido, dogon hanci kai sai son barka amma BOƊƊI the beautiful ce.
Lokacin da su Sayyid suka isa gida wanka yayi ya fito domin kowa gira shi yake bintu ce ta kamo hannun sa tana masa shirmen data saba, ummu ce ta hau mata fada cikin larabci, bayan sunci abinci ne sai Sayyid yace ummu inaso nadan shiga gari zamu hadu da wanine ummu tace Haba ya Sayyid yaushe kadawo bazaka bari ka hutaba, ai ummu abunne ba hutu kinsan aikin namu sai a hankali farouq ne yayi sallama……….
Share pls 🙏
🌀🌀🌀BOƊƊI the beautiful 🌀🌀
Story & writing
(Z. B. M)
09066017177
WOMEN WRITERS ASSOCIATION📚
(Domin Marubuta Mata)
✨(W.W.A)✨
https://www.facebook.com/106752595253176/posts/107924965135939/
I don’t talk any more 🤫 🤥
Page0️⃣3️⃣
……………. Farouq ne yayi sallama suka amsa ummu tace yau Kaine muke gani wato Sayyid yaxo yana sosa keya ya gaishe ta Sayyid yace yauwa bari mu fita ummu tace to sai mun dawo
Bintu Naji ta taso tana zata bisu ummu tayi mata tsawa Takoma Farouq yayi dariya yace gaskiya Sayyid Bintu na burgeni allah yasa idan ta girma zaku bani ita, Sayyid yace yanxu saika zauna ka jira Bintu she’s just a 5yrs yace zan jira mana Kaga yanxu muna 25 ai zaiyi, hmmmm kazaji dashi.
Tun fitan su Sayyid sai karfe 9pm suka dawo ummu ce tasameshi yace abbu yadawo yana jiranka a falo ba jimawa da fitan ta ya tashi ya nufi wajen abbu da sallama yashiga cike da farin cikin ganin juna suka gaisa abbu yaji daɗin ganin son din nashi maleek domin yafara girma sunyi taɗi sosai har ummu taxo tasa mesu abbu ne yace to yanxu inaso nan da 2 weeks zaka wuce can wajensu jaddun inaso kayi masters ɗinka acan batare da hayyaba yace to abbu Allah ya tabbatar da alkharinsa, bayan fitan Sayyid ummu taxo ta zauna kusa da abbu yace Meyasa ba kaso maleek yazauna tare damu yayi karatu yanxu kam ina bukatar shi yafara girma aka mata Ace yazauna shima mushaku abbu yace cikin yare larabci ya ummi shin yanxu maleek ba gida zai komaba kinsan Nigeria ban yarda zaman Sayyid ananba su jaddun suna bukatar sa suma domin zai debe musu kewa,
. ***Asalin ummu safeeyah yar Saudi ne inda shi kuma abbu ibraheem dan Nigeria ne jihar Kano shima abu kara tune yakai shi can inda ya haɗuda ummu har suka fara soyayya yasanarwa iyayen sa bayan ya shawo kansu da kyar suka yarda kan cewa zasu dawo nan Nijeriya su zauna, aɓangaren ummu itama iyayen ta da kyar suka amince dake rabo dangin ajali haka suka hakura tareda sanya albarka, a daura aure asaudi ango da Marya suka ran kayo Nigeria, bayan shekara biyu Allah ya axurtasu da yaro namiji wanda shine maleek Sayyid , sai kuma sun ƙara samun Aleeyu haidar daga nan basu kuma samun haihuwaba sai nan kusa suka haifi faɗeematu Bintu, Sayyid yayi karatu har zuwa secondry Nigeria daganan yakoma UK yayi degree to yanxu yadawo zai tafi Saudi domin yin masters, shi kuma Aleeyu anan Nigeria aka barshi domin yayi sabo da gidan kakaninsa. Sai Bintu yar nursery!
***wata rana wacce ameenatu bazata taɓa mance shiba lokacin BOƊƊI tanada shekara daya da rabi aduniya Abubakar yatafi jalingo wajen kasuwan ci sauri take domin anyi aihuwa a ana gidan su ta shirya BOƊƊI tayi kyau abun ta itama ta shiga wanka tabarta tana wasa ba tareda takawo komai a ranta ba, jim kadan ta fito sai bata ga kowaba kuma da tana ɗan jin mostinta, cikin sauri ta saka hijab ɗinta ta fito waje amma ko alamun BOƊƊI bata ganiba yara tasamu suna wasa awaje tace ko kunga BOƊƊI suka ce bawanda suka gani tashin hankali ba’a sa masa rana.
Sauri take kamar zata kife tabi jeji ita kanta bata san inda take biba…………
Share pls
🌀🌀🌀🌀BOƊƊI the beautiful
🌀🌀 🌀
Story and writing
(Z. B. M.)
WOMEN WRITERS ASSOCIATION📚
(Domin Marubuta Mata)
✨(W.W.A)✨
https://www.facebook.com/106752595253176/posts/107924965135939/
marubuciyar:
ZAINAB abu’ƙaya
BANI BA AUREN SOJA
NIMA DANAWA LAIFI
AUTAR MOMY
And now
BOƊƊI the beautiful
IN THE NAME OF ALLAH THE BENEFICIENT THE MOST MERCIFUL,
ALL PRISE BELONG TO YOU ALLAH LORD OF THE WORLD
🥰
“` ~NASA DAUKAR DA WANNAN BOOK ZUWAGA MAHAIFIYA can’t luv you lees mom 🥰 heart ♥ 🍀 much luv for you 🌷 😍 ammah~
I don talk any more🤫🤥
🆓And 🆕
0️⃣4️⃣………tayi nisan na ban mamaki domin tuni tafice cikin gari bakin wani dan duste da ruwa ke fitowa ta wajen ta ajiye BOƊƊI ta dauki kara taba ta domin yin wasa, ba tausayi juya ta kama hanya izuwa gida dafarin ciki fall domin tasan dole inda ta ajiye BOƊƊI tasal wanta, furera kenan.
Abun fa ya faskara domin a yanxu labari ya isa ga jama’a BOƊƊI ta ɓata, jama’a sai alhini ake kowa da abunda yake faɗi ameenatu tafice daga hayyacinta domin taruɗe matuka, Mariya ce zata gona taci karo da furera cikin son gulma tace ke furera daga ina? Kallon banza Tamata wani irin rashin mutunci ne wannan furera nifa shiyasa banason Higa harkarku kidubeni kinkai kimin raini ne yar yarinya dake, Mariya tace Allah yabaki hakuri furera dama zan faɗa mikine BOƊƊI yar gidan ameenatu ta bace yanxu haka cikin gari sai neman ta ake, furera takara haɗe ranta, toni meya shafeni nan lambun buba nashiga tun safe na ɗebo gajiya kin tareni da shirme ta buge Mariya tayi wucewarta kasan zuciyarta kuwa dariya ne. Mariya tace Allah ya kyauta amma furera har yanzu ba hankali nagama abokiyar dabin tace ameenatu, na dauka ko idan na faɗa mata zan samu wani abun, harda min faɗa batason raini to ninace kar tayi aure har mu isota, haka dai ta cigaba da faɗanta itama.
Yau kuma ina zaku haka Farooq naganka da sassafe, nasan dai wannan sammako bahaka kawai ba, cewar ummu data fito daga
kitchen, Farooq yace eh ummu wlh akoi wani abu important da zamujeyi, Allah yasa dai Sayyid ya tashi ummu tace to sai ka rasa ciki kagani, sama ya haura inda room ɗin Sayyid yake yasa meshi yana tace kansa mai launin na Larabawa domin Sayyid ba inda yabaro ummu mahaifiyarsa, saidai stayinsa na abbu ne, yace yauwa yanxu dama zan kiraka kada muma kara, fitowa suka yi atare ummu mene ne haka Allah yasa dai ba tafiya zakuyi ba baku yi break ba, Sayyid yace wlh zamuakarane ummu akoi nisa inda zamuje, bintu ce ta fito da alamu lokacin ta tashi barci, tana ganin farouq tace ya Farouq ina zakuje ne yace my bb have you wake up, kai taɗaga masa, yace “kaifa anti, bintu tace” ana bi khairi, farouq yace that’s my bb, ya farouq “ila Aina anta zahibun” ummu ce ta karbi zancen ta hanyar cewa bintu taje tayi brush sai taxo ba wani waje su Sayyid zasuba, bintu tayar da tana murna, Sayyid yace ummu “ma’assalama” tace to hazzan sa’iidah, sahibat kas salamah” da murmushi a face ɗinta har wajen mota tara kasu tana koro addu’a da larabci, abun gonin burgewa inji jidderh dama Ace sheikh ɗintane 😂lol
Tafiya suke yi ba wasa domin farouq ya rikewa motar fire kusan karfe uku suka iso jejin cike yakeda abubuwan burgewa saida suka samu wajen wani bishiya mai sanyi suka yi sallah sai Farouq yafara gudanar da aikin sa suna tafiya yana ta observing dajin abun sha’awa Sayyid na biye dashi suna dan hira
* baffa am, miɗo nana ɗonka, miyiɗi diyam cewar wata bahillatana daganinsu irin borinnan masu yawo da shanu domin kuwa ga shanun masu yawa suna kiwatawa, su biyune itada baffanta, wajen da taga ruwa na gudu takara sa jin sanyin waje yasa tace kai baffa wlh nagaji, yace kin fiye lala ci cikin yaren fulanci daidai ruwan takara sa tozali tayi da wannan kyakkyawar halitta wato BOƊƊI!! Itama abunda ta furta kenan dukda bata santaba amma ji tayi wannan sunan shiya dace da ita abunka da fulani sun saba ganin abubuwa a daji., ba wani tsoro takara sa tana murmushi ta kai hannu tadauketa tanamai kwalawa baffa kira yace lfy irin wannan kiran tace baffa Kaga nasamu ɓingel boɗɗi baffa saida ya duba gabar ya duba yamma baiga alamun waniba yace to yanxu ya zamuyi kenan, madara dijah ta dama ta sto tace baffa barina bata nasan tabajin yunwa, bayan yagama bata madaran, baffa yace kodai zamu shiga kauyukan gefe nan muduba ko zamu samu wanda yasanta, aiko dijah tatire furr bata ga mai rabata da BOƊƊI ba domin ita tasamu yarinya,. Haka ko suka tafi da ita gashi tafiyar tasu da nisa gabar zasu yi,.
Sayyid sun gama abunda yakawo su dajin suka kara kama hanya domin basaso Ace dare ya musu, cikin gudun farouq da baya duba gaban sa kawai ji suka yi karar buge abu burki ya taka dukan su sunyi bala’in tsorata………….
Share pls 🙏
🌀🌀🌀🌀BOƊƊI the beautiful
🌀🌀 🌀
Story and writing
(Z. B. M.)
marubuciyar:
ZAINAB abu’ƙaya
BANI BA AUREN SOJA
NIMA DANAWA LAIFI
AUTAR MOMY
And now
BOƊƊI the beautiful
Follow me on what’sapp 09066017177
Whatpad
Zainab7177
Gmail [email protected]
🆓And 🆕
I dedicated this page to you my sister’s I miss you alot Allah yakare ku aduk inda kuke. 💃🏼🥰😍🥰💕 💞 ❣️
0️⃣5️⃣………A gigice suka fito Dijah tamike ta falala da gudu domin tsoron daya kamata duk da ciwon da taji a ƙafarta baisa ta tsayaba Baffan tama kafin su Sayyid su juyo gareshi yakaɗa yan shanunsa sunyi cikin daji,
Farouq ne yafara bin bayan sa yana masa magana amma inaa tafiyar tasu tayi nisa.,
Dawowa Farouq yayi har zasu shiga Mota suka ji kukan jariri ya agefen titi wajen da kukan ke fitowa suka suka ƙarasa BOƊƊI ce kwance domin lokacin da Dijah ta fadi BOƊƊI dake hannun ta gefe tayi,
Cikin sauri Sayyid ya ɗauketa wani mai mota ne ya tsaya daidai su yace lfy kuwa kodai kuna bukatar tai mako ne, Farouq ne ya faɗa mishi abunda ya faru kuma yace gashi sun tafi sun bar yarinya, mutumin yace gaskiya yaka mata ahan zarta muje asibiti saboda kar wani abu yasa meta. Ni sunana Brister Sani,
Tare Da Brister suka ƙarasa asibiti dake nan wani Kauye kusa, dukda ƙauyene amma an kula da BOƊƊI sosai don likitocin daga cikin gari suke zuwa, bayan andubata an tabbatar ba komai lokacin har magrib ya kusa Brister yace to yanxu kuɗin inaso Naji daga ina kuke, Farouq ne yayi magana yafaɗa masa daga inda suke kuma da abunda ya kawo su,
Yace to gaskiya yanxu kuxo muje gidana banisa sosai kuma kan hanyar kuce inyaso gobe saiku wuce da farko sun ki kan zasuje hotel su kwana amma ganin Brister ya dage suka amince,.
Batun BOƊƊI kuwa Brister yace zai ɗauka kafin ayi cigiyar iyayen ta gashi ba’a san wani gari fulanin nan suke zamaba hasalima basu da wajen zama ɗaya, dagani masu tafiyane.
Sunje gidan Barrister an musu kyakkyawan tarba, koda gari ya waye sun shirya tsab domin tafiya, matar Barrister ne ta fito ɗaukeda BOƊƊI ahannunta an mata wanka ansauya mata kaya “tayi matukar kyau” lokacin Sayyid da Farouq su kayi tozali da BOƊƊI kallon juna sukayi, Farouq baiyi kasa aguiwaba yace, “amma wannan yarinyar muka xo da ita kuwa?
Barrister ne yayi dariya yace itace dai kunga ta BOƊƊI da yawa ko! Sayyid yace BOƊƊI me hakan yake nufi, Barrister ya bashi amsa da kyakkyawa, sunan kyakkyawan yaringa mai mai tawa cikin zuciyarshi, Domin a yanxu yaji yana matukar son yarinyar domin akoita da kyau gata fara wannan ya kenan idan ta girma.
Tun lokacin da aka ambaci kyakkyawa matar Barrister ta ɗaure fuska………….
Tofa…..akoi CA kwakiya kubiyoni domin yanxune aka fara wasan 🏇🏻🏇🏻🏇🏻🏇🏻
Comments naku shine karfin guiwana, nagode da kaunarku gareni, 😍
Share pls 🙏
🌀🌀🌀🌀BOƊƊI the beautiful
🌀🌀 🌀
Story and writing
By
(Z. B. M.)
marubuciyar:
ZAINAB abu’ƙaya
BANI BA AUREN SOJA
NIMA DANAWA LAIFI
AUTAR MOMY
And now
BOƊƊI the beautiful
Wannan page na sadaukar ƙyauta gareku masoya littafin BOƊƊI the beautiful, Allah yabarmu tare.
🆓And 🆕
0️⃣6️⃣………Matar Barrister ta ɗaure fuska lokacin da taga su Sayyid na kokarin tafiya ta tada bori., Ba kunya tace BOƊƊI baza ta zauna agidan taba. Barrister yayi magana amma tace sam ita ba tasan zancenba.,
Sayyid ne yaraba faɗan yace mungode Allah ya saka, Barrister amma ka kawota mune mukayi sanadin, Saboda haka zamu tafi da ita, kai kuma idan kaji wani lbr gameda yarinyar muna sauraro.
Farouq ma abun ya masa daɗi domin shima yanaso Ace su tafi da BOƊƊI, Babu yanda Barrister ya iya haka ya basu BOƊƊI suka yi sallama tareda musayar Number suka ɗauki hanyar TADABO TUNBIN GIWA. 🐘
*Ɓangaren Ameenatu kuwa abubuwa sun caɓe, duniya tayi masu zafi, ƴa daya tilo garesu amma an wayi gari ta bace babu lbr, kuka take mai tsuma zuciya kulu ce dake zaune agefenta itama sharar kwalla take, amma tayi karfin hali tace “waɗu muyal usani” Abubakar ne yashigo shima kallo ɗaya zaka mishi Kaga damuwa ƙakara afuskarsa, haduwa suka yi suna ta jimami, kowa yaxo amma ita Furera da mahaifiyarta babu abunda yadame su sai harkar su suke yi, suna ganin burinsu ya kusa cika.
Nasiha sosai kulu tayi musu kafin ta sallamesu tabar gidan duk da akoi kunya tsakanin ɗan fari da surkuwa, amma hakan bai hanata faɗa musu gaskiya ba domin kuwa uwa tagari ce kuma basu da wanda ya wuce ita A yanxu.
Koda Kulu Takoma gida tasamu Furera da maifiyarta suna ta shewa bata kulasuba tayi wucewarta ɗaki, saida aka yi kiran magrib tukun ta fito domin yin alwala, kunnuwan tane suka jiyo mata zancen su Furera a ɗaki, waya sanima ko ita Ameenatu ce ta boye BOƊƊI saboda ana cewa tanada kyau, innah tace waya gaya miki ai na daɗe da ce miki wannan yarinyar ba mutum bace yar aljan ce yanxuma sune sukaxo suka dauki abunsu, koda basuxoba idan ta girma zata bisu domin sune iyayen ta, dariya suka fashe dashi harda tafawa, jikin Kulu yayi sanyi ta wuce kawai ranta na mata kuna har yaushe wannan abun zai wuce kullum Innah da Furera bazasu rasa abun aibata waba.
Wata dariyar suka kuma saboda dama da gayya suke maganar burinsu taji kuma taji sunyi farin ciki, innah ce tace inadai kin ajiye ta inda yaka mata, Furera tace aiko Inaji yanxu haka ma bata raye ko ruwa yatafi da ita domin wannan waje ko Ameenatu nakai saita salwanta,. Dariya suka kuma yi kulu dake ɗaki tana jiyo dariyar su.
Bayan ta idarda sallah ta daga hannun ta sama, ta fara kaiwa mai komai mai kowa kukanta. Kulu kenan.,
Cikin dare tanajin matukar ciwo ta rasa meye ne ke damunta kirjinta kamar zai fito waje Abubakar yagama ruɗewa ya rasa yanda zaiyi, addu’a ya rinka tofa mata har bacci ya dauke ta.
Koda gari ya waye Abubakar ya je wajen Mahaifiyarsa bayan sun gaisane yake sanar da ita rashin lfy Ameenatu, ta jin~jina al’amarin tace yaka mata dai kuziyarci babban asibiti saboda kar a barta ba’a san me yake damun taba, gashi dukta saka damuwa na rashin BOƊƊI a kusa.
Yace shikenan Insha Allahu hakan za’ayi.
Kano state Sayyid da Farouq sun isa cikin aminci…………………
🤧Zazzabi harda mura na shirin kamani pray for me pls 🙏
WOMEN WRITERS ASSOCIATION📚
(Domin Marubuta Mata)
✨(W.W.A)✨
https://www.facebook.com/106752595253176/posts/107924965135939/
🌀🌀 BOƊƊI the beautiful
🌀 🌀
Story & writing
By
(Z. B. M)
Yar mutan gombawa.
Marubuciyar
~~ZAINAB abuƙaya
BANI BA AUREN SOJA
NIMA DANAWA LAIFI
Sc relationships
AUTAR MOMY
And now
BOƊƊI the beautiful~
Follow me on what’sapp
09066017177
Whatpad
Zainab7177
Gmail [email protected]
Bismillahi rrahmani rrahim
I dedicate this page to my kids tauheeda & imam, Allah yaramin ku yabaku ilimi mai amfani.
PAGE 7️⃣🔁8️⃣
……………. Cikin aminci da yardar Allah, Ummu tayi matukar jin daɗin ganin su saidai kuma ta gansu da yarinya, kallo take binsu dashi takasa cewa komai.
Farouq da sayyid jikin su yayi sanyi domin basu san dawani irin kalma zasu Fahim tar da Ummu ba lokacin Abbu shima yashigo amma da yake falon sa direct yanufa bai san da dawowarsu sayyid ba.,
Bayan sun gaishe cikin girma mawa, sai kuma suka yi shiru kowa na jiran abunda ɗan uwansa zaice, Farouq dai yasawa ransa koda Ummu bata amshi BOƊƊI ba zai kai ta wajen mamynshi.
Ummu ne takaste shirun nasu tace! Sayyid! Farouq! Shin ina kuka samo wannan yarinya? Farouq ne yayi karfin halin fara sanar da ita dukkan abunda ya faru lokacin tafiyar su, sayyid ba’a bunda yake faɗi sai na’am, 😅 tsoron sa bai san mai Ummu zatace ba dukda ya yarda da maifiyar tashi, shiru tayi tana nazari tace to Allah ya bayyanarda gaskiya amma wannan yarinya na tausaya miki.
BOƊƊI dake hannun Farouq Ummu tasa hannu ta karba yarinya ba ƙiwa tamiƙo hannu tana murmushi zuwa ga Ummu,
Tace Allah sarki dagani ba’a yaye taba, house girl takira tace takawo mata madara dakanta ta sha yarda BOƊƊI saida ta tabbatar da koshinta sannan tasa ta a kafaɗa ta fara shafa bayanta gyatsa tayi cikin minti kadan sai bacci, duk abunda ake Farouq da sayyid suna zaune suna kallo farin ciki ya mamayesu bazaka Gane wa yafi wani murna cikin suba.
Ummu ne tace to sai kuje kusanarwa Abbu shima yasan abunda ake ciki mikewa suka yi ummu kuma ta wuce sama takai BOƊƊI ɗakin ta, ‘ ta kwantar soyayya da kaunar yarinyar ya kama ta, “domin ko a chan Saudiyya wannan yarinya kyakkyawa ce,” bintu ce ta shigo aguje amma bakin ta ɗauke yakeda sallama, cikin Larabci tace, ” Ummu naga motar ya Sayyid, ai bata kara saba tace; wow Ummu wannan fine baby ɗinfa? gaskiya tanada kyau sosai dama kince zaki haifa min baby Irina ko Ummu? Duk wannan Tam bayoyi ai sai bintu, Umma tace eh bintu wannan itace bbyn danace zan haifa miki, farin ciki sosai ya kama bintu, to yanxu kije ko, saboda bby tana bacci karta tashi, bintu tace; Ummu ina zamuna kwana tareda ita, Ummu tace eh kije to kinji saiki faɗawa Abbu aiko cikin zumuɗi bintu ta fice tayi falon Abbu.
Karo tacida sayyid zai fito daga falon, tace ya sayyid momy ta haifo min fane baby girl, yace da gaske tace eh to barinaje na ganta nima,
** Gari na wayewa Abubakar suka shirya shida Ameenatu domin tafiya jalingo atare wajen da yake kasu wanci saboda rashin lafiyarta yaka mata Ace suna tare domin zuwa babban asibiti, sun sallami kowa kulu ta musu fatan nasara suka tafi cike da kawar juna.
Bayan sun isa kai tsaye asibiti suka nufa ba wani jimawa suka samu ganin likita an mata duk wani gwadi daya dace an tabbatar cewa tanada ciwon zuciya wanda tunani ya hadda sa mata,.
Abubakar yashiga tashin hankali matuka, an rubuta musu magani dakuma shawar wari da aka basu, sun isa masauki wajen wani mutumi wanda shine uban gidan Abubakar sunan sa mlm Haruna, tare suke kasuwanci shiya ɗaura Abubakar a hanya, matar mlm Haruna tanada matukar kirki ta karbesu hannu2 bayan samun labarin abunda ke faruwa da Ameenatu tausayin su yakara shiga zuciyar mlm Haruna , yayi kuma niya Insha Allah zai tai maka musu.
*BOƊƊI ne ke zaune cikin falon ƙasa itada bintu ansanya mata kaya masu kyau cikin kwana biyu takara kyau dakuma sabo mutanen gidan, wasa suke tareda bintu, BOƊƊI na faman dariya dama shine abunda tafi iyawa,.
Sayyid ne ya shigo BOƊƊI na hango shi tafara daga hannaye sama alamun ya dauke ta, dariya yake mata ya wuce yaki dauka ta kuka ta saka bintu tace ya sayyid kadau keta mana, juyowa yayi ya dauke ta yana dariya itama dariya tafara tayi shiru Ummu dake saukowa daga bene. Tace Bintu kece kika samun baby kuka ko? Tace; a’a Ummu sayyid ne yaki daukan ta shine take kuka, ah ah Sayyid yaushe kafara tsokanan babyna, Sayyid yace Ummu BOƊƊI sunanta fa tace to Haka kasa mata, yace no Ummu Barrister mukaji yana faɗin haka saboda yaga kyanta, wai a fula tanci kyakkyawa, BEUTIFULL, Ummu tace wow BOƊƊI to munji yanxu muma haka zamu kira ta,.
Yauwa Abbu yace gobene zaka wuce ko? Sayyid yace; eh To kayi magana da jaddun ne? Yace inaso dai nakira shi ko inaso na musu surprise ne, Ummu tace wani irin surprise daka musu da karka musu ai duk zasu yi farin cikin ganinka kasani kaima. Sama ya haura yana cewa gara dai amsun yana dariya.
Dakinsa ya wuce domin watsa ruwa yana matukar jin kewar Nigeria da ahlin sa baki ɗaya sai lokacin ya tuna yaushe rabonsa daya ziyarci gidan kaka nunsa ,
Bayan ya fito wankane ya shirya cikin kananun kaya domin magrib tayi masjid ya wuce wanda ke maƙale jikin gidan, bayan ya fito daga masallaci yashiga motar sa jidan kakansa ya wuce, koda shigar sa yasha magana A wajen tsohuwa, yayi ta bata hakuri, ai Aliyu kam bai jefar damu ba tunda kullum nan yakecin abinci, tayita faɗa shi kuma yana bata hakuri, suna cikin haka tsoho ya shigo tace yauwa gara da kazo, shima yace yau wanake gani badai Maleek tsohuwa tace shine dai yau yaxo, bayan sun gaisa ne tsoho yace yanxu Maleek sai yau tunda kadawo Kasar nan bakaxo gidannan ba, yace kuyi hakuri wlh ban samu lokaci bane, yanxuma naxo muku sallama ne zan wuce Saudiyya gobe, suka yi salati yanxu Maleeku saida kaxo tafiya tukun zaka xo mana sallama, hmmmm lallaikuwa Allah ya kyauta bayanda muka iya kai namu ne dole Musa maka albarka, dariya suka yi baki ɗayansu, suka ci gabada tadi gwanin burgewa.
Washe gari……………………………………………………….🥱
Wlh I’m so tired 😴
Comments & share pls 🥰
WOMEN WRITERS ASSOCIATION📚
(Domin Marubuta Mata)
✨(W.W.A)✨
https://www.facebook.com/106752595253176/posts/107924965135939/
🌀🌀 BOƊƊI the beautiful
🌀 🌀
Story & writing
By
(Z. B. M)
Yar mutan gombawa.
Marubuciyar
~~ZAINAB abuƙaya
BANI BA AUREN SOJA
NIMA DANAWA LAIFI
Sc relationships
AUTAR MOMY
And now
BOƊƊI the beautiful~
Follow me on what’sapp
09066017177
Whatpad
Zainab7177
Gmail [email protected]
Bismillahi rrahmani rrahim
Kawun alƙawari cikawa saboda haka na baki wannan page ƙyauta FATIMA ADAMU kiyi yanda kikeso dashi 💃🏼💃🏼💃🏼💃🏼💃🏼💃🏼💃🏼💃🏼
PAGE 9️⃣🔁1️⃣0️⃣
…………….washe gari Sayyid ya tashi jikin sa duk babu daɗi domin Sam baya so yabar Ummu da Abbu, yana son zama tareda su, “amma bai san shi wani irin kaddara ne kowani lokacin Ace baya tareda iyayen sa”
Cikin tunani yakara sa shiri, fitowar sa kwai Ummu suke jira domin sun shirya, karfe 11 plane ɗinsu zai tashi a yanxu kuma karfe 10:15
Jikin sa duk babu kwari ya fito Ummu ne tace; ya dai Sayyid kana abu kamar mara lafiya sai mun hanzarta domin lokaci ya kusa.
“Bintu sarkin surutu taxo tana cewa” ya Sayyid Abbu yace wajen su jaddun zaka je? dan Allah nima katafi dani wlh nikam inason zuwa, Sayyid yayi karfin halin cewa Bintu idan kika tafi to wazai zauna da BOƊƊI tace to itama saimu tafi da ita,. Ummu tace babyna bazata jeba kedai kitafi, tace a’a Ummu nima nafasa dariya Abbu yayi domin yana jinsu baiyi magana bane, don yasan Bintu yau da ba don BOƊƊI ba! koya za’ayi sai taje. Sayyid yasa hannu ya karbi BOƊƊI da aka mata ado yau yaga tayi matukar kyau, yace; Ummu zanyi kewar beauty ɗinki ummu kibani ita na kaiwa jaddun, Ummu tace su, basa bukatar ta yanxu kaidai kaje kabarni da beauty na, idan Kaga mun rabu to aure namata. Gaban sane yafaɗi yace kai Ummu har anfara maganar aure tun yanxu, tace kwarai kuwa ai lokaci ne idan muna da rai to zaixo.
Saboda holdup da yake hanya sai 11/40 suka isa lokacin har an fara kiran ma tafiya. BOƊƊI na hannun Sayyid Bintu itama sai binsa take tana cewa; ya Sayyid karfa ka tafi da ita, har ya gaji da surutu irin na Bintu, shi da zai iya rufa idoma ai da ai daya wuce da ita, can ta tashi cikin yan Larabawa.
Bajimawa kuwa jirgin su Sayyid ya ɗaga zuwa Saudiyya tareda barin amanar BOƊƊI ahannunta. Ita dai sai mamaki take yi, abun kuma dariya yake bata, kai Maleek Allah ya nunamin ɗanka domin zai sha so yayya 😁
Bayan su Ummu sun dawo daga rakiyyar Sayyid suka ta rarda Farouq yaxo Abbu yace ya dai Farouq ka makara gashi har sun tashi, yace wallahi phone ɗina ne yasamu problem shiyasa gashi bansan time ɗin tafiyar ba, kawai zamuyi waya dashi, yace Ummu gaskiya kina kula da babyn ki kalli yanda takara zama fresh, Ummu tana dariya tace zakaci kanka ai,.
* Alhamdulillah yanxu Ameenatu ta fara murmurewa sai dai abunda baza a rasa ba, wato har yanxu BOƊƊI tana ranta. Mlm haruna Da Abubakar suna zaune sai Mlm haruna yace yauwa Abubakar inada wata shawara wata kila tayi maka yace ina sau ra ronka domin nasan duk abunda zakace to Insha Allah alkhairi ne awagena.
Mlm haruna yaji dadi sosai domin Abubakar ya dauke shi tamkar dan uwa, yace ; dama shawara ta itace mai zai hana tunda inada ɗan uwa a Kano kaje can domin kasuwanci yana da kuɗi sosai kuma nasan idan na tura ka zai ɗaura ka kaima, har kasamu na kanka, kuma kaga can akoi samu ba kamar nanba.
Abubakar yaji dadin maganar amma sai kuma yace ai matsala ta Ameenatu kuma gashi inada Mahaifiya a ƙauye bazan iya tafiya nabar wannan nauyin ba, yanxuma na mata nisa bare kuma Ace natafi har Kano. Mlm haruna ya numfasa! Yace; karka damu Allah yana nan kuma nasan bazata hana ka tafiya ba saidai kawai ka rike alkawari aduk inda kake katuna dasu nasan zasu yi ta maka addu’a kuma addu’ar su shine nasara a gareka, karka damu Ameenatu zamu zauna tare da ita, kamar yanda kasani bazata taba kuka na shin wani ba.
Sosai Abubakar ya shiga farin ciki. Koda yadawo yasanarwa Ameenatu ita dai batace komaiba sai tafan alkhairi datayi,
Washe gari Abubakar ya shirya yanufi kauyen su, bayanda Ameenatu batayi ba domin ta bishi amma yace ta zauna in ya so taje daga baya,.
Koda ya isa kulu tayi farin ciki ganin ɗanta takuma tambayi jikin Ameenatu yace yanxu alhamdulillah ta warware, labarin tafiyar sa Kano yabata, da farko taso ta damu amma daya Fahim tar da ita da wasu kalmomi sai hankalinta ya kwanta, musamman data tuna abunda yake faruwa yanxu furera da mahaifiyarta sun baza labari a gari cewa BOƊƊI aljana ce, shiyasa ta ɓace,. Abun na damun kulu sosai data fita sai a fara nuna ta. Hakan yasa tayi farin ciki da Ameenatu bata samu wannan labari ba domin bazata iya jurewa ba.
Fatan nasara tayi wa ɗan nata yatafi basu hadu da furera ba tana can wajen ya won gulma, sa’anninta duk sun kusa samun jika a garin. Amma ita ko auren batayiba bare ɗa.
BOƊƊI sai kara wayo take kowa ya ganta sai son barka, Bintu kullum tana tareda ita wai dole sai ta koyawa BOƊƊI tafiya da magana ita ta gaji bata iya daukan taba don tayi nauyi yanxu.
Haka zasu zauna suyita gwalantu wani lokaci kuma tafiya anayi ana faduwa. Ummu dai dariyan su kawai take.
Sayyid ya isa cikin koshin lfy jaddun sunyi matukar farin ciki da ganin sa, ai kuwa a ranar daya isa bai bari ya kwana ba ya basu labarin BOƊƊI su kansu sunga yanda BOƊƊI tashiga zuciyar Sayyid,
Yafara zuwa makaranta abubu buwa suna tafiya yanda ya kama mata.
Abubakar yasamu shigowa garin Kano…………………………
Sai amin axuri da typing kadan banida enough charging ne
Mai Ƙaunarku Z. B. M😘🥰
Share pls 🙏
WOMEN WRITERS ASSOCIATION📚
(Domin Marubuta Mata)
✨(W.W.A)✨
https://www.facebook.com/106752595253176/posts/107924965135939/
🌀🌀 BOƊƊI the beautiful
🌀 🌀
Story & writing
By
(Z. B. M)
Yar mutan gombawa.
Marubuciyar
~~ZAINAB abuƙaya
BANI BA AUREN SOJA
NIMA DANAWA LAIFI
Sc relationships
AUTAR MOMY
And now
BOƊƊI the beautiful~
Follow me on what’sapp
09066017177
Whatpad
Zainab7177
Gmail [email protected]
Bismillahi rrahmani rrahim
Dole ne yar uwata sister mai bani karfin guiwa HASSANA BALA kema ganaki page ɗin kiyi yanda kikeso dashi Allah yabar zumunci 💃🏼💃🏼💃🏼💃🏼💃🏼💃🏼💃🏼💃🏼
PAGE 1️⃣1️⃣🔁1️⃣2️⃣
…………….Abubakar yasamu shigowa garin Kano Bai wani wahalaba wajen gano gidan dan uwan mlm haruna, “gidane nagani na faɗa katafare iya kallon mai kallo, Abubakar yayi mamaki gamida tsoro saboda azayonsa nanɗin wani wajene, tunda yake bai taba ganin irin wannan gida ba, haka bai kuma taɓa sawa ransa akoi aduniya ba, maganar da yaji ne yadawo dashi tunani, Bismillah, ka shigo.
bai tsinkayi lamarin ba sai da aka shigar dashi wani falo akace zauna alhaji yana fitowa,
Jikin sa na ɓari yadan rakuɓe jikin kujera,, ba jimawa sai ga wani mutum ya fito fusakarsa dauke da fara’a “yace ;maraba sannu da zuwa bayan ya zauna ne suka gaisa cikin mutum ci, Abubakar ya masa bayani daga inda yake yace tabbas nasamu labarin zuwan ka, yanxu saika huta kayi wanka,
Wani dakin aka raka shi, sanin cewa Abubakar ɗan kauyene yasa mai gadin yanuna masa yanda zaiyi komai, har yafara saduda da cewa nan gidan aljanna ne 😂 bayan yayi wanka yafito ya tarar da abinci an kawo masa ba wani iyaci sosai yayiba, saboda yunwar cikin sa nema yasamu ya tsakuli kaɗan.
Aguje ta fito da lunchbox ɗinta a hannu Sanye da kayan makaranta, “Bintu wait for me pls,” Ummu dake tsaye tana hangota dariya ta fara tace; gara dai su tafi tunda kullum ke kinfi so kuyi late, karasawa Tayi wajen motar tana haki kamar wanda tadaɗe tana gudun, tace Bintu dama zaki iya barina, Bintu tace daki rinka jawomin faɗa wajen uncle ɗinmu ai gara natafi, tace sorry bazan karaba to, hmmm zakiji dashi, muje driver cewar Bintu, . “
Lokaci shuɗewa yake duniya sauya wa take, abubuwa faruwa suke, kamar haka girman BOƊƊI yabani matukar mamaki, har cikin makaran tar aka shigar dasu suka fito gwanin sha’awa Bintu ta kama hannun BOƊƊI kowa yagan su sai yace masha Allah 🥰 Har kofar class ɗinsu Bintu takaita tana kuma mata gargaɗi pls banda faɗa kinji tace to Naji, ta shige ciki abun ta. Bintu ma class ɗinsu ta wuce,
Lokacin break Bintu tana zaune tana jiran BOƊƊI taxo don suyi break tare, saboda Ummu tace kar Bintu tayar da tayi break batare da BOƊƊI ba,.
wani yarone yaxo yace Bintu Kinga BOƊƊI ko. Tace;
“mekuma BOƊƊI tayi?
Yaron yace, tana magana aunty tana class nace zan faɗa shine tace saita dakeni, kuma ban faɗaba amma bayan Aunty tafita shine BOƊƊI ta jefar mun da home work Kuma anjuma uncle sani zai karba., tace sorry jekayi break anjuma zan kawo maka class kaji, yace to yauwa good boy,.
Ran Bintu ya ɓaci gashi har an kusa komawa BOƊƊI bata xoba. Har zata tashi sai ta hango ta, tana tahowa wata yarinya na biye da ita, Bintu tace da alamu BOƊƊI wani abun tama yarinyar nan, ai kuwa suna zuwa yarinyar tace ; Kinga BOƊƊI ta zubar mun da abinci na, BOƊƊI tace wlh karya take ni ban ganta bama, Saboda takaici Bintu ta Mike tabar abincin a wajen, BOƊƊI ne ta zauna domin cin abincin sai taga yarinyar ta zuba mata ido zabura tayi tayo kan yarinyar ai kuwa ta kwasa da aguje, nikaina abun yaban dariya, BOƊƊI kenan yar karama amma sai fitina.
Koda suka koma gida Bintu ta faɗa wa Ummu abunda BOƊƊI keyi a school sosai Ummu tayi mata faɗa ta ko nutsu tana sau raro kamar da gaske 🤪 lokacin islamiya suka shirya ba wasa domin BOƊƊI akoi son karatun addini.
Ban garen Abubakar saidai muce masha Allah domin fa abubuwa sunyi matukar kyau ahalin yanxu yanada shago na kansa a kwari market 😊
Ya ziyarci Ameenatu, lokacin daya je, Mlm haruna yayi matukar farin ciki sannan yace gaskiya Abubakar a yanxu yaka mata ka dauki matarka tunda kaima a yanxu kusan kasamu na kanka,
Hakane kam kuma dama inada niyar hakan nagode sosai bazan mance da khairin kaba agareni,.
Tareda Ameenatu suka je ƙauyen Genle, kowa yayi farin cikin ganin su, kulu taji dadin ganin Abubakar ɗinta yanda yayi kyau kamar ba wanda yafita daga Kauyeba a wannan lokacin ma saida suka tuna da BOƊƊI suka koka, ayanxu wata kila ma ƙashinta yayi fari a ƙasa,.😫 🥺 Hmmm BOƊƊI nacan tana tsula ciyar ta ajini da faɗi😄💃🏼💃🏼
Ameenatu ne tace inna kulu ya tunda na shigo banji ɗiriyar su Furera ba,, tace uhm ” bakida labarin Furera Mlm Tanimu mai almajirai ya aureta tace Mlm Tanimu dai? Kwarai kuwa ayanxu tana gidansa, Ameenatu tace to ina Innar tata, Naji ance mutumin nan baida kyau ana zargin shi, kowa ya sani cikin garin nan kuma Shine tayar da, kulu tace Kinga kiyi abunda ke gabanki wannan kuma susuka sani, nima ina nan zaune Naji za’a ɗaura aure.
To Allah shi kyauta, yamma liss Ameenatu suka bar Genle, washe gari kuma sai garin Kano,
Dama Abubakar lokacin daya fara kafuwa ya sayi wani ɗan gida, karami amma kuma yanada kyau ba laifi,
Three bedroom plant da kitchen da toilet gidan yayi dai masha Allah 🥰.
Da dare BOƊƊI na zaune tana kallo, Bintu tace yau bakida home work ne?
“ni gaskiya nagaji inason nayi kallo ne, Ummu ne ta sauko rana cewa baby na kixo ga ya Sayyid zaiyi magana dake cikin sauri ta diro……………..
💃🏼💃🏼💃🏼💃🏼💃🏼Yanxu ake Fara 💖
Comments & share pls 🥰
WOMEN WRITERS ASSOCIATION📚
(Domin Marubuta Mata)
✨(W.W.A)✨
https://www.facebook.com/106752595253176/posts/107924965135939/
🌀🌀 BOƊƊI the beautiful
🌀 🌀
Story & writing
By
(Z. B. M)
Yar mutan gombawa.
Marubuciyar
~~ZAINAB abuƙaya
BANI BA AUREN SOJA
NIMA DANAWA LAIFI
Sc relationships
AUTAR MOMY
And now
BOƊƊI the beautiful~
Follow me on what’sapp
09066017177
Whatpad
Zainab7177
Gmail [email protected]
Bismillahi rrahmani rrahim
Wannan page Na baiwa fadeema sajidah 💃🏼💃🏼💃🏼💃🏼💃🏼💃🏼💃🏼💃🏼kyauta kiyi yanda kikesooooooo 💃🏼💃🏼💖🥰
PAGE 1️⃣3️⃣🔁1️⃣4️⃣
…………….Dirowa tayi ta karɓi wayar, ta gudu falon Abbu, fara masa rigima tayi yace; `wait beauty, let me call you video call,” no ya Sayyid I don’t wan’t see you” yace sorry dear pls, let me call you yeah, OK ” kashe kiran yayi, sai ga video call yashigo, baki ta turo gaba kafin taɗauka yafara shagwaba shi kuma sai biye ta yake yi.
Bintu dake staye tun lokacin fara wayar tasu, dariya ya kusa kashe ta don duk wanda yaga yanda BOƊƊI da Sayyid keyi saiya dara😆Bintu ta leƙo kanta “HI ya Sayyid, yace Bintu kina lfy? Kai ya Sayyid wallahi kana kara sakal ta taka,.
Kasan yanxu tsokana take yi a sch, wlh ya Sayyid BOƊƊI kowa ta da meshi yaran class nasu ba wanda Tabari.
BOƊƊI takara haɗa fuska ta tashi tatafi ko kallon Bintu batayiba Sayyid yace oh, Meyasa kika yi haka gashi yanxu kin kore ta. Maza kije ki lallabata,. Ya kashe wayar mamaki Bintu take irin shakuwar BOƊƊI da ya Sayyid,.
Ameenatu na zaune cikin farin ciki sai son barka amma har yanxu damuwa na nan a ranta,
Tana zaune a falo Abubakar yashigo yace yauwa kin shirya eh to muje ko, Asibitin Aminu Kano, suka nufa, sun samu ganin doctor akan ciwon dake damun Ameenatu ne an mata duk gwaje – gwajen daya dace, abun farin ciki an tarar tanada ciki na sati 3, farin ciki sosai Abubakar yayi, koda suka dawo bacci tayi tayi, harda mafarkin sahibarta BOƊƊI, bayan ta farka ne, ta gane ba gaskiya bane mafarki tayi, hawaye ne suka taru a idon ta, Abubakar ya shigo ɗakin da ledoji a hannun sa, saurin gogewa tayi, sannu da dawowa yace yauwa sarkin bacci, nayo mana take away ne saboda a yanxu kema zaki huta nayiwa wani abokina magana za’a samo wacce zakuna zama tare domin debe miki kewa,, tace to shikenan nagode, dan Allah dama inaso na rinka fita waje kozan Saba da garin, shine nace tunda naga akoi Islamiyya tanan sai na shiga, yafi zama haka, yace kuma gaskiya kam, amma keda yanxu kina juna mezai sa ki wahala, amma tunda kinaso hakan za’ayi, dariya tayi tareda godiya.
Cikin ikon Allah Ameenatu ta cigaba da renon cikin ta tana zuwa islamiya, ansama mata yarinya wacce take taya ta aikace aikacen gida, Allah yakawo mu, lokaci Ameenatu ta sauka lfy, baby ta haifo har biyu kyawawa mace da namiji murna sosai Abubakar yayi,.
BOƊƊI ta cigaba da rayuwa cikin aminci da kulawar Ummu, ” yanxu Bintu tashiga ss, BOƊƊI kuma na junior, sosai ta kara kyau, A yanzu ta rage rigima,.
Alhaji Abubakar Genle shi aka rubuta a mashigar gidan,” gidane na gani na faɗa, ban ruɗeba saida na shiga ciki anya wannan gidan Abubakar ɗin Ameenatu ne” bayan na wuce first gate na shiga second saiga wasu kyawawan kids, suna wasa a compound, na mijin ne ya tura karamar ta faɗi da sauri tamike tashiga ciki tana kuka shima ya rufa mata baya har wajen, mamyn su, wato hajiya Ameenatu genle
Mamy Kinga Ayan yatureni, Ayan daya shigo yace Mamy kafana ta taka mun, Mamy takallesu tace ; ba kwajin magana yaran nan kullum kuka haɗu sai kunyi rigima, kufa yan uwan gunane, tace ma Ayan yabama Ayana hakuri yace to sorry, shikenan fadan yara har sun shirya, suka juya suna farin cikin.
Yau holiday su BOƊƊI sunje gidan kaka, da dare BOƊƊI ta ce ita dai sai tadawo gida bazata kwanaba, bayanda Bintu ta iya haka kaka tasa Aleeyu yadawo dasu, suna shigowa waye zasu gani……………. 😂
Comments and share pls. 🙏
WOMEN WRITERS ASSOCIATION📚
(Domin Marubuta Mata)
✨(W.W.A)✨
https://www.facebook.com/106752595253176/posts/107924965135939/
🌀🌀 BOƊƊI the beautiful
🌀 🌀
Story & writing
By
(Z. B. M)
Yar mutan gombawa.
Marubuciyar
~~ZAINAB abuƙaya
BANI BA AUREN SOJA
NIMA DANAWA LAIFI
Sc relationships
AUTAR MOMY
And now
BOƊƊI the beautiful~
Follow me on what’sapp
09066017177
Whatpad
Zainab7177
Gmail [email protected]
Bismillahi rrahmani rrahim
PAGE 1️⃣5️⃣🔁1️⃣6️⃣
…………….Farouq abokin Sayyid, da gudu BOƊƊI taxo oyoyo ya farouq munyi kewarka, yace beauty Ummu kece kika zama haka.
Kai masha Allah Ummu Kice mun kusa zuwa aure ga Bintu kam ma ta kusa kwantai, wani harara Bintu ta aika masa “dama bata kula shiba tun shigowarsu, dariya yayi yabita da kallo, Ummu tace idan ku ba kuyi kwantai ba ai Bintu bazatayiba kwata kwata nawa take, she’s just 18 kaifa da Sayyid 34 kuke, ai duk kun tsufa yana can yagama karatu narasa me yake jira kullum jaddun sai yayi magana Sayyid na stufa yaƙi aure,, shi kuma da anyi magana sai yace lokaci yake jira,.
Farouq yace tabbas lokaci muke jira Ummu kuci gaba da addu’a, tace munayi kullu kuma dai kusa niyya aranku,.
BOƊƊI ta bi bayan Bintu tashiga ɗaki tasamu tana karatun exam don neco yanxu take rubutawa,.
Bintu dan Allah ki ƙiramun ya Sayyid kwana biyu bamuyi magana ba. Tace wai ke Meyasa BOƊƊI bazaki bar mutum ya huta bane, bakya ganin abunda nake yi, hmmm 🤔 ta kama baki tafita, ta barta aɗakin.
Wajen Ummu taje tace; Ummu kibani Aron wa yarki naƙira ya Sayyid kwana biyufa bamuyi magana ba.
Ummu tace Tabb idan kun fara bakusan bariba keda Sayyid ɗin marasa aikin yi, baki ta turo gaba kamar zata yi kuka , Ummu ta kalle ta, Babyna kin girma yanxu fa, baki ga zaki shiga class na manya bane 14yr fa kike yanxu, tace Ummu kisayamun waya mana, dariya tayi to baby na kije kifaɗawa Abbu zai saya miki, kinji.
Wucewa tayi falon Abbu Ummu tasameshi yana zaune yana kallon news, ” babyn Ummu hala dai antaɓoki yanda naga face ɗinki, tace Abbu Bintu da Ummu sunki bani wayar su nayi magana da ya Sayyid, Abbu kasa yamun waya tunda nima yanxu ss zanshiga dariya yayi to, za’a saya miki yanxudai bari kuyi magana da Sayyid kar ran Babyn Ummu ya baci, daɗi taji sosai,.
Abbu video call zaka kira shi, ai kuwa haka aka yi. Abbu kansa yana mamakin shakuwar BOƊƊI da Sayyid duk da basa tare,.
Sayyid yana zaune a falon Jaddun sai surutu yake masa kan aure to meye ka rasa ne, matan Larabawa sonka suke kazaɓi ɗaya a ciki ka aura, Tabb nine zan auri balarabiya, kiran Abbu ya katse hirar tasu dama ya gundura da zancen vedio call,, yana ɗagawa BOƊƊI yagani tana masa smile “hi” ya Sayyid wani farin ciki yaji babyn Ummu yau kuma Abbu yabaki wayar sa,
Ƙara cuno baki tayi “ya Sayyid Bintu ta hanani wayar ta Ummu ma haka, amma Abbu yace zai sayamin., Kice yau Ummu tayi laifi. Ɗaki yashige suka cigaba da magana jaddun na kallonsa, ya girgiza kai kawai.
Ya Sayyid yau ya farouq yaxo yace da gaske eh yaxo yace wai na girma, tafaɗa tana dariya, Sayyid yace to kin girma ne shiyasa ya faɗa Kinga yanxu saiki maida hankali a kara tunki, karkiyi wasa kinji, sosai suka yi taɗi, yace mata ya kusa da wowa ai murna sosai BOƊƊI take yi, “Sayyid zai dawo kowa saida yaji batun dawowan sayyi hatta masu gadi duk BOƊƊI ta gaya musu,.
*ratsa daji suke da haɗaddiyar motar duk inda suka wuce kallo ake, su *Ayan da ayyana* har sunyi bacci sun farka. Mamy wai ina zamuje ne, mun gaji, dariya tayi saura kaɗan mun kusa isa,.
Ba jimawa kuwa suka isa ƙauyen genle, yara suka zagaye motar manya harda masu leƙe ta katanga lokacin da suka fito suka shiga cikin gidan kulu kanta saida tayi da gaske kafin ta gane Ameenatu, kukan farin ciki ne ya kufce mata tace, sosai ta rungume Ayan da ayyana suma kukan suka saka amma su na tsorone 😂.
Gida yacika makil da mutane alhaji Abubakar yaxo daga birni, bayan mutane sun lafane Abubakar yace innah kulu, tare zamu koma don kije kiga inda nake zaune tace to yanxu sai mutafi tare Ace nima nabiku.
Ai baiyiba. Yace innah kiyi hakuri bawai kin koma can duka bane zaki dawo amma sai kema zaki huta. Saida Ameena ta saka baki sannan kulu ta amince, Mahaifiyar, furera bakin ciki fall ranta guda gida tadawo bi tana cewa ai Abubakar ɗan kulu yanxu yazama ɗan yankan kai, duk abunda take cewa, bai hana washe gari lokacin da zasu koma yara ba kuɗi yan Kauye kam sai karbar abunsu suke suna murna. Itama Mahaifiyar furera nata daban harda kukan muna furuci amma a zuciyar mummunan addu’a take.
Zasu shiga motar kenan sai ga wata mata baƙa kamar mahau kaciya taxo tana sannu alhaji nima dan Allah abani kuɗin. Kulu ce tace furera kece, hawayene a idon ta taɗago ta kalli Ameenatu rungume ta tayi wani karni da wari ya bugi hancin ta da sauri ta janye. Kiyayeni Ameenatu alhaki bazai barni ba na gane dama innah tace ke ɗaurani hanya gashi ta kaini ta varoni, ni nayi sanadin BOƊƊI nakai ta na wurgar, da farko ba abunda kunnen Ameenatu keji amma anayin zancen BOƊƊI ta ware ido da karfi tace Furera kece kika yi silan rabani da farin Cikina ashe kece silan war gajewar rayuwa ta, furera kin cuceni kin raba uwa da ƴa, kin war Gaza farin ciki. Abubakar da kulu kasa motsi suka yi don tashin hankali ji suka yi Ameenatu ta faɗi dif akasa sumammiya……………….
Mu tare agaba 💃🏼💃🏼
Comments an share pls
WOMEN WRITERS ASSOCIATION📚
(Domin Marubuta Mata)
✨(W.W.A)✨
https://www.facebook.com/106752595253176/posts/107924965135939/
🌀🌀 BOƊƊI the beautiful
🌀 🌀
Story & writing
By
(Z. B. M)
Yar mutan gombawa.
Marubuciyar
~~ZAINAB abuƙaya
BANI BA AUREN SOJA
NIMA DANAWA LAIFI
Sc relationships
AUTAR MOMY
And now
BOƊƊI the beautiful~
Follow me on what’sapp
09066017177
Whatpad
Zainab7177
Gmail [email protected]
Bismillahi rrahmani rrahim
PAGE 1️⃣7️⃣🔁1️⃣8️⃣
……………. Cikin firgici suka sata a mota sai asibitin dake cikin mayobelwa don a bata tai makon gaggawa, labari yabaza gari abunda su furera suka ai kata.
Yau BOƊƊI bata jin dadi sosai tana kwance sai juyi take, Bintu ce tasamu Ummu tace ; BOƊƊI yau bata jin ɗadi tun dazu sai kuka take subahanallah! Ɗakin Ummu tashiga BOƊƊI ta kudun dune sai kuka take.
Ummu taxo ta ɗago kanta Baby na, meyeke damun ki. Ummu cikina ciwo, Sosai yake mun. Ayyerh sorry, kodai baby ta girma ne. Dariya Bintu tayi BOƊƊI kuma sai kara rike cikin ta take don stananin ciwo yake mata.
Family doctor Ummu takira ya duba ta, yayi mata allura sannan ya rubu ta magani.
Ya yiwa Ummu bayani sannan yayi sallama yatafi bacci ya dauke BOƊƊI lokacin da Ummu ta shigo, murmushi tayi lallefa baby tabar baby yanxu itama ta girma.
Lokacin da BOƊƊI ta tashi bacci jin ta tayi ajiƙe kamar wacce tayi fitsari. Ganin jan abu yasa ta tsorata, Bintu ta ce ya dai BOƊƊI, hawaye ne ya gangaro idon ta, dariya Bintu tayi ta taimaka mata zuwa toilet taba ta pad tasaka sannan ta mata duk wani bayani daya dace Ace tasani, .
Tunda ga lokacin BOƊƊI tazama so silen, magana ma yafara fin karfin bakin ta. Ummu tace BOƊƊI ga ya Sayyid ya ƙira, ɓata rai tayi Ummu na gaji zanje na huta, sai anjima,
Kallo Ummu tabita dashi, Sayyid yana jin duk abunda take faɗa.
Ummu wai meke damun BOƊƊI ne gaba ɗaya ta sauya, Ummu tace to kasan komai da lokacin sa, karabu da ita batason surutu ne,.
Ran Sayyid baiyi daɗiba haka ya hakura. A yanxu Sam BOƊƊI ta daina duk wani rashin ji data keyi. Abubuwa na manya taje yi, jinta take yanxu ta girma.
Ameenatu dan Allah kidai na kuka yanxu kam bansan yanda zanyi ba. An bincike da jin kaf amma ba’a samu ko gawar taba.
Cikin daga murya tace dama taya za’a samu gawar BOƊƊI na nasan tana nan da ranta, taba wani wajen, tana Raye itama kamar yanda nake Raye. Kukane yaci karfin ta.
Alhaji Abubakar, ya shiga bata baki, don bayaso ciwon ta yakara tashi gashi doctor ya masa gargaɗi akan hakan.
Kulu ce tasaka baki cikin rarrashin, karshe dai hakura sukayi don Ameenatu kamar ana zugata.
To Barrister Sani kaji abunda yake faruwa a yanxu rasa mafita, to alhaji gaskiya tunda kace an bincike dajin ba’a sameta ba, saidai kuma abada cigiya, ko a gidan marayu,, Hakan kuwa aka yi. Ko wani gidan marayu an bada cigiya da an samu labari Ameena jikin ta na ɓari zata je, amma kuma sai asamu ba ita bace.
BOƊƊI na kwance a ɗaki, kamar maiyin bacci amma kuma idon ta biyu Bintu ce tashigo cikin sauri! BOƊƊI kinsan kuwa meyake faruwa yau agidan nan. Cikin son jin gulma ta Mike, meya faru Bintu, ah Bintu ma zaki cemin, to sorry, ya Binty, faɗa min.
Kinsan me wannan guy ɗin yayi kuwa wlh ya shammace mu, wani guy ɗin BOƊƊI duk ta damu taji karshen zancen.
Kinsan muna zaune da Ummu yan a falo kawai……………….
More comments more typing
ZAINAB abu’ƙaya ce🤙😆
WOMEN WRITERS ASSOCIATION📚
(Domin Marubuta Mata)
✨(W.W.A)✨
https://www.facebook.com/106752595253176/posts/107924965135939/
🌀🌀 BOƊƊI the beautiful
🌀 🌀
Story & writing
By
(Z. B. M)
Yar mutan gombawa.
Marubuciyar
~~ZAINAB abuƙaya
BANI BA AUREN SOJA
NIMA DANAWA LAIFI
Sc relationships
AUTAR MOMY
And now
BOƊƊI the beautiful~
Follow me on what’sapp
09066017177
Whatpad
Zainab7177
Gmail [email protected]
Bismillahi rrahmani rrahim
PAGE 1️⃣9️⃣🔁2️⃣0️⃣
…………….kinsan muna zaune da Ummu a falo, kawai sai ga ya Sayyid yadawo, wai ya Farouq ne ya ɗaukoshi a airport, BOƊƊI ta tashi cikin sauri” wai dagaske ya Sayyid yadawo?.
“kwarai kuwa yadawo, yanxu haka, dama naxo miki al bishir ne’,
Stalle ta buga akan gadon murna sosai ya kamata, Bintu tace; to kixo muje ƙasa kowa yana can.
” Nidai bazani ba kije abunki.
Kamar ya bazakiba.? “keda ya Sayyid ɗinki please beauty stop joking kixo muje sai ku gaisa daya farouq karya tafi.,
Tashi tayi suka sauƙo kasa ba kowa a falon Bintu bata sake taba har suka ƙarasa dining area inda Ummu ke zaune,.
Ah ‘lallai Bintu kinyi ƙoƙari tunda kikasa BOƊƊI ta sauko,
Karamin bakin ta. Ta turo gaba, don yanxu kam ta fahimci Ummu da Bintu plan suka hada ” tun safe BOƊƊI na kwance a ɗaki batayi Breakfast ba, saida Bintu takai mata ɗaki.
Yauwa babyn Ummu, kixo kiyi dinner, Bada son ranta ba, taƙarasa tana tuna wani irin rashin mutunci yaka mata tayi wa, Bintu.
Ummu da kanta ta zuba mata abincin taci sosai don yunwa takeji ba ƙarya, kawai yan halin nata ne, suka mosta.
Bintu sai dariya take yi, Ummu wannan baby Naki kinsan saboda “nace ya Sayyid yadawo ne yasata fito.
Ummu tace `oh wato ƙarya kika mata, sorry babyna kirabu da Bintu. Kodai babyn ya Sayyid ne? Naga anfi son shi,.
A’a Ummu ni nayi fushi da shi” Bintu dake dariya a gefe, tace; BOƊƊI ya Sayyid yana ƙira kixo kuyi magana dashi, lokacin BOƊƊI tagama cika tun binta tasha ruwa, bata kalli, inda Bintu take ba, ta kama hanyar ta, sai falon Abbu. Baya nan saboda haka tayi kallon ta Ba mai takura mata.
Saida dare yayi kafin ta tashi taje ta kwanta, yau bata kula kowa sai Ummu kaɗai tayi fushi da Bintu,.
“BOƊƊI ga chocolate, Ummu tace na baki, amma saida safe zakisha.
Cikin sauri ta Mike don jin an faɗi chocolate, Dariya Bintu ta kwashe dashi wayyo BOƊƊI Ummu. Kefa yanxu you’re not a child, kin girma 16 kike August Ummu y tace zaki shiga 17 to Kinga ai kin girma.
Shiru tayi bata kula taba, a zuciyar ta tace I’m still a child wlh, tunda nice babyn Ummu har bacci ya ɗauketa tana jin haushin Bintu.,
Washe gari BOƊƊI taje school ta dawo, tashige ɗakin ya Sayyid domin itace kullum ke gyarawa, kamshin sosai ɗakin yakeyi ta rasa wani irin kamshine, ita dai kullum sai dai suyi waya ko video call, da Sayyid
Amma da wayonta bai taɓa zuwa Nigeria ba, kwanciya tayi akan gadon taci gaba da shakan kamshi.
, sai lokacin Islamiyya ta fito suka tafi da Bintu.
“Saura kadan BOƊƊI ta hada haddan ta, don ta haura 50, gata da ilimin littafai. Kullum sheikh saiya yaba mata.,
Lokacin da suka dawo BOƊƊI tace Ummu nikam zanyi dinner yanxu idan na hau sama bacci zanyi bazan sakko ba.
To shikenan baby na kiyi abunki. Bayan sallan magrib, BOƊƊI tana ɗanjin hayaniya sama-sama.
Bata kawo komai a ranta ba.
Can sai ga, Bintu taxo BOƊƊI kitaso Wlh Yau kam, ga ya Sayyid yadawo, ko kallo Bintu bata isheta ba.
Gajiya Bintu tayi ta fita, tana fita BOƊƊI ta tashi tasa key a kofar.
Sayyid na zaune kusa da Ummu ga ‘ya Aleeyu’ shima yau yaxo gidan, farouq duka suna nan sai murnar ganin juna ake.
Ganin Bintu ta dawo Basuga BOƊƊI ba yasa Sayyid cewa Ummu ina babyn kine? Batasan na dawo bane?.
Hmmm kasan bazata sauko ba, saboda Bintu ta ɓata mata rai.
Farouq ya amshe zance, Bintu me kika yiwa mata. Cikin fushi ta wurga mishi harara Batasan me taci wa ya farouq ba yake mata haka.
Kullum sai ya stokaneta sai dai baixo gidan ba.
Ummu ne ta faɗa musu abunda ya faru jiya, gaskiya Bintu baki kyau tawa beauty ba.
Yanxu dai bari naje rarrashi,.
Sayyid Jikinsa na ɓari yatashi ya yi dakin su BOƊƊI, su Ummu ne suka bishi da ido kowa sai dariya yake Ummu maleek zai kwace miki babyn ki.
Murɗa kifar yayi yaji ta gam a rufe, Knocking yayi BOƊƊI tayi shiru aza tonta Bintu ce…
Saida yayi magana BOƊƊI ki buɗe nine,..
Muryan kuma kamar na ya Sayyid, saida taji an kuma magana sannan ta sauko shan kali daga kan gadon, buɗe kofar ahan kali…………………..
💃🏼💃🏼💃🏼💃🏼💃🏼💃🏼 Wlh yawan comments yawan typing,
Abu’ƙaya ce 🤙😆
WOMEN WRITERS ASSOCIATION📚
(Domin Marubuta Mata)
✨(W.W.A)✨
https://www.facebook.com/106752595253176/posts/107924965135939/🌀🌀 BOƊƊI the beautiful
🌀 🌀
Story & writing
By
(Z. B. M)
Yar mutan gombawa.
Marubuciyar
~~ZAINAB abuƙaya
BANI BA AUREN SOJA
NIMA DANAWA LAIFI
Sc relationships
AUTAR MOMY
And now
BOƊƊI the beautiful~
Follow me on what’sapp
09066017177
Whatpad
Zainab7177
Gmail [email protected]
Message @SABAYA HERBAL on WhatsApp. https://wa.me/message/W7FSXOTK4DT4M1
Asalin had in gargajiya na Larabawa mai gyara brest da jiki, **SABAYA kowa Nasha amarya uwar gida, mai jego, mai shayarwa, bazawara, yan mata, mai ciki, sirrine na matan Larabawa,.
Idan kinsha SABAYA jikinki baya saurin lalacewa * * ** kuma baki saurin tsufa haka zalika mamman ki kullum kmr baki shayarwa.
Bismillahi rrahmani rrahim
PAGE 2️⃣1️⃣🔁2️⃣2️⃣
…………….muryan kuma kamar na ya Sayyid, saida taji an kuma magana sannan ta sauko a hankali daga kan gadon.
Buɗe kofar tayi, Takoma baya ta laɓe. Koda ta buɗe Sayyid baiga kowaba. Yashigo cikin ɗakin wayam, ba kowa.
BOƊƊI na ganin Sayyid sai dube dube yake, murmushi, tayi, “ta fito a hankali, ta fita da gudu, Sayyid bayan ta kawai ya hango.
😆OH, BOƊƊI kenan,
Bata ƙara sa fita ba, yayi saurin damƙo hannun ta.
Siririn ƙara ta saka, domin hannun ta daya damƙo. Taji zafi.
Lokacin da suka yi 2 eyes, kallon juna suka shiga yi.
Wow ya Sayyid Kaine? Bata san ma ta furta hakan ba.
Murmushi ya sakar mata, don ya kasa magana.
Sake hannun ta yayi. Batare da yace komai ba ya wuce zuwa dakin shi.
Bintu ce ta shigo, BOƊƊI yanxu kin tabbar ban miki karya ba. Kin gani da idonki.
Hummm ai dai nayi fushi dake.
Ta futo falo inda Ummu da farouq suke,
Jikin Ummu ta faɗa, tana ɓoye fuskar ta. Dariya suka saka baki ɗaya Ummu tace ya Sayyid ɗinki ya dawo ko.
Yanxu mun huta da Aron waya Akira shi.
Ganin sun dame ta da tsokana yasa ta tashi ta gudu falon Abbu.
Tana can tana kallon, zee world, suna yin, young dream, ta maida hankalin ta gaba ɗaya a kallon.
Karfe 9 aka saka, forbidden love,. Duk imanin ta yatafi akan TV, har Bintu da Sayyid suka shigo bata sani ba.
Ah lallaifa, babyn Ummu yanxu wato nan kika ɓuya Bata san sunayi ba.
Bintu tace ya Sayyid batasan muna nan ba fa.
Taɓata tayi saida ta razana. Dariya suka saka.
BOƊƊI ta ƙara haɗe rai ta juya, Sayyid ya zauna gefen ta, yace BEUTIFULL. Kinsan yanda kika kara kyau da kika haɗe rai.
Talk pls. Murmushi ya kwace mata don ya Sayyid ya bata dariya.
Bintu tace ya Sayyid yanxu Babyn Ummu bata son karatu kullum sai tayi ta shiga ɗaki tana rufe wa.
Yace, beauty meyake damun ki ne, karki damu na dawo zan zauna tare dake.. Dariya tayi, wanda ya bayyanarda wushiryar ta.
Kaii Bintu yaushe beauty tayi wushirya,, Bintu tace ; ya Sayyid ai tanada shi, wow meyasa ban taɓa ganiba.
Taɗi yake ta jan BOƊƊI saboda ya kula, tazama silent, Dakan sa ya tashi yaje ya ɗauko wasu manyan ledoji yabawa Bintu ɗaya BOƊƊI, ɗaya.
Cikin zumuɗi Bintu ta tashi nidai bazan buɗe anan ba, tayi ɗaki abunta.
Sayyid dakan sa, ya buɗewa BOƊƊI, wayace farkon abunda yafara fitowa dashi, sumsung xmas wani stalle tayi murna kamar ba itaba ya Sayyid, wannan nawane?
Kwarai kuwa naki ne.
Sauran kayan ta duba ABAYA ne guda 4 sunsha kyau iya kyau. Ga half cover shoe, wanda yasha stone,. Mayuka masu gyara fata irin na matan Larabawa, ga perfumed kam ba’a magana don Saudi akoi kamshi.
Sosai ranta yayi fari har ta rasa wani irin godiya zata yiwa Sayyid.
Farin cikin ta,! phone ɗin da tayi,, burin ta dama Itama tazama, yammata🤓.
Thank you so much ya Sayyid,
Koda tafita Ummu ta bi bayan ta da kallo, haka kawai wata rana take zama tayi ta, nuna nin ranar da BOƊƊI zata san Basu ne iyayen taba.
Kuma basu san ta inda zasu fara neman iya yen nataba.
Ko suna Raye ko’a mace, Allah kaɗai yasan daidai.
Ummu tayi alkawarin rike BOƊƊI iya karfin iya warta.
Har cikin zuciyarta take sonta kuma tana matukar tau saya mata.
Sayyid ne yace ; Ummu lfy, ganin tunanin nata yayi nisa.
Bakomai Sayyid, shima yasan abunda Ummu ke tunani kawai ya kawar da zancen, suka fara taɗin Saudi.
Abbu ya shigo shima aka ci gaba da taɗin dashi.
Wow BOƊƊI gaskiya kayan ki, sunfi nawa kyau.
Kai Bintu duk iri ɗayane phone kuma dama ai kinada shi, na huta da gorin dakike mun.
To kedai kika sani, daga ke har ya Sayyid ɗin.
Dariya BOƊƊI tayi, Bintu ta karɓi wayar, ta kunna, wayar tayi matukar burge ta. Harda simcard akan wayar,. Apps ta tura mata harda what’sapp da Instagram, da sauran su.
💃🏼💃🏼💃🏼Su BOƊƊI an Faso gariiii…
Sayyid na kwance yayi rigin gine. Kansa na kallon sama.
Yana riƙe da phone bacci ya kasa ɗaukan shi.
HI aka mishi a WhatsApp, yana ganin number ya gane number BOƊƊI kenan wanda yasa mata……..
Sorry for the short typing, bansamu zama bane. Amma kucigabada bibiyar BOƊƊI the beautiful, 🌀 🌀 🌀 yanxu za’a fara game ɗin💃🏼💃🏼💃🏼💃🏼💃🏼💃🏼💃🏼💃🏼💃🏼💃🏼💃🏼💃🏼💃🏼
Abu’ƙaya ce🤙😂
🌀🌀 BOƊƊI the beautiful
🌀 🌀
Story & writing
By
(Z. B. M)
Yar mutan gombawa.
Marubuciyar
~~ZAINAB abuƙaya
BANI BA AUREN SOJA
NIMA DANAWA LAIFI
Sc relationships
AUTAR MOMY
And now
BOƊƊI the beautiful~
Follow me on what’sapp
09066017177
Whatpad
Zainab7177
Gmail [email protected]
Bismillahi rrahmani rrahim
PAGE2️⃣3️⃣🔁2️⃣4️⃣
…………….Hi ya mayar mata Beauty ba kiyi bacci ba.
Eh ya Sayyid bana Jine.
Ya kamata kiyi saboda gobe akoi sch, ni zan kaiki da kaina makaran ta kinji ko.
To ya Sayyid, “Lailatun sa’iidah” mukwana lfy. 👋
Ya mayar mata, “ahlaman saiidah” mafarki mai daɗi. Sweet dreams 🥰
Wani farin ciki take ji, ba jimawa bacci ya dauke ta.
Haka Shima Sayyid bayan ya gama wasu abubuwan yaje ya ɗauro alwala, ya kwanta. Bacci yayi gaba dashi,
BOƊƊI kitashi fa, 7 tayi. To.. Saida Bintu ta gaji ta janyo ta.
Sannan ta tashi, tana kai mutum yasamu ya gama ya huta ma. Wlh
Bintu tace sai kijira ai lokaci ne.
Cikin kunci tashiga wanka shap shap,. Ta fito ta shirya yau ko break fast bazata samu yiba.
Tafito Sanye da uniform, cikin sauri ta fito Ummu ma lokacin fitowar ta kenan. BABY na yau mun makara, sorry, to ba zakiyi break bane. Ummu na makara fa.
1k Ummu ta mika mata to gashi sai kiyi acan godiya tayi wa Ummu ta tafita driver ya wuce da ita zuwa sch.
……zaune take ta rafka tagumi. Daka ganta kasan da muwa na damunta. Ayan da ayyana suka shigo, suna ta surutun su kallo kawai take bin su dashi amma ba ta Fahim tar me sukeyi.
Alhaji Abubakar ne yashigo, kallo ɗaya yamata, ya kauda kansa. Shi yanxu abun har ya fara damu sa shima,
Kixo ga barrister yaxo, yanaso kuyi magana.
Jikinta ba karfi tata so Tafito yana zaune a falon baki, gaisawa suka yi cikin mutun ci.
Shima yasan hajiya na cikin damuwa. Abunda yake ɗaure mishi kai. Har yanxu taki yarda cewa yarinyar bata Raye.
To abu na kuɗi zai cigaba da ƙoƙari, shima yasamu rabonsa don alhaji yana kashe kuɗi soasi don farin cikin Ameenatu.
Ya dai barrister akoi wani ci gaba,? Yace hajiya dama dai naxo da wata shawara ne.
Mezai hana kikawo hoton ta lokacin tana yarinya Kinga sai a yaɗa, ko za’a dace.
Eh to, barrister, kasan abun lokacin, bamuda hoton ta, abunka da Kauye. Amma hajiya zaki iya tuno yanda fuskar tata yake.
Kwarai kuwa ko a ina bazan taba Mancewa da fuskar BOƊƊI na ba.
Barrister ya kira wo mai zane, Babu ɓata lokaci sai gashi yaxo, Ameenatu na zayyano yanda ɗiyar tata take, kamar tana kallon ta.
An gama zame har color aka saka, lokacin da aka juyo da hoton abun mamaki sak BOƊƊI lokacin tana karama.
Hawaye ne ya ciko idon Ameenatu lokacin da tayi tozalo da kyakkyawar ɗiyar ta.
Tabbas tanaji a ranta zata yi nasarar sake ganin BOƊƊI, kuma Insha Allah tana Raye.
To hajiya yanxu zan tafi da wannan za’a saka a gidan TV da kuma jarida Insha Allah, zamu dace.
Jitayi zuciyar ta ta san yaya, alamun nasara na tin karowa.
Lokacin tashin BOƊƊI daga school yayi koda ta fito taga motar gidan nasu anxo ɗau karta.
Har ta bude baya zata shiga, yace beauty dawo gaba mana.
Laa ya Sayyid Kaine? Nine mana bana ce kitashe zan kaiki school da kaina ba amma kika tafi. Sorry ya Sayyid na makara ne.
Suna tafiya sai surutu take mishi, shi kuma yana biye mata suna shiri Rita.
Koda suka isa gida, Ummu tace oh kun ganku kamar twins, alla dagaskefa Ummu muna kama da ya Sayyid, ina nafiki kyau,.
Ba wani baka finiba. Suka shiga musu, Ummu dai tayi wuce warta tarabu dasu.
To shikenan shikenan, Naji kin fini kyau., ai wasa nake miki, ban isa na taɓa koda ya tsarki a kayuba. Kinji beauty Ummu. Hannun ta ya kama har kofar ɗaki ya buɗe mata kofa tashiga, yace to bye, zanje wani waje. To ya sayyid kataho min da chocolate, OK, saina dawo.
Washe gari BOƊƊI ta shirya da wuri taje ɗakin ya Sayyid bacci yake tayi.
Ta fara buga filon ya Sayyid ka tashi na kusa makara.
Ahan kali ya bude fararen idanun sa wanda suka sha bacci. Akan beauty face ɗinta ya sauke,.
Murmushi yayi yace, thank you, beauty. Tace nameye kuma godiyar, bai bata amsa ba, ta shi, yana cewa.
Kinyi breakfast ne. A’a to kije kiyi yanxu zan fito.
To tace ta juya ta fita.Daidai ta gama ya Sayyid ya fito, kananun kayane ajikinsa, amma sunyi bala’in karbar sa
BOƊƊI ta saki baki tana kallonsa, ido ya kashe mata, murmushi tayi, ta ɗau school bag ɗinta tariga shi fita tace Ummu sai mun dawo.
Har kofar class yara ka ta, kafin suka yi sallama kan zai dawo ya ɗauke ta.
Gidan kaka nunsa ya wuce dake rigiyar zaki, acan ya wuni har lokacin ɗauko BOƊƊI yayi,.
Koda yaje BOƊƊI na zaune da wasu yara da twins, wow beauty ina kika samo wannan fine kids haka.
Wlh yan ɗaki nane, sunan su, Ayan da Ayyana, suna matukar sona.
Sayyid yace ba axo daukan ku bane .
Ayyana sarkin surutu tace eh har yanxu muna jira.
Uncle, dan Allah mutafi tare inason zuwa gidan su, aunty Beauty.
Maganar yarinyar ya burge Sayyid, Ayan shi dama ba mai son surutu bane. Yana shiru abunsa.
Ayyana tace kullum sai na faɗawa mamy amma bata kawo mu.
Sayyid yace karki damu nida kaina zan kawo miki beauty kinji.
To uncle, ta miƙo hannu suka tafa.. Driver su ayyana yafara yin horn alamun ya iso, Ayan yace mutafi ayyana, har sun juya zasu tafi Sayyid yace ;
Baki kwatan tamun gidan Kuba. Tace gidan alhaji Abubakar Genle.
Wow sosai inajin sunan mutumin.
Harsu Ayan suka bar wajen. BOƊƊI na binsu da kallo……….
Abu’ƙaya ce 🤙🥰
🌀🌀 BOƊƊI the beautiful
🌀 🌀
~Free book~
Story and writing
By
Z. B. M.
Yar mutan gombawa
Follow me on what’sapp 09066017177
Whatpad Zainab7177
Gmail [email protected]
Facebook zeenerb bala zeenerb
Message @SABAYA HERBAL on WhatsApp. https://wa.me/message/W7FSXOTK4DT4M1
`` _Bismillahi rrahmani rrahim
_
I dedicated this page to Zaneera amarya, inajin daɗin comments ɗinki, ❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️
PAGE 2️⃣6️⃣🔁2️⃣7️⃣
———————-Bintu tace, laaa Ummu wannan kamar poton BOƊƊI,.
Sayyid ya kara kallon phone ɗinsa tabbas wannan BOƊƊI ce,..
Gabansa ne yafara bugawa cikin sauri-sauri Ummu ta kalli Abbu daya wuce zuwa falon sa.
BOƊƊI da bata fahimci komai ba tace, Bintu poto na kuma?
Kwarai BOƊƊI kigani mana hoton ta nuna mata wanda yake manne a jikin falon, kwarai kuwa.
Nice to menene ya sa kuma ake nuna poto na a TV,
Ummu dai takasa magana ta Mike itama tabi bayan Abbu..
BOƊƊI ta ƙara so ya Sayyid me yake faruwa ne..
Ciki. Karfin hali yace, BOƊƊI iyayen kine suke neman ki….
BOƊƊI da Bintu duk sun razana iyayen ta kuma, Bakin ta na rawa, Sam ta kasa fahimta…
Tashi Sayyid yayi ya nufi falon Abbu, ; to dama wai duk daɗe wanda aka yi BOƊƊI iyayen ta suna Raye.? Ikon Allah kenan Abbu yace….
Ba wani ɓata lokaci suka ƙira number da akasa..
Bugu biyu Barrister ya ɗauka………
BOƊƊI duk bata yarda da abunba,.. Saidai jikin ta yayi sanyi…
Wayar ta ce tayi ringing Barrister, ɗauka tayi jikin ta duk akace jin maganar dayayi yasa ta saurin mikewa.
Tace barrister yanxu ina take, yace; an turo address ɗin cikin garin nan ne.
Yanxu zamuje mu taho da ita.. Wait Barrister, kaxo gida yanxu,….
Sayyid yaƙira farouq awaya ya sanar dashi, ba jimawa sai ga farouq hakan yayi daidai da isowa motocin gidan alhaji Abubakar genle….
Barrister ne yafara fitowa. Farouq ya tsaya kallonsa…
Shima ɗan tsayawa yayi kamar yaso tuna face ɗinnan,..
Sayyid yace Barrister sani!! Kallon kallo,..
Ganin bai gane suba yasa yace sorry inata so natuna amma nakasa,
Farouq yace a hanyar, Adamawa, muka cinci wata yarinya, harr….. Kafin yakara sa Barrister,
Yataho da gudu ya rungume su, wow gaskiya na jin jina muku, kardai itace Wannan damuke nema?…
Kwarai kuwa, farin ciki sosai yakamasu.. To mu ka rasa ciki mana…
Barrister yace tareda Mahaipiyar ta muke, harda mahaifinta.
Fitowar Mamy wato Ameenatu, yasa Sayyid yin turus don idan da Ace wannan ba Babba bace to da yace BOƊƊI ce..
Farace tass ko Ummu da take balarabiya bazata nunawa Ameenatu kyauba saidai abunda ba’a rasaba…
Sayyid da farouq suka musu jagora har zuwa, falon baki..
Sanarwa Ummu da Abbu sukayi sun kara so, sunxo sun gaisa ankawo musu ruwa..
Hankalin Ameenatu duk yana kan BOƊƊI, ita burin ta tasa ta a idanun ta….
Sayyid da kansa yaje yace BOƊƊI suka taho tareda Bintu, shigowan ta yasa Ameenatu ta Mike “Allahu akbar,! Tabbas wannan ɗiya tace wannan yar ciki nane.. Hawaye duk ya wanke idanun ta….
Abun sai kulle wa BOƊƊI kai take nan aka bata lbr komai duk yanda akayi tun daga baran ta har samo ta… Zuwa girman ta…
Ameenatu sai godiya takeyiwa ummu don ta mata abunda Baza taɓa mantawaba…
Sun faɗa musu furera ce ta ɗauke BOƊƊI ya wurgar, sai mamaki sukeyi,..
Ameenatu ta roki Abbu da Ummu kan su bata BOƊƊI ta tafi da ita..
Bayan da suka iya tunda itace mahaifiyarta..
Sukace kuje badamuwa….
Kuka BOƊƊI ta saka wlh don batason rabuwa da Ummu da ya Sayyid ita dai zaman ta tareda su yafi mata dadi…
Ganin haka yasa alhaji Abubakar yace abarta daga baya a hankali zata saba..
Amma ganin yanda Ameenatu take ɗokin ganin yarta yasa Abbu yace su tafi kawai….
Manage pls…..
Masu bukatar karanta book ɗina ko litattafan women writers sai suyi magana ta wannan number 09066017177 💃 💃 💃 💃 💃
🌀🌀 BOƊƊI the beautiful 🌀 🌀
~Free book~
Story & writing
By
Z. B. M
Yar mutan gombawa
Follow me on Whatpad
Zainab7177
Gmail [email protected]
Facebook zeenerb bala zeenerb,
What’sapp
09066017177
Bismillahi rrahmani rrahim
PAGE 2️⃣5️⃣
…………… Harsu Ayan suka bar wajen BOƊƊI na binsu da kallo.
Sayyid ne ya taɓata. Hallo. Dariya tayi ya Sayyid ina son twins ɗin nan, suma ai suna sonki.
Ganin batada niyar tashi yasa shi kama hannun ta ya ɗagata. Har wajen mota, dariya ta fara, ya Sayyid ka maidani bb doll, .
To ai dama ke baby ce.
Awajen Ummu. Laa ya Sayyid kasan da munyi wannan exam ɗin zamu shiga ss2 da gaske, ashe fa yanxu kin bar baby. Daɗi BOƊƊI take ji, wato yanxu itama tazama yammata,
Sai hira suke har suka isa. Koda zata islamiya shiya kaita.
A yanxu BOƊƊI da Sayyid sai dai son barka, ko. Abinci tare suke ci Ummu dai nata ido….
Ummu na zaune a falo tana kallon news Sayyid yaxo ya zauna yana dannan wayar sa suna, hira da Ummu.
BOƊƊI da Bintu na ɗaki sun duƙufa akan waya, suna game. Bintu tace BOƊƊI muje falo, mana, ni yunwa ma nakeji,
Sayyid ya buɗe baki zaima Ummu magana! ABUNDA aka fara has kowa ne a TV yasa shi sakin Baki, kallon kallo suka shiga yi,
Abbu dake tahowa da jarida a hannun shi shima, tsayawa yayi, .
BOƊƊI da Bintu sun fito daga ɗaki suka ga abunda ke faruwa kowa yayi foster, suma sukayi foster…..lol. 😂
Ai kuwa kuma masu karatu sai kuyi foster, don nima zanyi foster anan!! 🤸♀️🤸♀️🤸♀️🚴♀️🚴♀️🚴♀️🚴♀️🚴♀️🚴♀️
Comments ɗinku shine ci gaban book ɗin BOƊƊI 😌
Comments an share pls
Show me luv, 💃🏼💃🏼💃🏼🙏🥰
🌀🌀 BOƊƊI the beautiful
🌀 🌀
NA
Zainab (Z. B. M)
Yar mutan gombawa
Message @SABAYA HERBAL on WhatsApp. https://wa.me/message/W7FSXOTK4DT4M1
Bismillahi rrahmani rrahim
Wannan page nakune yan group ɗin BOƊƊI. Ina alfahari dakuuuu💃🏼💃🏼💃🏼💃🏼💃🏼💃🏼💃🏼💃🏼💃🏼💃🏼 Kuyi yanda kukeso😘😘😘😘😘😘😘😘😘😘😘
PAGE 2️⃣8️⃣🔁2️⃣9️⃣
…………….Bawai Ran BOƊƊI yaso ba, tata shi da sauri tayi ciki, ɗaki tashiga ta kullo kofa,
Ameenatu hankalinta ya tashi, Sayyid ne yabi bayan ta…
Yasamu ta kulle kofar
kuka take, taya za’a ce wai ba Ummu bace maman ta, ina Sam ita baza yarda ba….
To koma menene ita tafin son zama da Ummu fiye da kowa….
Sayyid yafara buka kofar yana kiran sunanta…
Amma shiru
Bata amsaba sai kukan ta da yake juyowa….
Ummu ce taxo tace ya dai Sayyid,.. Ummu kuka take taki bude wa…..
Shikena rabu da ita…komawa tayi taba su hakuri tace dan Allah abar mata BOƊƊI inyaso daga baya sai akawo ta….
Alhaji Abubakar dama bai damuba, Ameenatu ce ta daga hankalin ta…..
Yayi matukar godiya, yaji dadi kuma ya godewa Allah tunda irin wannan gida yarsa ta tashi……
Bintu ce taxo BOƊƊI saiki bude kofar ai sun tafi….
Jin sun tafi yasa BOƊƊI bude wa… Ummu ce ta shigo,..
Beuty ! Meyasa kika ƙi bin iyayen ki,.. Ɗan karamin bakin ta turo gaba, Ummu ni gaskiya nafi sonki…
Ummu tayi murmushin jin dadi tace BOƊƊI Kamar yanda nake sonki ai suma suna sonki sosai….
Kinga yanxu kishiya sai Sayyid ya kaiki,… To Ummu amma dai idan naje zan dawo,… A’a Zaki musu kwana biyu daga nan sai dawo… To Ummu amma harda Bintu zamu je…
Eh kutafi tare shikenan…..
BOƊƊI sai farin ciki take yi zasu tafi da Bintu kuma, zata dawo bayan kwana biyu…..
Koda Suka isa gidan hajiya Ameenatu sai farin ciki take yi, akawo musu wannan akwo wancan, duk ta ruɗe domin farin cikin ganin ɗiyarta……
Kulu wato kakar BOƊƊI, mahaifiyar Abubakar, tace ashe da rabon zan ganki, Hauwa kulu kallon kallo suke waye ce kulu kuma?..
Kukan farin ciki take tace nice ta kwararki wato mahaifiyar mahaifinki..
Sayyid ya mai maita hauwa kulu mejiddah ashe dama haka ne suna beauty..
Ko ina na gidan an nuna musu…
Ayan da Ayyana suka shigo da gudu, saran su kenan kullum kagansu cikin faɗa basa zama waje ɗaya…
Turus sukayi,.. Laaaa aunty beauty!!! Kece? Cikin mamaki BOƊƊI ke kallon su…
Ayyana ta kalli Sayyid,.. Laaaa uncle, ka cika alkawari ka kawo mana beauty har gida..
Yace wow nanne gidan ku?
Cikin zumiɗi tace em mana..
Hajiya Ameenatu wato mamy! Tace; twins dama kun san sune?
Eh mamy sch ɗinmu ɗaya kullum tana bamu chocolate, kuma muyi taɗi….
Masha Allah, wucewa sukayi suna murna beauty taxo.. Abinka da yara basu staya ko inaba sai wajen masu aikin gidan suna basu lbr…
Sayyid yayi sallama yatafi da kewar BOƊƊI har wajen mota suka rakoshi,,, tareda twins..
Bintu dai tana ciki abunda bata fitoba..
Da dare Bintu da BOƊƊI suna ɗaki twins duk sun damesu da surutu…
Mamy ta shigo tace, BOƊƊI taxo abban ta baki ranta, wato alhaji Abubakar..
oh ni zainab ashe zanga wannan rana wanda BOƊƊI zata gana da iyayenta
Bayan mamy ta fita BOƊƊI ta Mike tana yamutsa fuska, Bintu barinaje, zan barki da wannan masu surutun…
Hmm ai kuwa nikam ki barminsu muyi taɗin mu…
Ahankalih ta tura kofar falon wanda take zaton na ABBA ne…
Da sallama tashiga ya amsa cikin fa’a, zata zauna a kasa yace no mama na zauna a gefena…
Tadan matsa ta zauna, kallon ta yayi cikin kulawa, yace; mamana tace na’am Abba, matukar daɗi yaji a ransa…
Yace…………
Comments pls
🌀🌀 BOƊƊI the beautiful
🌀 🌀
NA
Zainab (Z. B. M)
Yar mutan gombawa
Message @SABAYA HERBAL on WhatsApp. https://wa.me/message/W7FSXOTK4DT4M1
Bismillahi rrahmani rrahim
Wannan page nakune yan group ɗin BOƊƊI. Ina alfahari dakuuuu💃🏼💃🏼💃🏼💃🏼💃🏼💃🏼💃🏼💃🏼💃🏼💃🏼 Kuyi yanda kukeso😘😘😘😘😘😘😘😘😘😘😘
Page 3️⃣0️⃣🔁3️⃣1️⃣
…………….. Yace mu iyayen kine kuma, a yanxu kinsan komai game da rayuwar ki…..
Ada munyi kukan rashin ki har mun fidda rai amma da yake Allah yasan komai, cikin ikon sa gashi yadawo mana dake cikin aminci….
Abba yanata bawa BOƊƊI labarin su nada..
Da yanda suka rayu a ƙauye har zuwa yanxu da Allah ya hore musu….
Jikin ta duk yayi. Matukar sanyi…
Nan taji son iyayen nata yafara ɗarsuwa a ranta…
Yaushe ne zakuyi hutu sai muje ƙauye domin kiga tushenki….
Abba saura week daya mu fara exam, OK nashiga aji nawa, tace na ss3 masha Allah mama na 😊 nagodewa Allah nagodewa su Ummu da Abbu, tayi kasa da murya Abba harda ya Sayyid, da ya farouk da suka Cetoni,..
Dariyar farin ciki Abba yayi gaskiya kam ban san dame zan biyasu ba sai dai addu’a,….
Sayyid baiyi aure ba ko eh Abba amma ya gama karatu sa a can Saudi, masha Allah,… Taɗi sosai uba da ya suka yi…
Sai da BOƊƊI ta fara jin bacci tukun tayiwa Abba sallama ta wuce zuwa ɗakin su…
Tuni twins sunyi bacci… Sai Bintu dake fama waya,… Ta takure kanta can jikin gado..
BOƊƊI ta kalle ta, hmmm manya kenan dan Allah da waye kike waya..
Harara ta banko mata ta juyarda kanta… Dariya BOƊƊI tayi oh….
Itama ta ɗauko phone ɗinta tahaye online duk da baccin da take ji….
Ai kuwa tana hawa taga ya Sayyid yana mata Hi!!!!
Mayar mishi tayi.. Sai ga kira video call…
Kamar bazata dauka ba sai kuma ta dauka don yau tana missing gidan su…..
Murmushi ta sakar mishi barka da dare ya Sayyid,.. Yauwa sannu dai Hauwa, Jidderh Beauty
Idan uwa ta fitar ya Sayyid nidai… Ariyan yayi yace kedai me, shagwaba ta fara masa shi kuma ya tsaya yana kallon,..
Asalin Burgesa shagwabar BOƊƊI yake yi…. Ya shaga da kallon ta kamar wanda take kusa dashi
Bintu da tagama waya itama ta juyo ta fara kallon BOƊƊI irin yanda suke yi da ya Sayyid,..
Abun dariya… BOƊƊI ta juyo ta kalli Bintu,.. Bata rai tayi tace ya Sayyid good night,..
Bai mata musu ba yace OK. Bye 👋
Saida ta kashe phone ɗin sannan ta juyo ga Bintu ta murguɗa mata baki, ta Mike zuwa toilet….
Bintu dai BOƊƊI na burge ta don, akoi iya shawaɓa…
Ciki. Dare har BOƊƊI ta fara bacci raji wayar Bintu na ringing….
Bubbugata tayi keee Bintu ana gaskiya phone ɗinki na damuna…..
Tashi tayi cikin maganin bacci tagawo wayar, ya farouq ne tagani..
Wani dogon staki taga, BOƊƊI tace ; madam! ” are you OK, Who’s calling you at this night,”
Bintu tace ya farouq mana bansan me yake nema ba… Oh!! To kiɗauka mana sai kiji..
Bazan ɗauka ba, ah nikam karki mun faɗa ra’a yin kine….
Ta juya ta cigaba da baccin ta,,
…….
…
Abu’ƙaya ce 🤸♀️💃🏼
🌀🌀 BOƊƊI the beautiful
🌀 🌀
NA
Zainab (Z. B. M)
Yar mutan gombawa
Message @SABAYA HERBAL on WhatsApp. https://wa.me/message/W7FSXOTK4DT4M1
Bismillahi rrahmani rrahim
*this page I dedicated to my shugaba jidderh I love you shaaaaaaaa💃🏼💃🏼💃🏼💃🏼💃🏼💃🏼💃🏼💃🏼💃🏼💃🏼 *Kiyi yanda kikeso*😘😘😘😘😘😘😘😘😘😘😘
3️⃣2️⃣🔁3️⃣3️⃣
…………… Yau kwanan BOƊƊI da Bintu Kusan 4 kenan da dawowa gidan su BOƊƊI,..
Sosai Ayanxu suke jin daɗin gidan don sun saba da duk masu aikin gidan, ga hajiya Ameenatu sai abunda suka ce ake yi ta daure musu gindi….
Zaune suke a guarding, ɗin gidan, Ayan da Ayyana suna wasa a gefe, BOƊƊI na wasa da flowers dake zube a ƙasa ta gefen swimming pool!
Bintu kuma sai ɗaukan BOƊƊI photo da video take yi ba tareda sanin BOƊƊI ba…
Bintu tun jiya ya Sayyid bai xoba kuma bai ƙirani ba, yaƙiraki ne…
A’a BOƊƊI kema bai ƙiraki ba sai ni,..
Suna ciki magana kawai suka ji,..
Lalala dole na tura wannan pics, cewar Sayyid dake tahowa ta bayan Bintu…..
Laaa ya Sayyid kasan yanxu kuwa muke maganar ka… Na shiga ciki ai mamy tace kuna nan…
Bintu ki tura mun pic ɗin nan, BOƊƊI tace ya Sayyid wani pics yace, Bintu tayi saurin yiwa Sayyid ido, alamun karya faɗa…
Ya matso kusa yace, to amma zaki tura mun… Saboda kaima nayi….
Dariya suka yi suka tafa… BOƊƊI ta bisu da ido oh yan uwan juna wato warayya zasu nuna mun yanxu…
Suna taɗi banda ni…
Sayyid ya kalle ta yaga ta ɓata fuska, ;yace beauty yau kinyi kyau…
Juyarda face ɗinta tayi alamun fushi oh my God.. Yaje kusa da ita ya kama kunne I’m so sorry, bansan wani laifi nayi ba…
Tace me ka cewa Bintu, dariya yayi… Ce mata nayi yau Jidderh beauty tayi masifar kyau…
Dariya tayi, tace ba wani tana mai ɗiban ruwan s. Pool , ta wasta mishi a fuska…..
Owchh zan rama, ai kuwa ta ɗiba da gudu zuwa ciki,… Sayyid ya fashe da dariya….
Twins ne suka taso, uncle Sayyid, pls ka kaimu Bonbinos. Yace me zakuyi acan? Har suna hada baki, wajen cewa. wasaaa, dariya yayi oh twins iyayen wasa….
Ya Sayyid inaso naje gida fa yau, saboda Kaga Ummu ita kadai mun mata kewa dayawa…
Hakane kam amma kinsan beauty bazata yarda ki tafi ba…..
Eh to ya Sayyid ya zanyi dole tayi hakuri….
To shikenan kije ki shirya sai mu tafi no ya Sayyid kasan idan nace zan ɗau kayana bazata bari ba mutafi kawai…..
Bintu taje ta faɗa wa mamy zata tafi… Gaskiya kam kunyi wa, Ummu kewa. Abun arziki ta haɗa mata… Ta rakota har wajen mota..
Tace ina BOƊƊI, mamy tana ciki, nasan idan taga zan tafi bazata bari ba
Mamy tayi dariya gaskiya kam… Sayyid ya mata sallama, tace ah,.. Ina dai kai kam zakaxo mana hiran dare, yayi murmushi, eh mamy idan nasamu dama zan zo…
Sallama suka yi ya tada mota suka fice…..
Bayan sallar magrib, BOƊƊI ta sauko, domin yin dinner,.. Su Ayan da Ayyana ne kawai a falo,…
Tace , twins ina Bintu ayyana sarkin surutu tace sun tafi da ya Sayyid….
Kutumelesiiiii……….. 😂
Abu’ƙaya ce 🙄
🌀🌀 BOƊƊI the beautiful
🌀 🌀
NA
Zainab (Z. B. M)
Yar mutan gombawa
Message @SABAYA HERBAL on WhatsApp. https://wa.me/message/W7FSXOTK4DT4M1
Bismillahi rrahmani rrahim
Wannan page nakune yan group ɗin BOƊƊI. Ina alfahari dakuuuu💃🏼💃🏼💃🏼💃🏼💃🏼💃🏼💃🏼💃🏼💃🏼💃🏼 Kuyi yanda kukeso😘😘😘😘😘😘😘😘😘😘😘
3️⃣4️⃣🔁3️⃣5️⃣
…………….. Haɗarai tayi wato Bintu tafiya tayi,..
Shikenan daga yau nayi fushi da ya Sayyid…
Ɗakin inna kulu tashiga ta fasa cin abincin ma…
Yau ne karo na farko da BOƊƊI ta fara shiga Ɗakin ta….
Zaune take akan salla ta tana jan carbii…
OH, innah Addu’a kike mana, to ai dole na… Gaki ban aurar dakeba,
Dole na zauna asallaya. Dariya maganar yabawa BOƊƊI… Kiran wayar ta akayi Ummu ce…
Ta dauka he’ll Ummu,.
Sorry my Beauty kawai sai naga Bintu da Sayyid, sun dawo. Ummu ai laifin ya Sayyid ne, amma nayi fushi dasu duka..
Kai gaskiya basu kyau taba… Ummu ta ringa lallashi ta kamar wata baby…
Inna kulu dai sai kallon ta kawai take… Saida ta gama wayar tace oh, kekuwa ai kin girma…
Har yanxu shagwaba kike…. Humm, to ai lokaci nane, naki ya wuce. Oh O, kwarai kuwa yarinya…
Naji Abban naku nacewa zaki kyauye, eh haka dai yace…
To ai kuwa gara, maza ko za’a samo wani acan… BOƊƊI tace, lallefa…
Ta fice tabar inna kulu,…
Su BOƊƊI da twins kullum tare suke zuwa sch, abun burgewa…..
Ranar da suka gama Exam washe gari.. Su BOƊƊI suka kama hanyar ƙyauye…
Sosai BOƊƊI ta gaji don bata saba tafiya mai nisa ba….
Koda suka isa kowa yayi farin cikin ganinsu jama’ar garin Genle duk sai farin ciki suke ….
Har sun gama duk ziya rarsu BOƊƊI taga dangi sosai, abun sha’awa…
Har zasu tafi sai ga wata kayan jikinta duk ayage kamar mahaukaci ya, sai suru tai take…
BOƊƊI data ganta saida ta razana…
Matar ta masto kusa da ita na cewa.. Itace, itace wlh, sai dariya take tana nuna BOƊƊI tana soshe sohen jikin ta…..
Cikin sauri BOƊƊI ta bude mota tashiga, twins tuni suka saka kuka don ganin wannan mata….
Mutanen wajen suka fara korar ta, Alhaji Abubakar ya ciro kudi ya mika mata, cikin sauri ta wafcee..
Wani agefe yace alhaji wannan fa, furera ce..
Ya salam furera sai.. Kwarai kuwa, kasan mijin data aura kamar Boka yake…
To kuma kullum cikin dukan ta yake saboda bata ai huba…
Mahaifiyarta,, taje har gida tamai rashi mutun ci
.
Data dawo gida sai ta kama rashin lfy,,.
Ba jimawa tarasu…. Shine ita kuma furera, tace ai mijin ta ya kashe mata Mahaifiya, tayi yanda ta kashe shi shima, tun daga nan ta haukace…
Acan daji take kwana da safe ta shigo gari ta adda bemu kowa ko rarta yake yi….
Ameenatu ta fashe da matsa nancin kuka , tace alhaji, ba’a biye wa halin mutum dan Allah idan da hali katai make ta…
Shikenan to, hajiya duk yanda kikace..
Zansa azo adauketa ai mata magani….
Ciki al hini suka bar garin Genle suka yi Taraba wajen MLM haruna…
Shima yayi matukar farin cikin ganin Abubakar tareda iya lensa… Yaji dadin samun BOƊƊI da akayi….
Anan suka kwana sai washe gari suka kama hanyar gida wato kano…..
Sayyid sai kiran wayan BOƊƊI yake amma bata picking.. Yaxo gidan kuma basa nan…
Koda ya koma ya tambayi Ummu dariya tayi, to beauty na fushi daku,…
Tunda kaje ka ɗauko Bintu…
Munyi waya suna hanya sunje jalingo….
Hankalinsa ya ɗan kwata…
Zaune take a guarding, ita kadai su twins sun tafi islamiya,
yau ji take rana matukar kewar gidan Ummu, ga ɗakin ya Sayyid mai matukar kamshi,, ji take yau kwana sai gidan Ummu don baza iya ba…
Bayan ta ya hango wow.. Kara sowa yayi yace zan iya zama a gefen ki…
Juyowa tayi tana kallon shi shiba fari bane tasss kuma shiba za’a sashi cikin baƙakeba…
Ba laifi yanada kyau kam kuma alama akoi naira atare dashi……. 😂 😂 😂
Wayyo SAUDE ANGA KUDI.. TACE DAMA Nine……………
Abu’ƙaya ce💃🏼💃🏼💃🏼💃🏼
🌀🌀 BOƊƊI the beautiful
🌀 🌀
Yar mutan gombawa ce 🤙
Message @SABAYA HERBAL on WhatsApp. https://wa.me/message/W7FSXOTK4DT4M1
- Asalin had in gargajiya na Larabawa mai gyara brest da jiki, *SABAYA kowa Nasha amarya uwar gida, mai jego, mai shayarwa, bazawara, yan mata, mai ciki, sirrine na matan Larabawa,.
*Idan kinsha SABAYA jikinki baya saurin lalacewa * * ** *kuma baki saurin tsufa haka zalika mamman ki kullum kmr baki shayarwa
🅿️3️⃣6️⃣⏩3️⃣7️⃣
…………………. Ɗauke idanun ta tayi daga kallon shi.. Ya maimaita can I seat….. Bata jira kara sa warsa ba tayi saurin cewa…
Zauna mana.. Zama yayi yace beauty full,..tayi saurin juyowa tana kallon shi..
Yayi murmushi yace wajen nake nufi ya burgeni… Oho..
Shiru na mintuna suka yi.. Duk BOƊƊI ta takura gashi bata jin daɗin zaman ciki, shiyasa ta fito Siririn staki tayi ta tashi…
Yayi saurin cewa beauty ji mana,… Bata juyo ba ta wuce abunta…
Koda ta shiga falo mamy tana zaune,.. Ah ah BOƊƊI am, yanxu ahmad, yake tambayar ki..
Nace kina guarding, ya ganki kuwa… Mamy waye kuma Ahmad ni banga kowaba….
Yayi dai dai mamy, tare ma muke fa amma kinji wai bata ganni ba…
Juyowa BOƊƊI tayi suka haɗa ido da Ahmad ya kashe mata ido ɗaya…
Mamy tace zonan BOƊƊI am, wannan ɗin shine ɗan gidan, mai gidan mahaifinki ɗan uwan mlm haruna dake jalingo. Lokacin da mahaifinki yaxo Kano gidan su ya sauka…
Murmushi BOƊƊI tayi wanda yabayyanar da kyanta… Murmushi Ahmad ya mayar mata,
To mamy ni zan wuce to Ahmad ka gaida mutanen gidan..
BOƊƊI kiraka ni mana… Kodai ba kya farin ciki da ganina… Mamy ce ta kalle ta,, tayi saurin mikewa.. Domin tara kashi…
Suna tafe yana mata zance gaskiya Ahmad akoi surutu, twins ne suka shigo lokacin driver ya ɗauko su daga islamiya… Ayan ya mikowa Ahmad hannu.. Yace uncle Ahmad two days, ita kuwa ayyana haɗe rai tayi hmmm a’ah my wife yau kuma laifin mai nayi…..
Humm karka kulani….
Tashiga gida da gudu….
OH BOƊƊI kin gani ko my wife kishi take nasan saboda ta ganmu tare ne…
Hummm. Lallefa Sallama suka yi ta shiga ciki abun mamaki tasamu ayyana sai kuka take , mamy kuma sai dariya take…
BOƊƊI ta ƙara so.. Ayyana ta Harare ta.. Mamy tace to yau aunty beauty tayi laifi…
Tace mamy wai Meyasa meta… Cikin dariya mamy tace wai kin kula mata saurayin ta…
Laaaa 🤔 lalle yarinya.. Shirmen banza…
Da Dare BOƊƊI tana kwance ta hau online… Ya Sayyid ne ya mata magana hira suke yi, tana ta mishi mita..
Sai hakuri yake bata..
Kiran ta aka yi a waya… New number.. Koda ta ɗaga muryan Ahmad taji..
Beauty ba kiyi bacci ba? Eh banyi ba… Surutu yake ta mata. Duk yanda taso kauce wa, zance saida ta sake suka sha taɗi har ta fara hamma…
Sallama ta masa tayi bacci. Bata bi takan wayar ba bare taga ya Sayyid, ya ƙare……..
A kwana a tashi, shakuwa sai kara shiga tsakanin ahmad da BOƊƊI.. Ya Sayyid kuma sai a hankali ana Lalla bawa dai….
Abuƙaya ce.
🌀🌀 BOƊƊI the beautiful 🌀🌀
Yar mutan gombawa ce
PAGE 3️⃣8️⃣⏩3️⃣9️⃣
………………….. Zaune take a hara bar gidan motar ahmad ne yashigo… Murmushi tayi oh, Ahmad yanxu kullum sai kaxo gidannan..
Kara sowa yayi.. JIDDERH BEAUTY kina huta warki. Hmmm wani hutawa ne…
Zama yayi gefen ta, yayi shiru tace lfy dai ahmad, kallon ta yayi.. Yace BOƊƊI zaki aureni..
Dariya tayi abun y@ bata dariya, meyesa kika yi dariya, hmm to ai dolene nayi dariya aure fa kace..
Of course, aure BOƊƊI, tace nifa karatu nake yi, yanxu nema zan gama secondry, to menene BOƊƊI… Kaidai kabar wanna. Zancen pls…
Wani zancen ta kawo ta sha shan tarda maganar ahmad shi kuma sai kallon ta yake…
Da dare tana chatting da Ahmad maganar aure yake mata… Tace pls Ahmad kabar zancen nan I’m still a child ban kai aureba…
Dariya yayi pls kidai na wasa, yayi mata magana masu dadi yana sa mata son aure a ranta…
Shikenan to katam bayi Abba na idan ya yarda…
Wani stalle zubairu yayi yace yes nasa meta.. Allah ya mallaka minke BOƊƊI…..
Tuni ahmad cikin zumiɗi yasa narwa mahaifinsa, sunyi matukar murna. Ba bata lokaci suka samu alhaji Abubakar da maganar shima yayi murna yace Allah ya haɗa kansu….
To hajiya kinji labarin Ahmad yana son BOƊƊI zai aure ta…
Ahmad kuma? Eh da akoi matsa lane.. Babu komai kawai nayi wani tunani ne..
Allah ya tabbatar mana da alkhari..
Wai ina ya Sayyid ne… Sayyid na zaune yaji duk kewar BOƊƊI ta kama shi don ya daɗe bai jeba… Shirya wa yayi ya nufi gidan domin ganin ta…
Koda ya isa Hango BOƊƊI yayi tana bude wa wani kofar mota don yashi ga.. Sai fara’a take mishi wani abu Sayyid yaji ya tokareshi… Akirjin sa..
Me hakan yake nufi…
Koda ya isa kasa fitowa yayi daga motar har saida ahmad yaja motarsa.. BOƊƊI bata kula da Sayyid ba , ta juya ta shige ciki abunta…
Fitowa yayi ya shiga ciki.. A falo ya tarar da twins suna wasa oyoyo suka mishi..
Ayyana tace” yauwa ya Sayyid wlh kajawa auty beauty kunne..
Me kuma tayi.. Cikin shagwaɓa irin na BOƊƊI tace wai, Ahmad take so kuma ni yafara cewa yanaso….
Amma saboda ban iya girki da kwalliya ba shine yace wai ita zai aura… Daga baya sai ya aureni..
Cikin bacin rai Sayyid vaisan lokacin da yace wannan ai haukane…. 😂
….. Abuƙaya ce🤙♥️✨
🌀🌀 BOƊƊI the beautiful 🌀 🌀
Story and writing
By
Z. B. M
PAGE 4️⃣0️⃣⏩4️⃣1️⃣
…………….. BOƊƊI data fito daga kitchen tace, welcome ya Sayyid…
Bai wani saki ran saba ya amsa.. Mamy ce ta fito suka gaisa innah kulu ma taxo sun gaisa tace oh yaro mai hankali, ga nutsuwa…. Amma fa cikin ranta….
Bai wani jima kamar yanda yasa ba ba, yatafi hankalin sa duk ya tashi…
Ya ƙira farouq yasa nar dashi wani yana shirin masa kwacefa… 😂
To kaima meyasa baka faɗa mata ba..
GaskiyaKayi wauta..
Shiru yayi abun duk ya dame shi…
Abufa ya kankama Sayyid na sake da baki har ankawo sadakin BOƊƊI…. Ummu ce ta shigo ɗakin Sayyid lfy yau baka fita ba…
Yace Ummu ba komai, wani abu yana damun ka pls Sayyid kasanar dani, wazaka faɗawa inba niba…
Ummu BOƊƊI aure zata yi what Sayyid aure kuma shine bamuda lbr…
Karka damu nasan mastslar ka.. ..
Fita tayi cike da tausayin ɗanta ta daɗe da sanin yana son BOƊƊI yayi dakon so na tsawon lokaci……
BOƊƊI na zaune da twins a falo suna kallo, mamy ta fito itama ta zauna… Kenan suka ji sallamar Ummu, da gudu BOƊƊI ta tashi, tarun gumeta.. Oyoyo Ummu na, nayi missing naki..
Bawani baby na, bayan kin daina zuwa wajena…
Sorry Ummu kinxo tare zamu koma..
Mamy ce ta mata maraba har daki ta kaita.. Amma ta kyakkyawan tarba….
Koda ta tashi tafiya BOƊƊI tace Sam saita bita….
Abu ƙaya ce 🤙
WOMEN WRITERS ASSOCIATION📚
(Domin Marubuta Mata)
✨(W.W.A)✨
https://www.facebook.com/106752595253176/posts/107924965135939/
🌀🌀🌀🌀🌀🌀🌀
BOƊƊI the beautiful
🌀🌀🌀🌀🌀🌀🌀
By zainab Z. B. M
(ƴar mutan gombawa)
“`My beloved dad 😭 😭 😭 😭 I miss you so much but Allah loves you more 😭 😭 😭 😭 😭 😭 😭 😭 😭 😭 Ya rabbigfirli abii, may jannatul firdausi be your final abode… 😢😢😢😢😢😢😢😢😢
PAGE 4️⃣ 2️⃣⏩4️⃣3️⃣
-------------------------Sayyid na kwance a ɗaki Abbu ne yaƙirashi a waya cewar yana son ganin shi...
Tashi yayi ya nufi falon Abbu, yasamu yana zaune yana karatun jarida, dama Abbu ba'a raba shi kullum abun karatun sa jarida...
Akasa ya zauna cikin girmamawa. Abbu yace; yauwa Sayyid dama akan maganar aikin kane, munyi waya da *jaddun* dama Kaine kata kura sai kaxo, don haka ya kamata kakoma..
Shiru yayi Abbu yace Sayyid, magana naje maka.....
Yace Naji Abbu Insha Allah zan koma... That's good... Sayyid ka shirya fa idan zaka koma inaso ka koma tareda matarka...
Cikin sauri yaɗago yana kallon Abbu, ... Abbu nifa banida wanda nakeso...
Murmushi Abbu yayi to Naji, ai saboda bakada niyya shiyasa nida kaina naje na tambayo maka mata..
Naji awa nan da sati biyu za'a ɗaura auren, kafinnan bizan ku ya fito...
Jikin Sayyid ya gama yin sanyi ji yake wata zufa na kokarin ƙaryo masa, tabbas bazai iya jaa da batun Abbu ba...
Ya dai Maleek akoi matsala ne? A'a bakomai Abbu. To tashi kaje Allah ya maka albarka... Mikewa yayi ya fita.
Abbu yabi shi da ido, a fili ya furta Allah yamaka albarka maleek, Allah nagode maka daka axurtani da yaro biyayya,
Ummu ce ta shigo, da sallama,, Abbu yace yauwa dama yanxu zan kiraki...
Labarin auren Sayyid ya bata, Ummu ta jin jina abun,, tace kuma sati biyu, auren BOƊƊI ma fa nanda two weeks ɗinne..
To Ummu ai bikin magaji baya hana nama gajiya...
Duk za'ayi Allah dai yakai mu lokacin.. Numfashi taja tace, ameen..
Sayyid bai kula da BOƊƊI dake falo ba ya wuce abunsa.. Cikin tsokana tace ya Sayyid wato yau ko kallona bazaka yi ba....
Juyowa yayi ya kalle ta,, gani yayi takara masa kyau, gashi ta saka Maroon color kaya Kuma matukar amsar ta yake ya kuma haska ta......
Kirjinsa ne ya buga.. Cikin sauri ya shige ɗakinsa bai ce da ita komai ba...
Bintu dake gefe ta fashe da dariya, a zahiri ita da wayar ta take dariya suna chatting daya farouq, amma BOƊƊI ta ɗau ka da ita take, Hakan yasa ta jin matukar haushi.... Ta bar wajen...
Ummu ta zagefa wajen gyara ɗiyarta sosai BOƊƊI ta ƙara wata fresh domin taba amsar haɗin Larabawa daga Ummu...
Mamy ba yanda taiya domin Ummu ta karbe amarya.... Ga biki sai matso wa yake yi Sayyid duk baya cikin walwala, ga BOƊƊI fushi take yi dashi tsakanin ta da Allah, yanxu ta daina kula shi..
Kai ummu kalli yanda BOƊƊI taketa faman walwali, cewar Bintu..
hmm Kinga na manta yau ko wankan ma batayi ba.. Nidai gaskiya Ummu nagaji...
BOƊƊI am kidaure mana kije Bintu zata ta yaki shafawa gaskiya ni Ummu nagaji abun ƙarni yake mun...
Kai BOƊƊI ba wani bakyaso dai kawai cewar Bintu,
*to ina amare ga gyaran jiki kashi na ɗaya*
*kwanduwar kwai uku.
*manja cokali uku.
*cocumber
*kur-kur
. Kisami waɗannan kayan dana lissafa ko hada su waje ɗaya.. Ki kwaba amma cocumber saikin goga ko ki marka da. Sai ki tace ruwan
Kizuba akai saiki bashi kamar minti goma ko ashirin, sannan ki shafa a jikin ki, kibarshi kamar na hours 1 sannan kiyi wanka da sabulun gaba kona salo...
Sai an gwada, saboda haka na baki ki gwada sati ɗaya, za Kisha mamaki......
Mutare a page na gaba.. Nima na gaji Allah Allah nake naxo karshe.... 😂
Abuƙaya ce
*WOMEN WRITERS ASSOCIATION*📚
_(Domin Marubuta Mata)_
✨(W.W.A)✨
https://www.facebook.com/106752595253176/posts/107924965135939/
🌀🌀🌀🌀🌀🌀🌀
_BOƊƊI the beautiful_
🌀 🌀 🌀 🌀 🌀 🌀
NA zainab. Z. B. M
_Yar mutan gombawa_
PAGE 4️⃣4️⃣⏩4️⃣5️⃣
........... Shagali biki fa saura kwana biyu....
Ahmad yaxo Suna taɗi da BOƊƊI, yanda bikin zai kasance..
Sayyid yana hango su ya ɗauke kansa ya shige ciki.. BOƊƊI dai abun ya bata haushi wato ya Sayyid yanxu ya daina kula ta..
Ahmad ne ya kula da mood ɗinta ya sauya.. Yace lfy Beauty, murmushi ta kakalo bakomai inason shiga ciki ne..
Ya kuma bamu gama magana ba zaki tafi.. Tace mu ƙarasa ta waya kawai.. Bata jira amsar sa ba ta shige ciki...
Da ido yabita bai damu ba.. Ya shiga motar sa yatafi burinsa kawai BOƊƊI ta zamto matarsa...
Washe gari aka yi walima amarya taji kyau iya kyau...
Sayyid shi ko hidimar bikin sa ba abunda yake yi.. Har yau bai san wacece amaryar saba kuma bai tambaya ba..
Domin ji yake kamar ba shi bane duk duniya tayi masa zafi....
Shiga Ɗakinsa yayi yarufe kansa hatta wayar sa kashe ta yayi domin ji yake kamar zai bar duniya...
Ummu duk tana kula da lamarinsa hankalin ta yayi matukar tashi...
Abbu tasamu tasa nar dashi halin da taga Sayyid ya shiga...
Murmushi yayi ki rabu dashi domin ba a'a fasa wannan auren ba.. Nayi niyya..
To alhaji pls kasanar dani wayece amaryar har yanxu ba wani abu daya haɗamu da gidan amarya.. Kuma gobe ake shirin ɗaura aren..
Karki damu babu ruwan ki a wannan zance kedai kiyi addu'a. Allah yasa ayi asa'a, . Ameen ummu tace jikin ta duk yagama mutuwa...
Daki tadawo ta ɗauki waya taƙira Mamy....
Kafin na isa gidan mamy har sun fara magana da Ummu maganar tayi nisa don na tsinkaye ta ne 😂
Jinayi tana cewa, Ummu banida yanda zanyi ne... Amma alhaji koda na masa magana saidai yamun dariya yace nayi addu'a Allah yasa haka shi yafi alkhairi.. Kinsan da inada hali to danasa abun nan ya tabbata...
Kuma bayan da zanyi shima Ahmad iyayen sa sunyi mana rana sosai,, bazan iya kin jinin suba..
Ummu kiyi hakuri zabin Allah Shine daidai.....
Gidan ya cika da mutane kota ina saboda haka sai side ɗin Abban ta Takoma tareda Bintu.. Da yake BOƊƊI batada wasu kawaye....
Kwance take akan gado fuskar ta na kallon sama.. Bintu sai magana take mata tana stokanarta amarya....
Yanxufa ana can saura mintuna a ɗaura.. Gaban tane yayi mummunar faɗuwa ga ahmad tun dazu sai kiran ta yake amma taki ɗauka...
Wasu hawaye masu zafi suka fara gangaro wa a fuskar ta...
Wasa gaske kuka kam yadawo babba,, lfy BOƊƊI kiyi shiru mana, dan Allah kiyi hakuri amma sai kara sauti takeyi..
Can tafara cewa Bintu wlh bana son wannan aure na tsani Ahmad ko an auramun shi bazan iya zama ba..
Mamy dake kokarin shigowa tace meee kikace.. Lalle kuwa, BOƊƊI karki Mana haka pls.. Cikin gunjjn kuka tace wlh mamy bazan iya rayuwa dashi ba..
To yau ni Ameenatu BOƊƊI waye to zaki iya rayuwa dashi... Cikin sauri bajin kunya,, tace ; many ya Sayyid,! Ya Sayyid kadai zan zauna...
Ohohoho yau ake yinta...
Tsananin ciwon kai yasa Sayyid ko ɗa kai ba yayi.. Tun safe farouq yake nema Sayyid amma ina wayar bata shiga...
Da kyar yasamu yasha magani amma ina abun ba sauki... Allura yayiwa kansa na samu relief, ba jimawa kuwa bacci ya ɗauke shi.....
Karfe 11:00 jama'ar annabi suka shaida ɗaurin auren *Sayyid maleek Ibrahim* tareda amaryar sa wato, *Hauwa'u jidderh Abubakar* ..................
I nah kulu ta leƙo kanta...............
😂 😂 😂 😂 😂 😂
Abuƙaya ce
I'm not feeling fine pray for me pls
🌀🌀🌀🌀🌀🌀🌀
_BOƊƊI the beautiful_
🌀🌀🌀🌀🌀🌀🌀
By zainab Z. B. M
_Yar mutan gombawa_
PAGE 4️⃣6️⃣⏩4️⃣7️⃣
Ubangiji ka kare mun Mamana, ka ƙara mata lfy da nisan kwana, Allah yabi yaki da gidan aljanna, mom 🥰 heart ♥ 🍀 I can’t thank you enough for what you have done for me 😍 💕 loml 🔐 💖🌼 ina Ƙaunarki Ummi na…
----------------ameenatu saiki xo ana ƙiranki..
Tashi tayi jikinta duk ya mutu...
Koda ta fito yana falon dama falon babu kowa....
Fuskarsa da murmushi mai kayatar wa.. Masha Allah hajiya ameenatu! "yaudai burinki ya cika domin na aurar miki da,
Ɗiyarki wacce kike matukar ji da ita.. Wato Hauwa'u,, na aura mata Sayyid wato maleek..
Kallon sa tayi cikin sauri yace kwarai kuwa.. Kina mamaki ta yanda hakan ta kasance...
To abunda ya faru shine..
An ɗaura auren Ahmad da wacce za'a aurawa Sayyid saboda, duk yaran abokin mune.. Kuma ya rinya ce mai biyayya, dama Sayyid na zaɓin mahaifin tane...
To kuma kena naga kina matukar son hada zumunci da su Sayyid, kamar yanda Ummu itama take fata..
Saboda haka munyi wannan canji ne saboda hakan kamar yafi da cewa...
Kuma ina fatar yaran zasu yi mana biyayya...
To alhaji Allah yasa hakan shi yafi alkhairi...
Cikin zumiɗi mamy ta ɗau waya taƙira Ummu, sun yiwa juna murna da fatan alkhairi na haɗa zuri'a da suka yi.. Sosai Ummu ke cikin farin ciki...
Mamy ce ta shiga dakin da BOƊƊI take, wani kallo ta mata abun kunya kinji jiki wlh...
Yaran zamani wai har kinsan soyayya... Ta wuce tayi tafiyar ta, tana dariya kasa kasa
Mamaki ne yakama Bintu da BOƊƊI, Meyasa mamy ta sauya yanxu-yanxu.. Bayan yanxu take rarrashin BOƊƊI....
Sayyid lfy wai ka buɗe kofar mana cewar farouq dake tsaye bakin kofar dakin.. Don wayarsa bata shiga... Ummu tace sai kayi azama domin tun safe ya rufe kansa narasa meke damun sa.. Ai yanxu kam saiya buɗe tunda burinsa ta cika...
Murmushi farouq yayi, ya cigaba da bugawa...
Sayyid yana jin bugun kofar amma da kyar yasamu tashi ya bude bai duba ko wayeba ya juyo yayi kwanciyar sa, don har lokacin allurar bata sake shiba...
Farouq yace ango yana ganka haka.. Wani takaici ne yatasarma sayyid...
Hmmm ina Maka magana saina fasa faɗin albishir ɗin... Sayyid bai damuba domin ba sosai ma yake jin zance farouq ɗin ba...
Maganar da yaji ne yasa shi dan kallon farouq, kwarai kuwa Sayyid burinka ya cika domin Abbu ya nema maka auren BOƊƊI an ɗaura a yau ɗinnan,
Hmm to mara hankali haka Sayyid ya furta cikin muryar rashin lfy....
I swear to God, Sayyid yau BOƊƊI ta zama mallaki ka, an ɗaura muku aure idan baka yarda ba, muje ka Tam bayi Ummu da Abbu..
Sayyid bai jira maganar sa ba ya Mike jikin sa na bari duk ya mance da ciwon dake damunsa...
Gaban Ummu yazuve fana kallonta da wannan fararen idanun nasa... Murmushi tasa kar mishi tasan abunda yake nufi, kai ta ɗaga mishi alamar eh.
Fada mishi duk yanda aka yi tayi matukar dadi Sayyid yaji shi, burinsa yau yacika....
Agurin ya dur kushe yana jerowa Ummu godiya da Larabci....
Haka ya Mike cikin sauri ya rungume Abbu shima yayi ta jero masa addu'a dakuma godiya... 😂
*Mara kunyar yaro ko kunya babu. Inji Saude ne... 😂 To baniba*
What ya farouq me kake cewa? Kwarai kuwa Bintu an ɗaura auren Sayyid da BOƊƊI, ina ban yardaba shi kuma Ahmad ina yake..
Eh Bintu shi kuma an aura masa matarda za'a aurawa sayyid tunda duk abun na gida ne, dama itama yar abokin su Abba ne...
Wani stalle tasaka daga inda take, ta rungume BOƊƊI, to burinki yacika an aura miki ya Sayyid,,
Gaban tane ya fadi me kike cewa Bintu, fada mata duk yanda suka yi da farouq yanxu ta online tayi,,.
Taɗan yarda amma ba sosai ba...
Inna kulu ce ta shigo, tasamu suna musu.. Tace ke kinsamu kin auri mai hankali irin wannan ɗaaa Harkina karya tawa...
Wai dan Allah in ah da gaske ne... Hmmm yarinya sai kiyi kuma...
Wasu hawayen farin ciki ne suka zubo mata,... 😂
*To meye na kuka banda iyayi* _oh ni Abu'ƙaya bakina baya shuru_
Labarin bikin Sayyid da BOƊƊI ya zaga gari da media, kota ina ansan ɗan Gidan alhaji Ibrahim, ya auri yar alhaji Abubakar genle...
Feeyna! Feeyna! Anya kuwa kinji abunda nakeji yanxu,,
Kaji hanee da shirme me kuma ya faru.. Hmmm
Kece uwar shiririta wai an ɗaura aurenki da Ahmad, shi kuma naki angon an baiwa wata, wanda ahmad zai aura...
Wata uwar a shariya Feeyna ta doka,, Kutt idan wannan zance yayi Allah ya mun albarka,,
Saboda anga nayi shiru shine za'a a juyani kamar wata waina a tanda...
Afusace ta ranka ya ga momyn ta.........
Yanxu dai wato ahmad ban isa na yanke hukunci akanka kuma yayi ba ko? Cikin wata irin muryar bacin rai ahmad yace ina dad bazan iyaba BOƊƊI nakeso itace life ɗina..
Kuma ita kadai nayi niyar aure ba wata ba.......
_Yaune ake yin ta....._
LOL 😂 😂 😂 😂 😂 😂 😂 😂 😂 😂 😂 😂 😂 😂 😂 😂
Follow me...
Comments pls domin comments naku shizaisa ni cigaba da typing
*WOMEN WRITERS ASSOCIATION*📚
_(Domin Marubuta Mata)_
✨(W.W.A)✨
https://www.facebook.com/106752595253176/posts/107924965135939/🌀🌀🌀🌀🌀🌀🌀
_BOƊƊI the beautiful_
🌀🌀🌀🌀🌀🌀🌀
NA
Zainab Z. B. M
_Ƴar mutan gombawa_
PAGE 5️⃣0️⃣⏩5️⃣1️⃣
---------------------- Oh BOƊƊI ke kuma abincin shine sai a kitchen,. Cewar Bintu...
Wani ajiyar xuciya ta sauke...Bata kula Bintu ba, taje sink ta kunna fanko ta wanke hannun ta...
Shiga dakiTaji Sayyid yace beauty, xo kiji, kaii nikam gaskiya ya Sayyid ka dameni..
Dariyar yayi, na dameki, kamar yanda kika damu kanki, a kitchen,.. 😂 Dariya yayi, daidai lokacin Bintu taxo itama zata shiga daki.
Idanu BOƊƊI ta zuba mata, Bintu ko ta kashe mata ido.. Ta shige daki ta turo kofa...
BOƊƊI bata kula Sayyid ba da yake ta smile, juyawa tayi zata shiga dakin.. Taji Bintu ta rufe kofa kam..
Bubbugawa take Bintu ta ɗan bude kadan ta leko, lfy kike buga mun, akoi wani matsala ne....
Wani kallo na rashin fahimta BOƊƊI ke bin ta.. Kafin tayi magana tuni Bintu ta mayar da kofar ta rufe...
Kutttt.. Tana cikin wannan mamakin taji Sayyid ya kama hannun ta... Shork taji da sauri ta kwace,, zo mutafi mana,. Kallon rainin hankali ta masa ina zamu.... Kince bacci kikeji....
Ya Sayyid to Wai kana nufin a dakin ka zan kwana!? Of course. Tunda Bintu ta hana ki kwana... 😂 Wani bakin ciki ne ya kamata wlh nikam bazai yiwuba, dakin Ummu ai zan tafi.
To shikenan fatan nasara, ya juya ya shiga dakin sa...
Ummu na shirin kwanciya, BOƊƊI tashigo sai rakube rakube takeyi , Ummu ta kalle ta, beauty ba kiyi bacci ba...eh Ummu Bintu ta rufe daki dariya Ummu tayi...
To zoki zauna, wani cup ta dauko ta mika wa BOƊƊI ki shanye wannan.
Ummu na koshi, nasani ai madara ne fa, kuma nasan zata miki dadi, kamar yanda kike sonta..
Karba tayi takai baki ai kuwa tass ta shanye, ta dago Ummu da dadi Allah ko, eh to gobema zan baki,. Dariya tayi tana mai kwanciya kan gadon..
Ummu tace BOƊƊI ki tashi ki tafi wajen Sayyid mana... Idanu ta fito dasu ummu wajen shi kuma....
Ganin yanda tayi yasa ummu ta kamo hannun ta...
Kinga yanxu ke kinyi aure kuma Sayyid shine mijinki duk abunda yace kiyi shi zakiyi,, *Hauwa'u jidderh* shifa aure ba wasa bane, yanxu baka Mar da kike ba....toni ummu,, ke meye, Kinga yanxu ki taso muje, wani humrah mai bala'in kamshi ummu dakanta ta shafawa BOƊƊI, ita kuwa da bakin ta baya shiru Ummu wannan fa... Bata ce komai ba,
Hannun ta, takama har kofar dakin ta kaita...
Tace kishi ga, ummu to idan ya koroni fa, dariya Ummu tayi saiki dawo wajena...
Ummu ta juya abun ta tana dariyar BOƊƊI...
Saida taɗan tsaya kadan kafin ta tura kofar ahankali, tashiga Bakowa a dakin alamun Sayyid na toilet saboda taji karar ruwa..
Daida ta karewa dakin kallo sannan ta wuce zuwa kan gado ta kwanta ta dukun kune cikin bargo....
Sayyid daya fito bai san cewa BOƊƊI na nan ba...
Amma dai yaji kamshi na tashi... Fara duba turarukan dake kan mirro yayi amma naiga wani alamun sun fashe ba....
Shiryawa yayi ya saka kayan baccin sa.. Ya hauro gado domin kwanciya...
BOƊƊI da bacci ke ta faman san danta, amma taki sakin jikinta tayi baccin..
Har zai kwanta sai ya saka hannu ta kusa da gadon ya dannan wani ma danni sai wutan dakin ya ɗauke.. Bargon ya fara jaa wani kamshin yakuma bugan Hancinsa yace oh god........
*OH God nima na gaji*
Abu'ƙaya ce 🥰🥰
*WOMEN WRITERS ASSOCIATION*📚
_(Domin Marubuta Mata)_
✨(W.W.A)✨
https://www.facebook.com/106752595253176/posts/107924965135939/
🌀🌀🌀🌀🌀🌀🌀
_BOƊƊI the beautiful_
🌀🌀🌀🌀🌀🌀🌀
By zainab Z. B. M
_Yar mutan gombawa_
PAGE 4️⃣ 8️⃣⏩4️⃣9️⃣
------------------a fusace mom ɗin Ahmad tace wlh baka isaba yazama dole ka zauna da *feeyna* domin itace zaɓina,.
dama ni sam waccar yarinyar bata min ba kuma bata dace dakaiba wannan itace zaɓina..
Ahmad ransa yayi matukar ɓaci haka ya fice zuciyar sa kamar zata fito..
Da dare anxo daukar amarya mamy batayi wa BOƊƊI fadan komai ba saboda tasan Ummu zata kula da komai,.
Hankali kwance aka dau amarya aka kai gidan Ummu.. 💃🏼
*Wai kuji saude tace abun baiyiba ka girma agidan kuma akai auren ka gidan 😂 😂*
*Shine morewa mamana*♦️ kudai muje zuwa...
Amarya jikinta dai yayi sanyi, amma ko kuka batayi ba 😂 bayan yan biki sun watse nace nikam ina ya Sayyid ne..
Can na hango Sayyid gaban sallaya yana ta mikawa uban giji godiya...
BOƊƊI dai tuni ta yage kayan dake jikinta don ji take kamar ma, ba aure tayi ba..
Sai zuba taɗi suke da Bintu, Ummu ne ta shigo, ta fara'a, tace; beauty, kunci abinci kuwa... Eh Ummu banajin yunwa.
To Tace ta juya abin ta...
Dakin Sayyid ta leka lokacin yatashi kan sallaya, ganin Ummu yasashi yin kasa da kansa,.
Eh mna irin anyi aure.. 😂 Lol
Ummu ce ta kalle shi cikin kulawa Sayyid yaya jikin Naka, da sauki ummu, OK kaci abinci ne.. A'a Ummu abu mara nauyi nake bukata...
OK to barina sa BOƊƊI ta kawo maka..
To Ummu, ta juya ta fita,.. Wani smile yayi Najin dadi..
BOƊƊI na kwance bacci ne keson daukar ta, Bintu tace ke tashi, karki dameni pls na gaji...
Ummu ce ta kuma shigowa dauke da tray na abinci, BOƊƊI kinyi bacci ne, mikawa Sayyid wannan, inaso naje na haɗa wa Abbu abincin sa yadawo...
Batayi musu ba ta Mike ta amsa... Ta fita.. Cikin faɗuwar gaba ta tura kofar dakin,
ji take kamar yau ne karo na farko da zata fara ganin Sayyid...
Sallama tayi ya amsa ciki ciki, ta ajiye tajuya zata fita..
Da katar da ita yayi.. Ta hanyar kiran sunan ta.. Juyowa tayi ranta a matukar bace..
Ganin yanda tayi yasashi haɗe fuska.. Ummu da tace kikawo mun, haka tace kiyi..
Juyowa tayi ta ɗau plate din ta zuba abincin aciki ta cika plate din, Sayyid da hankalin sa yake kan wayar sa...
Gani kawai yayi an ɗaura masa abinci akan cinyar sa...
Mamakin ganin yanda ta shake plate din.. Murmushi yayi, yadan kalle ta, yace ;good kema kina jin yunwa ne..
Nikam bana jin yunwa, to abincin da kika saka nida waye... Baki ta kuma turowa.. Hakan ba karamin kyau ya mata ba.. Sayyid ya sauke plate din ya ajiye a kasa..
Bata an karaba ji tayi yajawo hannun ta ta fado gefen sa a zaune... Wayyo ya Sayyid zaka ballani...
Ashe yarinyar tasan sunana, ya faɗa cikin yaren Larabci..
Afili ta furta I'm not a child, dariya yayi to bari mugani ko da gaske ne...
Cikin sauri tayi baya, dariya yayi kidai yace ya dai ya Sayyid inajin bacci har na fara Ummu ta tashe ni...
To gashi kuma alamu sun nuna kinajin yunwa..
Nikam banaji..
To wannan abincin wazai cinye.. Dauko abincin yayi ya, yafara ci...
Bai kula BOƊƊI ba ita kuma bata motsa ba daga inda take, amma ta zuba mishi idanu.
Domin salon da yake cin abincin ya burge ta... Duk yana kallon ta.. Amma bai kulata ba saida yayi rabi tukun ya yace;
To matso kema kici naki don yanda ake ta kallona yau idan ban baki abincin nan ba, zakiyi mafarki...
Idan uwa ta zaro.. Allah kuwa nikam na koshi ya Sayyid.. Ina dole fa saikin ci tunda kika saka da hannun ki.
Zata masa gar dama.. Sayyid ya daure fuska ganin babu wasa yasa ta.. Kar ban plate din cikin sauri..
Da kansa ya dau spone din ya fara bata abaki...
Da kyar take bude bakin.. Duk wai cikin yanga, amma fa a gaskiya tana matukar enjoying, abincin don ya mata dadi 😋...
Sayyid duk yana kula da ita, ya kara ɗebowa har ta bude baki zai sama ta, sai kuma ya fasa ya, dauke plate din daga gareta, ya koma gefe ya cinye sauran abunsa.. 😂
BOƊƊI baka Ramin haushi abun ya bata ba..
Kallon sa kawai take, domin gaskiya abincin bai ishe taba..😂 *Kaji yar..*
Saida ya cinye tas yasha ruwa, yace da ita fitar da kwanukan batare da ya kalle ta Ba..
Tashi tayi ta dauka kitchen ta nufa.. Ai kuwa tana shiga kitchen ɗin ta bude kular, ko cokali bata dauka ba... Da yake ba yawa abunda ya rage.. Loma ta fara wurga wa.. Abin dariya, nan danan ta cinye ta sude hannun ta tass..
Motsin da taji a bayan ta yasa sauri juyowa sannu ko..... 😂 😂
Waye ne to!? .. 😂 😂 😂 😂 😂
Abu'ƙaya ce 🥰😘
*WOMEN WRITERS ASSOCIATION*📚
_(Domin Marubuta Mata)_
✨(W.W.A)✨
https://www.facebook.com/106752595253176/posts/107924965135939/🌀🌀🌀🌀🌀🌀🌀
_BOƊƊI the beautiful_
🌀🌀🌀🌀🌀🌀🌀
NA
Zainab Z. B. M
_Yar mutan gombawa_
PAGE 5️⃣2️⃣⏩5️⃣3️⃣
_______________
Adai dai lokacin yaji motsin BOƊƊI cikin sauri ya kai hannun sa tayi maza ta rike.. Murya na ɓari ya Sayyid nine,,
Wani numfashi ya sauke tareda murmushi mai sauti, Oh wato shine zaki tsoratar dani..
Lalle ya rinya. Wayyo nifa ba yarin ya bace....
OK ke ba yarinya bace To me cece,? shiru tayi..
Kara sa shiga cikin bargon yayi ya rufe su gaba daya...
BOƊƊI tace;! nikam ya Sayyid ka sauka,.
ah lallaifa nida dakina Kice na sauka to na kwanta a ina...
Ka kwanta a ƙasa.. Tab bani iyawa wallah ai jikina tsami ya kayi....
Dariya tasaka jin yanda yayi maganar kaima ashe ka iya irin maganar ah to, munti nawa ne...
Wata dariyar ta kuma yi...
shiru tayi jin ya run gumeta, ta baya... Pls ya Sayyid ka sake ni...
Kitsaya pls ba abunda zan miki kamshin kine yamun dadi inason inji...
Shin shina wuyan ta ya fara yi, duk jikinta bari yake... Cikin wata murya yace Calm down kinustu ba abunda zan miki I promise you, kamshinki kawai zanji....
Duk da abunda ya faɗa BOƊƊI bata yarda ba... Saida taji ya juyarda kansa, ...
Tashi tayi cikin sauri zata sauka kasa... Ya riko ta...
Ina zakije? zan kwanta a kasa ne...
A'a kiyi kwanciyar ki anan karki damu ni zan sauka...
Kwanciya tayi shi kuma Sayyid ya kwanta akan sofa, ba jimawa bacci yayi gaba da BOƊƊI Sayyid dama yana kula da ita...
Maganar gaskiya bazai iya kwanciyar kasan ba.. Saboda haka ya tashi ya koma gadon yayi musu addu'ar bacci ya fasha...
Yaja bargo tareda rungume BOƊƊI ya ci gaba da sha kar kamshinta.... *Asuba ta gari....*
Feeyna wai nufin ki, bazaki tare ba. , kwarai kuwa hanee wlh bazai yiyu ba.. Taya zasuyita bugani kamar wata ball,
Ance ga wanda za a aura mun sai da nagama falling in love with him sannan ace wai an sauya...
To Feeyna wan can din kin ganshi ne kwarai kuwa inada pictures nasa... Mu gani,
phone ɗinta ta dauka ta nuna wa hanee kawar tata, wow! gaskiya he's so handsome, kinyi missing wani ta kaici ya kara kama Feeyna,...
Suna cikin haka sai ga kanwar Feeyna ta shigo, aunty Feeyna kixo inji dad...
Bata jira amsar yar uwar tata ba ta juya abun ta...
Kai gaskiya hanee ba inda zani, bana bukatar kallon dad ɗin ma yanxu....
Haba Feeyna saikin daure ai kije mana ai baki san meye zai ceba...
Da kyar ta lallabeta, to amma kinyarda tare zamu je... Eh muje mana...
Falon dad ɗin suka nufa.. Sun sameshi zaune da Ahmad daya hada rai yana danna wayar sa..
Yauwa feeyna wannan shine Ahmad wato mijin ki...
Kallon sa tayi taga shi ko dago wa baiyi ba, tabbɗi jam, dagani shima baya bukatar wannan aure ai kuwa bazata yiwuba... Hanee ta sunkuyo cikin dabara tace feeyna shima ai babu laifi yanada kyau, kuma da Alama akoi cash.. Feeyna ta ya mutsa face kai ba wani komai wancan tafisa...
Dad ne yayi gyaran murya, kana ya muke ya kalli hanee kawar feeyna to saiki basu waje su tattauna....
Mikewa tayi tana mai xun gurar kafar feeyna,
Feeyna ta tashi ta koma kujerar dake gefen Ahmad, hello, da giwa yayi ciki. Second kadan ya kare mata kallo, ba laifi ya furta a fili...
Feeyna ta kalle shi, tace malam zaka ajiye phone dinne muyi magana kodai... Kallon ta yayi inajin ki...
Numfasawa tayi to da alamu kaima bason auren kakeba kamar yadda nima banida ya'ayi..
Yace kwarai kuwa, hmmm feeyna tace bansan Meyasa iyayen mu suka yanke mana wannan dayan hukun cin ba...
Saboda ni gaskiya na riga da na fara son, Sayyid maleek, kallon ta yayi bakiji da kika am baci Sayyid sai naji wani ta kaici ba, domin a yanxu shine ya auri.
Wacce take a birnin zuciyata wato BOƊƊI, maimai ta sunan tayi, take taji tsanar BOƊƊI ya darsu a ranta...
Wato itace Taraba ta da Sayyid, kallon sa tayi, cikin fushi idan kana tareda ni yazama dole mu dau fansa, akan su... Cikin sauri ahmad yace, amma saidai akan Sayyid don ban yarda wani abu yasamu BOƊƊI ba...
Cikin hasala feeyna tace Itadai domin Sayyid nawa ne....
Nan abun yaso zama musu babba, Hakan yasa feeyna tashi ta wuce zuwa ciki zuciyar ta kamar zai bullo...
Gari ya waye Sayyid anji dadin bacci domin kuwa ya makara,, BOƊƊI ce ta farka, jikin tayi dumu dumu a jikin Sayyid,.. Motsi ta fara yi tanason kwace jikin ta...
Amma ina duk ya kanannaye ta... Cixo taso kai mishi amma ina babu halin yin hakan harshen ta tafito dashi ta fara............... 😂 😂 😂
Abuƙaya ce 😘🥰
Share and comment saboda Allah.....
♥️ ♥️ ♥️ ♥️ ♥️ ♥️ DAN ALLAH DUK WACCE TA KARANTA BOOK ƊIN NAN TAYI KOKARIN COMMEN SANNAN TAYI SHARE ƊINSA ZUWA WASU GROUPS ƊIN.
DOMIN AIKA SAKO KAI TSAYE ZUWA GARENI 👇
[email protected]
Or
09066017177
Call or chat......
Thank you 😘 🥰 🙏 💖
🌀🌀🌀🌀🌀🌀🌀
_BOƊƊI the beautiful_
🌀 🌀 🌀 🌀 🌀 🌀
NA zainab Z. B. M.
_Yar mutan gombawa_
PAGE 5️⃣4️⃣⏩5️⃣5️⃣
_________________________________
✨ ✨ ✨ ✨ ✨ ✨ ✨ ✨ ✨ ✨ ✨ ✨ ✨ *Happy eid El khabir, taƙabbalalla Hu minna wa minkum* 🪄🪄🪄🪄🪄🪄
Cixo taso kai mishi amma babu halin yi hakan, harshen ta, ta fito dashi tabude maƙo goro tasa kara, ai kuwa cikin fir gici SayyidYa sake ta tareda rufe kunnen sa, domin har cikin kansa yaji karan...
Cikin sauri ta sauko daga gadon. Murmushi Sayyid yayi oh Meyasa kika yi kara, baki ta turo bata kula shiba ta Mike domin fita daga dakin, tana zuwa kofar taji a kulle ta juyo ta kalli sayyid daya mike yashige toilet abunsa....
Cikin jin haushi Takoma ta zauna a kasa daɓas tahaɗe face, koda Sayyid yafito kallon ta yayi yaga yanda tayi zaman ƴan bori abun ya bashi dariya,..
OH yau kuma baby na abunda muka tashi dashi kenan, 😆 ganin yanda takara hada fuska yasa shi kara sawa, wajen ta..
Meya faru baby na,, nidai ba bbyn ka bace, to bbyn waye inba nawa ba?
NA ummu, oh to Naji, kije kiyi alwala kixo kiyi sallah, yanxu ma gashi mun kusa makara,.. ya sunkuyo da bakin sa saitin kunnen ta yace, saboda yanda na kwana shakar kamshi...
Cikin sauri yashige toilet din yana mata dariya...
Tare suka yi sallah sukayi karatun Quran,bayan sun gama BOƊƊI tace ya sayyid ka bude mun kofa inje in gaida ummu...
Hmmm BOƊƊI kenan baki gaishe dani mijin kiba amma zakije gaida ummu, tashi yayi ya nufi gado yazauna a gefe tamike itama taxo gaban sa ina kwana ya Sayyid,..
"hannun ta ya kama ya zaunar gefen sa yace, kibar gaisuwan tunda ba kiyi niyya ba....
Yau kwana nawa rabon daki gaisheni...
Ahan kali tace to ya Sayyid Kaine kadaina kulani ai cikin kwana kin...
OH to ina gani wani zai kwace mun ke ba dole nashiga wani hali ba...
Cikin mamaki ta kalle sa mekace ya Sayyid, tunda bakijiba ya wuce....
Dariya tayi to ya Sayyid ka bude mun ta fita pls.. A'a ba zakije ko ina ba yanxu, muyi bacci,...
Ido ta zaro bacci fa kace yes bacci.. Ya kamo ta zata mai gardama ya kwantar da ita shima ya kwanta ta fara mita axuciyarsa kai beauty ta fiye mita...
Kanta yafara shafawa kamar wata bby domin so yake tayi bacci, ita kuma jin yanda Sayyid yake mata yasa ta rufe idanu..... Kamar tayi bacci can kuma tace kaii nikam ya Sayyid I'm not felling sleeping.. Jin shiru yasa BOƊƊI juyowa domin kallon face ɗinsa..
Gani tayi kamar yayi bacci hakan yabata damar mikewa,, direct wajen da take tsammanin keys ɗin suke ta nufa...
Cikin sa'a tasamu nasarar dauka.....
hanee! kinajin yanda mukayi da guy dinnan, to feeyna kiyi hakuri, yaka mata ku nustu kusa mu solution ɗin problem naku, to ya zanyi anee, kiransa zakiyi a waya saiku tattauna...
Kina ganin hakan yayi... Kwarai kuwa ki gwada... Amincewa tayi ta dauko Phone ɗinta amma ina ashe ma batada contact dinsa.. Oh shitt hanee bani da.......katse maganar tayi domin shigowar............
Abu ƙayace😀🤗
Domin aika sako kai tsaye zuwa gareni ko samun tsoffin books dina harda ma sabbin wanda zanyi anan gaba saiku tun tubeni tanan 👇
[email protected]
Aika sako kai tsaye zuwa gareni ko kira ta wannan number 09066017177 💃 💃 💃 💃 💃 💃 💃
Share pls and comments luv u all my fans Ina alfahari da rubutu...... 🤗
*WOMEN WRITERS ASSOCIATION*📚
_(Domin Marubuta Mata)_
✨(W.W.A)✨
https://www.facebook.com/106752595253176/posts/107924965135939/
🌀🌀🌀🌀🌀🌀🌀
_BOƊƊI the beautiful_
🌀 🌀 🌀 🌀 🌀 🌀
Story and writing
By
Z. B. M
_Yar mutan gombawa_
09066017177
PAGE 5️⃣6️⃣⏩5️⃣7️⃣
________________________________Momy wato mahaifiyar ta....
Zama tayi kusa da hanee tana kallon su, cikin raunanniyar murya tace feeyna saidai kiyi hakuri domin bayanda na iya...
Ddyn ki bayanda banyi dashi ba akan auren nan amma yaki....
Har hakan yana shirin taɓa min nawa auren...
Ke ƴata ce ba zanso wani abu yameki baKinga Ddyn ki I dan ya yanke abu to baya taɓa janyewa,.
Kuma nima nayi tunani auren ki shine darajar ki, saboda haka karnaji wani ani abu a tsaka ninki da mijinki kuma dan Allah koda ya miki wani abun kiyi hakuri ki daure karki sake Kice za kina kawo ƙararsa domin mu iyayen kine zamu rike shi a xuciya,! Bacin ke kuma daga baya ku shirya abunku....
Kuka kawai feeyna take yi har momyn ta ta gama faɗa mata duk abunda zata faɗa kana tace *hanee* ta shirya ta domin yanxu za'a kaita gidanta....
Kuka sosai take yi hanee tace; feeyna jikina yayi sanyi domin wlh duk abunda mom ke faɗa gaskiya ne,, babu mai auren mijin wata, kamar yanda babu mai auren matar wani.....
Dan Allah a yanxu ki aje dukkan maka manki, kitafi gidan mijin ki da kyakyawar zuciya,!
Haka dai *hanee* tayi ta bata shawara.....
*Allah ka azurtamu da kawar kirki kamar yanda ka azurtamu da iyayen kirki, ubangiji ka azur tamu da ƴaƴan kirki kabamu iko da Daman yi musu tarbiyya,* ♦️ ♦️ ♦️ ♦️
Amarya kinsha ƙamshi... Humm nikam karki mun magana ikon Allah me kuma nayi da har ba'a buƙatar magana na. Cewar Bintu, dake stokanar BOƊƊI
Ummu ina kwana murmushi tayi tace lfy lau ☺️ beauty, kin tashi lfy.. Lfy ummu...
Ina Sayyid bai tashi bane.. Sunkuyar da kai tayi,,, don taji kunya.. 😂 Ummu tayi murmushi cikin kulawa tace yaushe ne zaku fara exam..
Tace Ummu Monday, oh this coming Monday? Eh Insha Allah... To Allah ya nuna mana .. Amen ummu...
Bintu tace yeee ashe dai beauty ta girma ta kusa gama secondry.. Ahan kali tace nayi aure ma bare gama sch..... Oh mekikace no I didn't say anything 🤷♀️.... 😂 Dariya tayi yarinya kenan....
Bintu da BOƊƊI suna kitche ummu ta sasu aiki gashi ankusa kiran magrib.., BOƊƊI tace Hum shine jiya kika rufe mun kofa to yau ina nan ba inda zani....
Heeee ya rinya dole na rufe kofa, kafin kimun kuka yanda kika zauna Kina mana ran aure...
Ni yaya Sayyid nakeso... So.. So... So.... Ruwa ta ɗebo ta watsa mata..
Kaiii meye Hakan, kodai ba laifin ku bane stage ɗinku ne yanxu...
Sayyid ne yayi maganar cikin sauri suka juya, lokacin da suka haɗa ido da BOƊƊI ya kashe mata ido ɗaya tareda signa,
Wai kardar ya Sayyid yaji abunda muke cewa wayooooo Bintu.....
Cikin sauri ta shige ta fita zuwa daki tana mai jin haushin Bintu.....
✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨An kai amarya gidan su Ahmad domin anan aka ware apartment ɗaya kai Mata jere...
Momyn Ahmad sai farin ciki take ta tarbe su da kyau....
Ƴan kai amarya sun watse *hanee* tayiwa kwara ta fada sosai kafin ta tafi......
Shiru shiru ango bai shigo ba, feeyna da kirjin ta yaketa bugawa takalli a gogo taga har 1 na dare tayi.. Cikin tsoro ta shiga toilet tayi wanka taxo ta kwanta....
Ke Amarya ango yana kiran ki... Bintu wlh banason wannan abun da kike mun.....
Humm to ke kika sani bari na turo shi tunda kinki zuwa.. Bata kula Bintu ba tajuyar da kanta domin bacci take ji.. Sosai....
Sama taji anyi da ita zata yi ihu taji......................
Abu ƙaya ce......... 😂
♥️ ♥️ ♥️ ♥️ ♥️ ♥️ ♥️
Domin aika sako kai tsaye zuwa gareni 👇
[email protected]
Or
09066017177 💃 💃 💃 💃 💃 💃 💃 💃 💃 💃 💃 💃
Comments pls
🌀🌀🌀🌀🌀🌀🌀
_BOƊƊI the beautiful_
🌀🌀🌀🌀🌀🌀🌀
Story & writing
By
Z. B. M
_Ƴar mutan gombawa_
*Saboda saƙonni da suka mun yawa, na rage message ɗin phone ɗina, Hakan ya jawo na rasa books din na dake typing dama wasu daga cikin message da aka aiko min ta WhatsApp, so ina mai baku hakuri duk wanda yamun magana ban bashi amsaba, sai yamun uxuri yasake turowa! saboda abubuwa sunada yawa kafin na iso kan wasu sai ahankali nagode sosai ina ƙaunarku*🥰
~Lets continues~ 🌀🌀🌀🌀🌀💃🏼💃🏼💃🏼💃🏼💃🏼💃🏼
PAGE 5️⃣8️⃣
________________________taji Sayyid yace;
ahankali wato nikike cewa baki son damuwa?
Magana takeson yi amma bai bata damar hakan ba.... Saboda hannun sa na kan bakin ta har lokacin......
Ganin irin rikon daya mata yasa ta daina mutsu-mustu ta zuba mishi fararen idanun ta.....
Shima idon ya zuba mata, nan suka shiga kallon juna, so slowly voice yace " kinyi kuka ba saboda kina son aure na..
Murmushi yasakar mata wato dama ana sona ko? Yaushe ya rinya ta kware mun, wayyo ni ɗin dan gata ne ashe!
Da yanxu ba'a aura miki niba mezai faru..... Cikin jin kunya tace duk nayi ne saboda banason aure....
Hummm yarinya say the truth and shame d devi, Allah kuwa yaaa, bai bari ta ƙara ba yaɗau hannu akan bakin ta....
Tare da cewa it's OK.. Sassauta rikon daya mata yayi ya ɗagota ta zaunar, ya gefen gadon, bai kuma cewa komai ba..
Har ya kai ƙofa ya juyo yace, ina jiran ki........
Sai lokacin BOƊƊI tasamu karfin guiwar ma naga ita kadan ta,... ta fara surutu...
Kaiiii amma ya Sayyid ya dameni wayyo komai nayi idon sa na kaina wai Meyasa ya zamto kaddara ta,, wai harda cewa yana jirana ko a ina yake jiran nawa oho......
Kwanciya ta gyara abunta bacci kuwa yayi gaba da ita.....
Monday BOƊƊI suka fara exam sosai take maida hankali, a yanxu sosai take gudun Sayyid domin takura ta da yake yi....
Gashi tana matukar jin kunyar ummu saboda yanda takeson ganin su tare......
Shima sayyid busy yake domin shirin tafiyar su Saudi kawai yake don randa BOƊƊI ta gama washe gari zasu wuce tare don ita kadai yake jira........
Sayyid ke kaita sch din wata rana idan tayi saurin tafiya kuma to tana fitowa zata sa meshi a waje yana jiranta.....
Wai ke BOƊƊI bazaki ɗebi kaya da yawa bane cewar Bintu dake haɗawa BOƊƊI kayan tafiya....
Humm nikam kirabu dani, Haba 4 d first time fa kenan zaki Saudi ya kama ta kinuna musu ke matar sayyid maleek ne......
Ummu dake jinsu tace kirabu da ita, ko acan ma Sayyid saiya saya mata kayan tunda akoi su, wanda sukafi nan.....
Sayyid ya shigo ummu yaɗai inata jiran BOƊƊI kun riketa karmu makara fa..... Hum kaji shi kamar wani garin zaku bari inace gidan mamy zaku... Eh harda gidan tsohuwa da gidan su farouk kinsan dole muyi musu sallama....
Eh haka ne kammmm...
Bintu tace ta Sayyid inxo muje tare... Kallon ta yayi kici gaba da aikin ki....
Ah lallefa aikin ai na BOƊƊI ne saina ajiye oh haka zakice badon halin kiba shirya mutafi..... Kowa saida yayi dariya hatta ita mai maganar wato BOƊƊI....
Da gidan tsohuwa suka fara,, sai tsiya take musu, wai shikenan Sayyid kam Yakoma ɗan Larabawa..
Sun jima kafin suna hira,, har aleeyu ma yaxo kanin Sayyid,, Bintu tace kai ya aleeyu dama kana nan wlh har manta wa nake yi dakai wato tsohuwa ta mallake ka,, mun daina ganin ka....
To ja'ira sai kiyi kuma,, ai aleeyu ɗan albarka kullum yana nan yana mana hidima,, oh Kice bawa kika maida shi cewar Bintu lalle tsohuwa nan....
Ke dan gidan ku.... Kirufe baki, wato kinaso ki boye laifinki...
Ai auren ki zaixo ko kafata bazaki ganiba...
Bintu tace to dama bana bukatarki, tsohuwa lokacin auren ki da tsoho ai nima ban xoba...
Kai baki abun magana a dauki kunya, haka suka ta fafatawa da tsowa sayyid dai Bintu ce bakin sa......
Daga karshe yar tsohuwa tayi musu nasiha harda guntun hawayen ta,,
Koda suka fito Bintu sai dariya take, wai wai tsohuwa kenan!
Gidan su farouk ne next, anan basu wani jima ba... Sun gaida hajiyar farouk, sai kuma farouk ɗin da suka danyi taɗi da sayyid basu dai wani ɓata lokaci ba ya rakosu wajen mota suka yi sallama... Bintu sai wani sunkwui da kai take kamar ba ita tamaga zuva yanxu ba agidan tsohuwa........
Gidansu BOƊƊI shine na karshe domin zasu daɗe acan shiyasa suka fara da sauran.....
Twins sai murna suke aunty beauty taxo, sosai hajeeya Ameenatu tayi murnar ganin ɗiyar tata, akawo wannan akawo wancan....
Alhaji Abubakar yaxo shima sai hira ake ga inna kulu itama duk abu kam yayi matukar daɗi.. Kamar kar a rabe......
Sai karfe goma na dare tukun suka yi sallama domin tafiya Ameenatu tayi nasiha mai ratsa jiki da zuciya ga BOƊƊI wanda har ya sata zubar hawaye.....
Washe gari kowa ya hallara domin rakiya BOƊƊI da sayyid zuwa airport, sosai BOƊƊI take jin kewar gida, sai lokacin da aka fara kiran ma tafiya, ta fashe da kuka Ummu ma kuka take yi, hakadai sayyid ya kama hannun ta ya rike suka wuce xuwa cikin jirgi........
*To readers ya kuka ji aranku tausayi BOƊƊI tabaku kodai?*
*Saude dai tace BOƊƊI kinban guri tunda baki son tafiya.. 😂*
Karfe 7:pm BOƊƊI suka sauka, Sayyid na rungume da BOƊƊI kamar wani zai kwace ta.
tuni jaddun sunyi shirin tarba baki don tun safe suke hidima da dokin ganin jikan su tareda amaryar sa.....
Driver ne ya ɗauke su zuwa gida........BOƊƊI sai bin gari take da kallo dukda cewar darene amma kamar rana kota ina haskene mai daukar hankali......
Kyakkyawan tarba BOƊƊI tasamu fiye da sayyid,, ɗaki na mussam aka kaisu....
Gidan yayi bala'in mata kyau yanayin tsarin sa... Kuma ba wani girma sosai yakeda ba....
Tunda BOƊƊI ta shiga dakin tasamu wata kujera dake ciki ta zauna... Tana kallon Sayyid dake kokarin rage kayan jikin Sa......
Ido ya kashe mata, yaxo har inda take zaune, yasa sannu ya cire mata takalmi..
Sannan ya cire top din dake jikinta daga yayi cak tayi saurin lumshe idanu don agaskiya ta gaji, kamar Sayyid yasani bazata iya yin komai ba...
Gashi yunwa take ji sosai....
Idanun ta a rufe har ya cire mata kayan ya daura mata towel, hannu yasa domin karasa cire sauran ta rike hannun sa, no ya Sayyid..
Ahankali yace dasu zakiyi wankan, kasa tayi da idanun ta, bai ce komai ba ya kama hannun ta har cikin toilet ɗin hada mata ruwa yayi cikin bathtub yama ido alamun ta shiga...
OH ya Sayyid kafita...
Meyasa inason na tayaki ne fa naga kin gaji....
Thank you, kaje kawai zan iya, are you sure yeah,.. OK...
Fita yayi ya barta, koda ya fito kitchen ya nufa yace su kawo abincin daki don sun gaji ba zasu iya fitowa cin abun cin ba.....
Hakan kuwa aka yi an kawo musu abinci har daki ba jimawa BOƊƊI ta fito daga toilet din...
Sayyid ya shiga...
Agaban dreesin mirro ta zauna ta shapa mai kafin ta bude kayan ta tana duba wanne yakamata tasaka......
Sayyid ya fito yana kallonta sai ya mutsa kayan take yi.....
Har ya gama shiryawa BOƊƊI bata samu kayan da zata saka ba...
Matsowa yayi ya karewa kayan kallo wani riga ya gani yakai hannu ya dauko...
Ya mika mata kisaka wannan da idanu ta bishi wannan kuma?
Eh ki gwada, ya maida kayan data fitar ya rure, ya wuce ya dau plate ya xuba abunci don shima wunwa yake ji saboda bai wani ci abu sosai a cikin jirgi ba......
Koda tasaka riga ita kanta taga ya mata kyau amma kuma cinyarta duk awaje....
Gashi rigar ba wani hannun kirki gareta ba....
Haka da ta karasa wajen sayyid dake kai abinci bakin sa....
Wow kin hadufa yamma ta,, murmushi tayi tareda zama a gefen sa....
Saboda ya stura mata ido yasa takara matsawa kusa dashi ta manne da jikin sa...
Don hakan bai bashi damar kallonta sosaiba...
Are felling hungry? Girgiza kanta tayi cikin sauri...
Abaki yarinka bata abincin har saida suka koshi tare,...
Kana suka je yin brush.. Awajen yin brush din.....................
_Nayi iya kokari na_ _kuce mun sorry Allah kuwa na gaji_
🌀 🌀 🌀 🌀 🌀 🌀 🌀 🌀 🌀 🌀 🌀 🌀 🌀 🌀 🌀 🌀 🌀 🌀 🌀 🌀 🌀
Domin aika sako kai staye zuwa gareni👇
[email protected]
............... Abu ƘAYA ce.....
🥰 🥰 🥰 🥰 🥰 🥰 🥰
*WOMEN WRITERS ASSOCIATION*📚
_(Domin Marubuta Mata)_
✨(W.W.A)✨
https://www.facebook.com/106752595253176/posts/107924965135939/
🌀🌀🌀🌀🌀🌀🌀
_BOƊƊI the beautiful_
🌀🌀🌀🌀🌀🌀🌀
Story and writing
By
Z. B. M
_Ƴar mutan gombawa_
♥️ ♥️ ♥️ ♥️ ♥️ ♥️ ♥️ ♥️ ♥️ ♥️ ♥️ ♥️ ♥️ ♥️ ♥️ ♥️ ♥️ *HELLO MY FAN'S* _INASO NAI MUKU ALBISHIR DACEWA A PAGE NAGABA WATO ZAN KAWO KARSHEN LABARIN NAN WATO BOƊƊI the beautiful KUMA AKOI WATA GARAƁASA DAZAN BAKU,! TAMBAYOYI NE DASUKA SHAFI WANNAN LITTAFI AMMAFA MAKARANTA BOƊƊI NE KAƊAI ZASU IYA AMSAWA...._ 😂_
_TUKUICI GADUK WANDA YASAMU DAMA,,_
*Domin karin bayani saiku tun tuɓi wannan number 09066017177 💃 💃 💃* 💃 💃 💃
PAGE 5️⃣9️⃣⏩6️⃣0️⃣
_________________________Awajen yin brush ma BOƊƊI sai boyewa take...
Sayyid yace ;
Meke damun kine? Shiru ta masa, ta tsaya dayin brush ɗin...
Humm! Cigaba yayi dayin brush ɗinsa, saida ya gama ya karbi brush ɗin nata...
Nikam ya Sayyid kabari zanyi da kaina... " I know ai dama zakiyi just I wanted to help you ne"...
Sakar mishi brush ɗin tayi... Yace ; "open your mouth, ahankali ta buɗe yasa brush ɗin yafara goge Mata,,,
Idanun ta 'a rufe har yagama mata brush ɗin, sannan ya fesa mata mouth freshner.....
Sama ya ɗagata cakk har kan gado.. Buɗe idanu tayi ya Sayyid ka kaini kan kugera anan zan kwana...
Sayyid yace; ai kujerar bazata ɗauke mu. Mu biyu ba.....
To nifa ya Sayyid ni kaɗai nace...
Bai kula taba ya kwanta abunsa a gefe...
Tashi tayi daniyyar sauka ya rikota ya jawo zuwa jikin sa, nikam ya Sayyid kabari mana zan kwanta acan ne..
Rungume ta yayi,, zata fara mustu-2 yace calm down, my beauty wife...
Ina bacci kikeji? To kiyi abunki ya fara buga bayan ta yana shafawa ahankali....
Hakan daya keyi matukar daɗi yamata tuni bacci ya dauke ta,,...
✨✨✨✨✨✨✨✨Kiran sallah asuba ne ya tashi feeyna dake bacci wanda bata san lokacin daya dauke taba.....
Numfashi taji a jefen ta cikin tsoro ta fara kare masa kallo domin lokacin data kwanta baya nan..... Ko yaushe ya shigo oho...
Mikewa tayi tashiga toilet,, bayan ta fito tasa meshi ya tashi kallon kallo suke wa juna.....
Tazauna a gefen shi....
Amarya kinsha ƙamshi... Abunda feeyna bata kawo a ranta ba kenan....
Cikin mamaki take bin shi da kallo, ya kashe mata ido ɗaya kana ya mike yashiga toilet....
Gari ya fara yin haske, ahmad yadawo daga mosque,.. Feeyna tana zaune a falo... Tana danna wayar ta....
Zama yayi a gefen ta tareda karbar wayar a ajiye... A gefe...
Kallon sa tayi yanda taga ya mata wani kwarjini da batayi niyyar gaida shi ba amma sai tasamu kanta da cewa ina kwana...
Kanta a ƙasa murmushi yayi lfy lau,, Amarsu..
Kallon sa tayi da mamaki kafin tayi magana yari gata..
Kina mamakin yanda na sauya ko baki yi tsammanin haka bako...
*Fatima* cikin sauri ta ɗago. Kai ashe dama yasan real name ɗina..
Magana ya cigaba, Fatima komai Mu mikawa Allah domin yana sane...
Hakan da kika ga ya faru Allah yasa alkhairi domin yafimu sanin komai...
Kuma iyayen mu ba zasu taba zabar mana abunda zai cutar damuba...
Ada ban sankiba amma yanxu nasanki kuma kema kin sanni, wannan kamarin ubangiji ne, ba mai auren mijin wata kamar yanda ba wanda zai auri matar wani....
Koda a bangon duniya muke sai mun hadu domin muyi aure....
Daaa zuciya ta tana tafasa a dalilin rashin BOƊƊI amma a yanxu na saduda domin nagano tayi mun nisa kuma ita matar wani ce....
Meye amfanin addu'a da mukeyi a kowani lokaci, a yayin naiman auren..
Domin Allah ya mana zaɓi na gari.. To idan munyi aure babu kwanciyar hankali ya kike tunani zamu zauna...
Allah yasan komai,, saboda haka mu cigaba da addu'a, kimance da Sayyid muyi rayuwa cikin aminci...
Kai ta dago wanda tuni hawaye sun wanke mata fuska... Tunda ga na sihar da mom ɗinta tayi mata da hanee.. har wanda ahmad yayi mata,, ya matukar shiga jikinta....
Cikin muryar kuka tace Allah ya tabbatar mana da alkharinsa...
Cikin farin ciki ahmad ya rungume ta... Tareda danne wani abu cikin zuciyar sa....
Domin so yake ya savarwa zuciyar da son zama da feeyna, ya cire BOƊƊI cikin tunaninsa......
*********************************************cikin Larabci take magana masha Allah amarya gaskiya,, bazan yarda ba,, shine Sayyid zai samo wacce ta fini kyau...
Cikin Larabci ita ma BOƊƊI ta mayar mata... Na'isa nafiki kyau gashi dukda tsufar ki Amma har yanxu babu laifi....
Dariya duka suka saka...
BOƊƊI na matukar jin dadin hira da tsohuwar domin akoi ta da son taji,, kirki kuwa ashe ga inda ummu ta kwaso don wannan mata akoi kirki kowa nata ne..
Hatta ma aikatan gidan ya bonta suke....
Sayyid tareda jaddun suka shigo, nan jaddun ma yazauna yayi ta sanya wa BOƊƊI albarka...
Da yamma Sayyid ya ɗauki BOƊƊI suka tafi ganin gari....
Ya zaga da ita waje da dama abunda yake bata mamaki Koda tsohuwa ne zakaga mijin ta yariko hannun ta suna tafiya suna soyayyar su Baru wansu da stufa...
Sayyid yana ta kula da yanda take kallon mutane yace; oh yammata kina ganin inda ake love ko,, kiyi wasa wata tayi wuff dani...
Yayi dariya, tsume wa tayi don abunda Sayyid ya fada bai mata dadi ba....
Da dare BOƊƊI tana kwance a daki saboda tafi jin dadin zaman dakin...
Chatting take da Bintu tana bata labarin gari itama tana tambayar ta....
Bintu ke bata lbr wai kinsan,, ansa ranar aure na....
Me kikace Bintu, aure wazaki aura!? Ya rinya zauna ya farouq mana shine zan aura....
Wani tsalle BOƊƊI tayi nashiga murna gaskiya ina ta yaki murna...
Nan taki rata a waya suka yi ta taɗi......
Bintu cikin tsokana tace BOƊƊI Kinga kafin nan saiki xo da starab ciki....
Tafada tana dariya... BOƊƊI tace Allah ya sauwake! Ke bakida hankali ne...
Dama ai ina kula dake wallahi BOƊƊI Kinga inkikayi wasa wallahi matan lavawa su kwace miki miji....
BOƊƊI taji kirjin ta ya buga.... Nan Bintu tayi ta bata shawari sosai.....
Bayan sun gama waya BOƊƊI ta zauna shiru gim kadan tunani tayi tayi....
Sai kuma ta tashi cikin azama tashiga tayo wanka....
Light makeup tayi
Tasa wasu arnan kaya wanda suka matukar bin jikin ta,, turare kuwa ba'a bayani don tayi ɓarnansa a jikin ta..
Jin shiru har 11pm Sayyid bai shugoba gashi tsoro takeji da tayi baccin ta a yanxu ita idan ba wani a gefen ta bata iya bacci...
Tashi tayi tadau wani black after dress ta daura akan kayan ta fito falo....
Tun kafin ta karaso take jin dariyar Sayyid abun mamaki ko me suke cewa wanda yasa shi dariya haka kara sowa tayi,..
Budurwa ce fara tass balarabiya tana zaune gaff da Sayyid suna cin Popcorn tana mishi taɗi da Larabci shi kuma ya biye mata sai dariya yake yi.....
Wani abune ya to kare BOƊƊI a kirji don yaune karo na farko da taga sayyid tareda wata suna zaune suna taɗi.....
Sayyid yaji kamar mutum a tsaye tajuya BOƊƊI ce ya gani amma bai samu damar ganin face dinta ba domin ta riga ta juya.....
Wani smile yayi yaci gaba da tadinsa, koda boɗɗi ta shiga daki ta cire abayan tayi wurgi dashi ta cube akan kujera... Tunani ne kala kala yafara zuwa mata cikin xuciya...
Sai kusa 12 Sayyid ya shigo har lokacin idon boɗɗi biyu ta kasa yin bacci....
Tana jin shigowarsa amma sai tayi pretending kamar mai bacci.... Ganin irin kwanciyar da tayi yasa Sayyid yin murmushi ya karasa zuwa gareta.......
*Ayimun zuri da jin shiru kwana biyu ba update.. BOƊƊI naso na kawo karshen book ɗina page na gaba amma inaso Naji ra'ayin ku, idan hakan yayi muku to idan kuma kuna bukatar kari sai kuyi magana*
_Inason zan sauya sunana zuwa aunty peppe🌶️🌶️🌶️ shin ya kuka ji yayi kuwa? 😂_
Aika da ra’ayin ku ta nan“` 👇
Whatpad
Zainab7177
What’sapp
09066017177
Share.. VOTE Comments
WOMEN WRITERS ASSOCIATION📚
(Domin Marubuta Mata)
✨(W.W.A)✨
https://www.facebook.com/106752595253176/posts/107924965135939/
🌀🌀🌀🌀🌀🌀🌀
BOƊƊI the beautiful
🌀🌀🌀🌀🌀🌀🌀
Story & writing
By
Z. B. M
_Ƴar mutan gombawa_
♥️ ♥️ ♥️ ♥️ ♥️ ♥️ ♥️ ♥️ Jin jina agareku masoya book ɗin BOƊƊI aduk inda kuke ina gaisuwa agareku 🥰🥰🥰🥰wanda yaso ✍🏻yaso ka……
PAGE 6️⃣1️⃣⏩6️⃣2️⃣
_____________———–cak ya ɗagata ai kuwa ta bude idanun ta, jin ya direta kan gado yasa ta sauke numfashi ahankali, toilet yaShiga! Cikin sauri taja blanket tarufe jikinta.. baiwani jimaba ya fito, yayi shirin bacci.. , duk abunda yake BOƊƊI Naji sa. Amma ko mosti batayiba., Sayyid dai BOƊƊI na bashi dariya don ya tabbatar batayi bacci ba.. Gadon ya hau tun kafin yakaraso gareta turaren sa ya bugi hancin ta, hannu ya saka ya yaye blanket ɗin, ya maida gefensa… bata yi niyya motsawa ba, amma jin sanyin AC na damunta , tadan kai hannunta ahankali domin laluɓo inda yake idanunta arufe.. Sayyid ya rike hannu tareda janyo ta jikinsa.. Meye Hakan ya Sayyid, sanyi dai nakeji karufeni.. Bai mata musu ba ya rufe su duka da blanket ɗin, ta kuma cewa to kasakeni mana ya Sayyid bacci zanyi.. Yace to kiyi baccinki mana ba kin faraba… Barima na rarrasheki kiji dadin bacci bayan ta yafara shafawa ahankali, yana mammasta mata kafa ɗunta, ita dai tayi shiru tana jin abunda yake yi kamar mai yi mata masserge,, fuskar sa ya matso daidai kunnen ta kamar zai fada mata wani abu sai kuma ya xira harshen sa.. Bata san lokacin da tace wayyo Allah ya Sayyid.. Aikuwa kamar ta stikareshi wannan maganar da tayi Sayyid ya fara game da hannunsa a jikin ta.. Bai bata damar cewa komai ba saboda tuni ya sanya lips ɗinsa akan nata yafa bata sweet testy kiss. Laushi bakin nata ya kara tun zura sayyid domin har ya mance a inda yake…
Tuni BOƊƊI ta dauke wuta domi. Numfashinta ya soma barin ta.. Yau ce nara ta farko data fara tsintar kanta a wanna hali…
Duk yanda Sayyid yaso daurewa abun yafara fin karfinsa don yau wani irin abu yake ji yana yawo akansa jinsa yake tamkar ba shiba, jin Bata mustu mustu da take yi yasa shi kallon ta Aikuwa kamar dai bata numfashi.. Cikin sauri ya Mike ruwa ya dauko a cikin fridge ya yayyafa mata ajiyar xuciya ta sauke shima ya sauke tasa ajiyar xuciyar don ya tsorata..😂
Kuka ta fara Aikuwa yashiga aikin lallashi… Bata da wani zabin daya wuce shiru don hawayen ma yaki zuwa saidai fa bakin ta bai mutuba, tace ; ya Sayyid kasheni zaka yi ne ka kama ka toshe mun numfashi.. Dariya zancen yabawa Sayyid amma sai yace afuwan ” kiyi bacci abunki… Rungume ta yayi don tayi bacci amma ina taki wai saidai ya sake ta..
Kiyi shiru ba abunda zan miki just trust me.. Aikuwa taki yarda dashi bashi da zabin daya wuce ya koma gefe ya barta domin tasamu tayi bacci..Sayyid ya dafe cikinsa cikin sauri ya Mike yadau ruwa mai sanyi yasha ya kwanta gefe domin ya tabbatar yau zaiyi kwanan wahala, abubuwa yake faman kitsimawa acikin ransa, har bacci yayi nasarar daukansa..Karfe 3 Sayyid ya Mike ya dauro alwala BOƊƊI ya kalla sai bacci take, nafila ya fara yi yana mika kukan sa ga mahalicci domin har Can Kasar zuciyar sa BOƊƊI ce ta mamaye… Baya so yaga yayi mata abunda zai bakan ta mata rai amma kuma yana burin yaga sun haifi yara domin farin cikin iyayen su…BOƊƊI cikin baccin ta wani mafarki take yi mai saka shauki…..
Lokacin da aka kira asubahi Sayyid yaje da niyar tashin ta domin tayi sallah abun mamaki murmushi yagani kwance kan fuskanta hannu yakai domin ya tashe ta,, kafin ya karasa ta rike hannun cikin muryarda zaka tabbar cikin bacci take tace.. Ya Sayyid! Abun mamaki Sayyid ya zuba mata idanu ta kuma kiran sunan sa “ya Sayyid Meyasa kayi shiru kake kallona kana murmushi… Fuskanta sayyid ya kuma lekawa to lallaifa beauty bacci yayi daɗi kenan.. Ya Sayyid ka kama hannuna pls karka sakeni karka rabu dani karka gujeni.. Ai kuwa ya kama hannunta ahankali yana murzawa domin surutanta yasanyashi farin ciki don koba komai yau ya tabbatar wa zuciyar shi BOƊƊI tana kaunar sa kamar yanda shima yake kaunarta tunda har mafarkinsa take yi.. Abu Dayane wanda yanxu ya rage masa, yanaso ta fara nuna masa zazzafar kauna wanda zata iya mutuwa domin shi,.. Wani murmushi ta sake lokacin da ya tuna da wani abu… Hannun ta daya rike yake murzawa yadan matsa da karfi ai kuwa tace auwch!! Yafara bude idanu a hankali…
♥️ ♥️ ♥️ ♥️ ♥️ ♥️ ♥️ 🖤🖤🖤🖤🖤🖤
GIDAN ƘAWATA
🖤🖤🖤🖤🖤🖤
~Paid book~ 📚
Domin Samun damar karan tawa sai a biya 200# ko a tun tubeni ta wannan number 09066017177 💃 💃 💃 💃 💃 💃 💃 💃 💃 💃 💃 💃 💃 💃 💃 💃 💃
Share and comment pls 🙏
🌀🌀🌀🌀🌀🌀🌀
BOƊƊI the beautiful
🌀🌀🌀🌀🌀🌀🌀
NA_zainab Z. B. M.
Ƴar mutan gombawa
WOMEN WRITERS ASSOCIATION📚
(Domin Marubuta Mata)
✨(W.W.A)✨
https://www.facebook.com/106752595253176/posts/107924965135939/
❌🔞 This page is very dangerous pls don’t read if you’re not married….ok 👌
PAGE 6️⃣3️⃣🔁6️⃣4️⃣
…………….tozali tayi da sayyid da keta faman sakar mata murmushi, mikar da ita yayi tsaye, cikin muryar bacci tace ya Sayyid yanxu fa na kwanta baccin bai isheni ba..
Lalle kuwa! to asuba tayi idan kinyi sallah saiki koma bacci, cikin magagin bacci ta isa toilet tayi alwala taxo tayi sallah.. Sayyid kuma tafita masjid.. Karatun qur’an ta taɓa, wani bacci sosai takeji yana kuma daukanta.. Kwata kwata shafi biyu takaranta sai hamma take.. Rufe qur’an ɗin tayi ta haye gado abun ta, bacci kuwa ya kwashe ta….
Sayyid saida gari yafara yin haske suka dawo dama shida jaddun suka tafi… Koda yashigo boɗɗi sai bacci take a jefen ta ya kwanta tareda rungumota Tabaya.. ya sanya hannunsa yana wasa da gashin kanta wanda yake irin na fulani mai santsi..
Haka kawai yaji yana so yaga yanda face dinta yayi.. Juyo da ita yayi ya fara kare mata kallo.. BOƊƊI duk abunda ake ita baccinta take.. Tun daga kan idanun ta har zuwa hancin ta.. Bai taba kare mata kallo irin na yauba ji yake kamar yau yafara ganin ta.. Lokacin da idanun sa suka, sauka kan lips ɗinta.. Sunyi pink sosai burgesa abun yayi take yashiga shauki, aikuwa yakai nasa bakin.. Ahankali yake kissing lips din nata taushinsu yasan ya Sayyid zarce wa… BOƊƊI jitayi numfashi yamata wuya da kyar tasamu ta bude idanun ta akuwa abunda kwakwalwar ta ke sanar mata ya zarce tunani…
Sayyid fa ya zauce kota ina kai hannu yake ajikinta… Aikuwa ta tattaro duk karfin ta domin tureshi ina saima kara himma dayake wajen bata zazzafar soyayya.. Jikinta ne ya mutu domin sassan jikinta ya fara karban sakonninshi…
Tuni ya cire rigar jikinta.. Jikin sa sai rawa yake lokacin da yayi arba da na shanunta… Wasa sosai take da ita BOƊƊI sai Siririn hawaye dake fita cikin idon ta.. Kuma ta kasa komai don yau Sayyid ya kashe mata jiki…..Wani irin abu ne ya ziyarce ta lokacin daya kai hannu kasanta jin yanda ta jike da ruwa ya kara sanya sayyid wani hali… Tuni ya karasa ficewa hayya cinsa… Jin ya daina control ne BOƊƊI ta rikice tuni ta fara kukan gaske… Wayyo ke BOƊƊI yau hannun maza kike 😂
Shi kanshi Sayyid bai san awacce duniyar yake ba.. Kafin kace wani abu har yafara neman hanya babu irin ihu da son kwatar kanta daba tayiba amma ina Yau kam hakurin sa ya kare jiya ke zai iya mutuwa ….
Bayan 2 hours BOƊƊI na kwance sai hawaye wannan wani irin abune kukan zuci take dana fili…
Sayyid daya fito daga toilet yakaraso ganin yanda take ya rasa ta ina zai fara… Kokarin da gata yake amma ina sai ki take yi.. Da kyar yasamu ya ciccibeta xuwa toilet sai tirjewa take amma ahaka yayi mata wanka… Yana faman lallabata kamar kwai…
Da kansa ya shirya ta ya sanya mata wata riga mara nauyi har lokacin hawaye bai daina ambaliya a fuskar taba…
Gadon ya gyara ya dago ta ya kwantar kana yafice don karbo breakfast… Fitan sa keda wuya wayar BOƊƊI tayi kara so take ta tashi ta dauko amma ina wani zafi takeji ta kasa……
Haka ta Mike tana lallabawa har ta isa wajen da wayar yake ta zauna akan kujera tadan kwanta ta yanda zata ji dan dama-dama…
Bintu ce ke ƙiranta… Dagawa tayi Bintu ta fara magana amarya…. Wasu hawaye ne suka kuma fito mata Bintu tace hello BOƊƊI ina magana bazaki amsaba.. Jin alamin sheshekar kuka yasa Bintu tace kina lfy kuwa…
Da kyar BOƊƊI ta bude baki ta fara magana… Kwashe komai tayi ta fadawa Bintu…dariya tayi kai amma ashe ke bakida wayo… Wallahi ya Sayyid yayi kokari ni inace an wuce wajen tuni… Kukan da BOƊƊI keyi yasa Bintu cewa kiyi shiru BOƊƊI meye na kukan to…
Ni abunda yafi bani ta kaici ina jin ko a novel sai amarya ci kaza tukun ake yi sannan yayi ta lallabata amma ni babu wani shiri yaxo ya….. Wani dariya bintu tayi lalle kuwa,, yau zaki fara cin kaza hala… Karki damu wannan ba komai bane wlh ai mijin kine kuma ba haramun bane… Allah BOƊƊI kinyi sa’a ya Sayyid nada hakuri… Karki damu komai zaiyi daidai… Sannan wannan sirrin ki ne dan allah karki sake wani yakuma ji sannan karki bari wani ya gane wani abun…. Nima daga yanxu bana bukatar ki kuma sanar dani komai saboda ni kanwar Sayyid ne…. Sosai Bintu tayita bawa boɗɗi shawara.. Tareda kwantar mata hankali…
Tace bikinta saura 3 weeks bayan sun gama magana ta ajiye wayar nan wani sanyi yafara xiyartar ta don zata je bikin Bintu taga su Ummu da mamyn ta…
Sayyid ne ya dawo hannunsa dauke da plate na abinci… Ganin ta yayi akan kujera.. Yace beauty ya aka yi kika dawo nan…
Kice Harkin warke… Kallon sa tayi saboda ahankali yayi maganar amma har kunnen ta…
Zama yayi a hannun kujerar yace tashi kiyi break, yatsina fuska tayi alamun bazata ciba…
Lallashi yashiga yi… Ya dagota domin zaunar da ita… Jikinta yaji yadau zafi sosai yace Subhanallah soryy my beauty… Fever ya kamaki… Ya komar da ita ya kwantar ya tafi ya dauko wani magani tea yahada mata ya xo yace ta sheta ya bata tasha da kyar.. Amma taki cin abincin…
Haka ya hakura yabar ta, saboda tace zata yi bacci..
Sayyid na zaune a falo yana chatting yake da farouq batun aurensa da Bintu nanda three weeks,.
Sayyid yace wai kana nufin nanda 2 weeks muna Nigeria.. Farouq yace kwarai kuwa.. Kai nikam inag saidai BOƊƊI taxo saboda Kaga next week zan fara aiki kuma Ace daga farawa sai na tafi… Humm kaidai kasani Allah yabaka sa’a kuma karkaxo… Dariya Sayyid yayi suka ci gaba da tsokanar juna… Wani farin ciki Sayyid yaji yana faman da wainiya dashi.. Tsohuwa ce ta fito….
Yana ganka anan to ina kikeso ki ganni hummm ina kishiyar tawa shiru yayi mata.. Saida ta maimaita.. Kana Sayyid yace tana ciki fever ke damunta.. Ayyerh shine baka fadamunba.. Lalle kuwa Sayyid… Kansa ta zungure tawuce domin zuwa ta dubo BOƊƊI………….
♥️ ♥️ ♥️ ♥️ ♥️ ♥️ ♥️ ♥️ ♥️ ♥️ ♥️ ♥️ ♥️ ♥️ Ayimun uzuri da typing erro banida enough time din editing ne 🥰🥰 🥰🥰🥰🥰🥰🥰
Comments pls✍🏻
🌀🌀🌀🌀🌀🌀🌀
BOƊƊI the beautiful
🌀🌀🌀🌀🌀🌀🌀
Story & writing
By
Zainab Z. B. M
Ƴar mutan gombawa
WOMEN WRITERS ASSOCIATION📚
(Domin Marubuta Mata)
✨(W.W.A)✨
https://www.facebook.com/106752595253176/posts/107924965135939/
💃🏼💃🏼💃🏼💃🏼💃🏼💃🏼💃🏼💃🏼 SABAYA TRAINING CLASS muna muku maraba 🤗
KOYI DA KANKI CLASSIC LADY 🥰🥰👇
*HAƊIN AMARE NA MUSAMMAN
*HAƊIN UWAR GIDA DOMIN MOREWA🙈 🙊
*HADIN NORMAL SABAYA
*HADIN RAGE TUMBI
*HADI DOMIN SGAFE KOMAI ZAM-ZAM😆
akoi kuma na musamman domin mai shayarwa da kuma lokacin yaye!
🧏♀️ Karki manta Indai kinsha SABAYA ba kiyi kibaba to bakida kashin yin kibane saidai kiyi hakuri, duk wanda ya sha SABAYA ya huta da rama
PAGE 6️⃣5️⃣⏩6️⃣6️⃣
_____________________da sallama ta tura dakin hango BOƊƊI tayi ta kudundune cikin bargo, kara sawa tayi kusa da ita ganin yanda take rawar sanyi, tace subhanallah, Takai hannunta zuwa kanta taji zafi rauu.. Fitowa tayi tasamu Sayyid tace jikin nata da zafi sosai ko dai zaku hospital ne… Sayyid yace na bata wani medicine tasha Insha Allah zuwa anjima zata samu lfy.. To Allah ya bata lfy wani abu taje ta dauko nasu hadin na tsoffin Larabawa.. Takoma dakin tace BOƊƊI tashi kinji, bata jin zata iya tashi amma kuma bataso tayiwa tsohuwar musu, daurewa tayi ta Mike tana ciza baki ta karba tasha…. Sannan Takoma ta kwanta.. Sai sannu take mata, gaskiya tsohuwar
akoi tausayi, zaka tayi gefen ta ta rike hannunta tana murzawa ahankali dadin hakan BOƊƊI takeji tuni wani bacci mai dadi ya dauke ta..
Sai da taga tayi baccin ta Mike ta fito sayyid yana nan still inda ta barshi wani kallo take binsa dashi… Yace yadai yar tsohuwa.. Murmushi tayi tace sannu ko… Yauwa yace… Yaci gaba da danna wayarsa…
Sai kusa la’asar BOƊƊI ta farka bakowa a dakin ta Mike taji jikinta yayi mata garau taje toilet ta kara gasa jikinta sannan ta fito tayi sallah kana ta sanya kaya..kwanciya ta kuma lokacin aka yi knocked kofar kamar bazata Tashiba sai kuma ta Mike abunci ne aka kawo.. Ta karba ta jiye Takoma kwanciyar ta…
Saida aka yi la’asar Sayyid ya shigo yasamu tana kwance…
.my beauty kin tashi ne bata kula saba, dama yasan bazata kulaba, abincin ya debo yace yanxu kamata ciki abunci tunda kinki ci dazu, dakyar dai ya lallasheta ita kuma tanason ci don yunwa takeji amma kuma bakinta babu test sosai… Ahaka sayyid yayita jinyar ta yana lallashi idan yana wani lallashi abun har bata dariya yake….
Kwana biyu jikinta da sauki sosai, yau Sayyid yace ta shirya zata rakashi wani waje… Itama tana son fita domin ta kuma ganin gari. Shigowa yayi yasamu tana…
Gaskiya I’m so tired 😴 😴 😴
Comments pls
🌀🌀🌀🌀🌀🌀🌀 BOƊƊI the beautiful
🌀🌀🌀🌀🌀🌀🌀
Story & writing
By
Zainab Z. B. M
Ƴar mutan gombawa
WOMEN WRITERS ASSOCIATION📚
(Domin Marubuta Mata)
✨(W.W.A)✨
https://www.facebook.com/106752595253176/posts/107924965135939/
Akoi slimming tea 🍵 mai inganci daga campaning longrich, domin yin slimming na jiki ko tumbi domin. Fitarda shape,
09066017177 💃 💃 💃 💃 💃 💃 💃
PAGE 6️⃣7️⃣⏩6️⃣8️⃣
……………… Shigowa yayi yasamu tana gaban mirro so take ta sanya sarkan amma kuma yaƙi sa kuwa… Karasowa Sayyid yayi ganin yanda take shaning ya sanya saida yace madam kinyi kyaufa..
Murmushi tayi bata ce komai ba, karban sarkan yayiYansa mata jin yanda BOƊƊI ke tashin kamshi, Sayyid ya sunkuyo yana sun sunar wuyan ta, lumshe idanu yayi domin wani lokacin da lips ɗinsa suka sauka kan wuyan ta.. Jin yanda Sayyid yake yi yasa BOƊƊI juyowa stop ya Sayyid, sorry dear kullum inaso Naji ina jin kamshinki amma bakya barina, bari Naji pls ba yanda ta iya haka tana ji sayyid yayita kissing wuyanta gan garowa yafara yi cikin sauri ta dakatar dashi, ganin tana shirin kuka sayyid yace nabari sorry. Da kansa yasan mata mayafi yakama hannunta, suka fito,,
Sallama suka yiwa tsohuwa, suka fita, yauma BOƊƊI taga gari don duk inda ake zuwa sayyid ya kaita.. Sai dare tukun Sayyid suka dawo… Sosai boɗɗi tagaji saboda haka BOƊƊI wanka kawai tayi ta kwanta, karfe 12pm Sayyid dake faman danna laptop akan kujera ya kalli yanda take bacci, dagani ta gaji, saida yakara abunda yake ya Mike shima ya kwanta a gefen ta tareda rungumo ta, fuskar ta yafara shafawa yanda yake smooth, duk abunda Sayyid yake BOƊƊI bata ma san yanayiba…. Nidai nace muku asuba tagari….
Ahaka rayuwa ta cigaba da tafiya tsakanin sayyid da BOƊƊI duk yanda takeji a yanxu Sayyid kokari yake yarabata da kunya, a yanxu BOƊƊI itama ta rage abu dayawa don nuna ma sayyid dinta kulawa take tareda taimakon shawar wari wanda take samu ta bangarori da dama.. Kullum cikin browsing take a waya dakuma leka shafuka na ma’urata a Facebook da Twitter,.. Ba iyaka BOƊƊI ba hatta Sayyid yayi wani kyau mai daukar hankali.. Ita kuwa BOƊƊI ba’a magana…
Feeyna! Anya ba ciki ne dake ba.. Kee aneey ki rufa mun asiri yaushe ma aka yi abun da har zan dau ciki.. Dariya aneey tayi wlh feeyna I’m telling kinda ciki, kuma menene idan kinyi ciki yanxu.. Akoi abu gaskiya banaso nayi ciki yanxu gaskiya banaso na haihu nafiso na fara more amarcina da kyau kafin nan da shekara uku.. Aneey tace nanda 3 years dinma karki aihu ki huta kinji…
Dariya feeyna tayi Allah kuwa aneey Indai ma hakane sai dai ayi mun CS kafin aneey tabata amsa akayi sallah ma yarinya ce tashigo takawo musu abinci inji hajiya Mahaifiyar ahmad..
Aneey ce ta bude abincin da yawa, kaii gaskiya feeyna kinyi dace wai har yanzu bakya girki.. Wlh kuwa gashi kin gani.. I kuwa dai Kinga ribar biyayya ga iyaye, uwar miji na sonki, ga mijinki ma babu laifi yana sonki.. Gaskiya kam wlh ai bansan lokacin da nima na kamu ba da sonshi saboda ya iya luv……. Sallamar Ahmad yakaste mata zance…
Waii yau kuma aneey kece a gidan namu.. Murmushi tayi suka gaisa.. Ahmad dayake yana son tadi haka ya zauna sukayi ta taɗawa…
Masha Allah, Yau saura kwana 4 auren Bintu.. BOƊƊI ke zaune tana haɗa kayan ta domin Daxu suka dawo daga wajen sayayyan kaya, kayan sunyi mata yawa ga wanda taxo dasu kuma Sayyid ma yayi mata sayayya sosai…
Kowa saida ta saya masa tsaraba sosai twins kam akwati guda ta hada musu nasu.. Sayyid ne ya shigo da murna ya karaso beauty na kina shiryawa ne? Bari na tayaki, taya ta yayi ta hada kayan kaff… Yace good yanxu saura tafiya ko… Murmushi tayi, ta Sayyid yaushe ne tafiyar saida yadan jawo ta jikin sa sannan yace gobe Insha Allah by 11 plight din zai daga zuwa Nigeria 🇳🇬, wani farin ciki sosai ya kama BOƊƊI bata san lokacin da ya kam kame sayyid.. Shima ya rungumeta..
Washe gari har airport su jaddun suka rakasu cikin kewar su…BOƊƊI tana murna zata je taga su ummu da mamyn ta amma kuma tana kewarsu jaddun saboda tsofin akoi shiga rai idan ka zauna dasu zaka ga hidima..
Acan Nigeria kowa sai murna yake yi, da farin ciki sayyid da BOƊƊI zasuxo, sai shirye shiryen tarban su ake yi…
Alhamdulillah su BOƊƊI sun iso gida lfy kowa yana cikin farin cikin ganin su… Banda ma amarya Bintu da kuma twins don yanxu yawanci suna wajen ummu, bayan anci ansha,…
An gaisa. BOƊƊI da Bintu suna taɗi kan yanda bikin zai kasance… Bintu tace yauwa BOƊƊI ga Ankon ki a dinka miki su amm Akuma, yanda naga kinyi kiba zai miki kuwa…
Kaji mun Bintu dawani magama, mezai hana.. Karba tayi tafara gwadawa, aikuwa da kyar aka samu na farko yashiga nanma saida Bintu ta taimaka mata..
Sauran kam duk basu shigaba, gashi dinkin ya bala’in mata kyau taya za’ace bazata saka wannan kayanba,. Bintu da son shakarda BOƊƊI tace shikenan ai kin huta bake babu saka anko… Gashi kuma ance ya yanke a kasuwa don wata friend dina sai nema take itama… Kawai idan naki zai mata Sai na bata, Takaici ya kama BOƊƊI ita kanta ba tasan dalilin kiban da tayi ba… Sai ga hawaye…….. 😂 😂
BOƊƊI meye na kuka kuma…… Hawayefa kike.. Innalillahi.. Ni zainabu 😂 ummu ce tashigo ta tarar dasu Bintu ba dariya a gefe tana kuma bata hak’uri meya faru ne Bintu ta sanar mata, aikuwa ummu ta fara ma Bintu fada.. Sosai.. Tana mai rarrashin BOƊƊI.. Tace karki damu akoi tsokana ki Bintu keyi… gobe sai kuje a gwada ki ayi wani.. Sai lokacin hankalin boɗɗi yadan kwanta …..
Ayici gaba da yimun uxuri zan kawo karshen lbr na huta nima.. 🙏
Abu ƘAYA ce 👍
Comments & share pls🥰
🌀🌀 🌀 BOƊƊI 🌀🌀🌀
The last fage 🤗
Haƙiƙa sannu sannu! Baya hana tafiya, komai nisan dare gari zai waye, sannan komai nisan jifa ƙasa zai faɗo, Godiya gareku masoya aduk inda kuke alkamina bazai iya jero sunan Kuba,. Ina mai godiya ta musamman da bibiyar book ɗina da kuka yi
🤗TABBAS ✍️ ~Alƙalami yafi ta kwabi~⚔️🪓
PAGE 6️⃣9️⃣🔁7️⃣0️⃣
🔚🔚🔚🔚🔚🔚🔚🔚🔚🔚🔚🔚🔚🔚🔚🔚🔚🔚🔚🔚🔚🔚🔚🔚 A fusace ta fice daga dakin, Bintu da idanu ta bita wani dariyan yana kara taso mata…
“Shagali wai dama haka a keyi idan anyi auren, duk mutum yabi yayi ƙiba”. Bintu kenan!!
BOƊƊI ta tura kofar dakin nan dai wato na yaa sayyid, ba kowa aciki hakan yasa ta wuce ta kwanta abun ta..
Bata jima da kwanciya ba sayyid yashigo, beauty lfy kikaxo kika kwanta anan ke kadai..
Alamun ranta ya baci ne, yagani a face dinta.
Inda take kwance yatako yakai hannu ya taɓa gefen wuyanta tunanin sa ko bata jin daɗine.. Hannun nasa ta kama cikin shagwaɓa tace ; ashobe ne da aka ɗinka mun duk sunki shiga na, shine Bintu ke mun dariya…
Shima dariya abun ya bashi.. Amma sai yayi murmushi to banda abunki beauty ai yanxu kin kara kinfi haka.. Kuma tunda bake kadai bace ai kuwa dole yamiki kadan… Wani irin bani kadai bace… Dariya yayi ya shafa cikinta, ” ina nufin yanxu tumbinki yakara girma haka jikin kima.. To kinga ai dole kayan yamiki kadan… Shima kukan zata masa.. Yace sorry soryy karki damu za’a yi wani saiki saka.
to ai naga Bintu yace yakare ummu ce tace akoi wani… To ina dai ummu tace akoi shikenan sai muje ayi babba wanda zaku sake… ” wai nikam yaa Sayyid me kake cewa ne… Kinji nace wani abu ne, ta girgiza kai..
To shikenan muje ko. Ya kamo hannunta suka fito….
Shagali biki fa abu ya kan kama a yanxu gida yafara cika da mutane don ma yawanci bakin wani gari hotel ummu takama musu can suke sauka…
Yaune raran fulani day kowa sai caɓa ado yakeyi musamman kawayen amarya nasu da banne..
Ban garden Abbu suka koma Bintu da kawayen ta… Nima zainabu shigowa ta kenan, na hango wata cikin shigar fulani sosai tayi mun kyau, na sake baki ina kallo… Ashe BOƊƊI ce.. Tsarki ya tabbata ga ubangiji, domin BOƊƊI ta haske kowa dake wajen hatta Bintu jinin Larabawa bata kai BOƊƊI ba, sai dai itama tasha kyau don kana ganin ta kasan cewa amarya ce, saboda yanda take sheki..
Lokacin da aka fara gudanarda taro, duka kawayen amarya suka shigo da ƙwarya a hannun su… Dama sunyi rehazal din rawar da zasuyi… Tuni aka saki sauti suka shiga ta kawa…
BOƊƊI kam bata shiga ba tana can ana zuba mata zafafa fan picture wanda nima nasamu na liƙa a cover na labari dana kawo muku 😂
Anyi taro lfy an watse washe gari kuma Arabian day.. Shima dai anyi duk abunda ya dace ya matukar ƘAYA tarwa..
Next day aka yi dinner wannan kam Sayyid da BOƊƊI tare suke.. Don tunda aka fara hidima baya ganin ta sai dare…Wanka iya wanka kayansu kalan golden mai dauke idanu, sai da kowa ya hallara ango da amarya ma tuni sun zauna amazau ninsu.. Saura wajen BOƊƊI da sayyid, wannan kuma tsarin ummu ne, tasa aka tanadar musu suma na musamman…
Yana yin takun na daban ne lokacin shihowarsu tuni waje yadau shewa domin sun hasko taro, kowa ya Mike tsaye domin karama wannan lovers din, har wajen zaman suka zauna kana kowa ya Zauna… Mc yasaki kiɗa daga nan aka fara gudanarda program..
Sayyid na rike da hannun ta yaƙi yasaketa duk inda tasaka ƙafarta nan yake sakawa….
Itama bata damuba domin kawayen Bintu wannan masu iya yin sai kallon su suke yi,
Kowa sai turo baki take wasu kuwa son barka suke don BOƊƊI da Sayyid maleek suna burgesu….
Anyi biki lfy ankai amarya dakin ta..
Washe gari boɗɗi taje gidan su domin kewar gidan takeyi tunda tasuka dawo bata xova..
Hajiya Ameena tayi farin ciki sosai daganin diyar tata, ajiki ta jawo ta. ko twins ta hana su zuwa kusa da ita….
Saboda karsu dameta…
Mamy ina inna kulu ban ganta ba, tunda naxo.
Kinsan inna da ƙauye wallahi ta kasa zama shine aka kaita domin ta gano su kafin tadawo kwana biyu…
OH nima dai inason zuwa…
Ina ɗin, karki fara Sayyid ne zai barki ba..
Mamy Meyasa kikace haka, shi din mahaukaci ne dazai bari kije ƙauye da karamin ciki bare hanyar Adamawa babu kyau akoi gargada…
Mamy nifa banida komai wani kallo tabita dashi…
Kana tayi murmushi, yaushe rabonki da period,, shiru tayi tana tunani kuma sai yanxu abun yazo mata ashe ta daɗe….Sam ta manta ..
Ameenatu tayi murmushi, tace me kike bukatar ci insa akawo miki…
Cikin jin kunya tace nikam goro nakeso dariya mamy tayi to shohuwa….
Da yamma Sayyid yaxo daukar beauty yashigo suna ta taɗi da mamy, sai gab magrib suka tafi….
Sosai ummu take kula da BOƊƊI don cikin ta ya futo sayyid ma ji da ita yake kamar kwai..
Bintu amarya ana can ana shan amarci….
Itama feeyna nacan tana tura cikin ta…. Abu saidai muce masha Allah 🥰…
Ahaka rayuwar farin ciki suka ci gaba… Sosai Sayyid ya dage wajen kula da BOƊƊI da abunda ke cikinta…. Saidai kuma ana neman sayyid wajen aiki cikin gaggawa, badon yaso ba haka yatafi yabar sahibar tasa..
Kullum twins suna tareda boɗɗi suna debe mata kewa… Domin tunda Sayyid ya tafi gidan su takoma mamy na kula da ita yanda yaka mata…
Har wata rana Allah ya sauke ta lfy sosai kowa yayi farin ciki ansha suna kam don ba gidan TV da jariduba kaff media saida a kasan Sayyid da BOƊƊI sunyi ɗaaa…. 😂
✨✨✨✨✨✨✨✨Lokaci babu wuya wata rana sai naga BOƊƊI da baby boy Ahannu tana rike dashi a falo..
Wayar ta yayi ringin ta dauka hello! Ya Sayyid,.
Daga can Sayyid yace oh har yanxu ban tashi daga ya Sayyid ba kenan….
Cikin dariya tace to a hausa menene Sayyid? Ai ana nufin yallaɓoi kuma ai na girmama kane….
To banso idan girma ne ki kirani da, abu maheer”
Aikuwa kamar maheer yasan an kira shi ya callara ihu cikin sauri ummu ta taho meke faruwa…..
Nan aka shiga ji dashi….
Sayyid bazai iya zama a Saudi ba tareda BOƊƊI ba kuma gashi bayanda zaiyi dole can yake aiki hakan yasa yaxo domin su tafi tare….
Sunje har ƙauyen Genle domin BOƊƊI tana missing garin,..
Furera da akace mata ga BOƊƊI tayi ta kuka tana kara neman yafiya…
Domi lokacin data samu cutar hauka alhaji Abubakar yasa anyi mata magani gashi tadawo rass kuma cii da sha. Bai rage ta da komai ba.. Hatta sutura yana kokari sosai yanxu batada burin aure ma ita a yanxu burinta tarabu da duniya lfy….
Sosai BOƊƊI ta tausaya mata harda kwalla….
Basu kwana ba aranar suka juyo washe gari suka je gudajen yan uwa..na kusa,, abun burgewa har gidan su Ahmad da feeyna suka ziyarta…
Sosai suka ji dadin ganin su ansada zumunci sosai, suka yi musu sallama kan cewa gobe zasu wuce Saudi…
Gidan Bintu ne karshe itama taji dadin ganin su….
Ga maheer gwanin sha’awa Bintu ji take kamar ta kwace shi….
Addu’a take Allah ya bata rabon ta itama….
…….to a takaice BOƊƊI da SAYYI MALEEK gobe zasu Koma Saudi wajen su jaddun hakan ba karamin farin ciki yasa duka su biyun ba.. Domin murna suke na kasan cewa da juna….. 😂 😂 😂 😂 😂 😂 😂
Tuna yanda Allah yake lamarinsa BOƊƊI da aka jefar aka tsince ta, wanda suka tsinceta basu mata mugun taba …
Iyayen ta da zuciyar su daya Allah ya dubesu da idon rahama…
Feeyna da Ahmad da suka yi hakuri akan aure suka gane gaskiya sun matukar kai zuciya nesa..
Da naso najaa book ɗin yanayin abubuwa da kuma rayuwa yasa zan dakata anan abunda nayi kuskure Allah ya femun
Kuma boɗɗi batada girman ka kamar yanda Sayyid bashi da girman kai,, kuma rayuwar su dai-dai kamar na normal mutane.
Nagode sosai da bibiyar lbr BOƊƊI the beautiful 🌀 🌀 🌀 🌀 🌀 🌀 🌀
Allah yabarmun ku masoya sai mun hadu a sabon book ɗina NIDA KAKATA,..
Sannan batun gasar nan tana nan Gamai bukata sai yayi magana ba tareda fittiba Tam bayoyi kawai zaki amsa….. 😂 😂 😂 😂 😂 😂 😂
09066017177
Whatpad Zainab7177
Godiya ga kungiya ta WOMEN WRITERS ASSOCIATION 🤗🤗🤗🤗🤗🤗🤗🤗🤗… ✍️
♻️ Tabbas Alƙalami yafi takwabi⚔️